ZangonLabarai

ZangonLabarai Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from ZangonLabarai, Media/News Company, Nasarawa, Kano.

............................................................................
ZangonLabarai
🌎🌎🌎🌎🌎🌎
🫂 TASHAR TA KUCE!

INEC ta mika takardar shaidar nasara ga ƴan majalisun da aka zaɓe a zaɓen cike gurbiHukumar Zabe mai zaman kanta ta ƙasa...
21/08/2025

INEC ta mika takardar shaidar nasara ga ƴan majalisun da aka zaɓe a zaɓen cike gurbi

Hukumar Zabe mai zaman kanta ta ƙasa a ranar Alhamis ta bada takardar shaida ga zaɓabɓun ƴan takarar da s**a lashe zaɓe a zaɓen cike gurbi da aka gudanar ranar Asabar a faɗin jihohi 12.

Daga cikin waɗanda s**a je hedikwatar domin karbar takardun shaidar lashe zabe akwai zaɓaɓɓen Sanatan Edo ta tsakiya da na Anambra da zaɓaɓɓen ɗan majalisar tarayya na Ovia.

Mutane miliyan 90 a Najeriya za su mutu da wuri saboda amfani da gawayi a wajen girki - Binciken Masana
21/08/2025

Mutane miliyan 90 a Najeriya za su mutu da wuri saboda amfani da gawayi a wajen girki - Binciken Masana

Abba Kabir Yusuf Bazai ƙara Zama Gwamnan jihar Kano a 2027 Ba, Baffa Bichi Yasha Alwashin Sauke Abba Kabir Yusuf daga mu...
20/08/2025

Abba Kabir Yusuf Bazai ƙara Zama Gwamnan jihar Kano a 2027 Ba, Baffa Bichi Yasha Alwashin Sauke Abba Kabir Yusuf daga mulki a zaben 2027.

Tsohon sakataren Gwamnatin jihar Kano Dr Abdullahi Baffa Bichi Yasha Alwashin Sauke Abba Kabir Yusuf a zaben 2027 mai zuwa.

A cikin wani Gajeren jawabin a wani bidiyo dake yawo a kafafen sada zumunta an hango tsohon sakataren yana mai cewa, duk abinda muke zargin gwamnatin Dr Abdullahi Ganduje ta baya kan barna wannan gwamnatin ta maciya amana ta ninka su sau goma kuma muna da hujja shi kuwa Ganduje zargi ne.

Idan muka fara shiga Radio duk zai sun gudu -Inji Baffa Bichi.

Gani Ga Wane Ya Ishi Wane ....  Wani barawon Wayan Wutan Lantarki Ya Gamu Da Ajalinsa a Garin AbaWani barawo da ba a gan...
20/08/2025

Gani Ga Wane Ya Ishi Wane .... Wani barawon Wayan Wutan Lantarki Ya Gamu Da Ajalinsa a Garin Aba

Wani barawo da ba a gano sunansa ba ya rasa ransa bayan da ya hau kan transforma domin ya yi yunkurin satar manyan wayoyin wutan lantarki a unguwar Omuma Road, Aba, jihar Abia.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 2 na Dare inda mazauna yankin s**a wayi gari da ganin gawar barawon na makale a jikin transforma.

YANZU-YANZU: Jami'an kungiyar leƙen asirin Isra'ila watau MOSSAD Sun shigo najeriya. -Sheikh Ahmad Gumi.Babban malamin a...
19/08/2025

YANZU-YANZU: Jami'an kungiyar leƙen asirin Isra'ila watau MOSSAD Sun shigo najeriya. -Sheikh Ahmad Gumi.

Babban malamin addinin Islama a najeriya ya wallafa cewar ya'yan kungiyar sun shigo birnin Abuja.

Ya ƙara da cewar yanzu za'a fara kashe malaman addinin musulunci musamman na arewacin najeriya.

Shin me zaku iya cewa?

DA ƊUMI-ƊUMI: Kwamishinan Sufuri Na Jahar Oyo Prof. Raphael Ofanja Ya Karbi Addinin Musulunci Tsohon Komishinan Sufuri n...
19/08/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Kwamishinan Sufuri Na Jahar Oyo Prof. Raphael Ofanja Ya Karbi Addinin Musulunci

Tsohon Komishinan Sufuri na Jihar Oyo Farfesa Raphael Afonja , ya karbi addinin Musulunci, ya sauya suna daga Raphael zuwa Abdurrahman. Wane fata kuke masa?

Yadda 'Very Dark Man' Ya Jagoranci Hana Motocin Ɗangote Zirga-zirga  A Jihar EdoDaga Abubakar Shehu DokokiCikin wani bay...
19/08/2025

Yadda 'Very Dark Man' Ya Jagoranci Hana Motocin Ɗangote Zirga-zirga A Jihar Edo

Daga Abubakar Shehu Dokoki

Cikin wani bayani da ya fitar, ya bayyana cewa "rayuka da dukiyoyin jama'a suna salwanta ta sanadiyyar mòtocin Dangote, tare da jaddada cewa dole ne kamfanin ýa ɗauki ñauyin gyara hanyoyin, da kuma biyan diyya ģa waɗanda abin ya shafa, ya ƙara da cewa kowa zai iya wucewa, iya motocin Ɗangote ne ba za su wuce ba.

