Jakadiyar AREWA

Jakadiyar AREWA Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Jakadiyar AREWA, Broadcasting & media production company, Kano.

Jakadiyar AREWA is a Credible Hausa Mass Media that Specialized in Newspaper and TV broadcasting activities with head office in the Northern region capital (kano).

TIRKASHI: Bayan Tsawon Shekaru Biyu Ana Shan Soyayya Mace Mai Gemu Ta Amarce Da AngontaAicha Kante Mao Gemu Ta Amarce, I...
15/10/2025

TIRKASHI: Bayan Tsawon Shekaru Biyu Ana Shan Soyayya Mace Mai Gemu Ta Amarce Da Angonta

Aicha Kante Mao Gemu Ta Amarce, Inda Ta Auri Wani Dan Kasar Nijar Bayan Tsawon Shekaru Biyu Suna Shan Soyayya

An kammala zaman tattaunawar fahimtar juna tsakanin majalisar shura ta jihar Kano da Malam Lawal Triumph a ofishin hukum...
13/10/2025

An kammala zaman tattaunawar fahimtar juna tsakanin majalisar shura ta jihar Kano da Malam Lawal Triumph a ofishin hukumar tsaron farin kaya ta jihar Kano.

Tini Mal Lawan Triumph ya wallafa Alhamdullah a shafin sa na sada zumunta na Facebook, hakan na nufin cewa Lawan ya kare ƙimar maganganun sa kenan a gaban kwamitin Shura?

Wakilinmu da ya hallacci zaman ya tabbatar mana an samu daidaito tsakanin ɓangarorin biyu.

Ya kuke kallon wannan zaman na Shura?

Zafafan hotuna daga zaman tattaunawar kwamitin shura na Kano da Malam Lawan Triumph.Ku matso kusa za mu kawo muku yadda ...
13/10/2025

Zafafan hotuna daga zaman tattaunawar kwamitin shura na Kano da Malam Lawan Triumph.

Ku matso kusa za mu kawo muku yadda zaman ya kasance baki daya.

WATA SABUWA: 'Yan Ɗarika Suna Ba Ni Mamaki, Su Da Kansu S**a Rubuta Littafin Jawahirul Ma'ani, Amma Kuma Ba Sa So A Kara...
04/10/2025

WATA SABUWA: 'Yan Ɗarika Suna Ba Ni Mamaki, Su Da Kansu S**a Rubuta Littafin Jawahirul Ma'ani, Amma Kuma Ba Sa So A Karanta Shi, Inji Sheikh Barista Ishaq Adam Ishaq

02/10/2025

Weekly Tafsir,
delivered by Dr. Tajudeen Muhammad Adigun OON.
from MCC Masjid Wuse zone 3
Abuja Nigeria.

Part 1
Jakadiyar AREWA

Ƙasashen Burkina Faso, Mali da Nijar da sojoji ke mulki sun fice daga Kotun Duniya ta Hukunta Manyan Laifuka (ICC), suna...
23/09/2025

Ƙasashen Burkina Faso, Mali da Nijar da sojoji ke mulki sun fice daga Kotun Duniya ta Hukunta Manyan Laifuka (ICC), suna zargin ta da kasancewa “kayan aikin mulkin mallaka na zamani.”

Rikicin siyasa a Kebbi: Kungiyar Cigaban Arewa-Maso-Yamma ta yaba wa DSS bisa gayyatar MalamiKungiyar 'Northwest Progres...
23/09/2025

Rikicin siyasa a Kebbi: Kungiyar Cigaban Arewa-Maso-Yamma ta yaba wa DSS bisa gayyatar Malami

Kungiyar 'Northwest Progressive Mandate Frontiers' ta yaba wa Hukumar Tsaro ta Farin-kaya (DSS) bisa gayyatar tsohon Ministan Shari'a, Abubakar Malami (SAN), dangane da rikicin siyasa da ya faru a Jihar Kebbi kwanan nan.

Tsohon ministan ya bayyana a shafinsa na Facebook a jiya Litinin cewa DSS ta gayyace shi ne saboda wani rikici da ya faru tsakanin motocin ayarin sa da magoya bayan jam’iyyar APC, a birnin Kebbi na jihar Kebbi.

Malami ya zargi wasu manyan ’yan siyasa da ke adawa da shi a jihar da cewa su ne s**a ƙulla ƙorafin da ya kai ga gayyatar da aka yi masa.

Sai dai a wata sanarwa da mai magana da yawun kungiyar, Armayau Kabir Koko, ya fitar a yau Talata, ya ce gayyatar da aka yi wa Malami tanuna cewa DSS na da ƙwazo wajen tabbatar da gaskiya, adalci, da bin doka wajen magance matsalolin da ke barazana ga zaman lafiya da dimokuraɗiyya.

