Queen luba

Queen luba Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Queen luba, Digital creator, Kano.

Tashin hankali a Kebbe yayin da ake zargin Lakurawa sun shiga ƙauye da rana tsakaWasu al’ummar ƙaramar hukumar Kebbe da ...
15/08/2026

Tashin hankali a Kebbe yayin da ake zargin Lakurawa sun shiga ƙauye da rana tsaka

Wasu al’ummar ƙaramar hukumar Kebbe da ke jihar Sokoto sun shiga cikin halin tashin hankali da fargaba, bayan da ake zargin wasu ’yan ƙungiyar Lakurawa ɗauke da mak**ai sun shiga wani ƙauye da rana tsaka a ranar, Juma’a.

Rahotannin farko sun ce zuwan mutanen ya jefa mazauna yankin cikin firgici, inda wasu s**a fara neman mafaka tare da barin gidajensu saboda tsoron abin da ka iya biyo baya.

Har yanzu ba a samu cikakken bayani kan ko an samu asarar rayuka, jikkatawa ko kuma sace wasu mutane ba, yayin da bayanai kan abin da ya faru ke ci gaba da fitowa.

Lamarin ya ƙara haifar da damuwa a yankunan da ke fama da matsalar tsaro, musamman ganin yadda ƙungiyar Lakurawa ta kasance cikin manyan barazanar tsaro a sassan arewa maso yammacin Najeriya. Rahotannin bincike sun nuna cewa ƙungiyar ta kasance tana aiki a wasu sassan Sokoto da Kebbi, inda aka samu rahotannin hare-hare da kuma matsin lamba kan al’ummomin karkara.

A wasu lokuta, Lakurawa ta shiga rikici da sauran ƙungiyoyin ’yan bindiga, yayin da rahotanni s**a nuna cewa dabarunta da tasirinta sun bambanta daga yanki zuwa yanki.

Mazauna yankunan karkara na ci gaba da nuna damuwa kan yadda ’yan bindiga da sauran ƙungiyoyin masu ɗauke da mak**ai ke samun damar shiga al’umma, musamman a lokacin da mutane ke gudanar da harkokinsu na yau da kullum.

Ana sa ran hukumomin tsaro za su fitar da ƙarin bayani domin tabbatar da ainihin abin da ya faru, adadin mutanen da abin ya shafa, da kuma matakan da aka ɗauka domin kare mazauna yankin.

15/08/2026
Jami’an tsaro sun dakile wani yunkurin kai farmaki da ’yan bindiga s**a yi a wata unguwa da ke karamar hukumar Musawa, a...
15/08/2026

Jami’an tsaro sun dakile wani yunkurin kai farmaki da ’yan bindiga s**a yi a wata unguwa da ke karamar hukumar Musawa, a jihar Katsina.

Rahotanni sun bayyana cewa jami’an ’yan sanda tare da jami’an Katsina State Community Watch Corps sun yi gaggawar kai dauki bayan samun sahihin bayanan sirri kan shirin ’yan bindigar.

Jami’an tsaron sun yi arangama da ’yan bindigar, inda aka yi musayar wuta. Hakan ya tilasta wa ’yan bindigar tserewa tare da barin wurin.

Wannan hadin gwiwa tsakanin jami’an tsaro da masu sa-kai na ci gaba da taka muhimmiyar rawa wajen dakile hare-haren ’yan bindiga da kare rayuka da dukiyoyin al’ummomin karkara a jihar Katsina.

Sai dai kawo yanzu, ba a bayyana ko an kashe ko k**a wani daga cikin ’yan bindigar ba, sannan babu wani bayani a hukumance kan ko an samu asarar rayuka ko jikkata a yayin arangamar.

Hukumomin tsaro sun kuma yi kira ga al’umma da su ci gaba da bayar da bayanan sirri kan duk wani motsi ko shirin masu aikata laifuka, domin taimakawa jami’an tsaro wajen dakile hare-hare tare da tabbatar da tsaron al’umma.

