Queen luba

Queen luba Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Queen luba, Digital creator, Kano.

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Zamfara ta samu nasarar dakile wani mummunan hari bayan ta gano tare da lalata wata na’urar f...
14/06/2026

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Zamfara ta samu nasarar dakile wani mummunan hari bayan ta gano tare da lalata wata na’urar fashewa (IED) da ake zargin ’yan bindiga sun binne a hanyar Kunchin Kalgo da ke karamar hukumar Tsafe.

An gano bam din ne sak**akon sahihan bayanan sirri da hadin kan al’umma, lamarin da ya bai wa jami’an VCRU da EOD damar gaggauta kai dauki tare da kawar da barazanar kafin ta jawo asarar rayuka.

Rundunar ta yaba wa mazauna yankin bisa hadin kai da bayar da bayanai kan lokaci, tare da tabbatar da cewa tana ci gaba da farautar wadanda s**a shirya wannan aika-aika. Haka kuma an kara yawan sintiri a yankunan domin tabbatar da tsaron matafiya da mazauna jihar.

INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UNWallahi halin da al'ummar Dandume ke ciki a yau abin tausayi ne da takaici.Ana rasa ra...
14/06/2026

INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN

Wallahi halin da al'ummar Dandume ke ciki a yau abin tausayi ne da takaici.

Ana rasa rayuka, ana sace dukiyoyi, ana kuma yin garkuwa da bayin Allah marasa laifi. Al'umma sun gaji da rayuwa cikin tsoro. Iyaye sun gaji da zaman ɗar-ɗar kan 'ya'yansu, mata sun gaji da zaman jimami, yara kuma sun taso suna ganin tashin hankali a matsayin wani ɓangare na rayuwa. 😭

Ya Allah, Kai ne Mai iko a kan komai. Ka kawo mana mafita, Ka kare rayukanmu da dukiyoyinmu, Ka yaye mana wannan fitina. Ka sa zaman lafiya ya dawo a Dandume, Katsina da Najeriya baki ɗaya.

Mun gaji da kuka, mun gaji da zaman fargaba, mun gaji da rasa 'yan uwa da abokan arziki. Allah Ka kawo mana ɗauki.

Ameen summa Ameen 🤲

The protectors in some part of Zamfara state..... The Ordinary People 🙌🙌🙌,This is the kind of men we need in the army, u...
14/06/2026

The protectors in some part of Zamfara state..... The Ordinary People 🙌🙌🙌,

This is the kind of men we need in the army, unfortunately they will never apply, and when they do they will never get it. 💔💔💔

Dakarun Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda, Sun Ceto Fursunoni, Sun Kwato Mak**ai a Arewa Maso GabasDakarun rundunar haɗin ...
14/06/2026

Dakarun Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda, Sun Ceto Fursunoni, Sun Kwato Mak**ai a Arewa Maso Gabas

Dakarun rundunar haɗin gwiwa ta Operation HADIN KAI (OPHK), wadda ke aiki a karkashin Operation DESERT SANITY da sauran ayyukan tsaro a Arewa maso Gabashin Najeriya, sun samu gagarumar nasara a farmakin da s**a kaddamar kan ‘yan ta’adda a yankin.

A cewar rahoton ayyukan sojin, dakarun sun gudanar da hare-hare masu tsari tare da hadin gwiwar Civilian Joint Task Force (CJTF) a yankunan Valle, Ashigashiya da Gakara. A yayin farmakin, an ce dakarun sun hallaka wasu daga cikin ‘yan ta’addan tare da tarwatsa maboyarsu.

Baya ga hakan, sojojin sun kuma kubutar da wasu mutanen da aka yi garkuwa da su, tare da kwato mak**ai, harsasai da abubuwan fashewa da ake zargin ‘yan ta’addan na amfani da su wajen kai hare-hare kan al’umma da jami’an tsaro.

Rundunar ta ce wannan nasara na daga cikin ci gaba da ƙoƙarin da ake yi na tabbatar da zaman lafiya a yankin Arewa maso Gabas, inda take ci gaba da farmaki kan sansanonin ‘yan ta’adda tare da rage karfin su a fadin yankin.

Dazu na yi magana akan zargin da matar Saleem Goje ta yi akan alakarsa da Hadiza Aliyu Sai wasu su ke yin comments da ce...
14/06/2026

Dazu na yi magana akan zargin da matar Saleem Goje ta yi akan alakarsa da Hadiza Aliyu

Sai wasu su ke yin comments da cewa mu yan Arewa mun fi mayar da hankali akan abin da ba zai amfane mu ba, kuma mun fi mayar da hankali akan batun da ya shafi yan film alhali muna fuskantar matsalar tsaro.

1- Da farko idan mutum magana ya yi akan matsalar tsaro mutanenmu ba sa tsayawa su karanta rubutun bare su yi masa comments, like d sharings.

Sannan idan ka zurfafa akan maganar tsaro tsautsayi ya afka maka ka shiga hannun jami'an tsaro, mutanenmu da ka ke rubutu akan su, su ne za su fara fitowa su ke cewa kai ne ka jawowa kanka, akwai influencers da yawa da su ka yi magana akan tsaro aka k**a su, daga karshe cewa ake yi su ne su ka jawowa kansu.

2- Abu na biyu, shirme ne ka yi tunanin cewa domin ana fuskantar matsalar tsaro, ba za a yi magana akan wani batu da yake trending a social media ba musamman wanda ya shafi yan film, yan kwallo da mawaka.

