ZangonLabarai

  • Home
  • ZangonLabarai

ZangonLabarai Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from ZangonLabarai, Media/News Company, .

............................................................................
ZangonLabarai
🌎🌎🌎🌎🌎🌎
🫂 TASHAR TA KUCE!

Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta ce ta lashe kujeru 2 daga cikin kujeru 3 a zaben cike gurbi na majalisar ...
17/08/2025

Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta ce ta lashe kujeru 2 daga cikin kujeru 3 a zaben cike gurbi na majalisar jiha da na tarayya da aka gudanar a jihar Kaduna.

Ƙungiyar haɗin gwiwar ADC mai suna “ADC Vanguard” ce ta bayyana hakan a wata gajeriyar sanarwa da ta wallafa a shafinta na X ranar Asabar.

A Yau Tsohon Shugaban Mulkin Soja, Janar Ibrahim Badamasi Babangida (Rtd). Yake Cika Shekara 84 A Duniya Ga Wasu Daga Ci...
17/08/2025

A Yau Tsohon Shugaban Mulkin Soja, Janar Ibrahim Badamasi Babangida (Rtd). Yake Cika Shekara 84 A Duniya

Ga Wasu Daga Cikin Ayyuka
Dubu Da IBB Yayi Kasar Nan

Shugaba Ibrahim Badamasi Babangida Ne Ya Gina Villa Abuja kuma ya soma tarewa a cikinta, Shi Ne Ya Samar Da Gine-Ginen: Eagle Square, Federal Secretariat, FCDA Secretariat, National Mosque, National Church, National Assembly, Supreme Court, Court of Appeal, Barrack Guda Goma A Abuja, Wuse Market, NNPC Tower.

Shugaba Babangida Ne Ya Samar Da Irin Su:- NAFDAC, DIFRRI, MAMSER (NOA), CCT, CCB, CCN, Gifted Children's School, Suleja, NHIS, NEXIM, NDIC, NDLEA, FRSC, ECOMOG, Ministry of Women Affairs, NWC, National Mathematical Center, NDE, Ministry of Agriculture & Rural Development, NAFSESS, NSFCP, FUMTP, NPB, FEPA, NALDA, CDS, RMRC, CMEWS, NEPC, FMIDS, Petro-Chemical Plant, Kaduna, Petro-Chemical Plant, Eleme, Osaka Dam, Ajaokuta, Shiroro Hydro Power Station, Niger, Dukkanin Sakatariyoyin Gwamnatocin Jihohin Najeriya, Da Kuma Kafatanin Sakatariyoyin Da Yanzu Haka Ake Amfani Da Su A Kowace karamar hukuma, Delta IX Gas Turbine Plant, Bai Taba Siyo Tataccen Man Fetur Daga Wata Kasar Waje Ba, Duk Man Fetur Din Da Aka Sha Zamanin Mulkinsa, A matatun man da Nijeriya Ke Da Su Aka Tace Shi, Duk matatun man Nijeriya Suna Aiki 100% A Sanda Ya Sauka Daga Karagar Mulki.

Shugaba Babangida Ne Ya Kirkiro Jihohi Goma Sha Uku, A Duk Fadin Nijeriya, Inda Kafin Hakan, Da Kuma Bayan Hakan, Babu Wani Shugaban Nijeriya, Wanda Ya Girmama Al'umma, Ta Hanyar Maida Garuruwansu Su Koma Jihohi, Don Kowa Ya Samu 'Yanci, Amfanin Gwamnati Ya Zo Kusa. Ga Jerin Jihohin Da Ya 'Kirkiro Kamar Haka:

Jihar Adamawa.

Jihar Katsina.

Jihar Jigawa.

Jihar Yobe.

Jihar Kebbi.

Jihar Delta.

Jihar Edo.

Jihar Taraba.

Jihar Kogi.

Jihar Abia.

Jihar Osun.

Jihar Enugu.

