Darasi cikin Hikima

Darasi cikin Hikima Assalamu alaikum this is MUNASS Tv

24/05/2026

Falalar Yanka Ranar Sallah
'azi

Shin jama'a a halin da ake ciki a yanzu wane ne daga cikinsu ya fi cancanta da Najeriya?
10/05/2026

Shin jama'a a halin da ake ciki a yanzu wane ne daga cikinsu ya fi cancanta da Najeriya?

Jam'iyyar APC ta ce babu bukatar sake tantance Shugaba Bola Tinubu domin tsayawa takara.
07/05/2026

Jam'iyyar APC ta ce babu bukatar sake tantance Shugaba Bola Tinubu domin tsayawa takara.

Tsohon shugaban majalisar dokoki Cavayé Yeguié Djibril ya rasu yana da shekaru 86 a duniya. Mutumin da ake yi wa kallon ...
07/05/2026

Tsohon shugaban majalisar dokoki Cavayé Yeguié Djibril ya rasu yana da shekaru 86 a duniya. Mutumin da ake yi wa kallon na k*t da k*t da Paul Biya ya jagoranci majalisar dokokin Kamaru har tsawon shekaru 34, kafin daga bisani a maye gurbinsa.

Shugaba Tinubu ya tallata Najeriya ga masu zuba hannun jari na duniya a Faransa, inda ya ce da su cewar yana gudanar da ...
06/05/2026

Shugaba Tinubu ya tallata Najeriya ga masu zuba hannun jari na duniya a Faransa, inda ya ce da su cewar yana gudanar da sauye-sauye inganta tattalin arziki don dawo da aminci a tsaknin Najeriya da masu hannu da shuni.

Shugaban Chadi Mahamat Idriss Deby ya yi alkawarin kawo karshen 'yan ta'adda, bayan da wani harin mayakan Boko Haram ya ...
06/05/2026

Shugaban Chadi Mahamat Idriss Deby ya yi alkawarin kawo karshen 'yan ta'adda, bayan da wani harin mayakan Boko Haram ya yi ajalin sojojin kasar da dama a sansanin Barka Tolorom da ke gabar Tafkin Chadi.

bas Araghchi ya yi wata ganawa da takwaransa na kasar China Wang Yi a birnin Beijing.China wadda babbar kawar Iran ce ta...
06/05/2026

bas Araghchi ya yi wata ganawa da takwaransa na kasar China Wang Yi a birnin Beijing.

China wadda babbar kawar Iran ce tana yin biris da takunkuman da Amurka ta kakaba, ta hanyar ci gaba da shigo da danyen mai daga Iran zuwa matatunta.

Tafiyar Mista Araghchi na zuwa ne gabanin ziyarar da shugaba Trump zai kai China a mako mai zuwa, inda zai gana da shugaba Xi Jinping.

Mista Trump ya jinkirta ziyarar tasa ne bayan da gwamnatinsa da Isra'ila s**a kai wa Iran hari a karshen watan Fabrairu.

Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Kashe Dala Biliyan 3 Don Yin Jirgin Kasa A Kano Da Kaduna Da Legas​Gwamnatin Tarayya kark...
06/05/2026

Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Kashe Dala Biliyan 3 Don Yin Jirgin Kasa A Kano Da Kaduna Da Legas

​Gwamnatin Tarayya karkashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ta amince da bayar da kwangilar gina manyan ayyukan layin dogo guda uku a biranen Kano da Kaduna da kuma Legas, domin bunkasa tattalin arziki da saukaka zirga-zirga.

​Ministan Kudi da Tattalin Arziki, Taiwo Oyedele ne ya sanar da hakan ga manema labarai a fadar Shugaban Kasa da ke Abuja, jim kadan bayan kammala taron Majalisar Zartarwa ta Kasa (FEC) da aka gudanar ranar Alhamis.

​Ministan ya bayyana cewa an zabo wadannan biranen ne saboda matsayinsu na cibiyoyin kasuwanci da s**a dogara da kansu, inda ya ce zuba jari a cikinsu zai haifar da sakamako mai kyau ga rayuwar talakawa.

