Al'adun Hausawa a Da,da Yanzu.

Al'adun Hausawa a Da,da Yanzu. AN BUDE WANNAN SHAFI NE,SABODA TUNATAR DA KAWUKAN MU
BISA KYAWAWAN AL'ADUMMU NA HAUSA,

WADAN DA AYA Mungode

Dan Bunkasa Harshen Hausa da Al'adunsa,
Muna Maraba da shawarwarinku Domin wannan shafi naku ne.

INA FATA DA MAGUZAWAN DA ABOKAN BURMINSU DUK KUN GANE SU A FARAFAGANDAR TSIYA TA KARYAR HAUSA ZALLAYanzu mun fara ma hut...
14/12/2025

INA FATA DA MAGUZAWAN DA ABOKAN BURMINSU DUK KUN GANE SU A FARAFAGANDAR TSIYA TA KARYAR HAUSA ZALLA

Yanzu mun fara ma hutawa da dogon bayani kan wadannan ‘yan kwangilar rusa Arewa da yaki da musulunci masu fakewa da kwatowa Hausawa hakki alhali Hausawan su ke yaka, addinin Hausawan da Arewar Hausawa. Haba ai ni daga ganin yanda su ke salon rubutu na san ba Hausawa ba ne kuma ba su da alaka da Hausawa ko ruhin addinin Hausawa.

Yanzu ma sun fito fili tarwal sun fara kalmomi na logar addininsu. Haba waye bai taba jin masu s**ar jihadin Manzon Allah mai tsira da aminci ba da cewa “in dai addinin Allah ne, me ya sa sai an taya Allah yaki, ai ya fi karfin kowa a bar ma sa addininsa ya yi yaki da wadanda su ka bijire ma sa” To kun gani hatta sallah da musulmi ke yi wasu na ganin ai ba dole sai mutum ya yi kullum ba don ai in Allah ya na da tausayi ba zai umurci bayinsa su rika shan wahala haka ba!. Mutanen nan ba su dauka Allah ya sauko da mutum doron kasa don ya yi ma sa jarrabawa ba ne in ya ci jarrabawa ya samu sak**ako mai kyau in kuma ya fadi jarrabawa ga tanadin wadanda su ka fadi jarrabawa ko da ta nan makarantar duniya akwai maimaita aji ko in ya yi tsanani ma a sallami dalibi.

Don haka ina ribar ‘yan karyar Hausa zalla su bijirewa kananan kabilun da yawancinsu Allah ya nufa a ciki a ka haife su, su ka yi wuf su ka karbo kwangilar makiya su ka dinka rigar karya a soshiyal midiya ba sunan gaskiya, ba adireshi ba hoto sai zagin Shehu Mujaddadi da yi wa musulunci habaici? Matsoratan banza.

In Allah ya yarda an jima kadan zai dawo da cikekken bayani.

Nasiru Adamu El-hikaya

HOTUNA DA ZAYYANE-ZAYYANE KADAI SUN ISA NUNAWA DUNIYA, YANDA ‘YAN KARYAR HAUSA ZALLA SU KA RAINA HAUSA DA HAUSAWA!BA HOT...
14/12/2025

HOTUNA DA ZAYYANE-ZAYYANE KADAI SUN ISA NUNAWA DUNIYA, YANDA ‘YAN KARYAR HAUSA ZALLA SU KA RAINA HAUSA DA HAUSAWA!

BA HOTUNAN ALLO A TSANGAYA NA KASAR HAUSA SAI KAYAN KIDA KAMAR KUNGIYAR DUJJAL

Ko gabanin na yi bincike kan miyagun mutane da ke ikirarin karya na Hausa zalla, na fahimci sun raina Hausa da Hausawa tun da ai ba harshensu ba ne kuma cigaban Hausawa ba damuwarsu ba ce. K**ar yanda masu hikima ke cewa in ka na son gane kowaye mutum to dubi waye abokinsa. Daga yanayin hotunan karya da zayyane-zayyane da miyagun ke kwatanta Bahaushe da su za ka gane irin mummunan hoton Hausawa da ke zuciyarsu.

