ZangonLabarai

ZangonLabarai Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from ZangonLabarai, Media/News Company, Nasarawa, Kano.

............................................................................
ZangonLabarai
🌎🌎🌎🌎🌎🌎
🫂 TASHAR TA KUCE!

Tohfa: Wani mai Da'awar Annabta a Ƙasar ghana ya kammala Gina Jirgin ruwansa, wanda yace Ubangiji ne ya umarceshi da ya ...
03/12/2025

Tohfa: Wani mai Da'awar Annabta a Ƙasar ghana ya kammala Gina Jirgin ruwansa, wanda yace Ubangiji ne ya umarceshi da ya gina. Ya shafe sama da watanni 11 yana gina Jirgin. Ya gina Jirgin da hawa biyu, wanda duk hawa 1 yana iya ɗaukar mutane 5,000.

Mutumin mai suna Ebo Nuhu ya bayyana cewa Karshen duniya ya zo, saura ƙiris ayi tashin Duniya, saboda haka Ubangiji ya umarceshi da ya gina wannan Jirgi domin tseratar da mutane daga cikin sa. Mutane suna mai dariya, k**ar dai yanda ya faru a zamanin Annabi Nuhu (A.S)

Videon Yana Comment Section.

Tun a shekarar 1999 tayi ridda, inda ta bayyana cewa mafarki tayi da Yesu shi ya sa ta fita daga Musulumci ta koma Kiris...
24/11/2025

Tun a shekarar 1999 tayi ridda, inda ta bayyana cewa mafarki tayi da Yesu shi ya sa ta fita daga Musulumci ta koma Kirista, labarin ridda ta ya sake bayyana ne daga jiya zuwa yau, bayan da wasu mabiya Kirista s**a zakulo labarin s**a kuma sabunta shi, nan da nan kafafen soshiyal midiya s**a dauka suna ta yadawa.

KARIN BAYANI AKAN MATAR DA AKE ZARGIN TA KASHE MIJINTA Dan uwan Mamacin ya min karin bayani cewa basa zargin matar da la...
24/11/2025

KARIN BAYANI AKAN MATAR DA AKE ZARGIN TA KASHE MIJINTA

Dan uwan Mamacin ya min karin bayani cewa basa zargin matar da laifin kashe mijinta

Da farko sun yi soyayya sosai, sai aka hanashi aurenta aka bawa wani ta aura, zuwa wani lokaci sai auren ya mutu ta dawo ta auri wannan da s**a fara soyayya tun tana budurwa

Har ana zargin cewa ta dalilin wannan din ne yasa ta kashe aurenta ta dawo s**ayi aure saboda tana son shi sosai

Bayan kwana hudu da aurensu, jiya Lahadi da misalin karfe 12 zuwa 1 na rana, ya fita shagonsa zai bawa wani buhun shinkafa sai ya manta key na shagonsa a gida, ya dawo gida daukar key sai ake zargin ya tarar da wani a gidansa

Anan ne s**ayi bata kashi da wanda ya tarar ko da ita matar, saboda kafin a yanka shi sai da aka caka masa wuka a cinya har sau biyu, da karfinsa ya kare ne aka masa ¥ankan rag0, matar itace ta fito waje tana ihu ta sanar da mutane daga bisani ta fita cikin hayyacinta

Don haka batun kiyayya babu shi a tsakaninsu, auren soyayya s**ayi, kuma ba yana bacci bane aka kashe shi

Bincike ne zai tabbatar da wanda yake da hannu a kashe shi, matar zata zama abin zargi, sannan tsohon mijinta da s**a rabu shima zai zama abin zargi

'Yan sanda masu bincike zasu gano komai cikin sauki, wukar da aka kashe shi da ita, idan aka kaita Forensic lab za'a fitar da fingerprint na wadanda s**a taba wukar a lokacin da aka kashe shi

