Arewa Digital Politics

Arewa Digital Politics ๐“Ÿ๐“ธ๐“ต๐“ฒ๐“ฝ๐“ฒ๐“ฌ๐“ช๐“ต ๐“ช๐“ญ๐“ฟ๐“ธ๐“ฌ๐“ช๐“ฌ๐”‚.
*๐“ข๐“พ๐“น๐“น๐“ธ๐“ป๐“ฝ ๐“ช๐“ท๐“ญ ๐“œ๐“ธ๐“ซ๐“ฒ๐“ต๐“ฒ๐”ƒ๐“ช๐“ฝ๐“ฒ๐“ธ๐“ท.
*๐“’๐“ช๐“ถ๐“น๐“ช๐“ฒ๐“ฐ๐“ท ๐“ช๐“ท๐“ญ ๐“ฒ๐“ท๐“ฏ๐“ต๐“พ๐“ฎ๐“ท๐“ฌ๐“ฎ ๐“น๐“พ๐“ซ๐“ต๐“ฒ๐“ฌ ๐“ธ๐“น๐“ฒ๐“ท๐“ฒ๐“ธ๐“ท. *๐“ค๐“น๐“ต๐“ฒ๐“ฏ๐“ฝ๐“ฒ๐“ท๐“ฐ ๐“ฝ๐“ฑ๐“ฎ ๐“น๐“ธ๐“ต๐“ฒ๐“ฝ๐“ฒ๐“ฌ๐“ช๐“ต ๐“ฌ๐“ช๐“ป๐“ป๐“ฒ๐“ฎ๐“ป ๐“ธ๐“ฏ ๐“น๐“ช๐“ป๐“ฝ๐“ฒ๐“ผ๐“ช๐“ท.

26/03/2026

APC NATIONAL CONVENTION 2026....ABUJA.

YANZU-YANZU: Gwamnan Jihar Kano ya ฦ™addamar da rundunar tsaro ta cikin gida mai suna Kano State Security and Neighbourho...
23/12/2025

YANZU-YANZU: Gwamnan Jihar Kano ya ฦ™addamar da rundunar tsaro ta cikin gida mai suna Kano State Security and Neighbourhood Watch, wadda ta ฦ™unshi jamiโ€™ai 2,000, domin ฦ™arfafa tsaro da kare rayuka da dukiyoyin alโ€™umma a faษ—in jihar.

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN...ALLAH ya karbi ran justice Ibrahim tanko,ALKALIN ALKALAI lokacin BUHARI.
16/12/2025

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN...

ALLAH ya karbi ran justice Ibrahim tanko,ALKALIN ALKALAI lokacin BUHARI.

12/12/2025

Gwamnatin Jihar Kano, ta haramta kafa Hukumar Hisbah mai zaman kanta, wadda tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje, ya yi ฦ™oฦ™arin kafawa.

11/12/2025

ENGR.ABBA KABIR YUSIF.
Zai kara dauukar mutum 4,343 aikin koyarwa Domin bunkasa ilimin a fadin jihar baki Daya,

08/12/2025

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba K Yusuf, Ya Sami Karramawa Daga Nigeria Excellence Awards in Public Service (NEAPS)

Gwamnan Jihar Kano, Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sami gagarumar karramawa daga Nigeria Excellence Awards in Public Service (NEAPS) saboda rawar da yake takawa wajen inganta walwalar jamaโ€™a da gudanar da mulki mai tsafta da hangen nesa. Wannan lambar yabo ta zo ne a matsayin tabbatar da irin jajircewa, kishin aiki da tsantsar sadaukarwa da Gwamnan yake nunawa tun daga farkon hawansa mulki.

Wannan karramawa ba wai waiwayen gudummawar Gwamna Abba Kabir Yusuf kaษ—ai ba ce, illa kawai ta kasance moriyar dukkan alโ€™ummar Jihar Kano, kasancewar manufofin gwamnatinsa sun mayar da hankali ne kan inganta rayuwar talakawa ta fuskar ilimi, lafiya, tsaro, ababen more rayuwa, da tsaftace birane. NEAPS ta tabbatar da cewa shirye-shiryen da ake aiwatarwa a Kano sun nuna sabon salo na shugabanci mai maโ€™ana da tasiri.

A cewar kwamitin masu tantancewa, Gwamnan ya fito ne a matsayin shugaba mai kishin alโ€™umma, wanda ke samar da tsari mai dorewa, tare da jajircewa wajen kawar da kalubale da kuma gina ingantacciyar makoma ga jihar. Wannan ya hada da farfado da cibiyoyin gwamnati da s**a dade a durkushe, dawo da mutuncin makarantun gwamnati, karkata hankali ga jin dadin maโ€™aikata, da kuma aiwatar da sabbin ayyukan raya kasa a cikin birane da karkara.

