Littattafan yaki by Habibullah kbr

  • Home
  • Littattafan yaki by Habibullah kbr

Littattafan yaki by Habibullah kbr Domin Littattafan Hausa musamman na yaki domin littattafan yaki na hausa

23/04/2025

Babbar shela ga sababbin manyan masoyana! Shuaibu Yunusa, Mustapha Umar, Sulaiman A Mhd, Abdulmaleek Abdullahe Idress, Hamisu Abdu, Farida Said, Uthman Umar, Musa Umar Musa

WOHOHO !!!Jama'a Wannan Shine SARKI BALUNZAR DAN KURSADU MAI MULKIN BIRNIN LAHARIS.Sadauki Uban SadaukaiGagara badau Uba...
19/03/2025

WOHOHO !!!
Jama'a Wannan Shine SARKI BALUNZAR DAN KURSADU MAI MULKIN BIRNIN LAHARIS.

Sadauki Uban Sadaukai
Gagara badau Uban Gagararru
Ma'aboci Takubba Guda Biyu
Takobin Kulaibil
Takobin Luwaisar .

Minene SARKI BALUNZAR Yafi Burgeku Dashi Fans ?

✍️Admin Yusuf Imam Bashir Jega.

09/02/2025

GAWURTACCEN SARKI
***
CHAPTER 81*Hatsabibi Ya kaima Hatsabibi Ziyara* 2
**
✍️✍️✍️Marubuci: YUSUF IMAM BASHIR JEGA Y*I*B*J
***
*Gargadi*: Idan Kasan Bazaka iya Yin Like Da comment Da Sharhi ba, Pls Kada Kakarantamin Littafi.

***
~ My Whatsapp Number : 09036940004
***
*Ina Godiya Ga Wadanda Suke Karanta Wannan Litafin Gaskiya Kuna Sakani Cikin Farin Ciki allah Yabarmu Tare*.
***
*Kada K**anta Da Sharhi,
Don't Forget With Sharhi*
***
*Masha Allah Dayan Account Dina Yadawo Dan Allah Amin Addu,a Saura Daya*
***
Aljanin Yakaraso Daf Da Aljani Hubbus Dake Daukeda Dan Fashi Jurgus.

Aljannun Biyu S**a Tsaya Cak, Juna Kusa Da Juna, Sarki Ashram Da Kansa Yasauko Daga Kan Aljaninsa Yahawo Aljani Hubbus S**a Rungume Juna Tareda Yin Musabaha.

Kai Daga Gani Kasan An Dade Ba,a Haduba. Aljani Hubbus Yakarisa Dasu Daidai Tsakiyar Birnin Burshal Inda Nanne Fadar Sarki Ashram Take.

Yayo Kasa Luuu Daidai Bakin Kofar Fadar, Sarki Ashram Da Dan Fashi Jurgus S**a Sauka Daga Saman Aljani Hubbus.

Bakin Kofar Fadar Wasu Dakaru Ne Guda Uku Masu Shigar Ban Tsoro. Suna Rufe Da Fuskokinsu Da Jikinsu Gaba Daya.

Babu Abinda Kake Gani Har Da Idanuwansu Kuwa, Sannan Suna Rike Da Takubba Madaukaka Guda Uku Uku Ga kowane Badakare.

Suna Ganin Sarki Ashram Da Dan Fashi Jurgus, S**a Zube Kasa S**a Kwashi Gaisuwa Garesu.

Sannan S**a Budemusu Kofar Fadar, Sarki Ashram Da Jurgus S**a Shige Fadar Kai Tsaye.

Fadar Ta Kasance Gawurtacciyar Hadaddiya Wadda Tsayawa Siffantamuku Kyawunta Da Kawatuwarta Da Fasalinta Sai Littafi Mai Shafi Dubu Hudu Da Rabi Shima A Takaice.

Amma Dai Ko A Yanzu Kasan Ankashe Kudi Masu Tarin Yawa Yayin Ginata Domin Ko Abinda Akayi Tubalin Gininta Dashi Abin Kallone.

Sarku Ashram Yaja Dan Fashi Jurgus S**a Je Saman KARAGAR MULKI nsa S**a Zauna Su Biyu A Tare.

Sarki Ashram Yakasance Shirgegin Katone Mai Girman Jiki Da Girman Sawaye, Surar Jikinsa Kadai Kallonta Abin Tsorone .

Jikinsa Mummurde Yake Tamkar Wanda Aka Cuccure Wuri Guda. Yanada Faffadan Kirji Wanda Ko Kwarya Aka Ajiye Zata Iya Zama.

Gashin Kansa Bakine Wulik Babu Ko Digon Wata Kala ACiki, Sannan Yanada Wani Mugun Kyalli Kai Kace Mai Ne Aka Shafamata.

Sarki Ashram Yatafa Hannuwansa Sau Uku, Wata Kuyanga Ta Shigo Dauke Da Kwandon Kayan Marmari .

Sannan Ta Fice Daga Fadar, Sarki Ashram Yayima Dan Fashi Jurgus Bismilla.

Saida S**a Kimtsa Cikinsu, Sannan Sarkin Yam Fashin Jurgus Yadafa Wani Hatimi Dake A Hannunsa, Hauzul Da Basrul S**a Bayyana Suna Masu Kwasar Gaisuwa Garesu.

Dan Fashi Jurgus Yadubesu Yace :
Nasan Zuwa Yanzu Yarima Jarwazu Yasan Nakawo Ziyara A Birninnan Na Burshal, Zai Iya Yin Mugun Tunanin Gangancin Cewa Zai Biyoni Nan Yak**ani Domin Yakaini Ga Sarkin Matsafan Duniya Na Dajin Zalzal, Mai Gidan Su Shubairu Da Muzairu

"Amma Nasan Rashin Sani Ne Ke Dawainiya Da Jarwazu, Baisan Banbanci Tsakanin EMSAHIR 1 Da EMSAHIR 2 ba, Ina Son Ku Bada Tsaro Na Musamman A Sararin Samaniya Na Wannan Birnin Kamin Mugama Ganawa Da MAI GIDAN HATSABIBAI ASHRAM!!!.

Hadimi Hauzul Da Hadimi Basrul S**a Jinjina Kai alamun Bin Umarni Sannan S**a Bace Bat ! Daga Fadar .