Kowa ya duba zai ga kusan duk masu ruruta fitinar nan ta kabilanci ba hotonsu, ba sunan gaskiya ba adireshi. Mutum na zaune a Zangon Kataf jihar Kaduna zai rubuta ya na Gwadabawa a jihar Sokoto. Wani na Mangu a jihar Filato sai ya rubuta ya na Babura a jihar Jigawa ko Batagarawa a jihar Katsina. Mutum na zaune a Sabon Tasha jihar Kaduna zai rubuta ya na zaune a Shinkafi da ke jihar Zamfara. Suna kuma duk wanda ka ga ya rubuta shi ALHAWSAWI ne ko Bahaushe waye-waye to tantirin makiyin Hausawa ne don zai iya zama Emos Kaza, Damuna A na ruwa da sauransu. Wallahi duk ranar da mutanen nan su ka yi zuciya su ka fito da kan su, magana ta kare ko kadangare na Bokkos a Filato ba zai saye su sisin kobo ba.

Zayyane-zayyane kuma daga wata mata ta na tikar rawa wasu ‘yan iskan gari su na yi ma ta kida, sai mace tsirara, sai wani na busa k**ar baubawan burmi, sai wani ya daga hannu duk ya fusata k**ar kafuri ya ji kiran sallah. Kai hoton Hausawa a zuciyar mutanen nan ta yi muni.

Hakika yanda miyagun nan ke daukar al’adar Bahaushe cewa shagali ce ta rawa da waka da sharholia zai tabbatar ma na wadannan mutane ba Hausawa ba ne, hasalima yaki su ke yi da Hausawa da rigar karya ta Hausawa don kona kasar Hausa ala bashi su kafa kasar su ta MIDDLE BELT can kuma BIYAFARA su yi dabdala a Enugu. Rasar kunyar mutanen nan ta kai furta wai ba laifin da IPOB su ka yi wa Hausawa ko Arewa. Wani mugun yaro a cikinsu ma cewa ya yi bai san kisan gilla da mutan Gwanin Gora su ka yi ta yi ba, bai san kisan kare dangi da a ka yi wa musulmi a Zangon Kataf ba. Yanka matafiya a jihar Filato ma duk a wajensa shaci-fadi ne. Wani ma da ya yi mankas da kunu sai ya ce ‘yan Arewa munafukai ne sun ki magana kan ‘yan bindiga sun koma magana kan maharba da a ka kashe a jihar Edo! Shi a wajensa kar a yi magana kan kashe-kashe na Filato, kudancin Kaduna da Edo a koma batun ‘yan bindiga kadai na Arewa maso yamma. A fili ya nuna duk inda a ke kisan nan, garuruwan ‘yan Hausa zalla ne da yankinsu na kirkira wato MIDDLE BELT. Mun haska wani dan Eggon wato Alago da ke jihar Nasarawa da a ka dauka aikin Hausa zalla.

Ta hanyoyin daban-daban mun haska mutanen nan ba Hausawa ba ne kuma makiya kalmar shahada ne kazalika masoya IPOB ne. Zan haska wasu da har wa’azi su ke yi da sunan musulunci, amma shuka su a ka yi don su kunna wutar fitinar yaki tsakanin musulmi a Arewa.

A karshe k**ar yanda mu ka yi watsi da makiya Arewa da Najeriya su Ouba Ali Mohaman na K**aru, Kayode Salman Banjo da ‘yan IPOB da ke fesa fetur kan ciyayin kan jinkar Arewa; mu na godiya ga Allah da ya hutar da mu don miyagun nan da kan su, su ke tonawa kan su asiri, kuma dubunsu na gab da cika yayin da jami’an tsaro ke bincike kan su. Duk wani ALHAWASAWI da a ka cafke a maboyarsa kar ya ce ba mu gargade shi ba.

