Sharhin Siyasa TV

Sharhin Siyasa TV Wannan kafa an kirkire ta ne don yin sharhi kan al'amuran siyasar Nigeria da na kasashen ketare

Cikin wadannan Shugabannin wa ya fi yiwa NIGERIA aiki?Ga jerin sunayensu:1Abubakar Tafawa Balewa 2 Janar. Johnson Aguiyi...
08/06/2026

Cikin wadannan Shugabannin wa ya fi yiwa NIGERIA aiki?

Ga jerin sunayensu:

1Abubakar Tafawa Balewa
2 Janar. Johnson Aguiyi Ironsi
3. Janar Yakubu Gowon
4. Janar Murtala Ramat Muhammed
5 Janar Olusegun Obasanjo
6. Alhaji Shehu Aliyu Shagari
7. Manjo Janar Muhammadu BUHARI
8. Janar Ibrahim Badamasi Baba gida
9 Chief Earnest Shonekan
10. Janar Sani Abacha
11. Janar Abdussalam Alhaji Abubakar
12 Alhaji Umaru Musa YarAdua
13. Dr. Goodluck Ebele Azikiwe Jonathan
14. Bola Ahmed Tinubu

Asiwaju Bola Ahmed Tinubu Atiku Abubakar Mr. Peter Obi Rabiu Musa Kwankwaso ゚

TAMBAYA GA KWANKWASAWA: In MADUGU ya kwashe-ku zuwa wata Jam'iyyar za ku bi shi?       ゚
08/06/2026

TAMBAYA GA KWANKWASAWA: In MADUGU ya kwashe-ku zuwa wata Jam'iyyar za ku bi shi?

DANGOTE da ABDUSSAMAD ISYAKA RABIU 'yan LAGOS ne ba 'yan KANO ba ne domin LAGOS ce ta kai su matsayin masu kudi na daya ...
08/06/2026

DANGOTE da ABDUSSAMAD ISYAKA RABIU 'yan LAGOS ne ba 'yan KANO ba ne domin LAGOS ce ta kai su matsayin masu kudi na daya da na biyu a Afirka - Inji Kashim Shettima mataimakin shugaban kasar Nigeria.

Mataimakin Shugaban kasa Kashim Shettima ya ce fitaccen attajiri na daya a Afirka Alhaji Aliko Dangote dan LAGOS ne shi ba dan Kano ba haka zalika shima attajiri na biyu a Afirka Alhaji ABDUSSAMAD ISYAKA RABIU shima dan LAGOS ne ba dan Kano ba ne saboda gabà dayansu LAGOS ce ta yi sanadiyar kai su matakin da suke a yau.

ME za ku ce?

Kwankwaso ya fara shinshina Jam'iyyar APM mai alamar ROGO da PRP mai dan mukulli Rahotanni sun ce Madugun Kwankwasiyya k...
08/06/2026

Kwankwaso ya fara shinshina Jam'iyyar APM mai alamar ROGO da PRP mai dan mukulli

Rahotanni sun ce Madugun Kwankwasiyya kuma dan takarar Mataimakin Shugaban kasa a Jam'iyyar NDC Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya fara neman mafaka a Jam'iyyar APM ko PRP sakamakon yunkurin kwarfe 'yan takarar majalisar da ya tsayar a Kano da uwar Jam'iyyar ta kasa karkashin madugunta tsohon Gwamnan jihar Bayelsa Sanata Seriake Dickson.

Wata majiya da ta bukaci a sakaya sunanta da ke da kunnuwa a Miller Road ta shaidawa Sharhin Siyasa TV cewa tuni jagoran darikar Kwankwasiyyar har ya fara Cankulo-Cankuloto Tsakanin APM mai alamar ROGO da PRP mai mukulli.

Majiyar ta ce matukar uwar Jam'iyyar NDC ba ta sauya matsaya ba akan sauya :yan takara 'yan Kwankwasiyya da ta yi ta bai wa 'kaso 40 ga 'yan Jam'iyya na asali ba shakka Kwankwaso zai fice daga NDC zuwa daya daga cikin APM ko PRP

ME za ku ce?

