
16/09/2025
Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano ta sanar da cewa an haramta duk wani shiri ko muhawarar mawakan addini idan ba a samu izinin hukumar ba.
Babban Sakataren Hukumar, Alhaji Abba El-Mustapha, ya bayyana cewa matakin na da nufin tabbatar da zaman lafiya, fahimtar juna da kuma bin doka tsakanin masu ruwa da tsaki a fagen addini da nishaɗi.
Hukumar ta ɗauki wannan mataki ne bayan wata muhawara da aka gudanar tsakanin Usman Maidubun Isa da Shehi Mai Tajul’izzi ba tare da izini ba, abin da ta bayyana a matsayin karya dokokin hukumar.
Don haka, an kafa kwamitin bincike ƙarƙashin jagorancin Daraktan Ayyuka na Musamman, Malam Isa Abdullahi, tare da baiwa mawakan biyu da masu shirya tattaunawar sa’o’i 24 su bayyana a gaban kwamitin.
Hukumar ta kuma jaddada cewa shirya irin waɗannan tarurruka ba tare da izini ba ya saba wa dokar tace finafinai ta jihar Kano, kuma na iya jawo ɗaukar matakin shari’a.
Alhaji Abba El-Mustapha ya nanata kudirin hukumar na ci gaba da sa ido da daidaita harkokin mawakan addini da masu nishaɗi, tare da roƙon jama’a da su ba da goyon baya domin tabbatar da zaman lafiya, ci gaban al’adu da fahimtar juna a jihar.