09/02/2025
GAWURTACCEN SARKI
***
CHAPTER 81*Hatsabibi Ya kaima Hatsabibi Ziyara* 2
**
✍️✍️✍️Marubuci: YUSUF IMAM BASHIR JEGA Y*I*B*J
***
*Gargadi*: Idan Kasan Bazaka iya Yin Like Da comment Da Sharhi ba, Pls Kada Kakarantamin Littafi.
***
~ My Whatsapp Number : 09036940004
***
*Ina Godiya Ga Wadanda Suke Karanta Wannan Litafin Gaskiya Kuna Sakani Cikin Farin Ciki allah Yabarmu Tare*.
***
*Kada K**anta Da Sharhi,
Don't Forget With Sharhi*
***
*Masha Allah Dayan Account Dina Yadawo Dan Allah Amin Addu,a Saura Daya*
***
Aljanin Yakaraso Daf Da Aljani Hubbus Dake Daukeda Dan Fashi Jurgus.
Aljannun Biyu S**a Tsaya Cak, Juna Kusa Da Juna, Sarki Ashram Da Kansa Yasauko Daga Kan Aljaninsa Yahawo Aljani Hubbus S**a Rungume Juna Tareda Yin Musabaha.
Kai Daga Gani Kasan An Dade Ba,a Haduba. Aljani Hubbus Yakarisa Dasu Daidai Tsakiyar Birnin Burshal Inda Nanne Fadar Sarki Ashram Take.
Yayo Kasa Luuu Daidai Bakin Kofar Fadar, Sarki Ashram Da Dan Fashi Jurgus S**a Sauka Daga Saman Aljani Hubbus.
Bakin Kofar Fadar Wasu Dakaru Ne Guda Uku Masu Shigar Ban Tsoro. Suna Rufe Da Fuskokinsu Da Jikinsu Gaba Daya.
Babu Abinda Kake Gani Har Da Idanuwansu Kuwa, Sannan Suna Rike Da Takubba Madaukaka Guda Uku Uku Ga kowane Badakare.
Suna Ganin Sarki Ashram Da Dan Fashi Jurgus, S**a Zube Kasa S**a Kwashi Gaisuwa Garesu.
Sannan S**a Budemusu Kofar Fadar, Sarki Ashram Da Jurgus S**a Shige Fadar Kai Tsaye.
Fadar Ta Kasance Gawurtacciyar Hadaddiya Wadda Tsayawa Siffantamuku Kyawunta Da Kawatuwarta Da Fasalinta Sai Littafi Mai Shafi Dubu Hudu Da Rabi Shima A Takaice.
Amma Dai Ko A Yanzu Kasan Ankashe Kudi Masu Tarin Yawa Yayin Ginata Domin Ko Abinda Akayi Tubalin Gininta Dashi Abin Kallone.
Sarku Ashram Yaja Dan Fashi Jurgus S**a Je Saman KARAGAR MULKI nsa S**a Zauna Su Biyu A Tare.
Sarki Ashram Yakasance Shirgegin Katone Mai Girman Jiki Da Girman Sawaye, Surar Jikinsa Kadai Kallonta Abin Tsorone .
Jikinsa Mummurde Yake Tamkar Wanda Aka Cuccure Wuri Guda. Yanada Faffadan Kirji Wanda Ko Kwarya Aka Ajiye Zata Iya Zama.
Gashin Kansa Bakine Wulik Babu Ko Digon Wata Kala ACiki, Sannan Yanada Wani Mugun Kyalli Kai Kace Mai Ne Aka Shafamata.
Sarki Ashram Yatafa Hannuwansa Sau Uku, Wata Kuyanga Ta Shigo Dauke Da Kwandon Kayan Marmari .
Sannan Ta Fice Daga Fadar, Sarki Ashram Yayima Dan Fashi Jurgus Bismilla.
Saida S**a Kimtsa Cikinsu, Sannan Sarkin Yam Fashin Jurgus Yadafa Wani Hatimi Dake A Hannunsa, Hauzul Da Basrul S**a Bayyana Suna Masu Kwasar Gaisuwa Garesu.
