BAHASNet

BAHASNet ●Muna Kawo Muku Sahihan Labarai Masu tushe.👌
●Nishadantarwa tare da Wasanni👌
●Ilimantarwa 👌

20/04/2025

Abuja boys

19/04/2025

Idan zaa taimakawa mutane sai anyi musu hoto ana numawa duniya an taimake su

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Karyata Jita-jitar Hana Mataimakin Shugaban Ƙasa Shiga VillaFadar Shugaban Ƙasa ta ƙaryata rahota...
19/04/2025

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Karyata Jita-jitar Hana Mataimakin Shugaban Ƙasa Shiga Villa

Fadar Shugaban Ƙasa ta ƙaryata rahotannin da ke yawo a wasu kafafen yaɗa labarai na bogi da ke cewa an hana Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, GCON, shiga Fadar Shugaban Ƙasa, tana mai bayyana hakan a matsayin ƙarya marar tushe da nufin tada zaune tsaye da ɓata sunan gwamnati.

A wata sanarwa da mai taimaka wa Shugaban Ƙasa kan harkokin watsa labarai da sadarwa a ofishin Mataimakin Shugaban Ƙasa, Stanley Nkwocha, ya fitar, ya bayyana cewa rahoton da ke cewa an toshe hanyoyin shiga Villa ga Mataimakin Shugaban Ƙasa da dakarun soji ba gaskiya ba ne, kuma ya fito ne daga masu yaɗa sharri da ke ƙoƙarin haifar da rikici a tsakanin manyan shugabannin ƙasar.

“Wannan jita-jita wani ƙoƙari ne na ɓata suna da neman kirkirar rikici a cikin gwamnatin da ke aiki kafada da kafada don cika burin ’yan Najeriya,” in ji sanarwar.

Sanarwar ta bayyana cewa babu wani lokaci da aka taɓa hana Mataimakin Shugaban Ƙasa shiga Villa, kuma rahotannin da wasu shafukan yanar gizo na ƙarya s**a wallafa shaci faɗi ne.

“Wannan labari ya yi nisa da gaskiya fiye da yadda za a iya kwatanta shi da komai sai labarin almara,” in ji Nkwocha.

Fadar Shugaban Ƙasa ta yi nuni da cewa irin waɗannan rahotanni suna ƙoƙarin rusa hadin kai da amintakar da ke tsakanin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, GCFR, da Mataimakinsa, Kashim Shettima, GCON.

“Wadanda ke yaɗa irin wannan ƙaryar suna manta cewa shugabannin biyu sun gina dangantaka mai ƙarfi tsakanin su da mutunta juna da aiki tare wajen gina Najeriya. Irin waɗannan ƙagaggun labaran ba su da wani tasiri, illa kawai suyi ƙoƙarin kautar da hankali,” in ji sanarwar.

Sanarwar ta kara da cewa Mataimakin Shugaban Ƙasa na ci gaba da mayar da hankali kan ayyukansa da kuma tallafa wa Shugaban Ƙasa wajen cika alƙawarin da aka yi wa ’yan ƙasa. Babu lokacin da zai bata wajen amsa irin wannan jita-jita da ƙarya.

Fadar Shugaban Ƙasa ta yaba wa ‘yan Najeriya da s**a nuna goyon baya ga gwamnatin tare da kiran jama’a da su yi watsi da irin waɗannan rahotanni na ƙarya.

A ƙarshe, an bukaci kafafen yaɗa labarai su rika bincikar gaskiyar lamari daga sahihan majiyoyi kafin wallafa wani abu, tare da jaddada muhimmancin watsa gaskiya da gujewa ɗora ƙarya akan shugabanni.

06/10/2024

🚨Jam'iyyar APP ta lashe zaɓen kananan hukumomi a jihar Rivers

24/09/2024
Ayau Litinin ne Abdullahi Umar Ganduje zaisan matsayinsa na cigaba da Shugabancin Jam'iyyar APC ko kuma akasin  haka.Wan...
23/09/2024

Ayau Litinin ne Abdullahi Umar Ganduje zaisan matsayinsa na cigaba da Shugabancin Jam'iyyar APC ko kuma akasin haka.

Wanne fata kuke masa?

