KMH

KMH Multi Media Platform

Wanda ya bayyana cewa ana lalata da yara a Gidan gyaran hali bashi da gaskiya — cewar hukumar kula da gidan gyaran hali
04/05/2025

Wanda ya bayyana cewa ana lalata da yara a Gidan gyaran hali bashi da gaskiya — cewar hukumar kula da gidan gyaran hali

04/05/2025

Bayan gudanar da cikakken bincike da bibiyar gaskiyar abinda ke faruwa a gidajen ajiya da gyaran hali na Goron Dutse dake Kano, bayan yaɗuwar wani labari na wani matashi mai suna Ya Malam da ya bayyana yadda ake lalata da yara maza a gidan yari na Goron Dutse. KMH HAUSA ta gano cewa Labarin bashi d...

Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) ta k**a tsoffin daraktoci da wasu manyan jami’an matatun mai na Port Harcour...
03/05/2025

Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) ta k**a tsoffin daraktoci da wasu manyan jami’an matatun mai na Port Harcourt, Warri, da Kaduna da aka kora kwanan nan, bisa zargin almundahana da kudaden da aka ware don gyaran matatun.

Binciken da jaridar PUNCH ta gudanar ya nuna cewa EFCC na binciken dala biliyan 2.9, ciki har da dala biliyan 1.5 da aka ware wa matatar Port Harcourt, dala miliyan 740 don matatar Kaduna, da kuma dala miliyan 656 don matatar Warri.

Tsohon Manajan Darakta na Kamfanin Matatar Mai na Port Harcourt shine Mista Ibrahim Onoja, yayin da Efifia Chu shi ne tsohon Manajan Darakta na Kamfanin Matatar Mai da Sinadarai na Warri.

Majiyoyi daga babban ofishin kamfanin NNPCL sun tabbatar cewa an gano Naira biliyan 80 a asusun daya daga cikin tsoffin daraktocin da aka kora.

Wani babban jami’in EFCC da ya nemi a boye sunansa saboda ba shi da izinin magana da manema labarai ya shaidawa PUNCH ranar Juma’a cewa k**a tsoffin daraktocin guda uku da wasu manyan jami’ai na da alaka da binciken da ake gudanarwa kan kudaden gyaran matatun da gwamnatin tarayya ta fitar kwanan nan.

Wata takardar da PUNCH ta gani daga NNPCL, mai dauke da kwanan wata 28 ga Afrilu, 2025, mai taken ‘Investigation Activities: Request for Information’, ta nuna cewa binciken EFCC ya shafi tsohon Babban Shugaban Rukunin Kamfanin NNPCL, Mele Kyari.

Takardar ta EFCC ta kuma kunshi sunayen wasu tsofaffin manyan jami’an kamfanin guda 13 da ake bincike a kansu kan zargin karkatar da kudaden.

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, tare da tawagarsa sun ziyarci fadar Mai Martaba Sarkin Kano domin halartar ...
03/05/2025

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, tare da tawagarsa sun ziyarci fadar Mai Martaba Sarkin Kano domin halartar bikin nadin sabon Galadiman Kano da sauran masu sarauta hudu.

Ɗaruruwan jami’an gwamnati ciki har da Mataimakin Gwamna, Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo, Sakataren Gwamnatin Jiha Alhaji Umar Faruk Ibrahim, da dama daga cikin kwamishinoni da sauran su.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamna, Mustapha Muhammad, ya fitar a ranar Juma’a a Kano.

Cikin wadanda aka nada sun hada da:

1. Alhaji Munnir Sanusi Bayero a matsayin Galadiman Kano.

2. Alhaji Kabir Tijjani Hashim a matsayin Wamban Kano.

3. Alhaji Mahmud Ado Bayero a matsayin Turakin Kano.

4. Alhaji Ahmad Abbas Sanusi a matsayin Yariman Kano.

5. Alhaji Adam Lamido Sanusi a matsayin Tafidan Kano.

Mai Martaba Sarkin Kano, Khalifa Muhammadu Sanusi II, ya bukaci wadanda aka nada da su kasance masu biyayya, jajircewa, da girmama dan Adam.

Ya shaida wa taron cewa an zabi wadanda aka nada ne bisa cancantarsu, sadaukarwa, da kishin al’adun gargajiya da martabar masarautar Kano.

Mustapha Muhammad
Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamnan Jihar Kano.

Manajan Daraktan Bankin Masana’antun "Bank of Industry" (BOI), Dr. Olasupo Olusi, ne ya bayyana hakan yayin wani taron w...
03/05/2025

Manajan Daraktan Bankin Masana’antun "Bank of Industry" (BOI), Dr. Olasupo Olusi, ne ya bayyana hakan yayin wani taron wayar da kai dangane da shirin da aka gudanar a ranar Juma’a a jihar Kano.

Wakilinsa, Aminu Yusuf, wanda shi ne Manajan BOI na yanki Kano, ya bayyana cewa Jihar Kano kadai ta samu mutane 51,033 da s**a ci gajiyar shirin, inda aka raba musu fiye da Naira biliyan 12.54.

Ya ce an ware Naira biliyan 50 daga cikin kudaden tallafin domin taimakawa masu kananan sana’o’i guda miliyan daya, ciki har da Mata ‘yan kasuwa, masu gyaran tayoyi (Vulcanisers), masu sayar da abinci, masu sana'ar ɗinki (Teloli) da sauransu, da tallafin Naira 50,000 ga kowannensu cikin kananan hukumomi 774 a fadin Najeriya.