Gwamnatin Kano ta bayyana wannan karramawa a matsayin abin alfahari ga mutane miliyoyin Kano dake cikin gida da waje, tare da tabbatar da cewa wannan yabo zai kara ฦ™aimi da kwarin gwiwa ga Gwamna wajen aiwatar da muhimman manufofi da s**a shafi ci gaban alโ€™umma.

Gwamnatin Jihar Kano ta gode wa NEAPS bisa wannan girmamawa, tare da tabbatar da cewa za a ci gaba da gudanar da mulki mai inganci da gaskiya domin tabbatar da ganin Jihar Kano ta tsaya a sahun gaba a fannin ci gaba, zaman lafiya da bunฦ™asa tattalin arziki.

Muna adduโ€™ar ALLAH Ya ci gaba da bawa Mai Girma Gwamna ikon jagoranci cikin nasara, Ya kuma kara daukaka Jihar Kano da dukkan alโ€™ummar ta.

Sabon ministan tsaro Christopher Musa ya bukaci a dena biyan kuษ—in fansa ga masu garkuwa da mutane Majalisar Dattawa ta ...
03/12/2025

Sabon ministan tsaro Christopher Musa ya bukaci a dena biyan kuษ—in fansa ga masu garkuwa da mutane

Majalisar Dattawa ta tabbatar da tsohon Babban Hafsan Tsaro, Janar Christopher Musa, a matsayin sabon Ministan Tsaro na Najeriya.

Tabbatarwar ta biyo bayan tantancewa inda โ€˜yan majalisa s**a yi masa tambayoyi kan matsalolin tsaro da tarihin aikinsa.

Musa ya yi alkawarin aiki tare da dukkan hukumomin tsaro da jamaโ€™a don magance kalubalen tsaro.

Musa ya yi kira da a daina biyan kuษ—in fansa ga masu garkuwa da mutane da masu tayar da kayar baya, yana mai cewa hakan na ฦ™ara musu ฦ™arfin makamai.

Ya kuma bukaci samar da kundin bayanai na ฦ™asa guda ษ—aya, da kuma ฦ™arin tasiri daga jihohi da ฦ™ananan hukumomi wajen yaki da rashin tsaro.

Musa ya ce kisan-kisan da ake yi a ฦ™asar ya shafi kowa ba tare da bambanci ba.

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya yaba da irin amsoshin da Musa ya bayar, sannan โ€˜yan majalisa s**a amince da nadinsa ta hanyar kuriโ€™ar murya.

SABON MINISTER TSARON NIGERIA.
03/12/2025

SABON MINISTER TSARON NIGERIA.

Check out Arewa Digital Politicsโ€™s post.

MINISTER TSARO Nigeria ya ajiye mukaminsa.
02/12/2025

MINISTER TSARO Nigeria ya ajiye mukaminsa.

Check out Arewa Digital Politicsโ€™s post.

DEATH.๐Ÿ•Œ
27/11/2025

DEATH.๐Ÿ•Œ

Check out Arewa Digital Politicsโ€™s post.

26/11/2025

Yadda wasu Yan mata s**a Kubuta daga hannun bandit a jihar KEBBI.

Al'ummar AREWA na ci gaba da jan hankalin tsohon gwamnan jihar Kaduna Malam Nasir Ahmad El-Rufai da ya ษ—auki tsatsauran ...
26/11/2025

Al'ummar AREWA na ci gaba da jan hankalin tsohon gwamnan jihar Kaduna Malam Nasir Ahmad El-Rufai da ya ษ—auki tsatsauran mataki kan wasu yaransa biyu Ibrahim da Balkisu (Bilqis) a sakamakon wata hanya da su ka ษ—auka na kauce wa addinin muslunci.

Ibrahim wanda shi ne ษ—an auta ga mayar El-Rufai ta farko Hajiya Hadiza, ya bayyana ฦ™arara cewa bai รฝร ฤda akwai Alฤบร h ba, don haka ya jima daga fita addinin muslรนmci. Waษ—annan furuci na shi na cikin wasu bidiyoyin da ya ke sakewa a shafinsa na Instagram.

Ita kuwa Balkisu (Biliqis) ita ce babbar ฦดa (ฦดar fari) ga matar El-rufai ta biyu Barista Asiya. Ta bayyana wa duniya cewa ita mai fafutukar kare masu auren jinsi ce wato ma'ana ita ฦดar ฤนฤžBลขQ.

Wani abin lura a nan shi ne, dukka yaran biyu dai na zaune ne a ฦ™asashen waje.

Duk da cewa babu wani daga cikin ahalinsu da ya fito ya ฦ™aryata ko kuma ya gaskanta labarin da ke yawo a kansu biyo bayan fitan wasu hotuna marasa kyaun gani tare da bidiyoyin su suna iฦ™irari da ra'ayin abin da su ka yi imani da shi a kai ba tare da nadamar abin da su ke yi ba. A kan hakan ne ake jan hankalin mahaifisu da ya taka musu birki tun kafin lamarisu ya yinisa.

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Digital Politics posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category