Nasiru Adamu El-hikaya

DAGA SALON RUBUTUN ‘YAN KARYAR HAUSA ZALLAH KADAI ZA KA GANE ZAGON KASA SU KE YI DA RIGAR HAUSAWA, KUMA HARIN SU KAN MUS...
14/12/2025

DAGA SALON RUBUTUN ‘YAN KARYAR HAUSA ZALLAH KADAI ZA KA GANE ZAGON KASA SU KE YI DA RIGAR HAUSAWA, KUMA HARIN SU KAN MUSULUNCI NE

HATTA ZAYYANE-ZAYYANE DA ZANE-ZANE DA SU KE YI, NA FITO DA HAUSAWA A MATSAYIN MA’ABOTA KIDA DA WAKA NE BA KARATUN TSANGAYA BA

Zagin Shehu Mujaddadi na kan gaba cikin alamun muguwar kwangilar makirci ta ‘yan karyar Hausa zalla. Hikimar zagin Shehu ita ce rushe jigo a tarihin hidima ga musulunci a wannan yankin na mu. Ko sau daya ba za ka ga miyagun nan na maganar mai ya sa Bature ya kawo addininin kirista har wasu daga masu bautar GIJI su ka shiga addinin su ka nemi yi wa GIJI da gizagizai kishiya ba. Ba za ka taba ji ko gani sun soki lamirin Turawa da su ka rika jidar karfafan mutanen Afurka ta yamma zuwa aikin gonakin reke a Amurka daure da sarka a matsayin bayi ba. Ba sa korafi kan kwashe dukiya da kayan tarihinmu da Turawa su ka yi.

Abu na biyu duk da ya gaza samun nasara tun daure Nnamdi Kanu shi ne jinjinawa Chukwua Nzegwu wanda ya sa bindiga ya harbe Firminiya Sir Ahmadu Bello da matarsa. Mai yabawa wanda ya kashe Sardauna a matsayin jarumi tabbas makiyin al’ummar Arewacin Arewa ne kuma makiyin musulmi ne. Ba a je ko ina ba sai mutanen su ka fito da ajandarsu ta mara baya ga wasu tsirarun ‘yan siyasa mabiya addinin kirista na Arewa ta tsakiya da su ka kirkiro sunan MIDDLE BELT. Na sa mu ku inda su ke cewa su na mara baya, MIDDLE BELT su fice daga Arewa. Asalin dalilin MIDDLE BELT shi ne kin jinin hatta alakanta yankin da Arewa don su a ganinsu sunan Arewa na Hausawa ne kuma ma’anarsa ta biyu musulmi!. Ban da Maguzawa da ke rakube a Arewacin Arewa, gaggan ‘yan karyar Hausa zalla ‘yan kananan kabilun wannan yankin ne da makiya Arewa su ka kirkira.

Mun sha haska Hausawan bogi da su ka fito daga Arewa ta tsakiya da su ne kan gaba wajen mara baya ga Bishop Wilfred daga Binuwai, wanda ya kai kara don neman Amurka ta kawo hare-hare Najeriya da nuna a na yi wa mabiya addinin kirista kisan kare dangi. Yau da gaskiya ta yi halinta har wakilan Amurka su ka shigo Najeriya sai tsit ka ke ji har sunan Wilfred na neman zama tarihi. Duk masu dogon baki da ke fatar ganin Amurka ta auna masallatan Jumma’a ta kawo hare-hare ko rutsawa da wasu ‘yan kauyukanmu su na wani taro k**ar hatsarin da ya faru kan masu Maulidi a Tudun Biri; sun ji kunya kuma sun shiga bakin ciki don mugun nufinsu ya ci tura. Ai kun ga ba su fadawa Amurka kisan da su ka yi a Gwanin Gora da Zangon Kataf ba.

Ga uku daga cikin manyan muradun ‘yan karyar Hausa zalla:

1.Tada fitinar yakin kabilanci tsakanin musulmi a kokuwar Arewa don karfafa makircin MIDDLE BELT da tallafawa IPOB da ‘yan ta’addansu ESN su ayyana kafa Biyafara.