A taya mu yaɗawa (shariñģ) domin sanar da 'ýàñ Aŕewà matafiya masu bìñ ýànkin don su ànkarè. Saboda idan za a iya tùñawà a wani yankì na jihar ne aka kashè mafarautan nañ na Kano a watannin bayà.

DA DUMI-DUMI: Masu Garkuwa Da Mutane Sun Yi Hadari Bayan Sun Karɓi Kuɗin Fansa A Jihar Nassarawa ......sun bar bíndìgógî...
18/08/2025

DA DUMI-DUMI: Masu Garkuwa Da Mutane Sun Yi Hadari Bayan Sun Karɓi Kuɗin Fansa A Jihar Nassarawa
......sun bar bíndìgógî da kuɗi a mota

Daga Farfesa Akyala Ishaku

A safiyar yau, Farfesa Akyala Ishaku ya bayyana cewa yayin da suke hanyarsu ta zuwa aiki, wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun yi hatsari da motarsu kirar Peugeot 406 dauke da bindigogi da kuma kuɗin fansar da s**a karɓa.

Hatsarin ya faru ne a garin Angwan Mayo, kusa da Karamar Hukumar Kokona a jihar Nassarawa. A cewar Farfesa Ishaku, masu laifin sun tsere daga wurin, amma sun bar kuɗaden da s**a karɓa da bindigogi a cikin motarsu.

Ya kuma bayyana godiyarsa ga jami'an tsaro, sojoji da 'yan sanda, da s**a amsa kiran gaggawa cikin hanzari.

Lamarin na ci gaba da jawo ce-ce-ku-ce a yankin, yayin da ake cigaba da bincike.

Daga Muhammad Kwairi Waziri

'Yan kudancin Najeriya sun a soshiyal midiya sun taso Dangote a gaba kan yawan hatsarin da manyan motocinsa ke haddasawa...
18/08/2025

'Yan kudancin Najeriya sun a soshiyal midiya sun taso Dangote a gaba kan yawan hatsarin da manyan motocinsa ke haddasawa wanda suke zargin direbobinsa 'yan Arewa marasa kwarewa da haddasawa.

Wannan zarge zarge da fitaccen Dan soshiyal midiya a kudancin Najeriya da ake yiwa lakabi da Very Darkman ya ke jagoranta, ya taso ne baya da direben wars babban motar Dangote ya made wata dalibar Jami'a a jihad Edo lamarin da ya janyo yanke kafar ta guda, ana cikin hakan ne kuma wani direban Dangote ya kuma yi sanadiyar mutuwar mutum uku a wannan yankin, inda yanzu haka a soshiyar midiya na 'yan kudu Dangoten ke shan s**a.

A baya dai kamfanin Dangote ya shelanta daukar masu digiri aikin tukin manyan motocinsa lamarin da ya dauki hankali a wancan lokacin, sai dai a yanzu ana zargin direbobin Dangote da rashin nutsuwar tuki, tare da haddasa haddura masu kisan al'umma a sassan kasar nan.

INNA LILLAHI WA INNA ILAHIRRAJI UNAANA ZARGIN BABBAN MALAMIN IZALA DA  CIREWA YARA WANDO YANA SUMBATAR GABAN SU DA SUNAN...
18/08/2025

INNA LILLAHI WA INNA ILAHIRRAJI UNA

ANA ZARGIN BABBAN MALAMIN IZALA DA CIREWA YARA WANDO YANA SUMBATAR GABAN SU DA SUNAN SUNNA

MALA. Abdulwahab Togo ya bayyana haka ne cikin wani fyefyen video inda ya tabbatar da yana cire wandon yara kanana yana SUNBATAR GINDIN SU ya kira haka da sunnah ne

Kada kayi saurin zaginmu ka kwantar da hankalin ka zamu kawo maka video da kansa yake fada jujiramu gobe zamu samuku VIDIO insha Allah

Sannan sai ka tabbatar bamuyi masa sharri ba

Daga Ahmad Aliyu sani

RANAR HAUSA : 26 Agusta 2025, A bana za a yi taron ne a Fadar Sarkin Daura da ke jihar Katsina kuma ana sa ran baƙi daga...
17/08/2025

RANAR HAUSA : 26 Agusta 2025, A bana za a yi taron ne a Fadar Sarkin Daura da ke jihar Katsina kuma ana sa ran baƙi daga ƙasashe aƙalla 24 za su halarta.

Wane abu ku ka shiryawa ranar?

Ministan Gidaje na neman a soke zaben cike gurbin Bagwai da ShanonoKaramin Ministan Gidaje Yusuf Abdullahi Ata ya yi kir...
17/08/2025

Ministan Gidaje na neman a soke zaben cike gurbin Bagwai da Shanono

Karamin Ministan Gidaje Yusuf Abdullahi Ata ya yi kira ga Hukumar Zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa INEC da ta soke zaɓen cike gurbi na Bagwai/Shanono, yana mai cewa an yi tashe-tashen hankula da maguɗin zaɓe.

Abdullahi Ata ya yi wannan kiran ne a ranar Lahadi a Kano a lokacin da yake jawabi ga manema labarai kan sakamakon zaɓen da ya gudana.

Ya yi zargin cewa an yi amfani da ƴan daba a ciki da wajen Kano domin su lalata zaɓen Kano tare da hana masu zaɓe gudanar da damar da aka basu.

Address

Nasarawa
Kano
3166

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ZangonLabarai posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to ZangonLabarai:

Share