Dan Fashi Jurgus Ya Mayarda Kallonsa Ga Sarki Ashram Wanda Ya Kashe Kunnensa Yana Sauraron Abinda Jurgus Yace :
Ina Muka Kwana Danganeda Burinmu ?, Nidai Ta Gefena Komi Daidai Yake, Kaifa Mai Gida ?.

Sarki Ashram Ya Kashema Dan Fashi Jurgus Idanu, Cikin Sigar Dariya Ya Maimata 'Mai Gida' Yace: Jugus Bakada Daraja, Waye Ni A Duniya Da Zanzamo Mai Gidan Sarkin Hatsabiban Duniya Jugus, Eye ? Rufamin Asiiri Aboki.

Jugus Ya Harari Ashram Yace ,
Dalla Can Matsoracin Banza, Babu Mai Muhawarar Kaine MAI GIDAN HATSABIBAI, Idanni Ni Hatsabibine To Kai Mai Gidana Ne.

Ashram Yayi Murmushi Yace
Yaudai Iskanci KenN Kazo Kamin Jurgus, To !, Maganar Gaskiya Shine Nima Ina Nan ina Gudanarda Ayukana Daidai Bisa Tsari domin Cikin Guda Takwas Na Nemo Uku, Kaga Kuma Har Yanzu A Kwai Sauran Lokaci.

Dan Fashi Jurgus Yace, Kutumelesi!!! Ashe Ni Ina Can Ina Wasa Kaikuma Kayita Yin Naka,Nidai Na Nemo Biyu Saura Shida, Da Sarkar Zinare Wadda Na Amso Wurin Sarauniya Lubaina Matar Sarki Kulhum Na Birnin Hirtoliya, Sai Kuma Kambun Tsafi Daga Hannun Shugaba Fallaru, Saura Suma Zanyisu Nan Bada Jimawa Ba.

Sarki Ashram Ya Jinjina Kai Alamun Fahimta, Dan Fashi Jurgus Yaci Gaba Da Cewa: Na Biyu: wai Ya Maganar Gimbiya Lushbaira ne ?, Inane Bok Junudul-Jandul Ya Boyeta ?.

Sarki Ashram Ya Kurba Wani Shayi Dake Gabansu Yace, Gimbiya Lushbaira, Nayi Cikakken Bincike A Kanta, Amma Bari Na Takaitamaka Shi :👇👇👇
Gimbiya Lushbaira Diyar Wani Talakan Mutum ne Mai Suna Fairazul-Hausul, Fairazul-Hausul Bayada kudi Sannan Baya Da Koda Rufin Asiri Ne.

Abinci Ga Yini Wuya Yake Masa Koda Ci Guda Ne, Yanada Matar aure Guda Daya Tal Wadda Tarasu Wurin Haihuwa.

Inda Ta Haifomasa Wata Santaleliyar Jaririya,Fairazul-Hausul Bakin Ciki Da Farin Ciki S**a Ziyarceshi A Lokaci Guda.

Ga Bakin Cikin Mutuwar Matarsa Abar Begensa Mai Debemasa Kewa, Sannan Ga Farin Cikin Haihuwar Jaririya Wadda Saida Yayi Mutuwar Tsaye Lokacinda Yayi Arba Da Fuskarta.

Saboda Wani Kyawu Ya Gani, Wanda Ko A Labari Baitaba Ganiba, Saboda Tsananin Kyawunta Duk Wanda Yazo Ganin Diya Suma Yakeyi Saboda Dimaucewar Ganin Kyawun Diyar.

Kamin Kace-me Labari Yabazu A Birnin Nasu Da Kauyuka Akan Ga Jaririyar Da Ba,a taba Ganin Mai Kyawunta Koda Rabinsama A Duniya ba.

Bisa Dole A Ranar Suna Ana Gama Bikin Haihuwa Domin Jama,ar Duniya Kowa Sai Kyaututtuka Yake Kawoma Fairazul-Hausul Domin Kamun Kafa Akan Neman Auren Jaririyar idan Ta Girma.

Wasu Sarakuna Ko Attajirai Sai Nemawa Diyansu Ajiyar Auren Jaririyar Suke.

Aiko Cikin Kwana Bakwai Da Haihuwar Jaririyar, Fairazul-Hausul Yakoma Gawurtaccen Attajiri Mai Yawan Dukiya Da Rangamomi A Fadin Duniya.

Ranar Sunan Jaririya Anyi Suna Mai Cike Da Watsin Dukiya Da Bama Talakawa Abinci .

Kowane Sarki Saida Yahalarto Wannan Bikin Tareda Dansa Yarima Mai Jiran Gadon Sarauta, Wanda Akeson Ya auri Jaririyar.

Yarinya Taci Sunan Mahaifiyarta Saboda Tunawa Da Ita Wato Lushbaira, Tun A Taron Bikin Sunan Jama,a S**a Radamata Suna Mai Daraja Wato GIMBIYA LUSHBAIRA Aka Karamata Da Lakabin Gimbiya Tamkar Takasancs Yar Wani Basarake.

Akwai Wani Gawurtaccen Matsafin Boka Wanda duniya Ke Tsoro Mai Suna Boka Junudul-Jandul Wanda idan Yayimaka Abu Saidai Kace ALLAH YA ISA.

Tun Lokacinda Lushbaira Matar Attajiri Fairazul-Hausul Ta Haifi Gimbiya Lushbaira Yake Bibiyar Jaririyar, Yasaka Mummunan Nufi A Kanta.

Saida Gimbiya Lushbaira Tayi Shekara Shida A Duniya, Kyawunta Yakara Bayyana Ga Fili, Masu Nemanta S**a Kara Dimaucewa Akanta Sosai Da Sosai.

Sai Boka Junudul-Jandul Yazo Da Daddare Yasaceta Yatafi Da Ita Halarar Tsafinsa Domin Ya Aiwatarda Mummunan Nufinsa A Kanta.

Lokacinda Attajiri Fairazul-Hausul Yatashi Da Safe Yaga Baiga Diyarsa ba Wadda Kullum Da Safe Sai Tazo Gaisheshi Amma Har Karfe Goma Na Rana Cur Bai Gantaba.

Sai Hankalinsa Yadunguzuma Ainun Yabaza Dakaru Neman Bidarta Da Fatake Amma Babuta Babu Labarinta Har Birane Da Kauyuka Kuwa Kai Ko Wanda Yagantama Basu Ganiba.