Wacece asalin mai jegon anan
15/08/2026

Wacece asalin mai jegon anan

Burkina Faso 🇧🇫: Dakarun sojin ƙasar sun kai farmaki wata mafakar ’yan ta’adda, inda s**a hallaka sama da ’yan ta’adda 5...
13/08/2026

Burkina Faso 🇧🇫: Dakarun sojin ƙasar sun kai farmaki wata mafakar ’yan ta’adda, inda s**a hallaka sama da ’yan ta’adda 50, tare da kashe wasu da dama a yayin wani samame

💔 WANNAN HOTON ZAI IYA SA ZUCIYAR MUTUM TA TAUSAYA… 😭Wani lokaci mutum yana iya kallon mutum yana dariya, amma ba ya san...
13/08/2026

💔 WANNAN HOTON ZAI IYA SA ZUCIYAR MUTUM TA TAUSAYA… 😭

Wani lokaci mutum yana iya kallon mutum yana dariya, amma ba ya san irin azabar da yake ɓoye a zuciyarsa ko jikinsa.

Ga wannan ɗan’uwa, yanzu yana kwance yana fama da rashin lafiya, kuma abin da yake nema shi ne addu’a kawai. 🤲😭

Ya Allah, idan wannan bawan naka yana cikin wani hali mai wahala, Ka sauƙaƙa masa, Ka warkar da shi, Ka mayar masa da cikakkiyar lafiya, Ka kuma ba shi ƙarfin jurewa.

🤲 Ya Allah, duk wanda yake fama da rashin lafiya a yanzu, Ka ba shi lafiya. Wanda yake cikin damuwa, Ka yaye masa. Wanda yake cikin ciwo, Ka sauƙaƙa masa. Amin.

Don Allah, kada ku wuce ba tare da addu’a ba. ❤️🤲

🚨 ABIN TAKAICI! An K**a Wata Mata Bisa Zargin Alaƙa Da ’Yan BindigaRahotanni da ke yawo sun ce wata mata da ake ganin k*...
12/08/2026

🚨 ABIN TAKAICI! An K**a Wata Mata Bisa Zargin Alaƙa Da ’Yan Bindiga

Rahotanni da ke yawo sun ce wata mata da ake ganin k**ar ba ta da lafiya a hankali ta jawo hankalin jama’a bayan an ji tana waya tana cewa wani mutum kada ya zo tukuna, domin hanya ba ta gama zama lafiya ba.

Hakan ya sa aka kira jami’an tsaro, inda aka tafi da ita domin bincike. Ana zargin cewa tana da alaƙa da masu aikata laifuka, amma har yanzu wannan zargi na buƙatar tabbatarwa daga hukumomin tsaro.

⚠️ Jama’a su yi taka-tsantsan, amma kada su ɗauki doka a hannunsu.

🤲 Allah Ya tona duk wani makirci, Ya kare al’ummar Najeriya.

MUTANEN MU DA ABIN MAMAKI NI HAR ABIN YA ISHE NIKano gari ne na kasuwanci ko zumunci ko aiki ko akwai wani  dalilin ka n...
12/08/2026

MUTANEN MU DA ABIN MAMAKI NI HAR ABIN YA ISHE NI

Kano gari ne na kasuwanci ko zumunci ko aiki ko akwai wani dalilin ka na zuwa Kano, ni ba Gwamnan Kano ba ko Sarkin Kano ko kuma mai masaukin baƙi.

Mutum ban san shi ba babu wata muamala da ta taɓa haɗa mu ko ta messager. Kai koma nasan ka ɗin muna gaisawa ta messager ɗin ina ruwa na da ka shigo Kano?

Sai mutum yayi ta kira ta messager kai da kai k**ar masifa ina ɗaga waya sai ka ji na shigo Kano. Ina ruwana da ka shigo Kano? Ina ruwa na?

