Jakadiyar AREWA

Jakadiyar AREWA Jakadiyar AREWA Amintacciyar Kafar Yada labaran Duniya da Hausa, wadda ta kware a aikin Jarida da talabijin. ku tuntuɓe mu ta WhatsApp number +234 907 576 1901.
(1)

ko kuma ta WhatsApp Chennal din mu https://whatsapp.com/channel/0029VaFHdywKmCPPmkSb2i1o

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN Bøm Ya Tãșhi A Kasuwar Monday Market birnin Maiduguri na Jihar Borno. Allah Ya jikan ...
16/03/2026

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN

Bøm Ya Tãșhi A Kasuwar Monday Market birnin Maiduguri na Jihar Borno.

Allah Ya jikan waɗanda su ka rasa rayukansu

Da Dumi Dumi.ƙungiyar EU tayi watsi da buƙatar Shugaba Donald Trump na tura jami'an tsaro a tekun Hormuz a yaƙin da Amur...
16/03/2026

Da Dumi Dumi.

ƙungiyar EU tayi watsi da buƙatar Shugaba Donald Trump na tura jami'an tsaro a tekun Hormuz a yaƙin da Amurka da Isra'ila keyi da Iran.

Wanda ya fara karanta labarai a gidan talabijin na Al Jazeera, Jamal Rayyan ya rasu. An haifi Rayyan a ranar 23 ga watan...
16/03/2026

Wanda ya fara karanta labarai a gidan talabijin na Al Jazeera, Jamal Rayyan ya rasu.

An haifi Rayyan a ranar 23 ga watan Agusta, 1953 kuma shine ma'aikacin da aka fara haska wa a Al Jazeera.

Shi ne kuma ya fara karanta shirin kundin labarai na Al Jazeera a watan Nuwamba, 1996.

Allah Ya gafarta masa.

Sheikh Abdul Rehman Al Sudais zai jagoranci Sallar Tahujeed a masallacin Harami na Makkah a daren 27 ga watan Ramadan da...
15/03/2026

Sheikh Abdul Rehman Al Sudais zai jagoranci Sallar Tahujeed a masallacin Harami na Makkah a daren 27 ga watan Ramadan da ake kyautata zaton shi ne daren da ake dace da Laylatul Qadari.

📸 Inside Haramain | Twitter

Gwamnan Bauchi Bala Mohammed na shirin komawa APCRahotanni sun nuna cewa gwamnan jihar Bauchi kuma shugaban ƙungiyar gwa...
15/03/2026

Gwamnan Bauchi Bala Mohammed na shirin komawa APC

Rahotanni sun nuna cewa gwamnan jihar Bauchi kuma shugaban ƙungiyar gwamnonin jam’iyyar PDP, Bala Mohammed, na shirin sauya sheka zuwa jam’iyyar APC a cikin makon nan, idan har tattaunawar da ake yi ta yi nasara inji rahotan Arise News.

Majiyoyi sun bayyana cewa gwamnan ya gana da Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da shugabannin APC, inda ya nuna sha’awarsa ta shiga jam’iyyar mai mulki.

Ana kuma tattaunawa kan sharuddan sauya shekar tasa.

Rahotanni sun ce daga cikin abubuwan da ake tattaunawa akwai ba shi tikitin takarar Sanata, amma ba za a ba shi cikakken iko da tsarin jam’iyyar APC a jihar Bauchi ba, kuma ba zai iya zabar wanda zai gaje shi a matsayin gwamna ba.

An kuma ce an bukaci gwamnan ya ba da hakuri ga Seyi Tinubu, bayan wani rikici da ya faru a bara lokacin da dansa ya soki rabon tallafin Ramadan da Seyi ya yi a Bauchi.

A bangaren Seyi Makinde da wasu jiga-jigan PDP kuwa, an bayyana takaici kan wannan shiri, suna mai cewa sauya shekar shugaban gwamnonin PDP zai iya kara raunana jam’iyyar adawa a kasar.

Gwamna Abba ya rushe ma’aikatar ilimi mai zurfi yayin da mataimakin Gwamna ya rasa mukamin sa na kwamishinaGwamnan Jihar...
15/03/2026

Gwamna Abba ya rushe ma’aikatar ilimi mai zurfi yayin da mataimakin Gwamna ya rasa mukamin sa na kwamishina

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da rushe Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi ta jihar, matakin da ya sa Mataimakin Gwamnan jihar, Aminu Abdulsalam Gwarzo, ya daina rike mukamin kwamishinan da ke kula da ma’aikatar.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Lahadi.

Sanarwar ta ce gwamnatin jihar ta hade Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi da Ma’aikatar Ilimi domin karfafa daidaiton gudanarwa tare da hanzarta aiwatar da gyare-gyare a bangaren ilimi a jihar.