Sai Yarufe Kansa A Daki Yana Kuka,
Idan Yatuna Da Yarasa Matarsa Da Yarsa Wadda Yake Kallo Ya Mance Da Matarsa, Sai Kukansa Yatsananta.

Kuyanginsa Da Barorinsa Idan S**ayi Yunkurin Futowa Dashi Daga Dakin, Sai Suga Yarufe Ko,ina Ruf!, Sautin Kukansa Kawai Akeji A Gidan.

Al,amarin Boka Junudul-Jandul Kuwa,Lokacinda Yakebe Da Gimbiya Lushbaira Domin Yayimata Fyade Wadda Har Yasumar da ita.

Har Yakwabe Tufafinsa Domin Ya Aikata Nufinsa, Yasaka Hannunsa Domin Yacirema Gimbiya Lushbaira Kayan Jikinta, Yaga Wata Wuta Garwashi Uku Manya Manya Sun Gifta Ta Saman Hannunsa.

Saboda Mahaukacin Zafin Garwasan Wutar, Saida Boka Junudul-Jandul Yakwarara Ihu Wanda Yahaifarda Girgizar Halarar Tsafinsa .

Idanun Boka Junudul-Jandul idan Kakallesu Kasan A Tsorace Take, Tun Daga Haihuwar Boka Junudul-Jandul Har Kawo Zuwa Yanzu Baitaba Ihu Ba A Rayuwarsa.

Balantasa Aga Yaji Tsoron Abu Ba Sai Yau, Tabbas Bala,in Kwarai Boka Junudul-Jandul Yajiya.

Saboda Haka Ya Kurama Gimbiya Lushbaira idanu Yana Mamakinta, Sai Kawai Yazago Madubin Tsafinsa Yadafeshi Da Hannun Hagu Yafara Karanto Wasu Dalisman Tsafi.

Saida Madubin Yayi Haske Sannan Bokan Yasaita Madubin Daidai Fuskar Gimbiya Lushbaira Domin Yasamu Bincike Kan Hatsabibancinta.

Kawai Madubin Tsafin Yayi Bindiga Yatarwatse Yabi iska, A Karo Na Biyu Boka Junudul-Jandul Yaja Baya Atsorace Kuma A Tsananin Mamaki .

Kawai Sai Yazaro Takobinsa Yadaka Tsalle Da Nufin Saran Gimbiya Lushbaira Yarabata Gida Biyu.

Kawai Sai Yaga Hannunsa Na Dama Dake Rike Da Takobin Yaguntule Yafadi Kasa, Jini Ya Fara Malala Daga Hannun Bokan.

A Karo Na Biyu Yakwarara ihun Azaba Wanda Saida Wani Bangare Na Halarar Tsafin Yashige Cikin Kasa.

Ran Boka Junudul-Jandul Yabace, Zuciyarsa Ta K**a Harzuka Tamkar Zata Faso Ta Futo, Idanunsa S**a Kada S**ayi Jawur Yabude Muryarsa Mai K**ada Kukan Jaki Yace, Na Rantse Gemun Kakana Saina Hana Wannan Yarinyar Da Mahaifinta Da Masoyanta Sai Nakaita Inda Babu Wanda Ya,isa Yaganeta Har Abada, Sannan Tunda Har Tasakani Abin Kunya, Takuma Karyamin Alkadarina, Kuma Na Kasa Saduwa Da ita To Har Abada Babu Wanda Yasadu Ita Bazata Taba Aure Ba.

In Takaicemaka Saida Boka Junudul-Jandul Ya Aikata Alwashinsa Kuwa, Yaje Yaboyeta inda Duniya Ta Kasa Sanin Inane.

Sannan Yasamu Nasarar Bata Wasu Ruwan Guba A Matsayin Ruwan , Domin Ta Farfado Tacemasa Tanason Ruwa , Tana Shansu Gubar Taje Ta Bata Mata Sha,awa.

A Yanzu Boka Junudul-Jandul Yashekara Goma Da Yin Mutuwar Kaskanci.

Ranar Da Yaboye Gimbiya Lushbaira Tare Da Bata Guba Tasha, A Ranar Yaga Kawai Hancinsa Yafarke Jini Yafara Zubowa Tamkar Fanfo, Sanann Bakinsa Yafarke Da Jini Tamkar Ambaliya.

Sannan Shedarsa Ta Sarke Yayi Mutuwar Tsaye A Kaskance, A Halin Yanzu Gimbiya Lushbaira Tana A DAJIN MARLAD A Kogon SAULADU A Daure Cikin Kogon.

Dan Fashi Jurgus Yayi Ajiyar Zuciya Tareda Jinjina Mugun Zalunci Irin Na Wannan Bokan.

Yaso Ace Yataso Yatarar da Bokan Yana Raye Da Sai Yayimasa Mummunan Hukunci, Saboda Yaraba "Ya Da Ubanta Da Kuma Masoyanta.

Yanzu Tsawon Shekara Goma Tabbas Wannan Zaluncine Dole Yaceci Gimbiya Lushbaira Daga Wannan Kangin Wahala.
***
Gawurtaccen Sarki Littafin Yaki
Pls Follow This Page For More Book If War.

Assalamu Alaikum Fans.Yau Insha Allah Wannan Littafin Gawurtaccen Sarki Littafin Yaki Zai Zomuku Yau Insha Allah.Chapter...
09/02/2025

Assalamu Alaikum Fans.
Yau Insha Allah Wannan Littafin Gawurtaccen Sarki Littafin Yaki Zai Zomuku Yau Insha Allah.

Chapter 81.

📱Admin 002 Yusuf Imam Bashir Jega.

MUN TSAYA WANNAN LITTAFIN A WANNAN PAGE A CHAPTER 80.Kuna Bukatar Mu Cigaba Da Kawomuku Shi Ko Kuma Mu Kawomuku Wani Lit...
23/01/2025

MUN TSAYA WANNAN LITTAFIN A WANNAN PAGE A CHAPTER 80.
Kuna Bukatar Mu Cigaba Da Kawomuku Shi Ko Kuma Mu Kawomuku Wani Littafin.
*
Daga Admin Yusuf Imam Bashir Jega
Ma'aboci Page din Gawurtaccen Sarki Littafin Yaki.