Sai dai bana tunanin a jihar Katsina akwai standard Forensic lab da zai bada result din da ake bukata, karshenta sai an kai Police Force CID Abuja ko Lagos

Allah Ya jikansa da rahama, Ya tona asirin duk wanda yake da hannu a kisansa

Daga Datti Assalafiy

Yadda Aka K**a Fasto Dake Kai wa 'Yan Bindiga Mak**ai FilatoNajeriya ta shiga wani sabon babi mai ban al’ajabi — Inda ak...
17/11/2025

Yadda Aka K**a Fasto Dake Kai wa 'Yan Bindiga Mak**ai Filato

Najeriya ta shiga wani sabon babi mai ban al’ajabi — Inda aka k**a wani malamin addinin kirista (Reverend Father) da ake zargi da kai wa ‘yan bindiga muggan mak**ai a Jihar Filato da kewaye.

Eh, ka karanta daidai.
Wani limamin coci — wanda aka yarda da shi a matsayin mai addu’a, zaman lafiya da kare rayuka — yanzu ana zarginsa da taimakawa waɗanda ke hallaka al’umma marasa laifi.

Rahotanni sun ce jami’an tsaro sun gano yana *tsara safarar mak**ai iri-iri*, wanda ake zargi da taimakawa 'yan ta'adda wajen sace mutane, kai hari da kashe-kashe.

Yanzu sai na sake tambaya...

Lokacin da wasu daga cikinmu s**a ce *matsalar tsaro a Najeriya ba ta addini bace*, mutane s**a ci mutunci, suna cewa muna goyon bayan mugunta.

Amma yanzu, me za su ce?

Shin waɗanda s**a yi gaggawar garzayawa Amurka suna kiran abun “kisan kiyashi ga Kiristoci” za su kai wannan labari wajen Donald Trump domin daidaita labarin?

Domin gaskiya ita ce:

Tsaro a Najeriya ba ya da addini.
(1) Ba ya sanye da zobon saliba ko tesbihu.
(2) Ba ya rike Alƙur’ani ko Littafi Mai Tsarki.
(3) Yana buya a daji, yana sayen mak**ai, yana halaka rayuka — Musulmi, Kirista, kowa.

Amma duk lokacin da aka fadi gaskiya, mutane kan mayar da martani da ji ba da hankali ba.

Wannan k**a ta bayyana gaskiya mai zurfi:

(1) Matsala laifi ce, ba addini ba.
(2) Mugaye suna ko’ina — a coci, a masallaci.
(3) Kuma yaƙi yana da su ne, ba da addininsu gabaɗaya ba.

Idan har Reverend Father za a k**a da kai wa 'yan bindiga mak**ai, to watakila... matsalar Najeriya ta fi “kisan kiyashi a ɓangare guda” girma da rikitarwa.

Mu kira gara gari.
Mu gyara matsalar tsaro — ba mu juya ta ta zama siyasa ko neman tausayi daga ƙasashen waje ba.

Sulhu:Yadda shugaban karamar hukuma a Katsina ya ziyarci 'yan bindiga a wata makarantar FiramareShugaban Karamar Hukumar...
07/11/2025

Sulhu:Yadda shugaban karamar hukuma a Katsina ya ziyarci 'yan bindiga a wata makarantar Firamare

Shugaban Karamar Hukumar Funtua a Jihar Katsina Abdu Goya, Ya ziyarci Wasu Fulani Masu Rike da Bindiga Waɗanda Aka Ce Sun Karbi Zaman Sasanci Da Al'ummomin Yankin A Jihar Katsina,

Domin Ganin An Ƙara Samun Daidaito A Tsakanin Al'ummar Hausawa Da Fulani Masu Rike Da Bindiga, Tare da Kokarin Kubutar Da Waɗanda Akayi Garkuwa Da su A Sassan Karamar Hukumar Funtua.

