Hantsi Leka Gidan Kowa

Hantsi Leka Gidan Kowa Labaran da s**a shafi tattalin arziki da siyasa da kuma zamantakewar yau da kullum, daga cikin gida Najeriya da kuma kasashen ketare, kasance da Hantsi....
(5)

Wane irin tallafi gwamnati da al’umma za su iya bayarwa domin ganin matasanmu sun yi fice a irin wannan fage na duniya?G...
21/08/2025

Wane irin tallafi gwamnati da al’umma za su iya bayarwa domin ganin matasanmu sun yi fice a irin wannan fage na duniya?

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya karɓi bakuncin gwani Sanusi Bukhari Idris, wanda ya zama na uku a gasar Musabaqar Qur’ani ta duniya da aka gudanar a Masarautar Saudiyya.

A wata sanarwa da Kwamishinan Yaɗa Labarai na Kano, Kwamared Ibrahim Abdullahi Wayya, ya fitar ranar Litinin, ya bayyana cewa gwamna Yusuf ya taya matashin ɗan asalin Kano murnar samun wannan matsayi mai daraja a rukunin Qirā’āt da Tafsiri.

Sanarwar ta ce, wannan nasara ba kawai alfahari ce ga Sanusi Bukhari da iyalansa ba, har ila yau babban farin ciki ne ga Kano, Najeriya da al’ummar Musulmi gaba ɗaya.

Gwamnatin Kano ta bayyana cewa wannan gagarumar nasara ta sake ɗaga martabar jihar da ƙasar Najeriya a idon duniya, tare da tabbatar da kyakkyawan tarihi da Kano ke da shi wajen ilimin Qur’ani.

A ƙarshe, gwamnatin ta yi addu’ar Allah ya ci gaba da bai wa matashin ilimi mai amfani, ya kare shi kuma ya ɗaukaka matsayin sa wajen hidima ga addinin Musulunci da al’ummar Kano, musamman matasa.

A ganinku, me ya fi hana matasa aure a wannan lokaci: tsadar sadaki, ko kuma matsalolin tattalin arziki gaba ɗaya?Hukuma...
19/08/2025

A ganinku, me ya fi hana matasa aure a wannan lokaci: tsadar sadaki, ko kuma matsalolin tattalin arziki gaba ɗaya?

Hukumar shari’a ta jihar Kano ta karyata labaran da ke yawo cewa ta yanke hukunci kan kayyade sadakin aure a jihar zuwa Naira dubu Ashirin Mafi ƙaranci.

Shugaban hukumar, Malam Abbas Abubakar Daneji, ya bayyana wa manema labarai cewa abin da aka tattauna tare da hukumar Zakka da Hubusi, hukumar Hisba da sauran malamai shi ne sauƙaƙa al’amuran aure ga matasa, ba wai kayyade sadaki ba.

Ya ce shawara ce kawai hukumar ta bayar ba wai kayyadewa ba.

A cewarsa:

Ana ganin tsadar sadaki da buƙatun aure na hana matasa shiga aure.

Hukumar ta ba da shawara cewa sadaki zai iya zama Naira dubu 20 ko sama da haka gwargwadon yarjejeniya tsakanin iyaye da ma’aurata.

Wannan doka ce ta fahimtar juna, ba hukunci na tilas ba.

Shin za ku iya tuna dukkan kafafen sada zumunta da kuka yi amfani da su cikin shekaru biyar da s**a wuce?Ofishin jakadan...
18/08/2025

Shin za ku iya tuna dukkan kafafen sada zumunta da kuka yi amfani da su cikin shekaru biyar da s**a wuce?

Ofishin jakadancin Amurka a Najeriya ya fitar da sanarwa ga masu neman visa, inda ya umarce su da su bayyana dukkan sunayen social media da s**a yi amfani da su cikin shekaru biyar da s**a gabata.

Sanarwar, wadda aka wallafa a shafin X na ofishin jakadancin ranar Litinin, ta bayyana cewa wannan mataki ya biyo bayan tsauraran matakan tsaro da Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ta ɗauka domin ƙarfafa tsarin tantance masu neman visa.

Jakadancin ya ce dole ne masu neman visa su cika wannan bayanin a cikin fom ɗin DS-160, tare da samar da cikakken jerin sunayen shafukan sada zumunta da suke amfani da su.

Wane sakon taya murna kuke son aika wa ga Adam A. Zango da amaryarsa?Fitaccen jarumin Kannywood, Adam A. Zango, ya shiga...
17/08/2025

Wane sakon taya murna kuke son aika wa ga Adam A. Zango da amaryarsa?

