23/09/2025
Rikicin siyasa a Kebbi: Kungiyar Cigaban Arewa-Maso-Yamma ta yaba wa DSS bisa gayyatar Malami
Kungiyar 'Northwest Progressive Mandate Frontiers' ta yaba wa Hukumar Tsaro ta Farin-kaya (DSS) bisa gayyatar tsohon Ministan Shari'a, Abubakar Malami (SAN), dangane da rikicin siyasa da ya faru a Jihar Kebbi kwanan nan.
Tsohon ministan ya bayyana a shafinsa na Facebook a jiya Litinin cewa DSS ta gayyace shi ne saboda wani rikici da ya faru tsakanin motocin ayarin sa da magoya bayan jam’iyyar APC, a birnin Kebbi na jihar Kebbi.
Malami ya zargi wasu manyan ’yan siyasa da ke adawa da shi a jihar da cewa su ne s**a ƙulla ƙorafin da ya kai ga gayyatar da aka yi masa.
Sai dai a wata sanarwa da mai magana da yawun kungiyar, Armayau Kabir Koko, ya fitar a yau Talata, ya ce gayyatar da aka yi wa Malami tanuna cewa DSS na da ƙwazo wajen tabbatar da gaskiya, adalci, da bin doka wajen magance matsalolin da ke barazana ga zaman lafiya da dimokuraɗiyya.
Sanarwar ta kuma bukaci Hukumomin Yaki da Cin Hanci da Rashawa na EFCC da ICPC da su gudanar da bincike kan zarge-zargen cin hanci da amfani da ofis ta hanyar da bata dace da dokokin ƙasa ba da ake yi wa Malami.
A cewarsa: “Babu wani mutum, komai matsayinsa da tasirinsa na siyasa, da ya kamata ya kasance sama da doka, musamman idan zaman lafiya da ci gaban ƙasar mu na fuskantar haɗari.”
Ya ƙara da cewa, “Muna kuma kira ga DSS da ta faɗaɗa binciken nata har zuwa shekarun da Malami ya yi a ofis a matsayin Antoni Janar da Ministan Shari’a, domin akwai buƙatar sanin gaskiya kan yadda ya tafiyar da ofis din, in ji sanarwar.