An Yi Wannan Zamane A Wata Makarantar Firamare Mai Bukatar Gyara K**ar Yadda Kuke Gani A Hoto

Hotuna📸Comrd. Bilyaminu Lawal Funtua

Shin Sulhu Da 'Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajje Mak**ansu Ba, Abu Ne Da Zai Haifar Da Dah Mai Ido?

Gaskiyar Musulunci ta BayyanaA kwanakin baya wani kirista mai suna Usman Evengelis ya yi ikirarin cewa kafin ya bar duni...
17/10/2025

Gaskiyar Musulunci ta Bayyana

A kwanakin baya wani kirista mai suna Usman Evengelis ya yi ikirarin cewa kafin ya bar duniya sai an daina jin kiran sallah a Arewa. Ma’ana, sai ya mayar da kowa Kirista. 😂 Abin mamaki, abin dariya!

Mun yi duba da nazari, sai muka gano cewa ko mutum daya babu daga cikin Musulmi da ya bar addininsa ya koma Kiristanci. Wannan ya nuna karara cewa ikirarin Evengelis ba gaskiya ba ne, karya ce tsagwaronta! Shi da abokin tafiyarsa Mamman Kato duk sun kasa, sun sha kaye.

Abin burgewa kuma shine: gashi da ransa Malam Adam Ashaka da Baban Chinedu sun tasa keyar addinin Kiristoci suna cinye shi tamkar wutar daji. ✨ A hankali amma tabbas Kiristanci yana ja baya, Musulunci kuma yana cigaba da bazuwa da karfi. Da izzar ubangiji

Lallai, da rayuwar Evengelis zai shaida cewa an daina zuwa coci, an daina kiran Isah dan Allah
sak**akon burinsa na ganin a daina kiran sallah. A fadin Nigeria Baki daya sai dai a shafe addinin cristancin

Amma fa, Musulunci ya yi gaba, ya yi nasara akan makiyan addininmu tamkar wutar daji.

Allahu Akbar! 🕋🔥

Copy

Labarin Matar da ta Iso Amurka da Fasfon Ƙasar “Torenza”A kwanan nan, wani bidiyo ya yadu a dandalin sada zumunta k**ar ...
14/10/2025

Labarin Matar da ta Iso Amurka da Fasfon Ƙasar “Torenza”

A kwanan nan, wani bidiyo ya yadu a dandalin sada zumunta k**ar TikTok, Instagram da YouTube, wanda ya nuna wata mace da aka ce ta sauka a filin jirgin sama na John F. Kennedy (JFK) da ke New York, Amurka.

An ce ta fito ne daga Tokyo, Japan, sannan ta gabatar da fasfo daga ƙasa mai suna “Torenza” ƙasa da babu a taswirar duniya.

Lokacin da jami’an shige da fice (immigration officers) s**a duba fasfon nata, sun lura cewa:

Fasfon yana da cikakkun tsarukan tsaro , k**ar hologram, chip, stamp nazitar wasu kasashe.

Sai jami’an s**a tambaye ta, “wace kasa ce wannan ƙasar ta Torenza take?”

Ta amsa da cewa “ƙasar mu ba ta cikin wannan duniya” – wato tana nufin wani wuri daban.

Bayan haka, an ce jami’an s**a yi mamaki, s**a nemi karin bayani, amma daga karshe ance ta bace.

Bayan da labarin ya karade kafafen sada zumunta, masu bincike (fact-checkers) sun gudanar da cikakken bincike kan wannan labari.

Sun binciko cewa

Babu wata ƙungiyar tsaro ko hukumar shige da fice ta Amurka da ta tabbatar da cewa lamarin ya faru.

Babu wani rahoto daga hukumar jirgin sama (JFK Airport Authority) da ya tabbatar da hakan.

An gano cewa bidiyon na karya ne, an kirkire shi ta hanyar fasahar “AI-generated video” wato fasahar kwaikwayo ta kwamfuta (Artificial Intelligence).