Olusi ya bayyana cewa wannan rabon kudaden wani bangare ne na Naira biliyan 200 da gwamnatin Bola Tinubu ta ware a matsayin tallafin Gwamnatin Tarayya don farfado da kananan masana’antu da kuma bunkasa bangaren kera kayayyaki a Najeriya.

Ya bayyana cewa shirin yana bayar da lamunin har zuwa Naira miliyan 5 da kaso 9 cikin dari na riba cikin shekara ɗaya, tare da wa’adin biyan kudin cikin shekaru uku ba tare da bukatar jinginan komai ba.

Haka kuma, ya jaddada cewa har yanzu akwai Naira biliyan 75 a karkashin shirin tallafawa Masana’antun "Manufacturing Sector Fund" (MSF), wanda aka ware domin magance matsalolin da masana’antun Najeriya ke fuskanta, k**ar hauhawar farashin kayayyaki, gibin ababen more rayuwa da kuma cikas a tsarin samar da kayayyaki.

A nasa bangaren, Bashir Jafa, Manajan hukumar raya kananan da matsakaitan Masana’antu ta Najeriya (SMEDAN) reshen Jihar Kano, ya ce hukumar na ci gaba da wayar da kan ‘yan kasuwa yadda za su amfana da tallafin da kuma lamunin.

NAN

Da yake jawabi ga manema labarai, kwamishinan yaɗa labarai na Jihar Kano "Comrade Ibrahim Abdullahi Waiya" ya gargadi Ab...
02/05/2025

Da yake jawabi ga manema labarai, kwamishinan yaɗa labarai na Jihar Kano "Comrade Ibrahim Abdullahi Waiya" ya gargadi Abdullahi Baffa Bichi kan s**ar Gwamnatin Jihar Kano da yake yi bayan an rufa masa asiri.

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Kano Dr Abdullahi Baffa Bichi, ya yi kakkausar s**a ga gwamnatin Abba Kabir Yusuf, inda...
02/05/2025

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Kano Dr Abdullahi Baffa Bichi, ya yi kakkausar s**a ga gwamnatin Abba Kabir Yusuf, inda ya zarge ta da yin almundahana da rashawa fiye da na gwamnatin da ta gabata.

A cikin wani faifan bidiyo, Bichi ya yi ikirarin cewa gwamnati mai ci ta tafka kurakurai fiye da lokacin tsohon Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, wanda a baya ake zarginsa da cin hanci da rashawa a tsawon mulkinsa na shekaru takwas, a cewar jaridar Dailytrust.

Bichi ya yi nuni da cewa gwamnatin ba za ta kai labari ba a zaben 2027, saboda korafin da ake yi kanta inda ya yi alkawarin fallasa aika-aikar da ake zargin gwamnatin da aikatawa.

Sarkın Kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero ya naɗa Alhaji Sunusi Ado Bayero a matsayin sabon Galadiman Kano, daga tsagin ...
02/05/2025

Sarkın Kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero ya naɗa Alhaji Sunusi Ado Bayero a matsayin sabon Galadiman Kano, daga tsagin masarautar Nasarawa.

Hukumar yaki da cin hanci da Rashawa da laifuffukan da s**a shafi hakan (ICPC), a ranar Alhamis, ta bayyana cewa daga ci...
01/05/2025

Hukumar yaki da cin hanci da Rashawa da laifuffukan da s**a shafi hakan (ICPC), a ranar Alhamis, ta bayyana cewa daga cikin Naira biliyan 100 da aka fitar don lamunin ɗalibai, sai dai Naira biliyan 28.8 kacal ne aka raba wa ɗalibai a makarantu daban-daban na gaba da sakandare.

Mai magana da yawun hukumar, Demola Bakare, ya shaida wa manema labarai a Abuja cewa an gayyaci manyan jami’ai, ciki har da Darakta-Janar na Ofishin Kasafin Kuɗi da Akanta Janar na Tarayya.

Bakare ya kuma bayyana cewa an gayyaci manyan jami’ai daga Babban Bankin Najeriya (CBN), da Shugaba da Darakta-Janar na Hukumar Lamunin Ilimi ta Najeriya (NELFUND) domin su kawo takardu da bayani kan lamarin.

Yayin da yake bayyana rabon kuɗin, Bakare ya ce binciken ICPC ya gano cewa adadin kuɗin da NELFUND ta karɓa zuwa ranar 19 ga Maris, 2024, ya kai Naira biliyan 203.8.

Rahoton rabon ya nuna cewa Naira biliyan 10 na daga Asusun Rabon Tarayya (FAAC), Naira biliyan 50 daga EFCC, Naira biliyan 71.9 daga TETFund, sannan wani karin Naira biliyan 71.9 daga TETFund.

ICPC ta bayyana cewa kudin da aka raba daga farko zuwa yanzu ya kai kimanin Naira biliyan 44.2, inda makarantu 299 s**a ci gajiyar shirin.

Ya zuwa yanzu, adadin kuɗin da aka raba wa makarantu 299 ya kai kimanin Naira biliyan 44.2, kuma ɗalibai 293,178 ne s**a ci gajiyar shirin.

Mahaukaciyar guguwa ta auka wa kudancin Isra'ila da birnin Jenin da ke Gaɓar Yammacin Kogin Jordan, lamarin da ya kawo t...
01/05/2025

Mahaukaciyar guguwa ta auka wa kudancin Isra'ila da birnin Jenin da ke Gaɓar Yammacin Kogin Jordan, lamarin da ya kawo tsaiko ga harkokin yau da kullum. Hakan na faruwa ne a yayin da wata wutar daji ta auka wa Birnin Ƙudus, abin da ya tilasta wa mutane fita daga gidajensu.

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when KMH posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share