2.Shiga rigar Hausawa don zuga Bahaushe ya dauka akwai wani musulunci daban da na Shehu Mujaddadi don haka ba lallai ya damu da zuwa masallaci ya yi sallah ba don wai limaman mabiya Mujaddadi ne. Nuna Kabila ta fi addini na daga hanyoyin yaki da riko da musulunci na Hausawa.

3.Rage karfin fada ajin Arewa a siyasance don ya zama za a iya yi wa manyan ‘yan siyasar Lardin sharri da cewa ‘yan kabila kaza ne don haka kar a zabe su. Hakan tabbas zai iya dora makiya karfin Arewa a kan madafu da za su iya wargaza Najeriya gaba daya ta hanyar ware musulmi daban sauran mutane daban. Akwai wani dan karyar Hausa zalla da ya taba alwashin za a iya neman musulunci a rasa a Arewa.

Da yardar Allah miyagu da iyayen gidansu, irin su Ouba na K**aru mai cillo harshen wuta Najeriya ya na yayyafa ruwa a K**aru ba za su ci nasara ba. Tuni ma muguwar manufarsu ta fara narkewa k**ar kankarar ruwan sanyi a rana.

Nasiru Adamu El-hikaya

LABARI MAI GIRGIZA KASA!Wannan shi ne *Hoton Musabaha ta Ƙarshe (Last Handshake)* a tsakanin manyan shugabannin biyu, wa...
04/12/2025

LABARI MAI GIRGIZA KASA!

Wannan shi ne *Hoton Musabaha ta Ƙarshe (Last Handshake)* a tsakanin manyan shugabannin biyu, wanda aka ɗauka wata huɗu (4) kacal kafin Yaƙin Bïafran ya ɓarke, ya shiga tarihi!

1. Yakubu Gowon: Shine Shugaban Ƙasa na Tarayyar Najeriya a lokacin.

2. Emeka Odumegwu-Ojukwu: Kuma Shine Wanda ya zama Shugaban Jihar Bïafra mai neman cin gashin kai.

Wannan Musabaha ce ta ƙarshe kafin dangantaka ta lalace kuma ƙasar ta shiga cikin mummunan yaƙi!

Tafiyar Ojukwu da Mĩƙa Waya

Odumegwu-Ojukwu ya kasance jagoran Bïafra tsawon lokacin yaƙin, daga Shekarar 1967 har zuwa 1970. Amma lokacin da aka cika shi da ruwa a gaba, ya yi abin da ya girgiza tarihi:

* Ya hau Jirgin Sama ya tsere zuwa ketare
* Ya bar Philip Effiong, wanda shine ke biye da shi a matsayi, don ya miƙa wuya ga Gwamnatin Tarayyar Najeriya a madadin Bïafra.

Wannan hoto yana ɗauke da ƙarin ma'ana fiye da yadda ake zato. Ya nuna wani lokaci na ƙarshe da aka yi fatan za a sasanta kafin faɗa ya fara.

Wane darasi kuka koya daga wannan gagarumin babi na tarihinmu?

Ku faɗi ra'ayoyinku a ƙasa! 👇

Gordon, wani tsohon bawa, ya na nuna tabo a bayansa sak**akon bulala da aka yi masa a Baton Rouge cikin jihar Louisiana ...
22/11/2025

Gordon, wani tsohon bawa, ya na nuna tabo a bayansa sak**akon bulala da aka yi masa a Baton Rouge cikin jihar Louisiana ta kasar Amurka

Ya tsere daga wata gona a Mississippi. Bayan da jami'an kiwon lafiya s**a ga tabon sai s**a bukaci a dauki hotonsa don rubuta shi a cikin tarihi. An yi masa bulala sau da yawa har tabo ya fara tasowa a kan tabo, an dauki hoton a shekarar 1863 Yau Shekaru (162) Kenan.

ABIN MAMAKI: Yadda Aka K**a Fasto da Zargin Kai wa 'Yan Bindiga Mak**ai a Jihar Filato.Najeriya ta shiga wani sabon babi...
16/11/2025

ABIN MAMAKI: Yadda Aka K**a Fasto da Zargin Kai wa 'Yan Bindiga Mak**ai a Jihar Filato.