Sanarwar ta kuma bukaci Hukumomin Yaki da Cin Hanci da Rashawa na EFCC da ICPC da su gudanar da bincike kan zarge-zargen cin hanci da amfani da ofis ta hanyar da bata dace da dokokin ƙasa ba da ake yi wa Malami.

A cewarsa: “Babu wani mutum, komai matsayinsa da tasirinsa na siyasa, da ya kamata ya kasance sama da doka, musamman idan zaman lafiya da ci gaban ƙasar mu na fuskantar haɗari.”

Ya ƙara da cewa, “Muna kuma kira ga DSS da ta faɗaɗa binciken nata har zuwa shekarun da Malami ya yi a ofis a matsayin Antoni Janar da Ministan Shari’a, domin akwai buƙatar sanin gaskiya kan yadda ya tafiyar da ofis din, in ji sanarwar.

Hukumomi a Saudiyya sun sanar da rasuwar Babban Malamin ƙasar, Sheikh Abdulaziz Bin Abdullah Al al-Sheikh ranar Talata.S...
23/09/2025

Hukumomi a Saudiyya sun sanar da rasuwar Babban Malamin ƙasar, Sheikh Abdulaziz Bin Abdullah Al al-Sheikh ranar Talata.

Sanarwar ta ce za a yi jana'izar Sheikh Abdulaziz, wanda shi ne shugaban Majalisar Manyan Malaman Saudiyya, da rana a Masallacin Imam Turki bin Abdullah da ke birnin Riyadh.

Sarki Salman na Saudiyya ya bayar da umarni a yi masa salatul ghaib a Masallatan Harami da sauran masallatan da ke faɗin ƙasar.

Majalisar dattawan Nijeriya ta buɗe ofishin Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ranar Talata, 23 ga watan Satumba.Mataimakin ...
23/09/2025

Majalisar dattawan Nijeriya ta buɗe ofishin Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ranar Talata, 23 ga watan Satumba.

Mataimakin daraktan Sergent At Arms na majalisar dattawan, Alabi Adedeji, ne ya buɗe ofishin a wani mataki da ake gani zai share hanya ga dakatacciyar 'yar majalisar domin komawa bakin aiki.

A watan Maris ɗin da ya gabata ne aka rufe ofishin Sanata Natasha bayan majalisar dattawa ta dakatar da ita tsawon watanni shida sakamakon laifin rashin ɗa'a bayan da ta zargi shugaban majalisar dattawa Sanata Godswill Akpabio da neman yin lalata da ita, zargin da ya musanta.

Jami‘ar da ta musanta bai wa Rarara digirin DR ta yi masa tayin samun digirin daga baya ——Jami’ar European American Univ...
21/09/2025

Jami‘ar da ta musanta bai wa Rarara digirin DR ta yi masa tayin samun digirin daga baya

——

Jami’ar European American University ta bukaci Dauda Kahutu Rarara da wadanda aka ce an karrama da digirin girmamawa a Abuja su tuntube ta domin ta duba cancantarsu na samun matsayin.

A wata sanarwa da jami’ar ta fitar a shafinta na yanar gizo, ta bayyana cewa muddin wadanda ta ambata sun cancanci samun digirin, za ta karrama su da shi a taron yaye dalibai da za ta gudanar a Najeriya cikin watan Nuwamban 2025.

Kazalika ta ce babu wani kudi da za a bukaci wani ya biya saboda a kaucewa ayyukan 'yan damfara, kuma tuni ta fara daukar mataki don gano wadanda s**a shirya abinda ta kira da damfara.

Wannan ya biyo bayan sanarwar da jami'ar ta fitar na nesanta kanta da taron karrama mutanen da digirin girmamawa, wanda ya gudana a birnin Abuja jiya Asabar.

A halin yanzu al'ummar ƙasar Burkina Faso na ci gaba da gina daya daga cikin mafi girman mutun butumin shugabansu Ibrahi...
21/09/2025

A halin yanzu al'ummar ƙasar Burkina Faso na ci gaba da gina daya daga cikin mafi girman mutun butumin shugabansu Ibrahim Traore domin nuna murnar kokarin da ya yi na gyara kasar.

Sun ce ba za su jira sai ya mutu ba kafin suyi bikin nasa, sunce suna yin bikin shi ne tun yana raye domin yabawa kokarin sa.

Shin yaushe ne zaku yiwa naku shuwagabanni bikin yabawa domin tunawa da kokarin su ga kasashen da suke mulki....?

Address

Kano

Opening Hours

Monday 08:00 - 17:00
Tuesday 08:00 - 17:00
Wednesday 08:00 - 17:00
Thursday 08:00 - 17:00
Friday 08:00 - 15:00
Saturday 09:20 - 16:00
Sunday 10:00 - 16:00

Telephone

+2349162366294

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jakadiyar AREWA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Jakadiyar AREWA:

Share