Fitaccen jarumin Kannywood, Adam A. Zango, ya shiga sabon babi na rayuwa bayan ya ɗaura auren soyayya da amaryarsa Maimuna Musa wacce aka fi sani da Salamatu a shirin Garwashi.

Masoya da dama sun bayyana a shafukan sada zumunta cewa wannan aure ya zo da farin ciki, suna kuma addu’ar Allah ya albarkaci zaman su tare da zuri’a ta gari.

Shin kuna ganin akwai hujja mai ƙarfi da za ta sa INEC ta amince da wannan buƙata ta APC?Jam’iyyar APC ta nemi hukumar I...
17/08/2025

Shin kuna ganin akwai hujja mai ƙarfi da za ta sa INEC ta amince da wannan buƙata ta APC?

Jam’iyyar APC ta nemi hukumar INEC ta soke zaɓen cike gurbi da aka gudanar a Shanono/Bagwai da kuma Ghari a jihar Kano.

A cewar jam’iyyar, an samu rikice-rikice da tashin hankali a wuraren zaɓe, lamarin da ya tilasta masu kada ƙuri’a su gudu daga rumfunan zaɓe.

Kakakin jam’iyyar na ƙasa, Felix Morka, ya ce rahotanni sun tabbatar da cewa jami’an tsaro ba su iya shawo kan lamarin ba, wanda hakan ya haifar da barazana ga sahihancin zaɓen.

Zaben cike gurbi da aka gudanar a jihohin Ogun, Kaduna da Kano a ranar Asabar ya gamu da matsaloli na rikici, da siyan ƙ...
17/08/2025

Zaben cike gurbi da aka gudanar a jihohin Ogun, Kaduna da Kano a ranar Asabar ya gamu da matsaloli na rikici, da siyan ƙuri’u da kuma ƙarancin halartar masu jefa ƙuri’a.

A cewar hukumar INEC, sama da mutane miliyan 3 da dubu dari 5 ne s**a cancanci kada kuri’a a zaben, wanda ya gudana a kananan hukumomi 32, mazabu 356 da rumfunan zabe 6,987.

Sai dai a Kano, rundunar ‘yan sanda ta tabbatar da k**a matasa 288 dauke da mak**ai a wuraren zabe hudu da aka gudanar.

Wannan lamari ya sake tabbatar da matsalolin da ke ci gaba da hana sahihin zabe a Najeriya, wato rikici, da rashin tsoro, da rashin gaskiya da kuma siyasar kudi.

Shin me za mu iya yi a matsayin al'umma da hukumomi don ganin an samu gaskiya da adalci a zabe?

Rahotanni daga Bagwai, Jihar Kano sun tabbatar da cewa zaɓen cike-gurbi na gudana cikin kwanciyar hankali da lumana. Mas...
16/08/2025

Rahotanni daga Bagwai, Jihar Kano sun tabbatar da cewa zaɓen cike-gurbi na gudana cikin kwanciyar hankali da lumana.

Masu zaɓe na fitowa domin kada kuri'a k**ar yadda doka ta basu dama, ba tare da wata matsala ba a halin yanzu.

Yaya abin yake a mazabunku?

A kokarinsa na ci gaba da sauke nauyin da yake kan sa a madadin al’ummar Rano, Kibiya da Bunkure, RT Hon Kabiru Alhassan...
14/08/2025

A kokarinsa na ci gaba da sauke nauyin da yake kan sa a madadin al’ummar Rano, Kibiya da Bunkure, RT Hon Kabiru Alhassan Rurum (Turakin Rano) ya sake ɗaukar nauyin rukuni na uku da na huɗu na masu zuwa ƙasar mai tsarki don gudanar da ibadar Umra.

Bayan tura rukuni na farko da na biyu a baya, wannan sabon shirin ya haɗa da fitattun ‘yan siyasa, dattawa, da malamai daga yankin.

📍 Rukuni na 3:

1. Alh Auwalu Abdu Cm APC Rano

2. Alh Datti Rurum Cm NNPP Rano

3. Alh Rabi’u Halliru Gurjiya Cm APC Bunkure

4. Alh Nuhu Maigoro Cm APC Kibiya

5. Alh Usaini Sanda Kibiya Cm NNPP Kibiya

6. Albdulhadi Tarai Kibiya

7. Ibrahim Lawan Janare

8. Alh Taro Barkum

9. Alh Aminu Bala Gafan

10. Fatihu Yusuf Bichi

📍 Rukuni na 4:

1. DG Alh Alhassan Abubakar Kibiya

2. Alh Dauda Bala Mai Nama

3. Alh Hassan Ibrahim Minista

4. Alh Kabiru Chikago Rurum

5. Alaramma Mallam Gambo

6. Alh Rabi’u Bala Bunkure

Mazauna yankin sun yaba da wannan karamci, suna bayyana shi a matsayin wani muhimmin mataki na tallafa wa al’umma da inganta hadin kai.

