BAHASNet

BAHASNet ●Muna Kawo Muku Sahihan Labarai Masu tushe.👌
●Nishadantarwa tare da Wasanni👌
●Ilimantarwa 👌

"Za mu ɗauki nauyin kula da iyalan marigayiya Ummulkhairi da aka yi wa k15an gi||a a mararrabar Jos" 🎙 - Gwamnan Kaduna ...
30/06/2026

"Za mu ɗauki nauyin kula da iyalan marigayiya Ummulkhairi da aka yi wa k15an gi||a a mararrabar Jos"

🎙 - Gwamnan Kaduna

🚨 An Cafke Ɗan Sanda Kan Zargin Yi Wa 'Yar Shekara 13 Fyade a Jihar NigerAn cafke wani ɗan sanda tare da wasu mutum biyu...
30/06/2026

🚨 An Cafke Ɗan Sanda Kan Zargin Yi Wa 'Yar Shekara 13 Fyade a Jihar Niger

An cafke wani ɗan sanda tare da wasu mutum biyu bisa zargin yi wa wata yarinya mai shekara 13 fyade a Jihar Niger.

Kwamishinar Harkokin Mata ta jihar, Hajiya Hadiza Kuta, ta ce waɗanda ake zargin sun rika yaudarar yarinyar tare da lalata da ita bayan sun sayi kaji a wurinta.

Ta bayyana cewa an kuma yi ƙoƙarin dakile binciken lamarin ta hanyar zargin yarinyar da aikata sata, lamarin da ya sa iyayenta s**a garzaya Ma’aikatar Harkokin Mata domin neman taimako bayan sun kasa samun adalci.

A cewarta, ma’aikatar ta yi wa iyalan yarinyar alƙawarin tabbatar da cewa an bi musu haƙƙinsu tare da samar wa yarinyar cikakkiyar kulawa da kariya.

Kwamishinar ta nuna damuwa kan ƙaruwar yawan cin zarafin ƙananan yara ta hanyar fyade a jihar, tare da yin kira ga iyaye su guji tura ’ya’yansu talla saboda haɗarin da hakan ke jefa su.

Haka kuma, ta bayyana takaici kan yadda ake yawan sakin waɗanda ake zargi da irin waɗannan laifuka da beli jim kaɗan bayan an gurfanar da su a gaban kotu.

🚨An garzaya da wata Uwargida asibiti bayan ta sami labarin mijinta ya yi mata kishiya a boye.
27/06/2026

🚨An garzaya da wata Uwargida asibiti bayan ta sami labarin mijinta ya yi mata kishiya a boye.

27/06/2026

Zamfara , ‘Yan t4’4dda da rana tsaka😱😱😱

Allah ka kawo mana karshen wannan rashin tsaro🤲

🚨Gwamnatin Kano Ta Ware Tireloli 150 na Takin Zamani Domin Tallafawa Manoma a Fadin Jihar.Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir...
27/06/2026

🚨Gwamnatin Kano Ta Ware Tireloli 150 na Takin Zamani Domin Tallafawa Manoma a Fadin Jihar.

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bayyana cewa gwamnatinsa ta ware tireloli 150 na takin zamani domin tallafa wa manoma a dukkan ƙananan hukumomi 44 na jihar, a wani yunƙuri na bunƙasa harkar noma da ƙarfafa wadatar abinci.

Gwamnan ya ce za a sayar da takin ga manoma na gaskiya a farashi mai rahusa, tare da sauran kayan tallafin noma, domin ƙara yawan amfanin gona da bunƙasa ayyukan noma a faɗin jihar.

Ya bayyana cewa rabon takin zai gudana ne ta hannun ofisoshin hakimai, domin tabbatar da adalci da hana siyasantar da shirin. Haka kuma, ya gargadi shugabannin ƙananan hukumomi da su guji karkatar da rabon takin ko mayar da shi zuwa sakatariyoyin ƙananan hukumomi.

A wani ɓangare kuma, Gwamna Yusuf ya ce gwamnatinsa ta kammala shirye-shiryen samar da ƙananan motocin ɗaukar marasa lafiya guda 484, ɗaya ga kowace mazaɓa a jihar.

A cewarsa, za a yi amfani da motocin ne wajen kai mata masu juna biyu cibiyoyin lafiya cikin gaggawa, domin rage mace-macen mata masu juna biyu da kuma inganta ayyukan kiwon lafiya.

Gwamnan ya kuma buƙaci mata da matasa a faɗin jihar su yi rajista a cibiyoyi na musamman 24 da gwamnatin jihar ta kafa, domin cin gajiyar shirye-shiryen tallafi da bunƙasa rayuwa.

Address

Kano

Telephone

+2348117733195

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when BAHASNet posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to BAHASNet:

Shortcuts

Share