AKN Hausa

AKN Hausa Dan samun sahihan labarai Nishadantatwa fadakarwa ilimintarwa Da Tallata hajojinku

27/12/2023

By Abubakar Danbaba

Akwai wani lokachi wajen 2010 Ghali Umar Na Abba yazo har gida ya gaida Sheikh Sharif Sani Janbulo Shida Alh Jamilu Ali Salga sai bayan sun gama tattaunawa sai yace da Sharif yana neman wata alfarma sai Sharif yace ta menene ya fada, sai yace yanaso a wannan satin ranar juma'a kazo da tawagarka gidana dake sharada ayi zikirin juma'a a can bayan munyi sallar magariba ka fada mana Annabi S.A.W nida iyalaina sharif yace ba matsala zamuzo insha Allah bayan munje munyi zikirin juma'a da magariba, Sharif ya fara fadar girman Annabi S.A.W wallahi yanayin da ghali ya shiga a wannan lokachin na tabbatar ba karamin so yakewa Annabi ba. Bayan antashi s**a shiga cikin falonsa tare da Sharif ina cikin wadanda s**a shiga falon da wasu daga yan"uwa. Waye zai iya tuna abunda ghali ya fada sanda muka shiga falonsa?

Allah yajikan Alhaji Ghali Umar Na Abba kasadashi da masoyinsa Annabi Muhammad S.A.W

Cigiya!! Cigiya!!! Cigiya!!!!Muna cigiyar yan uwan wannan matashin da yayi hatsari akan hanyarsa ta zuwa Kano da lagos.H...
03/05/2023

Cigiya!! Cigiya!!! Cigiya!!!!
Muna cigiyar yan uwan wannan matashin da yayi hatsari akan hanyarsa ta zuwa Kano da lagos.
Hatsarin ya rutsa dashi ne a Obajana Kuma shi kadai ne ya rayu a cikin fasinjojin motar sannan baya iya magana.
Amma ya kokarta ya fadi sunansa wai AHMAD
Kuma ya bayyana shi Dan hotoro ne a Jihar Kano.
Yau kwana biyu kenan Baa Sami Yan uwansa ba Amma a halin yanzu yana kwanci a asibiti in kiwon lafiya (KOGI STATE SPECIALIST HOSPITAL lokoja). Rahoto: Mujahid Saleh Saad - Dan maliki

Duk Wanda yakaranta ya yada har Allah Yasa Yan Uwansa sugani

HATTARA IYAYE MATA: An K**a Wani Matashi Da Yake Tsintar Famfas Din Yara Da Aka Yi Amfani Da Shi Yana Sayarwa Matsafa Na...
03/05/2023

HATTARA IYAYE MATA: An K**a Wani Matashi Da Yake Tsintar Famfas Din Yara Da Aka Yi Amfani Da Shi Yana Sayarwa Matsafa Naira Milyan Daya

Wannan wani matashi ne da aka k**a da laifin tsintar famfas din yara da aka jefar bayan an yi amfani da shi yana sayarwa da masu yin asiri.

A yayin da yake fadin ko nawa yake sayar da famfas din ga matsafan, ya bayyana cewa yakan sayar da kowane famfas kan farashi mai tsoka. Sannan ya kara da cewa amfani da famfas din da matsafan suke yi yana shafar yaran.

Don haka akwai bukatar iyayen yara su dinga kona famfas din da yaransu s**a yi amfani da shi maimakon jefarwa, saboda irin wadannan miyagun mutane.

Jama'a akwai bukatar a yada (sharing) saboda al'umma su amfana.

Wata Babban Lauya A Saudiyya Tayi Tsaye Sai An Kori Christiano Ronaldo Daga Kungiyar Kwallon Kafa Ta Al-Nassr.Alfijir Ha...
02/05/2023

Wata Babban Lauya A Saudiyya Tayi Tsaye Sai An Kori Christiano Ronaldo Daga Kungiyar Kwallon Kafa Ta Al-Nassr.

Alfijir Hausa

Ga mai bukatar tuntubar mu ya neme mu a whatsapps din mu
02/05/2023

Ga mai bukatar tuntubar mu ya neme mu a whatsapps din mu

Fulani Sun Gamu Da Iftali'in Kasawar Shanu 34 A Kasuwar Lere Jihar Kaduna.Daga Aliyu Ishaq Saminaka.A yammacin ranar Alh...
02/05/2023

Fulani Sun Gamu Da Iftali'in Kasawar Shanu 34 A Kasuwar Lere Jihar Kaduna.

Daga Aliyu Ishaq Saminaka.

A yammacin ranar Alhamis 27 ga watan Afrilun 2023, al’ummar da suke maƙwabtaka gadar Lere na jihar Kaduna sun gamu da Iftila’in kasawar Shanu guda 34 inda aka yi nasarar yanka guda Ashirin da bakwai (27), guda ɗaya (1) ta mutu a ciki inda aka garzaya da Shanu shida (6) domin yi musu magani.

Lamarin ya faru ne biyo bayan fitowar shanun daga wata gonar Lambu bayan an cire amfanin da yake cikinta. Fulanin sun zargi da guba aka sanyawa Shanun su a cikin gonar.

Mun samu zantawa da me dabbobin kuma shi ne Kansilar Gundumar Sabon Birni a ƙaramar hukumar Lere. Hon. Maiwada Suleiman, inda ya ce; “Yaranmu sun shiga da shanun mu cikin wannan gonar bisa izininsa (me gonar) inda ya nemi mu siya gonan ya faɗi abin da zamu ba shi har mun yi ciniki mun biya kafin mu shiga da shanun amma da shanun s**a shiga, s**a ci ciyawar sai wani abu ya faru daban. Wanda ba mu yi tsammani ba. A halin yanzu mun sanar da Hukumar Ƴan sanda na ƙaramar hukumar Lere. Sun k**a me gonar tare da mai gadinta domin gudanar da bincike. Haka zalika, muna sanar da hukumar kiwon lafiya na Dabbobi domin gano wani irin nau’in guba s**a ci."

Shugaban Fulani makiyaya reshen Arewa ta tsakiya, Alhaji Gidaɗo Bebeji ya yi kira da gwamnati da shugabannin al'umma dangane da yanayin da ake ƙoƙarin shiga, inda ya ce; bai k**ata irin wannan al'amari yana faruwa a tsakaninmu ba! Domin Fulani da Manoma ba abokan gaba bane.

Daga karshe sun kara yin kira da a yi musu adalci.

AKN Hausa

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AKN Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share