DA DUMI-DUMI: Sojojin Nijeriya sunyi nasarar ka$h€ Shahararren b!nd!gar nan HAL!LU $UBUBU bayan ɗauki ba ɗaɗi tsakanin s...
13/09/2024

DA DUMI-DUMI: Sojojin Nijeriya sunyi nasarar ka$h€ Shahararren b!nd!gar nan HAL!LU $UBUBU bayan ɗauki ba ɗaɗi tsakanin su da 'yan b!nd!gar a tsakanin kwanar Dogon Ƙarfe zuwa Mayanki na ƙananan hukumomin Zurmi da Anka.

A jiya ne Kachalla Buzu ($UBUB) ya saki wani bidiyo yana kira ga Tvrj!, D0g0 G!de, Dankarami da sauransu dasu daina ka$he fararen hula su maida akalar zuwa jami'an tsar0.

Cikin ikon ubangiji, a kasa da awanni 24 da yin wannan bidiyon nasa S0j0jin s**ai nasarar sh€k€ shi.

Jam'iyyar PDP ta dakatar da Sanata Dino Melaye daga jam'iyyar saboda da zargin cin mutunci da yi wa jam'iyyar illa a kal...
13/09/2024

Jam'iyyar PDP ta dakatar da Sanata Dino Melaye daga jam'iyyar saboda da zargin cin mutunci da yi wa jam'iyyar illa a kalamansa.

An fara Shirye shiryen gyaran gidan Sarki Nassarawa, inda mai martaba Aminu Ado Bayero ke cikin a halin yanzu.
05/09/2024

An fara Shirye shiryen gyaran gidan Sarki Nassarawa, inda mai martaba Aminu Ado Bayero ke cikin a halin yanzu.

Mace ta farko da ta fara shan Sigari a kasar Hausa, Sunanta Ladi bushe bushe.Ko zaku iya fada mana 'yar wace jiha ce a A...
08/07/2024

Mace ta farko da ta fara shan Sigari a kasar Hausa, Sunanta Ladi bushe bushe.

Ko zaku iya fada mana 'yar wace jiha ce a Arewacin Najeriya?

TURƘASHI: Mariam kenan matar da ke riƙe da budurcinta yau shekara 107 tana jiran dawowar saurayinta John wanda suke soya...
07/07/2024

TURƘASHI: Mariam kenan matar da ke riƙe da budurcinta yau shekara 107 tana jiran dawowar saurayinta John wanda suke soyayya tun ƙuruciya.

Majiyarmu ta Jaridar Northern Broadcasters ta ruwaito John yaje Tanzania ne ci-rani a lokacinda s**a haɗu da Mariam amma tunda ya tafi ganin gida (ya koma ƙasarsa Ingila) ba ko sallama har yau bata sake jin ɗuriyarsa ba, amma duk da haka tace za ta cigaba da jiransa kuma za ta tsare budurcinta har lokacinda Allah zai masa dawowa ya zo suyi aure.

Me zaku ce?

"'Yan Najeriya fiye da miliyan 80 za su fuskanci yunwa nan da 2030"🎙~Majalisar Dinkin DUNIYA
07/07/2024

"'Yan Najeriya fiye da miliyan 80 za su fuskanci yunwa nan da 2030"
🎙~Majalisar Dinkin DUNIYA

Bayan dogon tonon silili a tsakaninta da G-Fresh, Sadiya Haruna ta sake amarecewa.
07/07/2024

Bayan dogon tonon silili a tsakaninta da G-Fresh, Sadiya Haruna ta sake amarecewa.

Fadar Shugaban ƙasa Ta Karrama Kwamishiniyar Mata ta jihar Borno da Lambar Yabo na Musamman kan ƙoƙarin ta wajen Jinkai ...
07/07/2024

Fadar Shugaban ƙasa Ta Karrama Kwamishiniyar Mata ta jihar Borno da Lambar Yabo na Musamman kan ƙoƙarin ta wajen Jinkai da inganta Rayuwar Mata da yara Marasa Galihu

Hon. Zuwaira Gambo kwamishiniyar ma'aikatar Harkokin mata da cigaban al'umma a jihar Borno, ta samu lambar yabo mai Daraja a fannin ci gaban mata da yara kan aikin Gwamnati (NEAPS). Kyautar wacce TBS Media tare da hadin gwiwar ofishin sakataren Gwamnatin tarayya s**a ba Hon. Zuwaira Gambo bisa ga irin gudunmawar da ta bayar wajen kyautata rayuwar mata da yara a jihar Borno.

