14/06/2026
Dazu na yi magana akan zargin da matar Saleem Goje ta yi akan alakarsa da Hadiza Aliyu
Sai wasu su ke yin comments da cewa mu yan Arewa mun fi mayar da hankali akan abin da ba zai amfane mu ba, kuma mun fi mayar da hankali akan batun da ya shafi yan film alhali muna fuskantar matsalar tsaro.
1- Da farko idan mutum magana ya yi akan matsalar tsaro mutanenmu ba sa tsayawa su karanta rubutun bare su yi masa comments, like d sharings.
Sannan idan ka zurfafa akan maganar tsaro tsautsayi ya afka maka ka shiga hannun jami'an tsaro, mutanenmu da ka ke rubutu akan su, su ne za su fara fitowa su ke cewa kai ne ka jawowa kanka, akwai influencers da yawa da su ka yi magana akan tsaro aka k**a su, daga karshe cewa ake yi su ne su ka jawowa kansu.
2- Abu na biyu, shirme ne ka yi tunanin cewa domin ana fuskantar matsalar tsaro, ba za a yi magana akan wani batu da yake trending a social media ba musamman wanda ya shafi yan film, yan kwallo da mawaka.
Raini ne yake sakawa za ka ji muna cewa wai yan Arewa ba mu san kanmu ba, a lokacin da mu ke fuskantar matsalar tsaro muna maganar yan film ko ball.
Duk duniya babu kasar duk tarin matsalolin da ta ke fuskanta da ba a maganar yan film ko kwallo domin a haka Allah Ya halicci dan adam da son yin magana akan mutanen da su ke taurari ko madaukaka.
Ko kasashen Turai mu ke ganin sun fi mu cigaba, babu kasar da za ka je wacce maganar yan kwallo da film ba ta fi kowacce daukar hankali ba.
Cece-kuce a social media akan matsalolin da su ke addabar mu, ba su ba ne za su saka mu samu sauki, illa kowa a ranar zabe ya zabi shugabanni nagari.