23/01/2025

Big shout-out to my newest top fans! Shuaibu Yunusa, Sulaiman A Mhd, Hamisu Abdu, Farida Said, Uthman Umar, Musa Umar Musa, Mustapha Umar

15/01/2025

SAIFUL LAIHAN 7 PART B

LBR

HABIBULLAH KBR

A wannan karo sai komai ya canja fasali saboda yadda ya dinga ragargazarsu Babu kakkautawa

Kuma daga inda yake baya matsawa wani wajen kawai Yana amfani da motsin Dake gilmawa a tsakanin bishiyun Dake gurin wajen Kai farmakin nasa tare da kare duk wani hari da suke kawo masa
Wanda hakan ya bashi damar Yi musu gagarumar barna
Don haka koda s**aga yadda yakeyi musu irin wannan barna take suma s**a canja salon fadan nasu
S**a fara karyo dogayen rassa daga jikin bishiyun suna yi masa rubdugu daga nesa
Hakan ne yasa s**a fara samun galaba akansa ta hanyar Yin wasa da hankalinsa
S**a dinga Yi masa rubdugu na duka ta inda baya tsammani
Aikuwa suma cikin lokaci kankani s**a fara Tara masa jini ajikinsa
Don dole shima ya canja salon fadansa ta hanyar tsalle tsalle a kan
wadannan bishiyu k**ar yadda wadannan birrai suke Yi Kuma Yana hadawa da bin sautin duk inda yajiyo motsinsu Yana rafkewa daya bayan daya
Kai kace shima ya kasance Dan biri
Kuma a hakan kawai da sautin da kunnuwansa suke jiyo masa
yake amfani bada idanunsa ba
Saboda gogewarsa a fannin farauta da sanin sirrikan daji saboda haka cikin kankanin lokaci ya sami damar gamawa da wadannan birrai
Ya Daina jiyo motsin koda guda daya daga cikinsu

Face kadawar ganyayen jikin bishiyun sak**akon iskar Dake ratsawa ta tsakankaninsu

Take ya kwance kyallen daya rufe fuskarsa dashi sannan ya karyi wani itace daga jikin wadannan bishiyu ya kunna wuta a Samansa
Ya fara Neman inda lardisa take acikin wannan daji sai daya Bata lokaci Mai tsawo Yana yawon nemanta a wannan daji ba tare da yaga duriyarta ba

Don haka ya fara kwalla mata kira da dukkan muryarsa ko zaiji sautin tata muryar Amma duk hakan ya zama na banza
Domin baiji wani sauti ba face na muryarsa wacce ke amsa amo acikin dajin
Don haka take ya yanke hukuncin Hawa Saman wadannan bishiyu domin duba ta da kansa

Koda yin wannan nazari ba tareda wani dogon tunani ba ya dinga k**a wadannan bishiyu Yana Hawa
Sai da yayi doguwar tafiya sannan ya cika da mamaki

Ba Komai ne ya sanya shi wannan mamaki ba face Ganin wani matsakaicin gari da wadannan birrai s**a Gina a Saman wadannan bishiyu domin kuwa harda dakuna da sauran abubuwan more rayuwa da wadannan birrai s**a kirkira domin gudanar da rayuwarsu

Amma Kuma garin a wannan lokaci tsit yake Babu motsin wani Abu Mai Rai acikinsa
Atsakiyar garin ne yayi arba da lardisa a daure jikin dirkar itace wacce aka ajiye a gurin

Gaba dayanta An daure tane da wasu manyan jijiyoyin bishiya
Wanda saboda wahalar data Sha a gurinsu tuni ta fita daga hayyacinta ta sume

Haka Nan Gaba daya kayan jikinta a yage suke da alama badon Rukyan ya tarwatsa suba suna Shirin dawowa wannan guri ne su keta mata haddi

Cikin sauri gami da rawar jiki Rukyan yasa takobinsa ya tsinke wadannan jijiyoyi
Sannan ya cire rigar jikinsa ya sanya ajikinta cikin sauri ya zaro battar ruwansa domin ya yayyafa mata a fuskar ta domin farfado da ita Amma sai yaji battar tasa Babu koda digon ruwa acikinta

Don haka hankalinsa Gaba daya ya dugunzuma ya fara tunanin hanyar daya k**ata yabi
Yana cikin wannan tunani ne kawai dabara ta Fado masa a zuciyar sa
Take ya sunkuya ya Dora bakinsa akan nata tareda hura mata iska da karfi acikin nata bakin
Yin hakan keda wuya take tayi atishawa da karfi tareda Jan dogon numfashi
A hankali idanunta s**a bude tayi arba da Rukyan a sunkuye a saitin fuskarta
Koda idanunta s**a Kai kan tufafin jikinta take zuciyar ta ta buga ta Dan ja baya kadan cikin rashin yarda tace dashi .
Mai ka aikata agareni ?
Kar kayi tunanin tarayyata da Kai Zata baka damar aikata mummunan aiki agareni

Kodajin wannan Batu cikin sanyin murya yace mata
Kardai har yanzu Babu aminci a tsakanin mu?
Banyi tunanin Zaki taba zargata da irin wannan mummunar dabi'a ba
Saidai duk da haka inaso ki sani badon nayi da gaske ba
Da tuni wadannan birrai sun sami damar aiwatar da mugun nufi akanki ta hanyar tozarta miki 'yan matancin ki

Don haka yanzu saiki kwantar da hankalinki Kuma ki dukufa wajen sawa raunin jikinki magani
Nima Kuma zanyiwa kaina saidai idan Ina bukatar taimako zan tambayeki
Haka kema idan kina bukata Zaki iya nemana

Yana gama fadin haka sai ya koma gefe daya tareda gyara zamansa Yana Mai sanyawa jikinsa magani
Akan raunikan da yaji yayin da yake fada da wadannan birrai
Haka itama lardisa ta zauna gefe tareda bada himma wajen sanyawa nata raunikan magani akansu

Tana cikin sanya maganin ne kawai ta fada dogon tunani akan rayuwarta ta baya
Tun daga kuruciyarta yadda ta taso agidan sarauta karkashin renon mahaifinta Wanda ke mulkin birnin sin a wannan lokaci wato sarki Ruziyal cikin kulawa da dukkan wani gata data samu daga gareshi