Bikin wanda ya samu halartar mataimakin shugaban tarayyar Najeriya Sen. Kashim Shettima a madadin mai girma shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu GCFR ya bayyana Hon Zuwaira Gambo . A matsayin wacce tayi fice wajen inganta rayuwar mata da yara. a fadin jihar Borno.

A jawabinta na Godiya, Hon. Zuwaira Gambo ta nuna jin dadin ta da karramawar tare da jaddada kudirinta na ganin ta samar da ayyukan da za su karfafa da kuma daukaka masu rauni a cikin al'umma. Ta mika godiya ta musamman ga Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, bisa yadda ya samar mata da tsarin yi wa al’ummar Borno hidima. Ta yaba da irin jagoranci na musamman da kuma goyon bayansa ba tare da kakkautawa ba, inda ta nuna cewa goyon bayansa ya taka rawar gani a kokarinta na yin tasiri sosai ga rayuwar mata da yara a jihar.

Ga kaɗan daga Cikin Nasarorin da Hon Zuwaira Gambo Ta samar Ga Ɓangaren Jinkai da Taimakon Mata da yara Marasa Galihu

Ambasada Hon. Zuwaira Gambo fitacciyar jaruma ce ta shahara wajen bayar da gudunmawar bangarori daban-daban Musamman ayyukan jin kai, Ta ɗauki tsawon lokaci Fiye da Shekaru ashirin, Tana ƙoƙari Ga al'ummomi masu rauni, Musamman a jihar Borno.

Hon. Zuwaira Gambo tayi Digirin ta na da Farko ne a Mass Communication a Jami’ar Bayero, dake Kano. Ta ƙara- Digiri na biyu A babbar jami'ar Calabar, inda ta nuna kwarewarta a fannin ilimi da Gogewarta a fannin Gudanar da Harkokin Gwamnati.

A matsayinta na tsohuwar Babbar Darakta na Initiative for Vulnerable and Marginalized (HIVAM), ta yi yunƙurin haɓakawa da Karfafa wa ƙungiyoyin marasa Galihu, ta mai da hankali musamman kan al'ummomin da aka ware. Tayi ƙoƙari Wajen aiwatar da shirye-shirye sama da 20 waɗanda s**a inganta Rayuwar mata da yara marasa Galihu a shiyyar Arewa maso Gabas, Arewa ta Tsakiya, da Arewa maso Yammacin Najeriya.

Ta kasance mai Baiwa Gwamnan Jihar Borno shawara na musamman kan harkokin mata da ayyuka na musamman har sau biyu daga 2014 zuwa 2019, inda ta taka muhimmiyar rawa wajen tsara manufofi dake inganta daidaito tsakanin jinsi da zamantakewa.BTa Bayar da shawarwarin da ya kai ga ƙoƙarin Gwamna Kashim Shettima na Ganin an shigar da mata cikin harkokin mulki a jihar Borno.

A yayinda take riƙe da muƙamin kwamishiniyar harkokin mata Ta samar da dabaru da nufin inganta rayuwar mata da kananan yara waɗanda rikicin da aka dade a jihar Borno ya fi shafa. Ta Samar da tsare-tsare daban-daban na cikin gida da waje, da nufin jawo hankalin ƙasashen waje don tallafawa mata da yara a jihar Borno.

Ambasada Hon. Zuwaira Gambo ta ba da gudunmawa sosai a matsayin mai kula da Wani shiri Na Tallafawa al'umma a yankin arewa maso Gabas, inda ta daidaita ayyukan yankin da manufofin ci gaban kasa a karkashin inuwar uwargidan Shugaban Najeriya. Ta Jagoranci shirye-shiryen karfafawa mata da matasa a yankin Arewa maso Gabashin Najeriyar da uwargidan tsohon shugaban kasar tayi, Musamman a cikin al'ummomin da ke da wuyar isa wurin da rikicin ya shafa.

Ta rike mukamin shugabar mata ta kasa mai daraja a cibiyar shugabannin zaman lafiya ta kasa da kasa, mai alaka da Majalisar Dinkin Duniya a Geneva, Wanda ke nuna tasirinta a duniya kan ayyukan samar da zaman lafiya.

