Hantsi Leka Gidan Kowa

Hantsi Leka Gidan Kowa Labaran da s**a shafi tattalin arziki da siyasa da kuma zamantakewar yau da kullum, daga cikin gida Najeriya da kuma kasashen ketare, kasance da Hantsi....
(5)

Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano ta sanar da cewa an haramta duk wani shiri ko muhawarar mawakan addini idan ba a sa...
16/09/2025

Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano ta sanar da cewa an haramta duk wani shiri ko muhawarar mawakan addini idan ba a samu izinin hukumar ba.

Babban Sakataren Hukumar, Alhaji Abba El-Mustapha, ya bayyana cewa matakin na da nufin tabbatar da zaman lafiya, fahimtar juna da kuma bin doka tsakanin masu ruwa da tsaki a fagen addini da nishaɗi.

Hukumar ta ɗauki wannan mataki ne bayan wata muhawara da aka gudanar tsakanin Usman Maidubun Isa da Shehi Mai Tajul’izzi ba tare da izini ba, abin da ta bayyana a matsayin karya dokokin hukumar.

Don haka, an kafa kwamitin bincike ƙarƙashin jagorancin Daraktan Ayyuka na Musamman, Malam Isa Abdullahi, tare da baiwa mawakan biyu da masu shirya tattaunawar sa’o’i 24 su bayyana a gaban kwamitin.

Hukumar ta kuma jaddada cewa shirya irin waɗannan tarurruka ba tare da izini ba ya saba wa dokar tace finafinai ta jihar Kano, kuma na iya jawo ɗaukar matakin shari’a.

Alhaji Abba El-Mustapha ya nanata kudirin hukumar na ci gaba da sa ido da daidaita harkokin mawakan addini da masu nishaɗi, tare da roƙon jama’a da su ba da goyon baya domin tabbatar da zaman lafiya, ci gaban al’adu da fahimtar juna a jihar.

Yaya mukabalar ta kasance?Wa Ya fi hujjoji?
15/09/2025

Yaya mukabalar ta kasance?
Wa Ya fi hujjoji?

Kuna gani ya dace Najeriya ta yi irin wannan mataki wajen yaƙi da rashawa?A wani sabon salo, gwamnatin Albania ta naɗa w...
13/09/2025

Kuna gani ya dace Najeriya ta yi irin wannan mataki wajen yaƙi da rashawa?

A wani sabon salo, gwamnatin Albania ta naɗa wani AI bot mai suna Diella a matsayin Minista da zai rika kula da dukkan kwangilolin gwamnati.

Firaminista Edi Rama ya bayyana cewa Diella ba za ta taɓa karɓar rashawa ba, ba za a iya tsoratar da ita ba, kuma ba za ta nuna son zuciya ba.

A cewarsa, wannan mataki zai tabbatar da cewa duk kwangilolin gwamnati za su kasance cikin gaskiya da rikon amana.

Me kuke tunani?

Shin za a yarda da gwamnati ta mika ayyuka ga AI a Najeriya?

Marigayi Mahmud din Sumayya kenan, na cikin shirin Labarina na Aminu Saira.
12/09/2025

Marigayi Mahmud din Sumayya kenan, na cikin shirin Labarina na Aminu Saira.

Kwamishinan Ƙasa da Safayo na jihar, Abduljabbar Umar Garko, ya bayyana haka bayan taron majalisar zartarwa, inda ya ce ...
12/09/2025

Kwamishinan Ƙasa da Safayo na jihar, Abduljabbar Umar Garko, ya bayyana haka bayan taron majalisar zartarwa, inda ya ce matakin na cikin shirin gwamnati na inganta tsari da walwalar al’umma a Kano gaba ɗaya.

Wannan na nufin kasuwar za ta samu sabon wuri da tsari, tare da rage cunkoso da matsalolin da ake samu a Na’ibawa.

Shin kuna ganin wannan sauyin zai inganta harkar kasuwanci a Kano?

Kuma ya dace gwamnati ta ci gaba da sauya wuraren kasuwanni domin kawo tsari a birnin?

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya bayyana cewa gwamnatin sa ta amince da kudirin doka da zai baiwa kananan...
12/09/2025

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya bayyana cewa gwamnatin sa ta amince da kudirin doka da zai baiwa kananan hukumomi 44 na jihar cikakken 'yancin kai a fuskar kuɗi da gudanar da harkokinsu.