Dan Fashi Jurgus Yadubesu Yace :
Nasan Zuwa Yanzu Yarima Jarwazu Yasan Nakawo Ziyara A Birninnan Na Burshal, Zai Iya Yin Mugun Tunanin Gangancin Cewa Zai Biyoni Nan Yak**ani Domin Yakaini Ga Sarkin Matsafan Duniya Na Dajin Zalzal, Mai Gidan Su Shubairu Da Muzairu
"Amma Nasan Rashin Sani Ne Ke Dawainiya Da Jarwazu, Baisan Banbanci Tsakanin EMSAHIR 1 Da EMSAHIR 2 ba, Ina Son Ku Bada Tsaro Na Musamman A Sararin Samaniya Na Wannan Birnin Kamin Mugama Ganawa Da MAI GIDAN HATSABIBAI ASHRAM!!!.
Hadimi Hauzul Da Hadimi Basrul S**a Jinjina Kai alamun Bin Umarni Sannan S**a Bace Bat ! Daga Fadar .
Dan Fashi Jurgus Ya Mayarda Kallonsa Ga Sarki Ashram Wanda Ya Kashe Kunnensa Yana Sauraron Abinda Jurgus Yace :
Ina Muka Kwana Danganeda Burinmu ?, Nidai Ta Gefena Komi Daidai Yake, Kaifa Mai Gida ?.
Sarki Ashram Ya Kashema Dan Fashi Jurgus Idanu, Cikin Sigar Dariya Ya Maimata 'Mai Gida' Yace: Jugus Bakada Daraja, Waye Ni A Duniya Da Zanzamo Mai Gidan Sarkin Hatsabiban Duniya Jugus, Eye ? Rufamin Asiiri Aboki.
Jugus Ya Harari Ashram Yace ,
Dalla Can Matsoracin Banza, Babu Mai Muhawarar Kaine MAI GIDAN HATSABIBAI, Idanni Ni Hatsabibine To Kai Mai Gidana Ne.
Ashram Yayi Murmushi Yace
Yaudai Iskanci KenN Kazo Kamin Jurgus, To !, Maganar Gaskiya Shine Nima Ina Nan ina Gudanarda Ayukana Daidai Bisa Tsari domin Cikin Guda Takwas Na Nemo Uku, Kaga Kuma Har Yanzu A Kwai Sauran Lokaci.
Dan Fashi Jurgus Yace, Kutumelesi!!! Ashe Ni Ina Can Ina Wasa Kaikuma Kayita Yin Naka,Nidai Na Nemo Biyu Saura Shida, Da Sarkar Zinare Wadda Na Amso Wurin Sarauniya Lubaina Matar Sarki Kulhum Na Birnin Hirtoliya, Sai Kuma Kambun Tsafi Daga Hannun Shugaba Fallaru, Saura Suma Zanyisu Nan Bada Jimawa Ba.
Sarki Ashram Ya Jinjina Kai Alamun Fahimta, Dan Fashi Jurgus Yaci Gaba Da Cewa: Na Biyu: wai Ya Maganar Gimbiya Lushbaira ne ?, Inane Bok Junudul-Jandul Ya Boyeta ?.
Sarki Ashram Ya Kurba Wani Shayi Dake Gabansu Yace, Gimbiya Lushbaira, Nayi Cikakken Bincike A Kanta, Amma Bari Na Takaitamaka Shi :👇👇👇
Gimbiya Lushbaira Diyar Wani Talakan Mutum ne Mai Suna Fairazul-Hausul, Fairazul-Hausul Bayada kudi Sannan Baya Da Koda Rufin Asiri Ne.
Abinci Ga Yini Wuya Yake Masa Koda Ci Guda Ne, Yanada Matar aure Guda Daya Tal Wadda Tarasu Wurin Haihuwa.
Inda Ta Haifomasa Wata Santaleliyar Jaririya,Fairazul-Hausul Bakin Ciki Da Farin Ciki S**a Ziyarceshi A Lokaci Guda.
Ga Bakin Cikin Mutuwar Matarsa Abar Begensa Mai Debemasa Kewa, Sannan Ga Farin Cikin Haihuwar Jaririya Wadda Saida Yayi Mutuwar Tsaye Lokacinda Yayi Arba Da Fuskarta.