Ka shigo ka yi abinda ya kawo ka ka ware, wurina ka zo? Ko kuma kana matsayin mai hankali baka tunanin idan duk wanda yake social media ya shigo Kano sai mun gaisa ai sai a yi layi cike a gidan mu kana daga cikin masu kafe hotuna na a zage ni kan cewa kowa ya zo Kano sai ya ganni

Malam idan ka shigo Kano ka je ka yi abinda ya kawo ka. Zumuncin mu a social media sai mu gaisa ta hanyar post ɗin ka ko nawa ko comment section da messenger.

IDAN KA ZO KANO BABU RUWA. AMMAN GA SAƘO NA BAI ƊAYA . Duk wanda ya shigo Kano sannu da zuwa Allah yasa albarka ga abinda ka zo yi ka zo lafiya ka koma lafiya🙏

Mata ma yan uwana tsoron su nake yi zumunci daga nesa nesa ne bare na yi ta tara zuga.

KUMA BA MA SU SIYAN KOMAI BA NE.

Nagode🙏





if if soldier is the best military work in the world choose A if if police is the best in the world choose B
10/08/2026

if if soldier is the best military work in the world choose A if if police is the best in the world choose B

SOJOJI SUN DAKILE AIYUKAN ’YAN TA’ADDA, SUN K**A MUTUM BIYU A ZAMFARAZAMFARA — Rundunar Operation FANSAN YAMMA ta ce dak...
10/08/2026

SOJOJI SUN DAKILE AIYUKAN ’YAN TA’ADDA, SUN K**A MUTUM BIYU A ZAMFARA

ZAMFARA — Rundunar Operation FANSAN YAMMA ta ce dakarunta sun dakile wasu ayyukan ’yan ta’adda tare da k**a wasu mutane biyu da ake zargi da taimaka wa ’yan ta’adda a wasu sassan Jihar Zamfara.

Rundunar ta bayyana cewa an samu nasarorin ne a wasu samame daban-daban da dakarunta s**a gudanar a ranar 7 ga Agusta, 2026.

A yankin Jabanda, Ƙaramar Hukumar Zurmi, sojoji tare da jami’an ’yan sanda masu aikin kwance bama-bamai sun gano wata na’urar fashewa da ake zargin an dasa a gefen hanya.

Jami’an sun yi nasarar kwance na’urar tare da gudanar da bincike a yankin domin tabbatar da cewa babu sauran barazana, kafin daga bisani a sake buɗe hanyar ga masu amfani da ita.

Yayin da dakarun ke dawowa daga aikin, sun yi arangama da wasu ’yan ta’adda a ƙauyen Birnin Tsaba, Ƙaramar Hukumar Birnin Magaji.

Rundunar ta ce an yi musayar wuta tsakanin sojojin da ’yan ta’addan, lamarin da ya tilasta wa ’yan ta’addan tserewa zuwa cikin daji.

Binciken yankin bayan arangamar ya kai ga gano babura biyu, hular sojojin daji, rediyon sadarwa da wasu kayayyaki.

Haka kuma, a Ƙaramar Hukumar Shinkafi, dakarun Sector 2 tare da jami’an ’yan sandan Mobile Police sun kai samame a yankin Kwanar Jolof, bisa bayanan sirri kan motsin ’yan ta’adda.

A cewar rundunar, sojojin sun yi musayar wuta da ’yan ta’addan tare da tilasta musu ja da baya cikin rudani.

Binciken da aka gudanar daga bisani ya gano babur guda ɗaya, kayan sojojin daji guda biyu, rigar kariya da hular sojojin daji, baya ga wasu kayayyaki.

A wani samame daban, dakarun da ke sintiri a kusa da Maradun sun k**a wani mutum mai shekaru 35, mai suna Lawali Dan Alo, wanda rundunar ta bayyana a matsayin wanda ake zargi da taimaka wa ’yan ta’adda da kuma kai musu kayayyaki.

Rundunar ta ce Lawali ya bayyana cewa kayan da ke cikin jakarsa abinci ne. Sai dai binciken jami’an tsaro ya gano sama da Naira miliyan 5.3 da kuma wata wayar hannu.

Binciken farko, a cewar rundunar,

Address

Kano

Telephone

+2348074198240

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Queen luba posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Queen luba:

Shortcuts

Share