Zuwa Lokacin da ciwon barin jiki ya k**a mahaifiyarta
A Lokacin shekarunta ba zasu haura takwas ba aduniya
Wanda hakan ya janyo hatta shashin kwakwalwarta Saida ya tabu Bata iya Gane kowa Dake tare da ita
Daga Lokacin Kuma Bata iya Kara magana da kowa ba kullum saidai a kwantar da ita a tayar
Abinci ma sai dai adura mata shi a Baki

Lamarin daya matukar tayar da hankalin sarki Ruziyal kenan da lardisa
S**a shiga cikin matukar damuwa akan hanyar da zasu Nemo mata maganin wannan ciwo nata
Saida aka Tara Gaba daya masu magungunan birnin sin da sauran nahiyoyin Dake makobtaka dasu s**a jarraba duk wasu dabaru nasu Amma s**a kasa Gano irin wannan ciwo

Daya bayan daya s**a dinga sulalewa suna guduwa saboda yadda s**a razana da lamarin wannan ciwo

Yayinda sarki Ruziyal ya fuskanci wadannan masu magani ba zasu iya wani aiki ba a kan wannan ciwo
Sai ya baza masu shela acikin duniya domin suyi shela
Cewar Yana gayyatar duk wani boka da yake da ilimin magunguna a fadar sa

Sannan duk Wanda ya sami nasara acikin aikin da aka umarceshi zai sami sak**akon dukiya Mai tarin yawa
Gami da bayi da kuyangi.
Cikin kankanin lokaci wannan cigiya ta karade ko Ina a sassan duniya inda manyan bokaye a wannan lokaci s**a dinga hallara a birnin sin

Saboda haka cikin abinda hai haura mako guda ba birnin ya cika da da manyan matsafa da masu magani
Inda dukkansu aka basu mazauni acikin fadar birnin
A ranar da s**a gama hallara acikin fadar ne sarki Ruziyal ya nufo fadar ruke da gimbiya lardisa a hannunsa wacce tun a wannan lokaci ta kasance Yarinya Mai son dadadan labarai da Kuma ganin abubuwan al'ajabi
Wadanda s**a kunshi labaran sarauta,jarumta ,tsafe tare Kuma da soyayya,Kuma wani abin al'ajabi a tattare d ita shine duk labarin data saurara take kwakwalwarta take haddacewa k**ar anyi rubutu ajikin dutse

Lokacin da sarki Ruziyal da lardisa s**a shigo cikin wannan fadar sai kowa Dake gurin yayi shiru tare da mayarda hankalinsu
Zuwa kan kofar da s**a shigo alokacin da wasu fadawa s**a rako bayansu suna busa wata sarewa Mai ratsa zuciya
Basu Daina busa wannan sarewa ba sai bayan sarki Ruziyal ya sami guri ya zauna haka itama lardisa ta zauna akan kujerar Dake kusa da tasa

Bayan sun Dan shafe wasu dakiku ba tareda wani yace uffan ba
Anan ne sarki Ruziyal ya katse shirun Dake tsakaninsu da cewa
Yaku wadannan manyan bokaye masu ilimi akan fannin cututtuka daban daban daga sassan duniya

A yau ni da Kaina Ruziyal inayi muku barka da isowa birnin sin cikin koshin lafiya

Kafin na sanar daku aikin da zakuyi min zan fara tunatar daku ladan aikin da zan bayar ga duk Wanda ya sami nasara acikin ku

Zan bashi ladan rabin Dukiyar Dana Tara sannan zan bashi
mulkin babban birni acikin biranen Dake karkashin wannan masarauta ta birnin sin
Tareda tarin zakwakuran dakarun yaki,gami da bayi da Kuma kuyangi masu tarin yawa

Don haka inaso ku karfafi zuciyar ku da nasara har sai kun samo mana mafita akan wannan lamari

Yana gama fadin haka sai ya Kalli wasu dakaru Dake bayansa tareda Yi musu inkiya

Nan take mutum biyu daga cikinsu s**a shige cikin gidan sarautar basu fito bayan dakiku masu yawa

S**a fito dauke da gimbiya yazarina kwance akan gado cikin mawuyacin hali k**a wacce ta shafe shekara tana famabda wannan ciwo

Bayan karasowar dakarun ne s**a ajiye karagar tata a tsakiyar wannan fadar
Sarki Ruziyal yace yaku wadannan bokaye ku sani matata ta kamu da wannan matsanancin ciwon barin jiki ne Lokaci guda alokacin da take tsaka da gudanar da ran gadin ta acikin wannan masarauta

Babu yadda likitoci basuyi ba domin magance wannan lalura Amma Abu ya gagaresu wannan daliline yasa na kirawo ku

Yanzu Kuma sai Ku fara gudanar da aikin Dake gabanku

Nan da Nan kuwa wadannan bokaye s**a dukufa akan wannan aiki da aka umarce su

Kowa ya shiga gwada tasa bajinta da Kuma baiwar da yake da ita ta hanyar tsatsubar magani Amma sai Abu ya gagara s**a kasa samo hanyar da zasu magance wannan cuta
Koda s**a matsa acikin bincike sai s**aji k**ar ana dora musu manyan duwatsu ajikinsu
Har sai da dukkansu s**a baje a kasa suna zanga haki tare da gumi ,idanunsu kuwa s**a kada
saboda tsabar azabar da s**aji ajikinsu Saida s**a tabbatar idan har s**a tsananta wannan bincike tofa dolene dukkansu su mutu a wannan guri

Don dole s**a dakata da wannan aiki s**a fara kallon junansu aka rasa Wanda zai iya fadawa sarki Ruziyal abinda ke faruwa saboda tsananin kunyar kasa samun nasara
Inda shi da lardisa kuwa s**a kura musu idanu suna sauraron amsar da zasu basu bayar

Suna cikin wannan hali ne kawai aka jiyo sautin haniniyar doki ya nufo cikin fadar
Dauke da wani mutum tsoho tukuf akansa Wanda shekarunsa sun haura Dari da doriya
Wanda Gaba daya jikinsa Babu bakin gashi ko guda daya
Sannan kana kallonsa kasan a matukar yunwace yace

Koda wadannan dakaru s**ayi arba da wannan doki take Gaba dayansu s**ayi rubdugu kansa s**a Hana wannan doki karasowa cikin fadar
Shi kuwa ya tsaya a gaban fadar Yana tutsu gami da haniniya domin don ganin ya ratsa ta cikin dakarun