A karkashin sabon tsarin, ma’aikatar da aka hade za ta ci gaba da aiki ne a karkashin suna Ma’aikatar Ilimi. Haka kuma za a kafa wani sashe na musamman mai kula da Ilimi Mai Zurfi a cikin ma’aikatar domin kula da harkokin manyan makarantu.

Sanarwar ta kara da cewa wannan sashe zai kasance karkashin jagorancin Babban Sakatare tare da samun goyon bayan ma’aikatan da s**a dace domin tabbatar da ingantaccen gudanar da cibiyoyin ilimi mai zurfi a jihar.

Har ila yau, dukkan hukumomi da ke karkashin tsohuwar Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi, ciki har da Hukumar Bada Tallafin Karatu (Scholarship Board), za su koma karkashin Ma’aikatar Ilimi. Haka kuma jami’o’in da gwamnatin jihar ta mallaka da sauran cibiyoyin ilimi mai zurfi za su kasance karkashin kulawar sabon sashen da aka kafa.

Gwamnatin ta bayyana cewa wannan mataki na daga cikin gyaran da take yi a bangaren ilimi domin sake farfado da shi, kawar da maimaita ayyuka tsakanin ma’aikatu, inganta hadin kai wajen tsara manufofi a dukkan matakan ilimi tare da rage kudin tafiyar da gwamnati.

Gwamna Yusuf ya ce gyaran tsarin na da nufin rage kashe kudaden gwamnati tare da kara inganci, gaskiya da rikon amana a tafiyar da harkokin ilimi a Jihar Kano.

Ya kuma jaddada kudurin gwamnatinsa na ci gaba da aiwatar da manyan gyare-gyare da za su farfado da bangaren ilimi tare da tabbatar da kyakkyawar makoma ga matasan jihar.

A karshe, gwamnan ya umurci Ofishin Sakataren Gwamnatin Jihar da na Shugaban Ma’aikatan Jihar da su tabbatar da aiwatar da sauye-sauyen cikin gaggawa tare da daidaita ayyukan ma’aikatun da abin ya shafa domin samun sauyin cikin sauki.

Isra’ila ta sanar da Amurka cewa kayan makaman da take amfani da su wajen kakkabe makamai masu linzami (ballistic missil...
15/03/2026

Isra’ila ta sanar da Amurka cewa kayan makaman da take amfani da su wajen kakkabe makamai masu linzami (ballistic missile interceptors) sun kusa ƙarewa matuƙa, yayin da rikicin da take yi da Iran ke ci gaba.

Jami’an Amurka sun tabbatar da cewa sun san cewa Isra’ila tana da ƙarancin waɗannan makaman kariya tun watanni da s**a gabata. Kamar yadda rahoton Iran Times ya tabbatar.

WATA SABUWA: Kim Jong Un Ya Gwada Makaman Rokoki Masu Iya Daukar Makamin NukiliyaShugaban ƙasar North Korea, Kim Jong Un...
15/03/2026

WATA SABUWA: Kim Jong Un Ya Gwada Makaman Rokoki Masu Iya Daukar Makamin Nukiliya

Shugaban ƙasar North Korea, Kim Jong Un, ya jagoranci gwajin wani sabon tsarin harba makamai masu linzami da dama (Multiple Rocket Launcher System, MRLS) waɗanda ke da ikon ɗaukar makaman nukiliya, kamar yadda kafafen yaɗa labaran gwamnatin ƙasar s**a bayyana.

Kamfanin dillancin labaran ƙasar, Korean Central News Agency (KCNA), ya ce gwajin ya gudana ne ranar Asabar inda aka yi amfani da harba rokoki guda 12 masu girman milimita 600 tare da rundunonin manyan bindigogi guda biyu.

Rahoton ya ce makaman sun kai hari kan wani tsibiri da ke cikin tekun gabashin ƙasar, inda s**a kai nisan kilomita 364.4, kuma an ce sun bugi wurin da ake nufi da daidaito kashi 100 cikin 100.

Kim Jong Un ya ce wannan gwajin zai sa abokan gaban ƙasarsa da ke cikin kilomita 420 na nisan kai hari su shiga cikin fargaba tare da fahimtar irin ƙarfin lalata da makaman nukiliya na dabara ke da shi.

A nasa bangaren, sojojin South Korea sun bayyana cewa sun gano harba makamai masu linzami sama da guda 10 da North Korea ta harba zuwa tekun da ake kira Sea of Japan ko kuma Tekun Gabas.

Fadar shugaban ƙasar South Korea ta yi Allah-wadai da wannan mataki, tana mai cewa tsokana ce da ta saba wa dokokin Majalisar Dinkin Duniya.

Wannan gwaji ya zo ne a daidai lokacin da sojojin United States da na South Korea ke gudanar da atisayen soji na hadin gwiwa mai suna Freedom Shield, wanda ya hada da sojoji kusan 18,000 kuma zai gudana har zuwa ranar 19 ga Maris.

