DOKIN KARFE 24

DOKIN KARFE 24 GASKIYA DOKIN KARFE

An wallafa wani littafi domin girmama rayuwa da gagarumar gudunmawar Hon. Dr. Baffa Babba Dan Agundi, Darakta Janar na N...
18/06/2025

An wallafa wani littafi domin girmama rayuwa da gagarumar gudunmawar Hon. Dr. Baffa Babba Dan Agundi, Darakta Janar na National Productivity Center a Abuja.

Littafin ya kunshi tarihin rayuwar sa daga tushe – iyayensa, gwagwarmayar neman ilimi, ayyuka da mukaman da ya rike, da jagoranci ba tare da hayaniya ba.

Za a sanar da ranar kaddamar da littafin nan bada jimawa ba,

Sanarwa daga marubucin littafin:

Comr. Abdurrahman Hussain Abdurrahman (Professor) – Shugaban Daliban Mazabar Dan Agundi.

Musulunci ne addini mafi saurin karbuwa a Duniya — cewar wani sabon binciken cibiyar PewKarin bayani: https://shorturl.a...
13/06/2025

Musulunci ne addini mafi saurin karbuwa a Duniya — cewar wani sabon binciken cibiyar Pew

Karin bayani: https://shorturl.at/BRymi

Subhanalillah: Jarumi Abdurrazaq sultan ya kamu da rashin lafiya jim kadan bayan kammala aikin Hajjinsa a kasa me tsarki...
09/06/2025

Subhanalillah: Jarumi Abdurrazaq sultan ya kamu da rashin lafiya jim kadan bayan kammala aikin Hajjinsa a kasa me tsarki.

Muna fatan Allah ya tashi kafadunsa.

~Abdussamad Ishaq

Tsohuwar Kyaftin Din 'Yan Kwallo Mata Na Kasar Lebenon Dake Horar Da Matasan Maza Kwallon Kafa A Kano, Inda Take Tura Su...
09/06/2025

Tsohuwar Kyaftin Din 'Yan Kwallo Mata Na Kasar Lebenon Dake Horar Da Matasan Maza Kwallon Kafa A Kano, Inda Take Tura Su Kasashen Turai Da Na Larabawa

Wace fata za ku yi mata?

Ina tausayin Tinubu domin gwamnonin PDP 22 ne su ka marawa Jonathan baya amma ya fadi zaɓe a 2015 - NdumeSanatan Borno t...
09/06/2025

Ina tausayin Tinubu domin gwamnonin PDP 22 ne su ka marawa Jonathan baya amma ya fadi zaɓe a 2015 - Ndume

Sanatan Borno ta Kudu, Ali Ndume, ya nesanta kansa da jaddada goyon baya ga shugaba Bola Tinubu na neman wa'adi na biyu.

Sanatan, wanda ya shafe sama da shekaru 20 a majalisar dokokin kasar, ya kasance bako a shirin Siyasa na ran Lahadi a gidan Talabijin na Channels.

A cewarsa, tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya samu amincewar gwamnonin jam’iyyarsa ta PDP 22 a zaben 2015 duk da haka ya sha kaye a zaben a hannun Muhammadu Buhari na jam’iyyar APC.

Channels TV ta tuna cewa a ranar 22 ga Mayu, 2025, gwamnonin jam’iyyar APC 22 ne s**a amince da Tinubu a matsayin dan takarar jam’iyyar APC a zaben 2027 mai zuwa.

Ndume, jigo a jam’iyyar APC, ya ce bai goyi bayan matakin da gwamnonin APC s**a dauka ba, saboda “abubuwa sun yi muni matuka a kasar nan” a halin yanzu.

Ya koka da irin mawuyacin halin da tattalin arzikin kasar ke ciki, da tsadar rayuwa a kasar da kuma matsalar rashin tsaro da ke addabar sassan Najeriya," in ji shi

Subhanalillah: Adam a zango ya gamu da hatsari a hanyarsa ta zuwa kano daga kaduna.Hatsarin daya rutsa da Fitaccen jarum...
09/06/2025

Subhanalillah: Adam a zango ya gamu da hatsari a hanyarsa ta zuwa kano daga kaduna.

Hatsarin daya rutsa da Fitaccen jarumin da wasu abokan sana’arsa ya afku ne a kwanar dan Gora kafin maiyaki, daga nan alummar yakin s**ayi gaggawar kaishi wani asibiti dake garin Kwankwaso a Karamar hukumar Madobin jihar kano, daga nan ake sa ran wucewa dashi wani babban asibitin kamar yanda daya daga cikin yaransa da s**a gamu da hatsarin tare ya sanar dani a daren yau.

Ko dayake jarumin ya fito ya bayyana godiyarsa ga masoyansa a shafinsa na fesibuk bisa ga addu’o’in da suke masa.ll

Gwamnatin jihar Kano ta nemi gwamnatin tarayya ta biya diyya sakamakon soke bukukuwan hawan sallah da aka yi a jere tsaw...
08/06/2025

Gwamnatin jihar Kano ta nemi gwamnatin tarayya ta biya diyya sakamakon soke bukukuwan hawan sallah da aka yi a jere tsawon shekaru biyu.

Kwamishinan kananan hukumomi da masarautu na jihar, Alhaji Tajo Uthman, ne ya bayyana hakan a lokacin da Sarkin Kano, Alhaji Muhammadu Sanusi II, ya kai gaisuwar Sallah ga Gwamna Abba Kabir Yusuf a fadar gwamnatin jihar.



Uthman ya ce jihar ta yi asarar kudade masu yawa saboda dakatar da wannan biki na al’ada da ake gudanarwa a kowace shekara, wanda ke jan hankalin masu yawon bude ido na cikin gida da na kasashen waje.

```Mai Martaba Ya Tabbatarwa da Alan Waka Sarautar Dan Amanar Kano Allah Ya Kama```
08/06/2025

```Mai Martaba Ya Tabbatarwa da Alan Waka Sarautar Dan Amanar Kano Allah Ya Kama```

Hakiman Masarautar Kano Allah yaja zamanin Mai Martaba Sarkin Kano Alh Aminu Ado Bayero CFR CNOL JP 🤲✊
08/06/2025

Hakiman Masarautar Kano
Allah yaja zamanin Mai Martaba Sarkin Kano Alh Aminu Ado Bayero CFR CNOL JP 🤲✊

Sarkin Kano na 14 Mallam Muhammadu Sanusi Lamido Na ll tare da matar ɗan sa.
08/06/2025

Sarkin Kano na 14 Mallam Muhammadu Sanusi Lamido Na ll tare da matar ɗan sa.

Ko me Mataimakin Gwamnan Kano ke nufi da hakan?
08/06/2025

Ko me Mataimakin Gwamnan Kano ke nufi da hakan?

Shin ya dace uba ya gaisa hannu da hannu da matar ɗansa?
08/06/2025

Shin ya dace uba ya gaisa hannu da hannu da matar ɗansa?

Address

No 857 Sharada Qtrs
Kano

Telephone

+2348168122392

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when DOKIN KARFE 24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to DOKIN KARFE 24:

Share