Bayanan sun fito ne a yayin zaman majalisar zartarwa ta 31 da aka gudanar a Gidan Gwamnati, Kwankwasiyya City, inda aka yanke shawarar tura kudirin ga majalisar dokokin jihar domin yin nazari da kuma tabbatar da shi.

A cewar Gwamnan, matakin zai baiwa kananan hukumomi damar gudanar da ayyukansu kai tsaye, su aiwatar da shirye-shirye cikin gaggawa, da kuma yanke hukunci bisa ga bukatun jama’a ba tare da tsangwama ba.

Gwamnan ya kara da cewa wannan sauyi zai tabbatar da gaskiya da riƙon amana, tare da hanzarta ci gaban al’umma da kuma zurfafa dimokuraɗiyya a Kano.

Wannan na kunshe ne a wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan Kano, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a safiyar Juma’a.

Gwamnatin Jihar Kano ta yi gargadin cewa za ta rufe duk wata makaranta mai zaman kanta da ta kara kuɗin makaranta ga ɗal...
11/09/2025

Gwamnatin Jihar Kano ta yi gargadin cewa za ta rufe duk wata makaranta mai zaman kanta da ta kara kuɗin makaranta ga ɗalibai ba tare da bin ƙa’ida ba.

Sakataren zartarwa na Hukumar Kula da Makarantu Masu Zaman Kansu da na Sakai a Kano, Kwamared Baba Abubakar Umar, ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai a ranar Alhamis.

Ya ce duk makarantar da aka samu da laifi ba kawai za a rufe ta ba, har ma za a gurfanar da ita a gaban kotu.

Kwamared Baba ya bayyana cewa matakin ya biyo bayan koke-koken da iyaye ke yi game da ƙarin kuɗin makaranta, tsadar littattafai da kayan makaranta da ake tilasta musu saya.

Ya ce hukumar za ta fara rufe makarantun da ke biyan malamai masu digiri ƙasa da naira dubu 20 a wata, da kuma waɗanda ke tilasta dalibai biyan kuɗin biki.

Kazalika, ya bukaci iyaye da su tabbatar da biyan kuɗin makarantar ’ya’yansu akan lokaci domin kauce wa tsaiko.

A wannan makon da aka koma makaranta, iyayen yara a Kano sun yi ta korafi kan ƙarin kuɗin makaranta da kuma tsadar littattafan da ake tursasawa a saya ba bisa ka’ida ba.

Daga Musbahu Bala Cediyar Yan Gurasa

Gwamnatin Jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf, ta kammala siyan gidaje 324 da ke Kwankwasiyya, ds Am...
11/09/2025

Gwamnatin Jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf, ta kammala siyan gidaje 324 da ke Kwankwasiyya, ds Amana da kuma Bandirawo daga hannun masu kula da kuɗaɗen fansho, inda aka mika su ga Hukumar Gidaje ta Jihar Kano (KSHC) domin gudanarwa da kuma sayarwa ga masu sha’awa.

An cimma wannan nasara bayan gwamnatin ta biya duk kuɗaɗen da s**a rage na fansho da aka jingina da gidajen, kimanin Naira Biliyan 4.5, ciki har da riba ta kashi 10% wato Naira Miliyan 450 ga masu kula da kuɗaɗen fansho.

Wannan mataki ya tabbatar da cewa an kare haƙƙin fansho na ma’aikata, tare da buɗe gidajen domin amfanin al’umma.

A yayin mika mulki, Manajan Darakta na Hukumar Gidaje, Alhaji Abdullahi Rabiu, ya bayyana cewa hukumar ta kuduri aniyar samar da gidaje masu inganci da kuma kula da su domin cika bukatun yawan jama’ar Kano da ke ƙaruwa da sauri.

Ya ce wannan ci gaban babbar alama ce ta canji a tsarin samar da gidaje a jihar.

A ganinku, shin wannan mataki zai rage matsalar rashin gidaje a Kano? Ko kuwa farashin sayarwar zai sa talakawa su kasa samun damar mallakar gidajen?

A ganin ku, wannan korar ta NNPP ga Abdulmumin Jibrin alheri ce gare shi ko kuma illa ce ga jam’iyyar?Ɗan majalisar waki...
07/09/2025

A ganin ku, wannan korar ta NNPP ga Abdulmumin Jibrin alheri ce gare shi ko kuma illa ce ga jam’iyyar?

Ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru/Bebeji, Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ya bayyana cewa ƙungiyarsa da jam’iyyar NNPP ta zo ƙarshe bayan sanarwar da jam’iyyar ta yi na cewa ta kore shi daga cikin mambobinta.

Jibrin ya ce korar ta zo masa da mamaki da takaici, inda ya bayyana cewa maganganun da ya yi a wata hira kwanan nan ba su kamata su zama dalilin irin wannan hukunci mai tsauri ba.

Ya kuma nuna cewa jam’iyyar ta ɗauki wannan mataki ba tare da ta ba shi damar kare kansa ba, abin da ya ce ya saba da tsarin adalci.

Duk da haka, ya bayyana cewa zai karɓi hukuncin cikin haƙuri, tare da yi wa jam’iyyar fatan alheri yayin da shi kuma zai ci gaba da nazari kan inda zai ɗora sabuwar tafiyarsa ta siyasa.

Jam’iyyar (NNPP) reshen jihar Kano ta sanar da korar ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazaɓar Kiru/Bebeji, Abdulmumin ...
06/09/2025

Jam’iyyar (NNPP) reshen jihar Kano ta sanar da korar ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazaɓar Kiru/Bebeji, Abdulmumin Jibrin Kofa.

Shugaban jam’iyyar a Kano, Hashim Sulaiman Dungurawa, ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da ’yan jarida a ranar Asabar.

Ya ce hukuncin korar ya biyo bayan zarge-zargen zagon ƙasa ga jam’iyyar da kuma rashin biyan kuɗin da ake buƙata a matsayin haƙƙin zama ɗan jam’iyya.

A cewarsa, Kofa ya saba dokokin jam’iyya ta hanyar fitowa a kafafen watsa labarai daban-daban yana s**ar jam’iyyar da shugabanninta, abin da ya sa aka ɗauki wannan mataki.

Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Kano ta gayyaci shugabar ƙaramar hukumar Tudunwada, Sa’adatu Salisu, bisa zargin jagorantar...
04/09/2025

Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Kano ta gayyaci shugabar ƙaramar hukumar Tudunwada, Sa’adatu Salisu, bisa zargin jagorantar ’yan daba wajen kai hari ga ma’aikatan wani kamfani a yankin.

Jaridar Daily Nigerian ta ruwaito cewa ma’aikatan kamfanin Tasarrufi General Enterprise sun kai ƙara hedikwatar ’yan sanda da ke Bompai, inda s**a zargi shugabar ƙaramar hukumar, wacce kuma ita ce shugabar ALGON ta Kano, da umartar ’yan daba da su kai musu hari da adduna tare da umartar ɗan sanda mai tsaronta ya buɗe musu wuta.

Kakakin rundunar ’yan sanda ta Kano, Abdullahi Kiyawa, ya tabbatar da cewa an fara bincike kan lamarin, kuma an aika da takardar gayyata ga duk masu ruwa da tsaki, ciki har da shugabar ƙaramar hukumar da abin ya shafa.

Kungiyar Bagwai First ta yi gargadi cewa akwai barazanar ambaliyar ruwa a garin Bagwai idan ba a kammala aikin hanyar da...
03/09/2025

Kungiyar Bagwai First ta yi gargadi cewa akwai barazanar ambaliyar ruwa a garin Bagwai idan ba a kammala aikin hanyar da ta kai tsawon kilomita biyar ba.

Kungiyar ta bayyana cewa aikin hanyar na da matuƙar muhimmanci wajen sauƙaƙa matsalar ambaliyar ruwa, kuma jinkiri wajen kammalawa zai iya jawo mummunar ambaliyar da ka iya shafar al’umma da dukiyoyinsu.

Kungiyar ta nemi gwamnatin jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf, da ta dauki matakan gaggawa domin kare rayuka da amfanin jama’ar yankin.

Address

Zoo Road
Kano
700101

Telephone

08076042952

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hantsi Leka Gidan Kowa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Hantsi Leka Gidan Kowa:

Share

Hantsi...

Kasance da jaridar Hantsi... domin samun sahihan labarai na gida Najeriya da kasashen waje cikin sauki...