A halin da ake ciki kuma, tsohon shugaban Amurka Donald Trump ya nuna cewa yana ganin zai yi kyau idan aka sake gudanar da tattaunawa tsakanin Amurka da shugabannin North Korea.

Sai dai ‘yar uwar shugaban ƙasar, Kim Yo Jong, ta yi gargadi cewa wannan atisayen soji na iya haifar da mummunan sakamako da ba za a iya tsammani ba.

Kazalika, North Korea ta yi Allah-wadai da harin da United States da Israel s**a kai wa Iran, tana mai cewa hakan ya nuna halin da Amurka ke ciki na keta dokokin kasa da kasa.

Akwai Gwamnoni 19 a Arewa, Sanatoci 57, kusan 'yan majalisar wakilai 191, da kuma sarakuna masu lamba daya sama da 30Amm...
15/03/2026

Akwai Gwamnoni 19 a Arewa, Sanatoci 57, kusan 'yan majalisar wakilai 191, da kuma sarakuna masu lamba daya sama da 30

Amma babu daya daga cikinsu da yayi magana akan rashin adalcin da akawa Malam Nasiru Ahmad El-Rufai

Amma yanzu da an ce babu dattawa a Arewa sai ku fara haushi.

Inji Imran U. Wakili

Shugaba Donald Trump ya bukaci sauran kasashen duniya da su aike da jiragen ruwan yaki domin tabbatar da tsaron mashigin...
15/03/2026

Shugaba Donald Trump ya bukaci sauran kasashen duniya da su aike da jiragen ruwan yaki domin tabbatar da tsaron mashigin Hormuz, bayan da Iran ta yi barazanar kawo cikas ga jirga-zirgar jiragen dakon mai saboda yakin da take gwabzawa da kawancen Amurka da Isra'ila.

Idan ma Netanyahu bai mutu yanzu ba to nan gaba kaɗan za mu hallaka shi - Iran Rundunar Sojojin Juyin-Juya-hali ta Iran ...
15/03/2026

Idan ma Netanyahu bai mutu yanzu ba to nan gaba kaɗan za mu hallaka shi - Iran

Rundunar Sojojin Juyin-Juya-hali ta Iran (IRGC) ta ci alwashin hallaka Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu.

Daily Trust ta rawaito cewa a wani sako da ta wallafa a shafin ta na yanar gizo mai suna Sepah News, IRGC idan ma Netanyahu, wanda ta kira da "azzalumi makashin ƙananan yara" ya na raye a halin yanzu, to ba makawa za ta ci gaba da fakon shi har sai ta hallaka shi da ƙarfin tuwo.

Hakan na zuwa ne yayin da jita-jita ta ke ƙara ƙarfi cewa an kashe Netanyahu a hare-haren da Iran din ke kai wa Isra'ila.

Tun a karshen mako jita-jitar ke ta yaɗuwa, duk da cewa Ma'aikatar Tsaro ta Isra'ila (IDF) ta ƙaryata raɗe-raɗin.

Ana zargin rundunar sojin Najeriya da tsare wani babban jami’inta mai suna Manjo Shamsudeen Sani, wanda ke aikin wanzar ...
15/03/2026

Ana zargin rundunar sojin Najeriya da tsare wani babban jami’inta mai suna Manjo Shamsudeen Sani, wanda ke aikin wanzar da zaman lafiya a yankin Arewa maso Gabas, tsawon watanni bisa zargin janye dakarun da ke ƙarƙashinsa daga filin daga.

Bayanai da majiyarmu ta tashar Dandal Kura Radio da ke Maiduguri ta ruwaito sun ce jami’in sojin ya janye dakarun ne bayan ya nemi ɗaukin gaggawa na ƙarin sojoji da kayan aiki a lokacin da suke tsaka da gwabza faɗa da mayaƙan Boko Haram/ISWAP. Rahotanni sun ce ba a samu damar kai musu ɗauki ba, kuma faɗan ya fara rinjayar su, lamarin da ya sa ya umarci dakarun da kowa ya yi ta kansa domin tsira da rayukansu.

Rahotanni sun ƙara da cewa tun bayan tsare jami’in, an hana matansa biyu damar ganinsa, b***e ma ‘ya’yansa.

Idan wannan zargin da ake yi wa rundunar na tsare shi ya tabbata, kuna ganin an yi masa adalci?

Address

Kano

Opening Hours

Monday 08:00 - 17:00
Tuesday 08:00 - 17:00
Wednesday 08:00 - 17:00
Thursday 08:00 - 17:00
Friday 08:00 - 15:00
Saturday 09:20 - 16:00
Sunday 10:00 - 16:00

Telephone

+2349162366294

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jakadiyar AREWA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Jakadiyar AREWA:

Share