Jihar Akwa Ibom.

Shugaba Babangida Ne Ya Yawaita kananan hukumomi Har Yawansu Ya Kai 774, Babu Mamaki Kai Da Ke Karanta Rubutun Nan, Idan Ba Domin Hakan Da IBB Ya Yi Ba, Da Wata'kin

DA DUMI-DIMI: Sarkin Zuru, Janar Muhammad Sani Sami, Ya RasuRahotanni daga Jihar Kebbi sun tabbatar da rasuwar Mai Marta...
17/08/2025

DA DUMI-DIMI: Sarkin Zuru, Janar Muhammad Sani Sami, Ya Rasu

Rahotanni daga Jihar Kebbi sun tabbatar da rasuwar Mai Martaba Sarkin Zuru, Janar Muhammad Sani Sami (rtd).

An haifi Marigayi Sarkin a shekarar 1943, inda daga baya ya shiga aikin soja a shekarar 1962. A matsayinsa na soja, ya rike muk**ai da dama ciki har da Gwamnan Jihar Bauchi a zamanin mulkin soja a shekarar 1984.

Janar Muhammad Sani Sami ya yi ritaya daga aikin soja a matsayin Manjo Janar a shekarar 1990.

Allah Ya jikansa da rahama, Ya gafarta masa, Ya ba iyalai da al’ummar Zuru da Jihar Kebbi baki ɗaya haƙuri da juriya.

WATA SABUWA: Sheikh Masuss**a Ya Karyata Zancen Azabar Kabari a MusulunciShahararren malamin addinin Musulunci, Sheikh M...
17/08/2025

WATA SABUWA: Sheikh Masuss**a Ya Karyata Zancen Azabar Kabari a Musulunci

Shahararren malamin addinin Musulunci, Sheikh Masuss**a, ya bayyana cewa babu wani abu da ake kira Azabar Kabari a Musulunci, yana mai cewa zancen damfara ne kawai da ake amfani da shi wajen tsoratar da bayin Allah.

A cewarsa, mutuwa sau ɗaya ake yi, kuma duk wanda ya riga ya bar duniya, to ya gama da ita. Sheikh Masuss**a ya ƙara da cewa babu wani tashin mutum ko tambayoyin kabari bayan mutuwa, illa dai a ranar Alƙiyama ne za a tashe shi domin yin hisabi.

Ya ce: “Wannan magana ta cewa akwai tashin mutum a kabari da tambayoyin Mala’iku duk ƙarya ce. Mutum idan ya mutu ya tafi kenan, daga nan kai tsaye sai tashin Alƙiyama.”

Ba Ni Na Auri Rahama Sadau Ba, Wani Dan Kasar Chana Ta Aura Mai Suna Cheun Hei, Cewar Abdullahi Aliyu (R9)Matashin ya ka...
17/08/2025

Ba Ni Na Auri Rahama Sadau Ba, Wani Dan Kasar Chana Ta Aura Mai Suna Cheun Hei, Cewar Abdullahi Aliyu (R9)

Matashin ya kara da cewa hotunansa da ake ta yadawa da Rahama Sadau tsoffin hotuna ne da s**a dauka shekaru shida da s**a wuce.

Yanzu Yanzu APC ta lashe zabe a KanoJam'iyyar APC ta yi nasara a zaɓen cike gurbi na Ghari/Tsanyawa a Jihar Kano.Da yake...
17/08/2025

Yanzu Yanzu APC ta lashe zabe a Kano

Jam'iyyar APC ta yi nasara a zaɓen cike gurbi na Ghari/Tsanyawa a Jihar Kano.

Da yake sanar da sak**akon zaben da misalin karfe 6:10 na safiyar Lahadi, babban jami’in da ya tattara sak**akon zabe, Farfesa Muhammad Waziri na Jami’ar Bayero, ya bayyana Garba Ya’u Gwarmai na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben da kuri’u 31,472.