Najeriya ta shiga wani sabon babi mai ban al’ajabi — Inda aka k**a wani malamin addinin kirista (Reverend Father) da ake zargi da kai wa ‘yan bindiga muggan mak**ai a Jihar Filato da kewaye.

Eh, ka karanta daidai.
Wani limamin coci — wanda aka yarda da shi a matsayin mai addu’a, zaman lafiya da kare rayuka — yanzu ana zarginsa da taimakawa waɗanda ke hallaka al’umma marasa laifi.

Rahotanni sun ce jami’an tsaro sun gano yana *tsara safarar mak**ai iri-iri*, wanda ake zargi da taimakawa 'yan ta'adda wajen sace mutane, kai hari da kashe-kashe.

Yanzu sai na sake tambaya...

Lokacin da wasu daga cikinmu s**a ce *matsalar tsaro a Najeriya ba ta addini bace*, mutane s**a ci mutunci, suna cewa muna goyon bayan mugunta.

Amma yanzu, me za su ce?

Shin waɗanda s**a yi gaggawar garzayawa Amurka suna kiran abun “kisan kiyashi ga Kiristoci” za su kai wannan labari wajen Donald Trump domin daidaita labarin?

Domin gaskiya ita ce:

Tsaro a Najeriya ba ya da addini.
(1) Ba ya sanye da zobon saliba ko tesbihu.
(2) Ba ya rike Alƙur’ani ko Littafi Mai Tsarki.
(3) Yana buya a daji, yana sayen mak**ai, yana halaka rayuka — Musulmi, Kirista, kowa.

Amma duk lokacin da aka fadi gaskiya, mutane kan mayar da martani da ji ba da hankali ba.

Wannan k**a ta bayyana gaskiya mai zurfi:

(1) Matsala laifi ce, ba addini ba.
(2) Mugaye suna ko’ina — a coci, a masallaci.
(3) Kuma yaƙi yana da su ne, ba da addininsu gabaɗaya ba.

Idan har Reverend Father za a k**a da kai wa 'yan bindiga mak**ai, to watakila... matsalar Najeriya ta fi “kisan kiyashi a ɓangare guda” girma da rikitarwa.

Mu kira gara gari.
Mu gyara matsalar tsaro — ba mu juya ta ta zama siyasa ko neman tausayi daga ƙasashen waje ba.

Daga: Abdul Mdk

CIGABAN MANTA SALLAH — MAI RUBUTU A TSAYEBayan da aka zauna gaban kwamiti domin binciken zargin da Mista Barry Burgess y...
10/11/2025

CIGABAN MANTA SALLAH — MAI RUBUTU A TSAYE

Bayan da aka zauna gaban kwamiti domin binciken zargin da Mista Barry Burgess yake yi a kan Getso, sai shi Barry ya ce yana son shirin Manta Sallah na mako na 5, 7, 10, da kuma ragowar ukun ƙarshe a fassarasu zuwa Turanci.

Hakan kuwa aka yi, domin ma, mai gaba ɗaya aka yi. Duka guda goma sha uku sai da aka fassarasu zuwa Turanci. Daga nan ne aka ba Halilu Getso damar kare kansa a kan zargin Barry.

Ya ce, da farko dai, wannan shiri ya ta’allaka ne a kan yadda rayuwar Turawa take, wato abubuwan da suke yi na al’adunsu da tsare-tsarensu waɗanda ba a sani ba. Sai kuma abubuwan da ba sa yi amma ake jita-jita cewa suna yi, da kuma waɗanda suna yi ɗin amma an juya labarin sama ta koma ƙasa.

Ya ƙara da cewa, misali: mu a Najeriya, akwai Hausawa da suke tunanin cewa Bature zai fito waje ya je majalisa ko wata maciya a ƙarƙashin bishiya ko rumfa ya zauna, a kawo masa abinci yaci, ko kuma ya fita wajen mai shayi a haɗa masa shayi da biredi da ƙwai 🥚 k**ar yadda tamu al’adar take.