​Ayyukan da aka amince da su sun hada da:

​Birnin Kano: Za a gina layin jirgin kasa na cikin gari (Kano Metro City Rail) wanda zai rika daukar mutane zuwa sassan birnin.

​Birnin Kaduna: Za a samar da tsarin jirgin kasa na "Light Rail" (wanda Gwamna Uba Sani ya nuna godiyarsa a kai a safiyar yau).

​Birnin Legas: Za a fara aikin layin jirgin kasa na "Green Line" (Phase 1A).

​Oyedele ya bayyana cewa wadannan ayyuka guda uku za su ci kimanin dala biliyan 2.99 (kusan Naira tiriliyan hudu da rabi).

​Ya kara da cewa za a samar da kudaden ne ta hanyar kamfanin hannun jari na Ma'aikatar Kudin Kasa (MOFI), tare da hadin gwiwar wasu hukumomin bayar da tallafi na musamman.

​"Mun sani cewa babu ci gaba ba tare da ingantattun hanyoyi da sufuri ba. Wadannan ayyukan an tsara su ne don bunkasa kasuwanci, saukaka wa ma’aikata da dalibai zirga-zirga, da kuma kyautata rayuwar jama’a a wadannan manyan biranen," in ji Ministan.

​Wannan mataki na zuwa ne a matsayin wani bangare na shirin Shugaba Tinubu na tabbatar da cewa an farfado da bangaren sufuri domin rage tsadar rayuwa da kuma samar da ayyukan yi ga matasa a fadin kasar nan.

​Masana tattalin arziki na ganin cewa idan aka kammala wadannan ayyukan, birnin Kano da Kaduna za su zama manyan cibiyoyin sufuri a Arewacin Najeriya, wanda hakan zai rage cinkoson ababen hawa da kuma saukaka jigilar kayan amfanin gona.

A wani faifan bidiyo da ya bazu a shafukan sada zumunta, an ji Oshiomhole na kira ga gwamnati da ta tsaurara matakan kas...
06/05/2026

A wani faifan bidiyo da ya bazu a shafukan sada zumunta, an ji Oshiomhole na kira ga gwamnati da ta tsaurara matakan kasuwanci kan kamfanonin Afirka ta Kudu da ke aiki a Najeriya.

Ya ce matakin zai zama wata hanya ta nuna rashin jin daɗi kan yadda ake cin zarafin ‘yan Najeriya a ƙasar, musamman a batun ayyukan yi.

Oshiomhole ya ƙara da cewa ɗaukar irin waɗannan matakai na iya tilasta wa shugabannin Afirka ta Kudu neman sulhu, tare da sanya su fahimci darajar ‘yan Najeriya.

Tarihi ya sake maimaita kansa a fagen siyasar Jihar Kano! Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya ba...
06/05/2026

Tarihi ya sake maimaita kansa a fagen siyasar Jihar Kano! Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya ba kowa mamaki inda ya fito fili ya kira Muhammadu Sanusi II a matsayin ainihin Sarkin Kano kuma Shugaban Majalisar Sarakunan Jihar.

Wannan lamari ya faru ne a Gidan Gwamnatin Jihar Kano a yayin taron rantsar da sabon mataimakin gwamna, Murtala Sule Garo. Yayin da Ganduje ke gabatar da jawabi, ya ambaci sunan Sarki Sanusi tare da girmamawa.

Nan take mahalarta taron s**a kaure da tafi, suna nuna jin daɗinsu ganin yadda Ganduje ya gaishe da Sarkin tare da tabbatar da matsayinsa a bainar jama'a.

Idan ba a manta ba, a shekarar 2020 ne dai Ganduje ya sauke Sarki Sanusi daga kan karagar mulki, kafin daga bisani Gwamna Abba Kabir Yusuf ya dawo da shi kan kujerarsa bayan lashe zaɓen da ya gabata. Wannan ne karon farko da Ganduje ya amince da sarautar tasa tun bayan wannan takaddamar!

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Darasi cikin Hikima posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share