24/10/2025
MAI HASKE NE A CIKIN DUNIYAR ALHERI
Na rayu da mutane iri daban-daban tun daga yarinta zuwa girma na— na hadu da masu hali iri-iri: masu kirki, masu tausayi, da masu son kai. Amma gaskiya, ban taɓa ganin irin Abdul Amart Maikwashewa ba.
Mutum ne da zuciyarsa ta ginu a kan adalci, halacci, taimako, da kyakkyawar niyya.
A hulɗarsa da mutane, gaskiya da adalci su ne ginshiƙansa.
Yana kallon kowa da idon mutunci, yana yanke hukunci bisa gaskiya, ba tare da son rai ba.
A rayuwarsa, kirki, kyauta, da taimako sun zama al’ada.
Yana haɗa zumunci, yana gina abokantaka, kuma yana yafe wa waɗanda s**a saɓa masa domin zuciyarsa ta fahimci cewa yafiya tana kawo natsuwa.
Tausayin na ƙasa da shi ya zama abin alfahari.
A dalilinsa, wasu sun samu muhalli, wasu sun samu abin hawa, wasu sun yi aure da kwanciyar hankali.
Akwai kuma waɗanda Allah Ya basu waraka daga rashin lafiya ta dalilin taimakon sa.
Iyalai da dama da s**a rasa mafaka, yau suna cikin farin ciki da murmushi saboda kulawarsa da gudunmawarsa.
Allah Madaukaki ya yi bushara da irin waɗannan mutane a cikin Al-Kur’ani mai girma, inda Ya ce:
> “Wa man ya‘mal mithqāla dharratin khayran yarah.”
(“Duk wanda ya aikata koda ƙwayar zarra ta alheri, to zai gan ta.”)
— Suratul Zalzala: 7
Haka kuma Allah Ya ce:
“Inna alladhīna āmanū wa ‘amilus-sālihāti innā lā nuḍī‘u ajra man aḥsana ‘amala.”
(“Lalle waɗanda s**a yi imani s**a aikata ayyukan ƙwarai, ba za Mu ɓata lada ga wanda ya aikata alheri ba.”)
— Suratul Kahf: 30
Wannan shi ne Abdul Amart Maikwashewa — mutum mai imani, tausayi, hangen nesa, da adalci.
Halinsa ya zama darasi ga matasa, abin koyi ga shugabanni, kuma haske ga al’umma baki ɗaya.
A gaskiya, tsohon abokina ne, amma saboda irin kyawawan halayensa, tausayi, da kulawa da yake nuna wa mutane — yanzu ya zama ɗan uwa a zuciyata.
Allah Ya ƙara maka lafiya, natsuwa, da albarka a dukkan al’amuranka.
Allah Ya saka maka da alkhairi a duniya da lahira.
Barka da Juma’a — Allah Ya amshi ibadunmu, Ya sanya mu cikin waɗanda ake yi musu rahama a yau.