Idan a yau za a yi zabe, wa za ka zaba daga cikin wadannan ukun, kuma me ya ja hankalinka zuwa gare shi?A sabon zaben ya...
14/08/2025

Idan a yau za a yi zabe, wa za ka zaba daga cikin wadannan ukun, kuma me ya ja hankalinka zuwa gare shi?

A sabon zaben yanar gizo da Jaridar Hantsi Leka Gidan Kowa ta gudanar tsakanin manyan ‘yan takara guda uku, Goodluck Jonathan (PDP), da Atiku Abubakar (ADC), da Bola Ahmed Tinubu (APC), sak**akon ya nuna cewa Jonathan ya yi nasara da kaso mafi yawa na kuri’un da aka kaɗa.

Kuri’u 1,210 ne aka jefa, amma ga yadda sak**akon ya kasasnce:

✅ Jonathan (PDP) – 631 kuri’u (52%)
✅ Atiku (ADC) – 427 kuri’u (35%)
✅ Tinubu (APC) – 152 kuri’u (12%)

Wannan sak**ako na nuna ra’ayin jama’a a wannan tattaunawar ta yanar gizo, ba wai sak**akon zabe na hukuma ba.

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu zai bar Abuja a gobe Alhamis, 14 ga Agusta, domin ziyarar aiki zuwa ƙasashen Japan da Br...
13/08/2025

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu zai bar Abuja a gobe Alhamis, 14 ga Agusta, domin ziyarar aiki zuwa ƙasashen Japan da Brazil.

A hanyarsa, zai tsaya a Dubai, Hadaddiyar Daular Larabawa, kafin ya isa Japan.

A Japan, Shugaban zai halarci Taron Ci gaban Afirka karo na tara na Tokyo (TICAD9) wanda zai gudana a birnin Yokohama daga 20 zuwa 22 ga watan Agusta.

Bayan kammala taron TICAD9, Shugaba Tinubu zai wuce zuwa Brasilia, babban birnin Ƙasar Brazil, domin ziyarar aiki ta kwanaki biyu daga Lahadi, 24 ga Agusta zuwa Litinin, 25 ga Agusta.

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Bichi a Jihar Kano, Abubakar Kabir Bichi, ya bayyana cewa za a gina sabon t**...
13/08/2025

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Bichi a Jihar Kano, Abubakar Kabir Bichi, ya bayyana cewa za a gina sabon t**i mai hannu biyu daga Bichi zuwa Bagwai, Shanono har zuwa Gwarzo, karkashin kulawar Ma’aikatar Ayyuka ta Kasa.

Hon. Bichi ya ce wannan muhimmin aiki zai taimaka wajen saukaka sufuri, bunkasa kasuwanci, da kara hadin kai tsakanin al’ummomin yankunan.

Shin kuna ganin Majalisar ta dauki matakin da ya dace?Majalisar Dokokin Jihar Kano ta dakatar da Shugaban Karamar Hukuma...
13/08/2025

Shin kuna ganin Majalisar ta dauki matakin da ya dace?

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta dakatar da Shugaban Karamar Hukumar Rano, Naziru Ya’u, na tsawon watanni uku.

Wata majiya daga Majalisar ta shaida cewa har yanzu ana cigaba da tattaunawa kan matakin da za a dauka a gaba.

An dauki matakin dakatarwar ne bisa zargin cewa shugaban ya sayar da tsohuwar kasuwar Rano, tare da karkatar da takin zamani da Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya rabawa kananan hukumomi a watan Yuli.

Rahoton ya nuna cewa kowacce karamar hukuma ta samu tirela uku na taki (buhu 600 kowacce mota), wanda ake zargin ya shiga hannu ba bisa ka’ida ba.

Address

Zoo Road
Kano
700101

Telephone

08076042952

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hantsi Leka Gidan Kowa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Hantsi Leka Gidan Kowa:

Share

Category

Hantsi...

Kasance da jaridar Hantsi... domin samun sahihan labarai na gida Najeriya da kasashen waje cikin sauki...