Amma koda yaga ya kasa samun wannan dama take ya daga kafafunsa na Gaba sama yayi jifa da wannan mahayi Dake bayansa
Har Saida kansa ya gwaru ajikin bango sannan wannan doki gudu daga wannan guri ya shige cikin gari

Nan take wannan tsohon ya fara magana cikin sanyin murya Yana rokon wani daga cikin dakarun da ya bashi ruwan da zaisha kafin AJALI ya riske shi

Su kuwa wadannan dakaru Gaba dayansu s**a kewaye shi suna masu jiran yayi wani motsi domin su afka masa
Sannan aka rasa Wanda zai bashi koda ruwa makurwa daya daga cikinsu
Nan take sarki Ruziyal yaga lardisa ta sauka daga kan wannan kujera da take zaune
Ta Shuri wani kofin zinare Dake gabanta Wanda Babu Komai acikinsa sai tataccen ruwan inibi
Ta ruga da gudu
zuwa inda wannan tsohon mahayin doki yake kwance gadan gadan
Kafin wani daga cikin dakarun yayi yunkurin dakatar da ita tuni isa gurin da wannan mahayi yake
Tana isa inda yake sai ta sunkuya ta dura masa wannan ruwan inibi acikin bakinsa

Duk wannan Abu Dake faruwa tsakanin wannan mahayi da Kuma dakaru sarki Ruziyal Yana kallo daga kan karagarsa

Don haka koda yaga wannan Abu da lardisa ta aikata a wannan lokaci sai yaji ya Kara kamuwa da kaunarta saboda yadda ta nuna tausayawa ga wannan mahayi amatsayinta na karamar yarinya

Bayan wannan mahayi ya gama shanye wannan ruwan inibi kawai sai ya daga hannunsa na dama ya shafa gashin kan lardisa
Har dakaru sun yunkura zasu far masa sai kawai s**aji hannayen nasu sun ruke sun kasa motsasu

Nan take wannan mahayi ya rikede ya koma siffar wani tsohon matsafi Wanda duk cikin matsafan Dake cikin wannan fadar Babu Mai yawan shekarunsa
Hannunsa na ruke da wani kwagiri na tsafi Wanda yake dogarawa dashi
Gaba daya jikin wannan boka cike yake da guraye na tsafe
Su kansu bokayen da suke cikin wannan fadar Saida s**a juyo da kallonsu zuwa bakin wannan kofa

Bayan wannan bakon boka ya mike tsaye sai kawai ya k**a hannun lardisa Yana Mai dogarawa da wannan sanda wacce ke ruke a hannunsa
Jikinsa kuwa Yana rawa ya jata s**a shiga cikin wannan fadar
Shigarsu keda wuya sai ya rissina tareda mika gaisuwa ga sarki Ruziyal
Sannan yace yakai wannan sarki Mai girman Mulki a wannan nahiya
Ina rokonka gafara abisa rashin halartar wannan taro akan lokaci da banyi ba
Ina Mai tabbatar maka da cewa ni boka maksasul zaljas Ina tafe da duk wani bayani Dan Gane da wannan hali da matarka take ciki da Kuma abinda zai zamo sanadin warakarta
DUK da cewa wannan lamari ba Mai sauki bane.

Yayinda boka maksasul zaljas yazo Nan a zancensa sai sarki Ruziyal ya dubeshi cikin murna yace yakai wannan boka Ina rokonka daka gaggauta sanar Dani wannan hanya da kake da tabbacin samun lafiyar matata
Idan kuwa har kayi haka yanzu take zan cika alkawarin Dana dauka akan duk Wanda ya taimaka min !!!
Dajin wannan Batu sai wannan boka ya bushe da dariya wacce ta baiwa kowa mamaki daga bisani Kuma ya tsuke bakinsa ga barin dariyar yace

Yakai wannan sarki zanyi maka wannan aiki ne ba don dukiyar daka alkawarta min ba

Domin kuwa a halin yanzu na Tara dukiyar da bansan adadinta
Wadanda inda ace za'a tattara ta guri guda sai an cika manyan rijiyoyi masu zurfin Gaba dubu

Kuma na adana su aguri Mafi tsaro Wanda Babu Wanda ya San inda suke a halin yanzu face ni
Saboda haka yanzu Babu wani sarki daya Tara dukiya Mai yawan wacce na Tara a fadin duniya

Don haka a wannan shekaru nawa bana bukatar dukiya ko Kuma daukaka
Abin da nake bukata kawai shine girmamawa tareda tausayawar duk Wanda zanyiwa aiki

DUK mutumin da zanyiwa aiki Ina jarraba karfin tausayinsa ne ga talakawan Da yake tare dasu

Saboda haka yanzu zan sanar dakai komai dangane da matarka albarkacin tausayin da lardisa ta juna a gareni

Yakai Ruziyal inaso ka sani wannan ciwo daya sami matarka ba zai taba warkewaba koda kuwa za'a Tara Gaba daya matsafan duniya su dukufa akanta

Idan baka mantaba magabata sun bayyana cewa aduk Lokacin da SAIFUL LAIHAN Ta tashi bayyana wani al'amari yakan faru Wanda yake hada dukkan matsafan duniya aguri daya

K**ar yadda ya hada Farhan,boka,Hulbaz, Nauwaratul Hasnal, husnaila,safran da kuma mufran guri guda wato birnin misra domin daukar lasmira

To k**ar hakace ta Kara faruwa a wannan Karni Kuma akan matarka
Tunda gashi an hada duk wasu matsafa domin samo mata magani Amma hakan ya gagara
Abu dayane kawai zai magance mata wannan cuta

WANNAN Abu kuwa ba komai bane face sihirin Dake jikin saiful LAIHAN

In baka mantaba kafin shudewar Farhan ya samar da wasu matakan kariya ga SAIFUL LAIHAN
Wanda hakan ya Hana kowa kusantar inda suke domin wanzuwar zaman lafiya acikin duniyoyin da muke dasu