To a can, sam, ba haka bane. Ya ce, mu bamu da juriyar bibiyar abu, ko da kuwa haƙƙinmu ne, bama iya kai-kawo wajen ganin an biya ko an bayar. Amma a can, idan akwai wani haƙƙi na mutum ko na gwamnati, to dole sai an bibiya.

Ya ce, maganar ta’addanci da Mista Barry yake cewa na ce Turawa suna yi, to bai fahimta bane. Wato farkon zuwana nan (London), na kunna talabijin a gidan da nake, sai naga wata mata da aka nuna cewa Allah ya bata haihuwa, kuma mace mai lalura ce. Ita kuma bata son ƴa mace, ballantana mai lalura.

Kullum sai ta fito da ita waje ta ajiye a kan keken masu lalura, ta barta a nan babu kayan kirki a jikinta, ga kuma dusar ƙanƙara 🌨️. Ita a dabararta, bata so a tuhume ta da laifin kisan kai, shiyasa take yi mata wannan azabar domin ta mutu ta huta.

To kuma da yake Allah shi ne mai kashewa da rayawa, sai gashi ta ƙi mutuwa, amma tana matuƙar shan wahala. Ko ni daga inda gidana yake a London zuwa ofishinmu na BBC, train 🚉 nake hawa. Kuma daga inda yake ajiyeni zuwa harabar BBC, yawanci rigata da hulata suna cike da ƙanƙarar snow.

Wannan labarin ba ƙirƙira bane, a labarai na gani kuma ana hira da ita wannan matar. Ku bincika, zaku tabbatar da cewa haka abin yake. A Afrika kuwa, abin mamaki ne a ce uwa ta yiwa ɗiyarta haka.
Sai na tambayi Mista Barry,

“Yanzu ka gamsu da abin da nake faɗa, ko har yanzu kana kan batunka na cewa ina ɓata muku suna?”

🧾 Batun bin haƙƙi

Getso ya ce, akwai abokin aikina da ya hau jirgin ƙasa daga wata unguwa a London zuwa wata unguwa, sai aka samu matsala, wato a inda zai sauka jirgin bai tsaya ba sai a tasha ta gaba.
Mai karɓar tikiti (ticket collector) ya rubuta masa adireshin inda zai biya ragowar kuɗin da ake binshi, sannan ya bashi da nashi adireshin.

Amma abokin aikin ya ƙi zuwa ya biya. Bayan wa’adin da s**a bashi ya cika, sai s**a sake rubuta masa wasika ta tunatarwa cewa har yanzu bai biya ba. Wani abin mamaki, wasikar haɗe take da kan sarki (official letter), kuma kuɗin kan sarkin sun fi waɗanda ake binshi yawa.

Sai dai duk da haka, s**a rubuta masa sau uku ba tare da gajiyawa ba, har sai da ya gaji da kanshi, yana mita da surutu, ya je ya biya haƙƙinsu sannan ya huta.

“Wannan abin cigaba ne,” in ji Getso.
“Zai nuna wa shugabannin Afrika da ‘yan Afrika yadda ake riƙe aiki da gaskiya da rikon amana.
Kuma zai haskawa al’ummarmu yadda ake bautawa ƙasa da gudummawar da kowane ɗan ƙasa zai iya bayarwa domin cigaban ƙasarsa.”

A taƙaice dai, kwamiti ya gano cewa Getso yana kan daidai, kuma ya bayar da umarni cewa ya ci gaba daga inda ya tsaya — saboda abin birgewa ne.

Saboda haka, bashi da wata matsala. An ba da damar ci gaba da shirin daga inda aka tsaya.

Wannan shi ne cikakken abin da ya faru tsakanin Bature Mista Barry Burgess da kuma Bahaushe Halilu Ahmad Getso a Rediyo BBC Hausa London.

© Jiya Ba Yau Ba.

