Jakadiyar AREWA

  • Home
  • Jakadiyar AREWA

Jakadiyar AREWA Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Jakadiyar AREWA, Broadcasting & media production company, .
(1)

Jakadiyar AREWA is a Credible Hausa Mass Media that Specialized in Newspaper and TV broadcasting activities with head office in the Northern region capital (kano).

Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un. Allah Ya jiƙan Mai Martaba Sarkin Katsinan Gusau, Dr. Ibrahim Bello. Allah Ya gafar...
25/07/2025

Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un.

Allah Ya jiƙan Mai Martaba Sarkin Katsinan Gusau, Dr. Ibrahim Bello.

Allah Ya gafartawa mishi, Ya kyautata makwancinshi, Ya yi mishi makoma da Aljannah Firdausi. Aameen

Salamun Alaikum.Yau chikin ikon Allah Kwamitin da nake jagoranta na Sports a Majalisar Tarayya Abuja, mun gabatar da pro...
24/07/2025

Salamun Alaikum.

Yau chikin ikon Allah Kwamitin da nake jagoranta na Sports a Majalisar Tarayya Abuja, mun gabatar da program na kaddamar da Raba kayan wasa ga kanan nan kungiyoyin kwallo kafa guda 5,460 a duka fadin Nigeria. Wannan na chikin tsarin ayukkan da wannan kwamiti ya tsara na wannan Assembly na 10.

Yan Majalisa guda 72 ne aka kaddamar da wadann kayan kakrkashin mazabun su, Wanda sune zasuje su rabawa teams 20 a kowache Mazaba da muka zakalo, akallla kowache jiha kanan kungiyoyin kwallo guda 80 zuwa 100 zau amfana da wadannan kayan

Kayan sun hada da Match Jessy sets 20, Training Jessy sets 40, Sai kwallaye 40 ga duk member na wannan kwamiti namu. Shugaban Majalisa Rt. Hon. Tajudden Abbas Phd iyan Zazzau shine ya jagoranci kaddamar da wadann nan Kaya tare da shugaban Hukumar wasanni ta kasa wato Mal. Shehu Dikko, da shugaban hukumar kwallo kafa Ta Nigeria Wanda sakataren sa ya WAKILCHESHI, da DG National institute for Sports da duka shugabannin Majalisa.

Ina Godiya ta musamman ga Haj. Lubna Muhammad Baba Gusau Sarauniyar kasar Hausa da ta halarchi wannan taro daga farko har muka kammala.

Haka Ina Godiya ga Yan Majalisar mu na tarrayya na Jihar Zamfara da s**a halartar s**a ka Sanche Tare da ni har muka kammala wanann taro

1. Hon. Aminu Sani jaji
2. Hon. Dr Engr. Suleman Gummi
3. Hon. Bello Hassan shinkafi
4. Hon Isah Muhammed Anka.

Nagode sosai. Allah saka da Alheri.
Allah shi yabbamu
Allah mun gode.

Hon. Kabiru Amadu Mai palace
MHR Gusau /Tsafe federal constituency Zamfara State
Chairman House Committee on Sports
23July 2025

2027: Tinubu zaɓin Allah ne, babu wata gamayyar siyasa da za ta iya kada shi - Gwamnan Ebonyi Gwamnan Jihar Ebonyi, Fran...
23/07/2025

2027: Tinubu zaɓin Allah ne, babu wata gamayyar siyasa da za ta iya kada shi - Gwamnan Ebonyi

Gwamnan Jihar Ebonyi, Francis Nwifuru, ya bayyana cewa babu wata gamayyar siyasa da za ta iya kada Bola Tinubu a zaben 2027 saboda shi zaɓin Allah ne.

Don haka Nwifuru ya buƙaci ƴan adawa da masu neman takara su hakura da buri, su kuma goyawa gwamnatin da ke ci yanzu baya.

Da ya ke jawabi a taron shugabannin jam’iyyar APC na Kudu maso Gabas da aka gudanar a Abakaliki, Gwamna Nwifuru ya ce fitowar Tinubu a matsayin shugaban kasa a 2023 nufin Allah ne ba nufin dan Adam ba, kuma ya jaddada cewa babu wani kawance ko hadakar ‘yan adawa da za ta iya hana nasarar Tinubu a 2027.