To bisa wasu alamu da bincike na ya nuna min na cewa SAIFUL LAIHAN tana daf da sake bayyana kanta acikin duniya
Silar wasu bakin mutane daga nahiyoyi daban daban da zasu bazama cikin duniya don daukar SAIFUL LAIHAN din daga ma'ajiyar da Farhan ya boye ta
Sanin kankune dubunnan rayuka sun mutu a kan wannan tafarki musamman ma tsohuwar masarautar Dake kusa da wannan birni wato DARUL MAUT
Badon komai Farhan ya tsananta musu tsaro ba a wancan zamanin face don sanin cewa Babu Wanda ya cancanci mallakar su aduk karnikan da s**a shude
To Amma fa yanzu lokaci ya canja SAIFUL LAIHAN ba Zata cigaba da zama a boye ba
Nan da wasu 'yan shekaru Zata Kara bayyana saidai Babu Wanda yasan hannun Wanda Zata Kara fadawa tsakanin hannun kirki ko Kuma Wanda ba'a bukata
Kuma idan har ta fada mugun to Ina tabbatar maka dacewa a ranar zaiyi amfani da sihirin da suke tattare da KARAGAR AJALI wajen rushe duk manyan daulolin Dake Doron kasa acikin harda wannan birni Wanda ya zama mahaifar SADAUKI FARHAN DA Tarihi ba zai taba mantawa dashi ba

Don haka idan har kana son ceton wannan birni da Kuma rayuwar matarka
Dolene kaima ka wakilta 'yarka lardisa ta shiga duniya don haduwa da daya daga cikin masu neman SAIFUL LAIHAN din

Wanda Ina da tabbacin Zata hadu dashi ne acikin daya daga cikin dajujjukan Dake kewaye da wannan birni
Saidai Kuma koda ta hadu dashi din akwai wata Bakar kaddara da Zata dinga bibiyarsu har zuwa sanda zasu Kai inda SAIFUL LAIHAN take

Koda boka maksasul zaljas yazo Nan a zancensa sai hankali kowa Dake wannan fadar ya dugunzuma s**a k**a kallon junansu
Kai da Ganin yanayin da s**a kasance a wannan hali kasan sun razana dajin wannan bayani nasa
Guri ya yamutse da kace nace dinsu kowa na fadin abindake cikin bakinsa

Kaf cikinsu Babu Wanda yafi kowa shiga cikin tashin hankali k**ar sarki Ruziyal Amma ko kadan Bai nuna damuwarsa a fili ba

Don haka ya Kara duban bokan a karo na biyu yace yakai wannan boka Mai abun al'ajabi

Mai zai Hana a cire wannan kankanuwar yarinya acikin wannan lamari Mai girma
ni da Kaina zan shiga sahun masu Neman wannan karagar k**ar yadda kakanni na s**ayi koda kuwa zan rasa rayuwata akan wannan tafarkin

Domin lardisa yarinyace karama ba Zata iya wannan aiki ba

Kodajin wannan Batu sai bokan ya Kara bushewa da dariya a karo ba biyu bayan yayi dariyar ta isheshi sai ya tsuke bakinsa tareda cewa

Kwarai kuwa maganar ka gaskiya ce saidai wani Lokacin hakkin da mutum ya raina shine yake yin abin da Bai taba zato ba

Saidai fa a wannan karo Ina tabbatar ma lardisa zatayi abinda kaima a tarihin samartakarka baka Yi ba
Domin Kai yanzu shekarunka sunja don haka ba zaka iya chakuduwa da wadannan mutane ba
Saboda tun suna kanana s**a fara bincike da shirye shiryen zuwa inda SAIFUL LAIHAN take

Don haka ita kuwa lardisa Zata hadu dasu ne a Lokacin da suke tsaka da wannan aiki a Sannan ta gama mallakar hankalin kanta

Kuma Nima saboda abin alherin da tayi a gareni zanyi mata kyautar da ban taba yiwa wani ba
Domin kuwa zanyi mata kyauta ne da abinda ya zamto rayuwata

Wanda hakan itama zai taimaka mata wajen tattara baiwar da take da ita rubuta duk wasu abubuwan tarihi da s**a wanzu a wannan duniyar

Tunda yanzu ne take da ganiyar kuruciyarta Kuma su mata suna da wata baiwa ta musamman fiye da wacce Namiji yake da ita

Saboda haka Ina tabbatar maka Zata sadu dasu Kuma har su isa duniyar hallaka

DUK wannan Abu Dake wakana tsakanin sarki Ruziyal da boka maksasul jaljas
Kowa Dake wannan guri yanaji Kuma Yana sauraro don haka sai gurin yayi tsit Babu sautin komai hatta numfashi ma kadan ake shakarsa don Kar ya haifar da sautin da zai Hanasu Jin wannan tattaunwa Dake gudana

A wannan lokaci ne wannan boka ya dauki lardisa ya mayar da ita kan kujerar da take zaune
Kawai sai ya runtse idanunsa Yana Mai karanta wasu kalmomin tsafi
Yin hakan keda wuya take dardumar haske ta Shure shi tareda daga shi sama daidai fuskar lardisa

Ba tankwashe kafafunsa Yana fuskantar daidai fuskar ta Yana Mai wangame bakinsa tareda furta wasu sirrikan tsafi masu karfi
Harsaidai sautin muryar tasa ya karade fadar Gaba daya tareda iska wacce ta dinga jijiiya kofofi da tagogin Dake jikin fadar

Ana cikin wannan yanayi ne kawai s**a hango wani dunkulen haske Mai k**a da kwan kaza ya ratso ta cikin bakin wannan boka ya shiga cikin bakin lardisa

Faruwar hakan keda wuya jikin boka maksasul jaljas ya dau wani irin sanyi Kai kace Wanda aka tsamo daga cikin kogin kankara
Fatar jikinsa kuwa ta sauya launi zuwa fari fat tamkar jini Bai taba gudana acikinta ba

Take iskar da take ruke dashi ta sake shi ya fado kasa Yana burgima wata farar dafara na fita daga cikin bakinsa

Da ganin haka sai sarki Ruziyal ya dakawa likitocin Dake kula da matarsa tsawa kan su ceto rayuwar wannan boka
Har sun yunkura zasu koma gareshi kawai sai ya dakatar dasu da hannunsa Yana Mai cewa
Ai ilimin ku ba zai taba tasiri akaina ba domin haka ka'idar sihirina yake .
A ranar Dana rabu dashi to a ranar zan mutu saboda haka Ina Mai shawartarka daka baiwa lardisa dukkan gudunmawar daya k**ata ka Bata na daga horon yakin da Zata iya kare kanta dashi cikin abinda ba zai haura shekara guda ba

A wannan lokaci ne zatayi bankwana da wannan gari ta shiga duniya don tattara duk wasu tsofaffin labarai na tarihin magabata
Bincike na ya tabbatar min acikin wannan tafiyar ne Zata hadu da daya daga cikin mutanen da take Nema

Saidai fa dukkansu zasu fuskanci kalubale Mai yawa a tarayyarsu.....