Raini ne yake sakawa za ka ji muna cewa wai yan Arewa ba mu san kanmu ba, a lokacin da mu ke fuskantar matsalar tsaro muna maganar yan film ko ball.

Duk duniya babu kasar duk tarin matsalolin da ta ke fuskanta da ba a maganar yan film ko kwallo domin a haka Allah Ya halicci dan adam da son yin magana akan mutanen da su ke taurari ko madaukaka.

Ko kasashen Turai mu ke ganin sun fi mu cigaba, babu kasar da za ka je wacce maganar yan kwallo da film ba ta fi kowacce daukar hankali ba.

Cece-kuce a social media akan matsalolin da su ke addabar mu, ba su ba ne za su saka mu samu sauki, illa kowa a ranar zabe ya zabi shugabanni nagari.

Ƴan Sanda Sun Ceto Mutane Uku da Aka Yi Garkuwa da Su a Hanyar Gurusu–AnkaRundunar ’Yan Sandan Jihar Zamfara ta samu wan...
14/06/2026

Ƴan Sanda Sun Ceto Mutane Uku da Aka Yi Garkuwa da Su a Hanyar Gurusu–Anka

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Zamfara ta samu wani gagarumin nasara a yaƙi da miyagun laifuka bayan jami’anta na Sashen Yaƙi da Manyan Laifuka (VCRU) sun ceto mutane uku da ’yan bindiga s**a yi garkuwa da su a hanyar Gurusu–Anka.

Lamarin ya faru ne ranar 13 ga Yuni, 2026, lokacin da ’yan bindiga masu ɗauke da manyan mak**ai s**a tare hanya tare da sace matafiya uku da ke kan hanyarsu daga Bukuyum zuwa Talata Mafara.

Bayan samun rahoto, jami’an ’yan sanda sun bi sawun maharan zuwa cikin daji inda aka yi musayar wuta mai zafi. Sak**akon dabarun aiki da jarumtakar jami’an, an fatattaki ’yan bindigar tare da jikkata wasu daga cikinsu, yayin da s**a tsere cikin daji.

An yi nasarar ceto dukkan waɗanda aka sace ba tare da sun ji rauni ba. Sai dai maharan sun gudu da wayar Android ta ɗaya daga cikin waɗanda aka ceto.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Zamfara, CP Ahmad Muhammad Bello, ya yaba da ƙwazon jami’an da s**a gudanar da aikin, tare da tabbatar wa al’umma cewa rundunar za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin jama’a a faɗin jihar.

13/06/2026
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Zamfara ta kâshe shugaban ’yan bindiga, ta k**a mutum uku tare da kwato mak**ai da babura.A w...
10/06/2026

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Zamfara ta kâshe shugaban ’yan bindiga, ta k**a mutum uku tare da kwato mak**ai da babura.

A wani samame da jami’an Sashen Yaki da Manyan Laifuka (VCRU) s**a kai a yankin Birisawa da ke Karamar Hukumar Gummi bayan samun sahihan bayanan sirri, sun yi artabu da ’yan bindiga. A yayin musayar wuta, an kashe shugaban kungiyar ’yan bindigar, an k**a mutum uku, yayin da wasu s**a tsere da raunukan harbi.

Jami’an sun kuma lalata sansanin ’yan bindigar tare da kwato bindigogi uku da babura biyar. Rundunar ta ce tana ci gaba da farautar sauran wadanda s**a tsere domin tabbatar da tsaro a jihar.

‎Rundunar tsaron hadin gwiwa mai yaki da 'yan ta'adda a Arewa maso Yammacin Najeriya ta kashe barayin mutane 6, kuma ta ...
10/06/2026

‎Rundunar tsaron hadin gwiwa mai yaki da 'yan ta'adda a Arewa maso Yammacin Najeriya ta kashe barayin mutane 6, kuma ta dakile yunƙurin kwasar jama'ar Kanoma da kauyen Gidan daji na karamar Hukumar Maru a Zamfara.

‎Sanarwar da kakakin rundunar 'yan sanda DSP Yazid Abubakar ya fitar ta bayyana cewa lamarin ya faru ne a ranar Talata 9/Yuni/2026 inda 'yan bindiga rike da mak**ai wanda s**a hada da RPGs, GPMGs, da bindigu ƙirar AK-47 sanan s**a kai hari kan wasu al"ummomi

‎Kakakin ya ce jami'an tsaro sun yi gaggawan Kai ɗauki bayan sun samu kiran neman agaji na gaggawa , wanda nan take aka tura tawaga da ta ƙunshi jami’an rundunar 'yan sanda ta Maru da Sojojin Operation Fansan Yamma da jami'an VCRU da kuma 'yan sa-kai, karkashin jagorancin DPO na yankin.

‎Kakakin ya ƙara da cewa jami'an tsaron sun yi musayar wuta da 'yan bindigar, lamarin da ya tilasta wa 'yan bindigar guduwa.

‎DSP Yazid ya ƙara da cewa babu asarar rai ko jikkata a tsakanin jami’an tsaro da mazauna yankunan da lamarin ya shafa. Ya kuma tabbatar da cewa an ƙara tsaurara matakan tsaro a yankin, yayin da ake ci gaba da farautar waɗanda s**a tsere.

Allah sarki uwa Kenan Allah ya karawa mahaifiyar kowa lafiya da nisan kwana 🤲
10/06/2026

Allah sarki uwa Kenan Allah ya karawa mahaifiyar kowa lafiya da nisan kwana 🤲

Address

Kano

Telephone

+2348074198240

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Queen luba posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Queen luba:

Share