Ya yabawa Tinubu bisa sauye-sauyen tattalin arzikin da ya ke yi, inda ya bayyana shi a matsayin jarumin shugaba mai karfin zuciya da iya yanke shawara mai tsauri domin farfado da kasa. Nwifuru ya roki ‘yan Najeriya, musamman ‘yan Kudu maso Gabas, da su ci gaba da hakuri tare da mara wa shugaban kasa baya.

Mu ba ma son Adeleke ya dawo jam'iyyar mu domin ƙajaga zai zame mana - APC Biyo bayan hukuncin Gwamna Ademola Adeleke na...
23/07/2025

Mu ba ma son Adeleke ya dawo jam'iyyar mu domin ƙajaga zai zame mana - APC

Biyo bayan hukuncin Gwamna Ademola Adeleke na ci gaba da kasancewa cikin jam’iyyar PDP bayan makonni da dama na rade-radin sauya sheka zuwa jam’iyyar APC, jam’iyyar ta APC, reshen jihar Osun ta bayyana cewa ta ƙi karɓarsa saboda gazawarsa a mulki, wanda ya mai da shi ƙajaga ga jam’iyyar.

A wata sanarwa da Daraktan Yaɗa Labarai na jam’iyyar APC, Kola Olabisi, ya fitar a yau Laraba, Shugaban jam’iyyar, Tajudeen Lawal, ya bayyana cewa sauya sheƙa daga wata jam’iyya zuwa wata ba wani abu bane, amma sun ƙi karɓar Adeleke saboda tarin matsalolin da ke tattare da shi, wanda ke iya jawo wa jam’iyyar matsala.

“Ba ma son Gwamna Ademola Adeleke ya shigo APC ne saboda ana masa kallon wanda w zai shigo da ɓarna, wanda da zai lalata mutuncin jam’iyyar APC.”

Jam’iyyar ta ƙara da cewa PDP ta zama kamar gidan kutare da manyan ƴan siyasa masu nagarta ke barin sa.

Sai dai PDP, a cikin martaninta, ta bayyana cewa jam’iyyar nan cike take da ƙarfi kuma tana da goyon bayan al’umma a jihar.

Gwamnan Kano ya sake lashe lambar yabo ta gwarzon shekara Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano ya lashe lambar yabo ta ...
23/07/2025

Gwamnan Kano ya sake lashe lambar yabo ta gwarzon shekara

Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano ya lashe lambar yabo ta “Gwamnan Shekara ta 2025” daga Jaridar Blueprint.

An ba da wannan lambar yabo ne sakamakon gagarumar gudunmawa da gwamnan ya bayar wajen bunkasa fannin ilimi, inda ya ware mafi yawan kudin kasafin kudi zuwa bangaren ilimi fiye da kowace jiha a Najeriya a 2025.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Sanusi Dawakin-Tofa, mai magana da yawun gwamnan, ya fitar a Kano a jiya Talata.

A yayin taron, Sanusi Bature Dawakin-Tofa, wanda ya wakilci gwamnan, ya sake jaddada kudurin gwamnatin sa na sauya tsarin mulki da tafiyar da gwamnati tare da mayar da hankali sosai kan ilimi.

Mataimakin Shugaban Ƙasa Shettima Ya Kai Ziyarar Dubiya Ga Gwamna RaddaMataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima,...
23/07/2025

Mataimakin Shugaban Ƙasa Shettima Ya Kai Ziyarar Dubiya Ga Gwamna Radda

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ya kai ziyarar dubiya ga Gwamna Dikko Umar Radda a gidan gwamnati dake Asokoro, Abuja, bayan hatsarin mota da ya rutsa da shi kwanan nan.

An gudanar da addu’a ta musamman karkashin jagorancin Shugaban Hukumar Hajji na Ƙasa, Farfesa Abdullahi Saleh Usman (Pakistan), inda aka roƙi Allah ya ƙara wa Gwamna Radda lafiya da tsawon rai.