Koda boka maksasul jaljas yazo Nan a zancesa take harshensa ya sarke idanunsa s**a kakkafe ya zama gawar
Ita kuwa gawar tasa take akaga wasu tsuntsaye sun ratso cikin fadar wadanda ba'a San daga inda suke ba sun lullubeta
Kafin dakiku sittin sun cinye gangar jikin nasa Gaba daya sannan s**a tashi s**a fice daga fadar ta hanyoyin da s**a shigo ba tareda kowacce ta sauya hanya ba
Tun daga wannan lokaci ta sarki Ruziyal ya fara baiwa lardisa horon yaki
Bayan wa'adin da aka dibar mata ya cika ne ta bazama duniya domin tattara duk wasu shahararrun labarai da tarihin magabata da take bincikowa agurin manyan masana tarihi da Kuma bokaye,sarakuna da Kuma mayaka tana rubutawa acikin wani littafinta da takewa lakabi da kundun labarai

Tana tsaka da wannan tunanin ne Rukyan yazo inda take Yana Mai Yi mata gyraran murya

Firgigit ta d**o da kanta tana Mai duban fuskar sa
Suna hada idanu ya fahimci lallai akwai damuwa akan fuskarta
Don haka sai ya sami guri a kusa da ita ya zauna suna masu kurawa juna ido yace
Yake lardisa na tabbata akwai wani sirrin acikin zuciyarki Wanda kika kasance kina boye min shi
Kuma ban fahimci hakan ba tun farkon haduwarmu sai a wannan lokaci
Amma duk da haka yardar da nayi Dake wacce har tasanya ni amincewa yin wannan tafiyar Dake ba Zata gushe ba agareni
Saidai Kuma shawarar da zan baki a yanzu itace ki gaggauta sanyawa wannan rauni Dake jikinki magani tunda baki San irin gubar Dake tattare da wadannan birrai ba

Dajin wannan Batu sai lardisa cikin damuwa ta fara sanyawa rauninta magani tareda bashi amsa da cewa
Tabbas akwai abin Dana boye maka wannan Abu Kuma ba komai bane face lalurar da mahaifiyarta take faman da ita na tsawon shekaru
Take ta kwashe masa labarin duk abinda ya faru tsakanin ta da boka maksasul jaljas ta fada masa

Daga karshe tace yanzu ba komai nake tunani akansa ba face kalubalen dayace zamu fuskanta
Domin tabbas inaji ajikina a wannan lokaci da muke Kara fuskantar narkakken dutsen wuta a sannan ne wannan kalubale zai bayyana kansa

Kodajin wannan labari sai jarumi Rukyan ya kyalkyale da dariya Wanda hakan yasa lardisa ta fahimci lallai Bai fuskanci maganarta ba
Bayan dariyar ta isheshi ne ya tsuke bakinsa ga barin dariyar da yakeyi

Yace ai duk wani Abu da muka tarar a wannan guri ba zai razanani ko ya bani mamaki ba
Tunda nasan k**ar mune muka saye shi da hannayen mu
Don haka sai ki kwantar da hankalinki tunda yanzu dagani harke Muna bukatar samun hutu sai mu kwana a wannan guri idan gari ya waye Kuma mu tashi muci Gaba da tafiya
Daga wannan furuci lardisa Bata Kara to masa gardama ba domin tasan Bai Gane abinda take son nuna masa ba
Haka s**a zauna s**aci Gaba da Hira har barci ya dauke su
A wannan guri s**a kwana Kashe gari da sassafe s**a tashi s**a tashi domin ci gaba da tafiyar Dake gabansu

Fara tafiyarsu keda wuya a Saman wadannan bishiyu kawai sai s**a riski wata siririyar iyaka wacce kaurinta Bai wuce kaurin tafiyar kiyashi ba data raba wannan daji da kuma daji na gaba

Saidai shi dajin Dake gabansu Babu Komai acikinsa face wani rairayi Wanda yake linkaya da kansa k**ar yadda igiyar ruwa take kadawa yayin da a Samansa Kuma wasu irin jinsin aljanune masu k**a da jemagu suna shawagi a Saman dajin
Kowanne daya daga cikinsu kuwa Yana ruke da wata gajeriyar adda a hannunsa

Dukkansu suna shawagi a Saman wannan rairayi tamkar yadda tsuntsaye suke shawagi a sararin samaniyar

Koda s**a tsaya s**a Karewa wannan daji kallo sai s**a tabbatar da cewa lallai fa yau sun hadu da gamonsu kuskuren Taku daya mutum idan mutum yayi acikin wannan daji zai iya rasa rayuwarsa k**ar yadda SADAUKI mufran yayi acikin HIKAYAR su SADAUKI FARHAN

Don haka sai s**a tsaya s**a fara tunanin hanyar daya k**ata su shiga wannan daji

Bayan sun danyi nazari gami da dogon tunani take s**a koma da baya inda aka daure lardisa s**a dauki wannan igiyar
Sannan s**a dawo bakin iyakar tareda kulle jikin junansu

Daga Nan s**a tsallaka wannan iyaka tareda shiga cikin daji na Gaba

Suna shiga cikin wannan daji sai Gaba daya wadannan aljanu s**a sunkuyo da kawunansu kasa

Koda s**a Hango bakin halittu suna shigowa cikin wannan daji
Sai Kuma s**a Kara dauke kansu ga barin kallonsu baki daya s**a cigaba da shawagi abinsu

Su kansu su Rukyan Saida s**a tsargu da lamarin wadannan aljanu domin sun San ruwa baya tsami banza akwai wani Shirin da suke Yi acikin zukatansu

WANNAN SHINE ABINDA YA FARU GASU JARUMI RUKYAN A HANYAR SU TA ISA TSAKIYAR NARKAKKEN DUTSEN WUTA
+++++. ++++++. +++++

Address


Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Littattafan yaki by Habibullah kbr posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share