Jam’iyyar NDC ta ce ita fa ba mallakin wani ba ne kuma ba wata jam’iyya ce ta mutum guda ko wata ƙungiya ta musamman da ...
08/06/2026

Jam’iyyar NDC ta ce ita fa ba mallakin wani ba ne kuma ba wata jam’iyya ce ta mutum guda ko wata ƙungiya ta musamman da za a iya “amfani da ita a lokacin da ake bukata ayi watsi da ita ba bayan anci moriyar ganga,,

A cikin wata sanarwa da daraktan yada labarai na kasa na NDC, Osa, ya fitar a ranar Lahadi, ya ce kwamitin zartarwa na kasa (NEC) a taron da aka yi a Abuja, ya sake jaddada cewa “jam’iyya ce mafi girma, kuma duk shirye-shirye, manufofi, da nadin mukamai da gwamnatoci da aka zaba a kan dandamalin ta dole ne a yi su ne da shawarar jam’iyya.”

Ku saka kwankwaso a cikin adduar-ku don kuwa yana cikin lukutar masifa ta siyasa, lissafin siyasa ya kwace masa - Inji F...
08/06/2026

Ku saka kwankwaso a cikin adduar-ku don kuwa yana cikin lukutar masifa ta siyasa, lissafin siyasa ya kwace masa - Inji FAIZU ALFINDIKI.

Sun fara shirin fita daga NDC zuwa PRP - Inji Sunusi Bature Dawakin-Tofa, daraktan yada labarai na Gwamnan Kano.A ganin-...
08/06/2026

Sun fara shirin fita daga NDC zuwa PRP - Inji Sunusi Bature Dawakin-Tofa, daraktan yada labarai na Gwamnan Kano.

A ganin-ku da su wa DG ke wannan maganar cewa za su bar NDC zuwa PRP?

Ku dai-na alakanta wata kabila da ta'addanci cikin kowacce kabila akwai batagari - Inji PETER OBI...Me za ku ce?
08/06/2026

Ku dai-na alakanta wata kabila da ta'addanci cikin kowacce kabila akwai batagari - Inji PETER OBI...

Me za ku ce?

An Nemi INEC ta Soke Rijistar NDC, An Shigar da Sabon Kara a KotuAhidjo Karlahi, daraktan ADA, ya shigar da kara a kan N...
08/06/2026

An Nemi INEC ta Soke Rijistar NDC, An Shigar da Sabon Kara a Kotu

Ahidjo Karlahi, daraktan ADA, ya shigar da kara a kan NDC, yana neman INEC ta soke rijistar jam’iyyar.

An shigar da karar ne a ranar Talata da ta gabata a gaban Babban Kotun Tarayya dake Abuja, mai lamba FHC/ABJ/CS/1115/2026, kuma Shugaban babbar Kotun tarayya (FHC), shine ya bai wa Justice Mohammed Umar alhakin sauraron karar.

Rahoton Daily Trust ya nuna cewa Seriake Dickson, jagoran NDC, ya tabbatar cewa babu wata kara ko daukaka kara da ke kalubalantar rijistar jam’iyyar. Dickson ya bayyana hakan ne a yayin taron farko na kasa na jam’iyyar da aka gudanar a Abuja, inda ya ce jam’iyyar tana da cikakken halaccin aiki kuma an hade ta a shirye-shiryen zaben 2027.

Amma a cikin karar da Karlahi ya shigar, ADA ta ce NDC ba ta cika sharuddan doka da kundin tsarin mulki da ake bukata ba kamar yadda aka tanada a Sashe na 221-225A na Kundin Tsarin Mulkin Tarayyar Najeriya, 1999 (kamar yadda aka gyara) da kuma Sashe na 75 da 79 na Dokar Zabe, 2022.

Karlahi, wanda ya hada INEC da NDC a matsayin wadanda ake kara da su na farko da na biyu, ya yi ikirarin cewa NDC ba ta cikin jerin kungiyoyin da aka cancanci su yi rajista a 2025. Ya ce NDC ta kauce wa duk matakan da doka ta tanada, don haka bai kamata a yi mata rijista a matsayin jam’iyya ba.
Ya ce:
“NDC ba ta cikin jerin kungiyoyin da aka amince su yi rajista a 2025.
NDC ba ta biya kudin gudanarwa na Naira miliyan 2 ba kuma ba ta samu lambobin shiga tsarin rajista na INEC ba.

NDC ba ta amfani da shafin rajistar jam’iyyu na INEC wajen cike fom EC15A ba, wanda shi ne hanyar da doka ta amince da ita don yin rajista.
Wannan ba zargi kawai ba ne – abubuwan suna cikin kundin tarihi na jama’a.”