MANTA SALLAH, MAI RUBUTU A TSAYE. Wannan shi ne sunan wani shiri da Alhaji Halilu Ahmad Getso ya gabatar lokacin da yake...
10/11/2025

MANTA SALLAH, MAI RUBUTU A TSAYE.

Wannan shi ne sunan wani shiri da Alhaji Halilu Ahmad Getso ya gabatar lokacin da yake aiki da BBC Hausa, Landan. Shiri ne da ya jawo masa s**a daga wasu Turawan ƙasar Birtaniya, wadanda s**a yi zargin cewa yana cin zarafinsu ne ta hanyar abin da ke ƙunshe a cikin shirin.

Tabbas, labarin da nake son bayarwa zai ɗan iya ɗaukar lokaci, amma kuwa zai amfanar da ma’abota son aikin jarida, musamman ɗaliban ilimi, da duk wanda ke da son tarihi. Don haka, ku biyo mu a hankali.

Karin magana ta “Manta Sallah Mai Rubutu a Tsaye” ta samo asali ne tun lokacin da Turawan mulkin mallaka s**a shigo Najeriya, musamman yankin Arewa. Karin maganar tana da tsawo, amma yawancin ɗaliban ilimi basa sanin ƙarshenta. Ga cikakkiyar karin maganar k**ar yadda take:

“Manta Sallah Mai Rubutu a Tsaye, Huntu Ubangijin Mai Riga, Mai Shawara Ɗari Ɗaya Babu, Ta Ɗarin Ya Fasa, Ku Ci Gari Ku Kwana a Daji.”

Yanzu bari mu ajiye wannan bangaren, mu koma ga labarin shirin “Manta Sallah Mai Rubutu a Tsaye”, wanda aka gabatar a shekarar 1975 a BBC Hausa. Wannan ya faru ne bisa tsarin da gidan rediyon ke amfani da shi a lokacin, cewa duk wanda ya yi aiki a BBC, ana ba shi damar ƙirƙirar shiri na musamman na tsawon kwata ɗaya ko biyu kafin ya kammala aikinsa ya koma gida.

Haka abin ya kasance ga Halilu Getso, wanda FRCN Kaduna s**a ba da aron sa zuwa BBC na tsawon shekaru biyu. Kafin cikar wannan wa’adin, sai ya ƙirƙiri shirin Manta Sallah Mai Rubutu a Tsaye, wanda ya ƙunshi season ɗaya mai episodes goma sha uku.

Sai dai daga baya aka kai ƙarar Getso wajen shugabansu na lokacin, David Warren, sannan aka mika ƙarar zuwa ma’aikatar cikin gida ta Ingila da kuma ofishin jakadancin ƙasar a Landan. Wanda ya kai ƙarar kuwa shi ne wani Bature mai suna Barry Burgess.

A cikin ƙarar da ya gabatar, Barry Burgess ya zargi Halilu Getso da cin zarafin Turawa a cikin shirin, yana cewa kalamansa sun ƙunshi ƙazafi, ɓatanci, da nuna bambancin launin fata.

David Warren, babban daraktan BBC Hausa a lokacin, bai ɗauki zancen da wasa ba. Sai dai kafin ya yanke hukunci, ya tabbatar da cewa an kafa kwamitin bincike domin gano gaskiyar lamarin, k**ar yadda umarni ya zo daga sama.

A cikin rahoton ƙarar, an zargi Getso da cewa:

Yana nuna cewa Turawa basa da imani,

Yana cewa suna ƙin wanda ba nasu ba,

Kuma yana zarginsu da rashin yafiya da girman kai.

Waɗannan sune manyan tuhume-tuhumen da aka gabatar a kansa a wancan lokaci. Ba tare da bata lokaci ba, aka kira shi domin ya kare kansa idan yana da abin karewa.

Zamu ci gaba da wannan labarin a gaba.

© Jiya Ba Yau Ba.

