Arewa Daily News

Arewa Daily News Domin Labarai da Nishaɗi.

A siyasa, adalci shi ne ginshiƙin zaman lafiya, kuma gaskiya ita ce tubalin amincewar jama'a da kowace jam'iyya. A yau m...
05/08/2026

A siyasa, adalci shi ne ginshiƙin zaman lafiya, kuma gaskiya ita ce tubalin amincewar jama'a da kowace jam'iyya. A yau muna kira ga shugabannin jam'iyyar ADC na ƙasa da su tsaya tsayin daka wajen kare mutuncin tsarin da s**a kafa, domin tarihin jam'iyya yana ginuwa ne a kan gaskiya da adalci, ba son rai ko tasirin wasu ba.

His Excellency Shuaibu Idris Miƙati ya shiga wannan fafatawa bisa ƙa'ida, kuma kwamitin ɗaukaka ƙara (Appeal Committee) da jam'iyyar ta kafa ya tabbatar da sahihancin zaɓen da ya ba shi nasara. Wannan ya ƙara tabbatar da cewa an bi doka da ƙa'ida wajen gudanar da aikin da aka ɗora wa kwamitin.

Saboda haka, muna roƙon shugabannin jam'iyyar ADC na ƙasa da su mutunta rahoton kwamitin nasu, domin hakan zai ƙara ɗaukaka martabar jam'iyyar a idanun 'ya'yanta da sauran al'umma. Adalcin da aka yi shi ne ke haifar da haɗin kai da kwanciyar hankali a cikin jam'iyya.

Idan kuma, saɓanin abin da kwamitin ya tabbatar, aka ayyana wani daban a matsayin wanda ya yi nasara ba tare da hujja mai ƙarfi ba, to hakan zai zama abin takaici matuƙa. Duk da haka, za mu bi duk hanyoyin da doka ta tanada cikin lumana da mutunci wajen neman haƙƙinmu.

Mun yi imani cewa akwai kotuna da ke tabbatar da adalci, amma sama da komai akwai Kotun Ubangiji, wadda ba ta yin kuskure, ba ta karɓar son zuciya, kuma babu mai kuɓuta daga hukuncinta. Wannan shi ne abin da ke ƙarfafa zukatan masu gaskiya.

Allah Ya sa shugabannin ADC na ƙasa su yanke hukunci bisa gaskiya da adalci, domin nasarar jam'iyya ba ta ta'allaka ga wanda ya fi ƙarfi ba, sai dai ga wanda ya fi gaskiya. Adalci shi ne abin da ke gina jam'iyya, kuma zalunci shi ne abin da ke rusa ta.

Saƙon Comrd Muneer Abdullahi Yusuf
05/08/2027

KAJI KO:  Masoyin Kashim Shattima yayi tattaki don nuna goyon bayansa daga Birnin Sokoto.‎‎Fitaccen matashi Muhammad M. ...
20/07/2026

KAJI KO: Masoyin Kashim Shattima yayi tattaki don nuna goyon bayansa daga Birnin Sokoto.

‎Fitaccen matashi Muhammad M. Shehu, Masoyin Tinubu da Kashim, Yayi tattaki daga Birnin Sokoto, har Zuwa Birnin Tarayya Abuja. Don nuna goyon bayansa ga Tikitin Tinubu da Kashim Shattima karo na Biyu.

‎A cewar Matashi Muhammad M Shehu, Ya zabi yayi wannan tattaki ne don nuna cikakken goyon bayansa ga Kashim da Tinubu, hakazalika ya rike kyauta ta musamman da yake bukatar bawa Kashim Hannu da hannu a matsayin girmamawa ga Al'ummar jihar Sokoto

Alboom Hausa TV

14/07/2026
18/06/2026

Isah Ashiru kudan ya daina kiran kansa ɗan takarar gwamnan jihar Kaduna a ƙarƙashin jam'iyyar ADC - Comrd Imrana Mansur

Address

Kano
420241

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Daily News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share