Karlahi ya bukaci kotu ta bayyana cewa ci gaba da daukar NDC a matsayin jam’iyya abu ne marar doka, ba halatta, ba daidai ba, kuma babu tasiri.

Ya kara da cewa:
“Kara ta na neman kotu ta bayyana cewa:
Kundin tsarin mulki ba ya ba da damar rajistar wata kungiya da bata cika sharuddan doka ba.
Ci gaba da daukar NDC a matsayin jam’iyya da INEC ke yi ba bisa doka ba ne.

A soke takardar rajistar NDC da INEC ta bayar. A umarci INEC ta dakatar da duk wata hulda da NDC a matsayin jam’iyya.

A hana NDC ci gaba da gabatar da kanta ko shiga harkokin zabe a matsayin jam’iyya mai rajista.

Karlahi ya bayyana cewa wannan karar ba ta da wata manufar siyasa ko ta kashin kai, kuma ba a shigar da ita ne a madadin wata kungiya ko rukunin mutane ba, ciki har da ADA.
Ya ce:

“Na yi imani cewa gaskiya a zabe shi ne ginshikin dimokuradiyya. Idan tsarin rajistar jam’iyyu ya lalace, dukan tsarin dimokuradiyya zai shiga cikin hadari. Wannan karar gudummawa ce ta kokarin kiyaye tsarin.”

Ya kuma yi kira ga duk ‘yan Najeriya, ba tare da la’akari da jam’iyya, kabila ko addini ba, da su fahimci wannan lamari, su tallafa, kuma su hakura yayin da shari’a ke gudana.
Ya kara da cewa:

“Kotu ita ce mafaka ta karshe ga talakawa kuma ita ce babban mai kiyaye kundin tsarin mulki. Ina da cikakken amincewa ga hukuncin kotu.”

Me za ku ce?

Jagoran Jam'iyyar NDC na kasa Sanata Seriake Dickson ya sauya sunayen wasu daga cikin 'yan takarar majalisar wakilai da ...
08/06/2026

Jagoran Jam'iyyar NDC na kasa Sanata Seriake Dickson ya sauya sunayen wasu daga cikin 'yan takarar majalisar wakilai da bangaren Kwankwasiyya ya gabatar mata a Kano, domin cika yarjejeniyar rabon tikitin takara da aka cimma tsakanin bangaren jam'iyyar da aka tarar da kuma bangaren Kwankwasiyya.

A cikin wata takarda da shugaban jam'iyyar a Kano, Hon. Hussaini Isah Mairiga, ya sanya wa hannu, wadda aka aikewa jagoran jam'iyyar na kasa, Sanata Seriake Dickson, jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso, da shugaban NDC na shiyyar Arewa maso Yamma, Alhaji Muhammadu Rabi'u Sabo Bakinzuwo.

A cewar takardar, jam'iyyar ta amince da Barista Isma'il Idris Sani a matsayin dan takarar Jam'iyyar a Kumbotso, Hon. Nasiru Ali Ahmed a Nassarawa, Kabiru Ishaq Sa'id a Kano Municipal, sai kuma Barista. Ɗayyabu Jamilu Ibrahim a Doguwa da Tudunwada, Muhammad Hamisu Abubakar a Dawakin Tofa, Rimin Gado da Tofa, Ibrahim Bashir Bango a Sumaila da Takai, da kuma Abdulmajid Isa Umar Mairigar fata a Gwale a matsayin 'yan takarar Majalisar Tarayya.

Haka kuma, an samu sauye-sauye a tikitin takarar Majalisar Jiha a mazabun Dala, Tarauni, Kumbotso, Ungogo da Dawakin Kudu.

Jam'iyyar ta bayyana tun a farko akwai yarjejeniya tsakaninta da Kwankwaso cewar za a yi rabon mukaman jam'iyyar da na takara a tsarin kaso 60 bangaren Kwankwasiyya sai kuma jam'iyya za ta ɗauki kaso 40.

Bayanan da Siyasarmu TV ta tattara, ta gano babu wata kujera da ɓangaren Kwankwasiyyar ya ba wa bangaren jam'iyya, lamarin da ya kawo saɓani da har ta kai jam'iyyar ta ɗauki matakin ɗaukar kason ta.

Madogara: Siyasarmu TV

Address

Kumbotso Street Dan Maliki
Kano
KANO

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Sharhin Siyasa TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Sharhin Siyasa TV:

Share