Saboda Wani Kyawu Ya Gani, Wanda Ko A Labari Baitaba Ganiba, Saboda Tsananin Kyawunta Duk Wanda Yazo Ganin Diya Suma Yakeyi Saboda Dimaucewar Ganin Kyawun Diyar.
Kamin Kace-me Labari Yabazu A Birnin Nasu Da Kauyuka Akan Ga Jaririyar Da Ba,a taba Ganin Mai Kyawunta Koda Rabinsama A Duniya ba.
Bisa Dole A Ranar Suna Ana Gama Bikin Haihuwa Domin Jama,ar Duniya Kowa Sai Kyaututtuka Yake Kawoma Fairazul-Hausul Domin Kamun Kafa Akan Neman Auren Jaririyar idan Ta Girma.
Wasu Sarakuna Ko Attajirai Sai Nemawa Diyansu Ajiyar Auren Jaririyar Suke.
Aiko Cikin Kwana Bakwai Da Haihuwar Jaririyar, Fairazul-Hausul Yakoma Gawurtaccen Attajiri Mai Yawan Dukiya Da Rangamomi A Fadin Duniya.
Ranar Sunan Jaririya Anyi Suna Mai Cike Da Watsin Dukiya Da Bama Talakawa Abinci .
Kowane Sarki Saida Yahalarto Wannan Bikin Tareda Dansa Yarima Mai Jiran Gadon Sarauta, Wanda Akeson Ya auri Jaririyar.
Yarinya Taci Sunan Mahaifiyarta Saboda Tunawa Da Ita Wato Lushbaira, Tun A Taron Bikin Sunan Jama,a S**a Radamata Suna Mai Daraja Wato GIMBIYA LUSHBAIRA Aka Karamata Da Lakabin Gimbiya Tamkar Takasancs Yar Wani Basarake.
Akwai Wani Gawurtaccen Matsafin Boka Wanda duniya Ke Tsoro Mai Suna Boka Junudul-Jandul Wanda idan Yayimaka Abu Saidai Kace ALLAH YA ISA.
Tun Lokacinda Lushbaira Matar Attajiri Fairazul-Hausul Ta Haifi Gimbiya Lushbaira Yake Bibiyar Jaririyar, Yasaka Mummunan Nufi A Kanta.
Saida Gimbiya Lushbaira Tayi Shekara Shida A Duniya, Kyawunta Yakara Bayyana Ga Fili, Masu Nemanta S**a Kara Dimaucewa Akanta Sosai Da Sosai.
Sai Boka Junudul-Jandul Yazo Da Daddare Yasaceta Yatafi Da Ita Halarar Tsafinsa Domin Ya Aiwatarda Mummunan Nufinsa A Kanta.
Lokacinda Attajiri Fairazul-Hausul Yatashi Da Safe Yaga Baiga Diyarsa ba Wadda Kullum Da Safe Sai Tazo Gaisheshi Amma Har Karfe Goma Na Rana Cur Bai Gantaba.
Sai Hankalinsa Yadunguzuma Ainun Yabaza Dakaru Neman Bidarta Da Fatake Amma Babuta Babu Labarinta Har Birane Da Kauyuka Kuwa Kai Ko Wanda Yagantama Basu Ganiba.
Sai Yarufe Kansa A Daki Yana Kuka,
Idan Yatuna Da Yarasa Matarsa Da Yarsa Wadda Yake Kallo Ya Mance Da Matarsa, Sai Kukansa Yatsananta.
Kuyanginsa Da Barorinsa Idan S**ayi Yunkurin Futowa Dashi Daga Dakin, Sai Suga Yarufe Ko,ina Ruf!, Sautin Kukansa Kawai Akeji A Gidan.
Al,amarin Boka Junudul-Jandul Kuwa,Lokacinda Yakebe Da Gimbiya Lushbaira Domin Yayimata Fyade Wadda Har Yasumar da ita.
Har Yakwabe Tufafinsa Domin Ya Aikata Nufinsa, Yasaka Hannunsa Domin Yacirema Gimbiya Lushbaira Kayan Jikinta, Yaga Wata Wuta Garwashi Uku Manya Manya Sun Gifta Ta Saman Hannunsa.