10/11/2025

❤️يَأَيُّهَا الَّذِينَ امَنُوا صَلُّوا عَلَيْهِ وَسَلِّمُوا تَسْلِيمًا❤️

- _Lugude_ MAKAMAN KANO BA KA YI KIWON BANZA BA. Ran 2 ga watan Fabrairu na shekarar 1942, Mak**an Kano ya ta da baraden...
07/11/2025

- _Lugude_

MAKAMAN KANO BA KA YI KIWON BANZA BA.

Ran 2 ga watan Fabrairu na shekarar 1942, Mak**an Kano ya ta da baradensa, ya ce su tafi duk inda Amareta ya ke, a bugo shi da jama’a tasa, a kawo su a ɗaure. Aka yi shiri aka tafi. Da zuwan baraden nan, sai s**a iske Amareta bisa kujera mutane sun kewaye shi, sai molo da warin giya ke tashi. Ana masa kirari: ‘‘Umaru dan Kurtullu Sarkin Ɓarayi! Sata a wurinku ba dashe ba ce, gado ce. Ubanka ya yi, kakanka ya yi, kuma ɗanka zai yi, jikanka zai yi!’

Da s**a yi arba da baraden nan, sai ya yi wa sojansa umurni, nan da nan sai ga su kowa da kibiya ɗane a bakansa. Da ganin haka sai Kutiki ya murza hular layu, ya sauko daga doki, ya tara ƙasa a gabansa misalin tukubar tsire. Sai ya koma kan doki ya ce, ‘Bismilla!’ ‘Ɓarayin nan s**a yi ta aikowa da kibiyoyi k**ar zubar ruwan sama. To, kowace kibiya ta zo, ba ta sauka ko ina, sai kan ’yar tarin ƙasar nan, har kibiyoyi s**a ƙare duk.
Kutiki da Afilu s**a matsa dawaki, sai ga su a tsakiyar askarawan. Sai takuba da gatura da wuƙaƙe a ke ta amfani da su. Duk mak**an ɓarayin s**a lalace, aka shiryo su a ankwa aka kawo su gun mak**a. Mak**a ya yi murna ƙwarai da gaske da wannan.
—M. Talle Daura diresan Wudil.

📌DAYA DAGA CIKIN KAYAN AZABTARWA MAFI BAN TSORO😨Sun kira shi Kujerar Yahuda. Wani nau'in azabtarwa ne da ake fara wa mut...
28/10/2025

📌DAYA DAGA CIKIN KAYAN AZABTARWA MAFI BAN TSORO😨

Sun kira shi Kujerar Yahuda.
Wani nau'in azabtarwa ne da ake fara wa mutum tsirara, a zaunar da mutum kan tsinin samansa.
Sai a fara gangaro da mutum a hankali, cike da radadi.

An ce akan soka mutane ne ta wuraren da s**a Fi rauni a jiki, ko ta dub*ra(Namiji kenan) ko ta far*i (mace kenan).
Azabtarwan kan iya ɗaukan sa’o’i, wani lokacin har kwanaki.
Masu azabtarwan har ma suna rataye abubuwa masu nauyi daga idon sawun wa'anda ake azabtarwan. s**an tilasta musu gangarowa ta inci da inci.
An fara ambaton Kujerar a cikin Turai, ƙarni na 19.

An nufi Kujerar Yahuda ne an don azabtar da mutane a bainar jama’a. An ce an yi amfani da ita don tilasta ikirari, hukunta ’yan bidi’a, ko tsoratar da duk wanda ya ƙalubalanci iko.
Wahalar ba ta ɓoye ba, akan nuna ta ga bainar jama'a, dan a wulakanta mutum.

A yau, ana iya gani kwafin(copy) Kujerar Yahuda a gidajen tarihi na azabtarwa a duk faɗin duniya.

Darasi: Wato duk Wanda ya kirkiri wannan abun, ba karamin mugu bane. Tabdi jam😱



ENGLISH TRANSLATION IN THE COMMENT SECTION 👇

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Al'adun Hausawa a Da,da Yanzu. posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Al'adun Hausawa a Da,da Yanzu.:

Share