Gwamnan ya nuna jin daɗinsa da godiya, yana mai cewa ziyarar ta nuna ƙauna, hadin kai da ɗan Adamci.

Ziyarar ta samu halartar manyan jami’an gwamnati ciki har da Ministan Noma, Sanata Abubakar Kyari, da mataimakin gwamnan Katsina, Faruq Lawal Jobe, da sauransu.

'Yan majalisa a Nijeriya na wani yunkurin kafa dokar da za ta hana ma'aikatan gwamnati kai 'ya'yansu makarantun kudi da ...
23/07/2025

'Yan majalisa a Nijeriya na wani yunkurin kafa dokar da za ta hana ma'aikatan gwamnati kai 'ya'yansu makarantun kudi da kuma zuwa asibitin kudi don neman lafiya.

Salamun Alaikum                                     SANARWA!     SANARWA!!      SANARWA!!! Kamar yadda nayi sanarwa sati...
22/07/2025

Salamun Alaikum

SANARWA! SANARWA!! SANARWA!!!

Kamar yadda nayi sanarwa sati biyu da s**a wuche akan kokarin da Majalisar kasa ke kanyi na Gyaran kundin tsarin Mulkin Nigeria wato (CONSTITUTION OF THE FEDERAL REPUBLIC OF NIGERIA).

Gobe idan Allah ya kaimu zan gabatar wa Kwamitin Majalisa wadanda da s**a nemi su gabatar da korafi su da koken su akan abunda suke bukata ayi musu ko a saka a chikin dokokin kasa, ko rashin amin chewa da wata doka da ke chiki yanzun wadda ake ganin chutarwa che ga addinin mu da Aladarmu.

Wadanda s**a turamun da takardu Don neman basu damar gabatarwa su sune kamar haka:-

1. Council of Ulamah Zamfara State Branch. Karkashin Jagoranchin Sheikh Ahmad Umar kanoma

2. Ulamah Cunsultative Forum Zamfara State. Karkashin Jagoranchin Sheikh Ahmad Umar kanoma

3. Zamfara State Coalition of NGO's, 2 Groups. Karkashin Jagoranchin Ambassador Ibrahim Tudu

3. National Council of Civil Society and NGO's Northwest region.

4. Movement for the creation SAURI LG from present Tsafe LG. Mutane 80 s**a saka hannu

5. Movement for the creation of DUTSI LG from present ZURMI LG. Mutum 32 s**a saka hannu.

6. Waziri Tsafe Cunsultative forum. Kakrkashin Jagoranchin Alh. Lawali saidu

7. Movement for the creation of MAGAMI LG from present GUSAU LG. Mutum 60 s**a saka hannu.

8. Movement for the creation of KWATARKWASHI LG From present BUNGUƊU LG. Advocacy Group for LG Development

9. Movement for the creation of KUYAMBANA LG (DANSADAU EMIRATE) from PRESENT MARU LG. Mutane 119 s**a saka hannu kakrkashin Jagoranchin Sarkin kudun Dan sadau. Alh Muhammadu Garba Atu II

10. Movement for the creation of YANKUZO LG From present TSAFE LG. Mutum 23 s**a saka hannu kakrkashin Yankuzo Development Association.

11. Movement for the creation of FEGIN MAHE WARD from PRESENT RUWA BORE WARD in Gusau LG. Mutane 16 s**a turo da irin wannan sakon kakrkashin Jagoranchin NURA ISAH.

Wadannan sune na samu sakon su ta Email Dina Kuma gobe inshaAllah zan gabatar wa da kwamiti su domin asaka su chikin wadanda zasu gabatar a Sokoto gaban kwamiti Kuma a dauko Azo da su Majalisa domin tattauna su.

Kowa zaije da 2 copies na Presentation dinsa, mutum 2 ko 3 sun Isa Wakilchi wajen gabatarwa idan a je gabatarwa summary kawai Mai gabatarwa zai gabatar sannan ya isar da copies din ga hannun chairman na Kwamitin a wurin.