Saboda Mahaukacin Zafin Garwasan Wutar, Saida Boka Junudul-Jandul Yakwarara Ihu Wanda Yahaifarda Girgizar Halarar Tsafinsa .
Idanun Boka Junudul-Jandul idan Kakallesu Kasan A Tsorace Take, Tun Daga Haihuwar Boka Junudul-Jandul Har Kawo Zuwa Yanzu Baitaba Ihu Ba A Rayuwarsa.
Balantasa Aga Yaji Tsoron Abu Ba Sai Yau, Tabbas Bala,in Kwarai Boka Junudul-Jandul Yajiya.
Saboda Haka Ya Kurama Gimbiya Lushbaira idanu Yana Mamakinta, Sai Kawai Yazago Madubin Tsafinsa Yadafeshi Da Hannun Hagu Yafara Karanto Wasu Dalisman Tsafi.
Saida Madubin Yayi Haske Sannan Bokan Yasaita Madubin Daidai Fuskar Gimbiya Lushbaira Domin Yasamu Bincike Kan Hatsabibancinta.
Kawai Madubin Tsafin Yayi Bindiga Yatarwatse Yabi iska, A Karo Na Biyu Boka Junudul-Jandul Yaja Baya Atsorace Kuma A Tsananin Mamaki .
Kawai Sai Yazaro Takobinsa Yadaka Tsalle Da Nufin Saran Gimbiya Lushbaira Yarabata Gida Biyu.
Kawai Sai Yaga Hannunsa Na Dama Dake Rike Da Takobin Yaguntule Yafadi Kasa, Jini Ya Fara Malala Daga Hannun Bokan.
A Karo Na Biyu Yakwarara ihun Azaba Wanda Saida Wani Bangare Na Halarar Tsafin Yashige Cikin Kasa.
Ran Boka Junudul-Jandul Yabace, Zuciyarsa Ta K**a Harzuka Tamkar Zata Faso Ta Futo, Idanunsa S**a Kada S**ayi Jawur Yabude Muryarsa Mai K**ada Kukan Jaki Yace, Na Rantse Gemun Kakana Saina Hana Wannan Yarinyar Da Mahaifinta Da Masoyanta Sai Nakaita Inda Babu Wanda Ya,isa Yaganeta Har Abada, Sannan Tunda Har Tasakani Abin Kunya, Takuma Karyamin Alkadarina, Kuma Na Kasa Saduwa Da ita To Har Abada Babu Wanda Yasadu Ita Bazata Taba Aure Ba.
In Takaicemaka Saida Boka Junudul-Jandul Ya Aikata Alwashinsa Kuwa, Yaje Yaboyeta inda Duniya Ta Kasa Sanin Inane.
Sannan Yasamu Nasarar Bata Wasu Ruwan Guba A Matsayin Ruwan , Domin Ta Farfado Tacemasa Tanason Ruwa , Tana Shansu Gubar Taje Ta Bata Mata Sha,awa.
A Yanzu Boka Junudul-Jandul Yashekara Goma Da Yin Mutuwar Kaskanci.
Ranar Da Yaboye Gimbiya Lushbaira Tare Da Bata Guba Tasha, A Ranar Yaga Kawai Hancinsa Yafarke Jini Yafara Zubowa Tamkar Fanfo, Sanann Bakinsa Yafarke Da Jini Tamkar Ambaliya.
Sannan Shedarsa Ta Sarke Yayi Mutuwar Tsaye A Kaskance, A Halin Yanzu Gimbiya Lushbaira Tana A DAJIN MARLAD A Kogon SAULADU A Daure Cikin Kogon.
Dan Fashi Jurgus Yayi Ajiyar Zuciya Tareda Jinjina Mugun Zalunci Irin Na Wannan Bokan.
Yaso Ace Yataso Yatarar da Bokan Yana Raye Da Sai Yayimasa Mummunan Hukunci, Saboda Yaraba "Ya Da Ubanta Da Kuma Masoyanta.
Yanzu Tsawon Shekara Goma Tabbas Wannan Zaluncine Dole Yaceci Gimbiya Lushbaira Daga Wannan Kangin Wahala.
***
Gawurtaccen Sarki Littafin Yaki
Pls Follow This Page For More Book If War.