Garba Gwarmai ya kayar da dan takarar jam'iyyar NNPP, Yusuf Ali Maigado wanda ya samu kuri'u 27,931.

Babban Titin 'Trans-Sahara' Zai Ƙarfafa Haɗin Gwiwa Da Ƙarin Damar Tattalin Arziki – Minista IdrisMinistan Yaɗa Labarai ...
16/08/2025

Babban Titin 'Trans-Sahara' Zai Ƙarfafa Haɗin Gwiwa Da Ƙarin Damar Tattalin Arziki – Minista Idris

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce an tsara babban titin 'Trans-Sahara' ne domin ƙarfafa haɗin gwiwar yankuna da buɗe damarmakin tattalin arziki.

Idris ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin da ya jagoranci tawagar Gwamnatin Tarayya wajen duba aikin wanda ake ci gaba da yi mai tsawon kilomita 118 da ya tashi daga Kalaba zuwa Ibonyi.

Ya bayyana babban titin a matsayin ɗaya daga cikin manyan ayyukan gwamnati da ake aiwatarwa a ƙarƙashin shirin Sabunta Fata na Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu.

Ministan ya bayyana cewa gina gada mai tsawon mita 700 da faɗin 12 a kan titin zai magance matsalar ambaliyar da ta daɗe tana addabar yankin Bakin Ruwa na N’dibe tare da dawo da damar zirga-zirga ga al’ummomin da abin ya shafa.

A cewar sa, yanzu ne karon farko da Jihar Ibonyi take samun manyan ayyuka masu yawa na Gwamnatin Tarayya a lokaci guda, wanda hakan alama ce ta jajircewar gwamnati wajen tabbatar da cigaba daidaitacce.

Haka kuma ya shawarci masu kwangilar aikin da su kiyaye inganci tare da hanzarta kammala aikin, yana tabbatar wa da jama'ar Nijeriya cewa gwamnati ta mayar da hankali kan ayyukan raya ƙasa da za su inganta rayuwa da hanyoyin samun abin dogaro a duk faɗin ƙasar nan.

Ana gina babban titin 'Trans-Sahara' ɗin ne ta hannun kamfanin Infouest Nigeria Limited a kan kuɗin da ya kai naira biliyan 445, kuma yana da shimfiɗar kankare mai ƙarfi, sannan ya haɗa Kalaba, Ibonyi, Binuwai, Nasarawa da Abuja.

Matatar Dangote za ta fara jigilar mai kyauta ga gidajen mai
16/08/2025

Matatar Dangote za ta fara jigilar mai kyauta ga gidajen mai

DA DUMI-DUMI: Jami'an tsaron farin kaya a jihar Kaduna sun k**a Shehu Aliyu Patangi da tsabar kuɗi kimanin miliyan 30 da...
16/08/2025

DA DUMI-DUMI: Jami'an tsaron farin kaya a jihar Kaduna sun k**a Shehu Aliyu Patangi da tsabar kuɗi kimanin miliyan 30 da niyyar zuwa sayen ƙuri'a yayin zaɓen cike gibi da za'a gudanar yau na ɗan majalisar wakilai mai wakiltar chikun/Kajuru a jihar.

Misalin ƙarfe 3 na daren jiya jami'an s**a damƙe shi a wani sanannen Otel dake cikin garin Kaduna.

Daga Abdulkadir Nafi'u

16/08/2025
DA ƊUMI-ƊUMI: Dan Bello Ya Samu Sarautar Sarkin Yakin Talakawan NijeriyaMajalisar Malamai Mahaddata Kur'ani ne s**a ba s...
15/08/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Dan Bello Ya Samu Sarautar Sarkin Yakin Talakawan Nijeriya

Majalisar Malamai Mahaddata Kur'ani ne s**a ba shi wannan sarauta.

Wane fata zaku yi masa?

Address


Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ZangonLabarai posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to ZangonLabarai:

  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share