An gayyachi Mai girma Gwamnan jihar Zamfara a madadin Gwamnatin jiha da Alumma baki daya inda zai gabatar da Jawabi a madadin bukatun Alumma Zamfara baki daya.

An gayyachi sarakuna guda 4 daga Zamfara suma Mai Martaba sarkin Zamfara Anka zai gabatar da Jawabi a madadin su.

Wadannan sune kadai zaa ba dama suyi magana, Kuma abubuwan da s**a gabatar sue kadai abubuwan da zaa tattauna a Majalisa idan angama.

Yana da kyau kowa yasan haka saboda abune da ya shafi dukkan DAN Asalin Zamfara baki daya.
Muna rokon duka masu yin media suyi sharing a kowane group pls don kowa yasan me ake chiki, haka nasa ayi sanarwa a gidanjen Radio Don saboda wasu Alumma da basu amfani da kafofin sadarwa na Zamani.

Idan Kuma akwai Wanda na tsallake nasu ban saka ba pls. Su Kara turamun a Email Dina. [email protected]

Ranar Assabar 26th July, karfe 10 na safe a Garin Sokoto inshaAllah.

Allah shi yabbamu
Allah mungode

Hon. Kabiru Amadu Mai palace
MHR Gusau /Tsafe federal constituency Zamfara State
Chairman House Committee on Sports
21st July 2025.

Jakadiyar AREWA ta samu labarin cewa, Wata kungiya ta farar hula a Nijar.mai suna MINNJE ta shirya gudanar da zanga-zang...
21/07/2025

Jakadiyar AREWA ta samu labarin cewa, Wata kungiya ta farar hula a Nijar.mai suna MINNJE ta shirya gudanar da zanga-zanga a birnin Yamai don neman adalci, tsaro, da kuma sakin tsohon shugaban kasa Mohamed Bazoum.

Majiyar tamu ta Mi ke labari.? Yaci gaba da cewa Kungiyar ta aika da sanarwa zuwa ga wakilin birnin Yamai a ranar 21 ga Yuli, inda ta bayyana niyyarta na gudanar da zanga-zangar lumana a ranar 27 ga Yuli, 2025.

Abubuwan da kungiyar ke nema sun hada da:
1. 'Yancin cin gashin kai ga shari'a,
2. Gurfanar da masu laifin cin hanci da rashawa a gaban kuliya,
3. Karfafa jami'an tsaro wajen yaki da ta'addanci,
4. A saki Mohamed Bazoum ba tare da wani sharadi ba, wanda ake tsare da shi tun 26 ga watan Yuli, 2023.

Rahoton ya kara da cewa mai jagorantar kungiyar, Abdourhamane Idé Hassane, ya bayyana cewa za a fara zanga-zangar daga dandalin Toumo zuwa dandalin Concertation, inda za a gudanar da babban taro.

YANZU-YANZU: An fara gudanar da zanga-zangar 'yan sanda a Abuja, wadda su Sowore da Dan Bello suke jagoranta a halin yan...
21/07/2025

YANZU-YANZU: An fara gudanar da zanga-zangar 'yan sanda a Abuja, wadda su Sowore da Dan Bello suke jagoranta a halin yanzu.

Tsohon ministan Shari'a a zamanin mulkin marigayi tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari kenan Abubakar Malami kuma jigo ...
21/07/2025

Tsohon ministan Shari'a a zamanin mulkin marigayi tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari kenan Abubakar Malami kuma jigo a jam'iyyar haɗaka ta ADC wanda ke shirin tsayawa takaran gwamna a jihar Kebbi.

Me za ku iya tunawa da game da shi a lokacin da ya ke kan karagar mulki?

Address


Opening Hours

Monday 08:00 - 17:00
Tuesday 08:00 - 17:00
Wednesday 08:00 - 17:00
Thursday 08:00 - 17:00
Friday 08:00 - 15:00
Saturday 09:20 - 16:00
Sunday 10:00 - 16:00

Telephone

+2349162366294

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jakadiyar AREWA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Jakadiyar AREWA:

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Opening Hours
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share