Ta Jagoranci Sanya kwarin Gwiwa Ga matan Najeriya wajen samar da zaman lafiya.
Ta Jagoranci yunƙurin bayar da shawarwari don kariya da shigar da mata cikin harkokin mulki da ayyukan da s**a danganci su.
a Majalisar Dinkin Duniya.

A yanzu haka tana aiki karo na uku a matsayin kwamishiniyar Harkokin mata da ci gaban al’umma a jihar Borno ƙarƙashin jagorancin mai girma Farfesa Babagana Umara Zulum, Ambasada Hon. Zuwaira Gambo ta ci gaba da zama zakaran gwajin dafi da ke inganta walwala da zamantakewar mata da kungiyoyi masu kansu.

Ga Wasu Daga Cikin shirye-shiryen da ta jagoranta Ta Jagoranci Gudanar da duk wani shiri na Gwamnatin jihar Borno ga mata da yara. Samar da jagoranci ga duk wani shiri na hadin gwiwa na ci gaba da ya shafi mata da yara a jihar Borno Ta Samar da dabarun aiki ga abokan hulɗa da ke amsawa a jihar Borno don inganta sakamakon ayyukan da suke yi ga mata da yara.

Ambasada Hon. Zuwaira Gambo Ta kasance ƙwararriyar mai wayar da kan jama'a kuma ƙwararriyar shirye-shiryen jin kai. Jagorancinta yana da muhimmanci a cikin zamantakewa da tattalin arziki na sake hadewar mayaƙan da s**a tuba Na (Boko Haram) ta hanyar tsarin Borno Model Framework, tare da haɗin gwiwar Majalisar Dinkin Duniya. Wannan yunƙurin ya ƙara jaddada aniyarta na tabbatar da ɗorewar zaman lafiya da ƙoƙarce-ƙoƙarce a yankunan da ke fama da tashe-tashen hankula A Arewa maso Gabashin Najeriya (Borno, Adamawa, da Yobe

A matsayinta na fitacciyar mai gabatar da korafin al'umma a tarukan kasa da kasa da nufin samar da mafita mai ɗorewa don kawo karshe tashe-tashen hankula da s**a dade a Arewa maso Gabashin Najeriya. Shawararta na ci gaba da tsayawa tsayin daka wajen Ganin an samar da ingantacciyar Rayuwa Ga mata da ƙananan yara Marasa Galihu a faɗin Najeriya Musamman a Jihar Borno.

Ga Wasu Daga Ayyukan kwanan nan da ta jagoranta Ta Jagoranci Babban taro kan wani ɓangare na dabarun yaki da tada kayar baya, Tare da ba da muhimmanci na musamman kan tsarin Nijeriya ta fuskar shiyya-shiyya da ma duniya baki daya, Wanda Ma'aikatar Harkokin Waje ta Tarayya ta Switzerland ta shirya. Ta Jagoranci Babban taro kan yankin tafkin Chadi karo na 3 a Yamai. Tattaunawar zaman lafiya a yammacin Afirka kan ci gaban hanyoyin magance tashe-tashen hankula da cibiyar magance rikice-rikice ta kasar Norway ta shirya a birnin Dakar na kasar Senegal.
- Karo na Uku na Dandalin ASWAN na Zaman Lafiya da Ci Gaba a Alkahira, Masar.
- Tattaunawar Wilton Park akan Tekun Chadi Basin: Binciko Matakai Don Magance Matsalolin Yanki da aka shirya a Wiston House, Ingila.

Aikin Zuwaira Gambo Bazai Misaltu ba sadaukarwa, tausayi, da jagoranci mai inganci wajen ciyar da al'amuran jin kai da inganta zamantakewa da tattalin arziki. Gudunmawarta na ci gaba da haifar da canji mai kyau da juriya a cikin al'ummomin da rikici da wariya s**a shafa. Bayanan martabar ta shaida ce ga fitattun nasarorin da ta samu da kuma jajircewarta ga hidima, tare da samar da mafi girman manufofin jagoranci da jin kai.

BAHASNet

Address

Kano

Telephone

+2348117733195

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when BAHASNet posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to BAHASNet:

Share