Haka kuma, babu wata ƙasa mai suna “Torenza” a cikin bayanan Majalisar Ɗinkin Duniya, Google Maps, ko duk wata taswirar ƙasashe na duniya.

Asalin tatsuniyar da aka kwaikwaya

Wannan labarin “Torenza” ya samo asali ne daga wata tsohuwar tatsuniya da ake kira “The Man from Taured” (mutum daga ƙasar Taured).

A cewar labarin da aka ruwaito tun shekarar 1954, wani mutum ya isa Tokyo Airport da fasfo daga ƙasa mai suna Taured.
Ya ce ƙasarsa tana tsakanin Faransa da Spain, amma lokacin da jami’an s**a bincika taswira, ba su sami wannan ƙasar ba.
An tsare shi a ɗaki don bincike, amma washegari ya ɓace ba tare da wata alama ba.
Wannan labari ya zama sanannen labari

Gwamnatin tarayya ta sanar da soke faretin zagayowar ranar samun ‘yancin kai da aka shirya gudanarwa a ranar Laraba, 1 g...
29/09/2025

Gwamnatin tarayya ta sanar da soke faretin zagayowar ranar samun ‘yancin kai da aka shirya gudanarwa a ranar Laraba, 1 ga Oktoba, 2025, domin cika shekaru 65 da samun ‘yancin kai a Najeriya.

ya sunan wannan abun.bari muga yan bana bakwai🤣
25/09/2025

ya sunan wannan abun.bari muga yan bana bakwai🤣

INEC ta mika takardar shaidar nasara ga ƴan majalisun da aka zaɓe a zaɓen cike gurbiHukumar Zabe mai zaman kanta ta ƙasa...
21/08/2025

INEC ta mika takardar shaidar nasara ga ƴan majalisun da aka zaɓe a zaɓen cike gurbi

Hukumar Zabe mai zaman kanta ta ƙasa a ranar Alhamis ta bada takardar shaida ga zaɓabɓun ƴan takarar da s**a lashe zaɓe a zaɓen cike gurbi da aka gudanar ranar Asabar a faɗin jihohi 12.

Daga cikin waɗanda s**a je hedikwatar domin karbar takardun shaidar lashe zabe akwai zaɓaɓɓen Sanatan Edo ta tsakiya da na Anambra da zaɓaɓɓen ɗan majalisar tarayya na Ovia.

Mutane miliyan 90 a Najeriya za su mutu da wuri saboda amfani da gawayi a wajen girki - Binciken Masana
21/08/2025

Mutane miliyan 90 a Najeriya za su mutu da wuri saboda amfani da gawayi a wajen girki - Binciken Masana

Abba Kabir Yusuf Bazai ƙara Zama Gwamnan jihar Kano a 2027 Ba, Baffa Bichi Yasha Alwashin Sauke Abba Kabir Yusuf daga mu...
20/08/2025

Abba Kabir Yusuf Bazai ƙara Zama Gwamnan jihar Kano a 2027 Ba, Baffa Bichi Yasha Alwashin Sauke Abba Kabir Yusuf daga mulki a zaben 2027.

Tsohon sakataren Gwamnatin jihar Kano Dr Abdullahi Baffa Bichi Yasha Alwashin Sauke Abba Kabir Yusuf a zaben 2027 mai zuwa.

A cikin wani Gajeren jawabin a wani bidiyo dake yawo a kafafen sada zumunta an hango tsohon sakataren yana mai cewa, duk abinda muke zargin gwamnatin Dr Abdullahi Ganduje ta baya kan barna wannan gwamnatin ta maciya amana ta ninka su sau goma kuma muna da hujja shi kuwa Ganduje zargi ne.

Idan muka fara shiga Radio duk zai sun gudu -Inji Baffa Bichi.

Address

Nasarawa
Kano
3166

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ZangonLabarai posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to ZangonLabarai:

Share