Al'adun Hausawa a Da,da Yanzu.

Al'adun Hausawa a Da,da Yanzu. AN BUDE WANNAN SHAFI NE,SABODA TUNATAR DA KAWUKAN MU
BISA KYAWAWAN AL'ADUMMU NA HAUSA,

WADAN DA AYA Mungode

Dan Bunkasa Harshen Hausa da Al'adunsa,
Muna Maraba da shawarwarinku Domin wannan shafi naku ne.

TARIHIN SHEIKH MODIBBO JELANI AL-TIJJANI, YOLAAn haifi Sheikh Modibbo Abdul-Qadir Jelani Ibn Modibbo Altine wanda aka fi...
25/10/2025

TARIHIN SHEIKH MODIBBO JELANI AL-TIJJANI, YOLA

An haifi Sheikh Modibbo Abdul-Qadir Jelani Ibn Modibbo Altine wanda aka fi sani da "Sheikh Modibbob Jelani Yola" a shekara ta 1903 a wani kauye mai suna "Badara" dake cikin jihar Bauchi. An ba shi sunan Abdul-Qadir Jelani saboda mahaifinsa wato (Modibbo Altine) ya kasance mai riko da Darikar Sufate ta Kadiriyya.

Modibbo Jelani ya fara koyo a wurin mahaifinsa tun yana dan shekara 14. Mahaifinsa ya rasu, ya bar Modibbo Jelani, kaninsa Muhammad Tukur da kuma wata kanwa mai suna Sutrah.

Don ci gaba da karatu, Modibb Jelani ya zagaya wurare da dama, ya kuma koyi darasi daga manyan malamai na wancan lokacin. Daga cikin wuraren da ya ziyarta da kuma malaman da ya koyo da su sun hada da Kano da Zariya; wato Mallam Sani Harazimi da Shariff Sani Tudun Wada Zaria. Daga nan ya koma Kano zagaye na biyu domin karin neman ilimin addinin Musulunci bayan ya karbi Darikar Sufaye ta Tijjaniyya. Yayi "Tarbiyyah" a hannun Babban Shehi, "Shaikh Tijjani Usman Yan Mota" , Kano (wanda Sheikhul Islam Alhaji Ibrahim Inyass RTA ya sabunta masa shi).

Bayan shekaru, Modibbo Jelani ya koma garinsu (Badara) ya yanke shawarar ci gaba da tafiya Makka kamar yadda mahaifinsa marigayi ya fara. Ya zauna a wurare daban-daban a cikin garin Gombe kuma yana da mabiya da yawa wadanda dalibansa ne da sahabbansa. Ya shiga Adamawa ya sauka a “Gudumiya” (wani kauye a karkashin Hong L.G.A, Adamawa). Lamido Muhammadu Mustafa (1928-1946) ya gayyace shi kan cewa ya dawo Yola da zama, amma shi kuma ya zabi zama a Gudumiya sabida ya fi jin dadin zama a garin.
Duk da haka, bayan wasu shekaru Modibbo Jelani ya gamsu da bukatar Lamido Ahmadu (1946-1953) daga bisani ya koma Yola da zama.

Ya sadaukar da rayuwarsa wajen koyo da koyarwa da yada addinin Musulunci da Daular Sufanci ta Jijjaniya ta hanyar manyan dalibansa, mabiyansa da kuma yayansa. Modibb Jelani ya rasu, aka binne shi a gidansa da ke Yola yana da shekaru 83 a duniya a shekara ta 1986.
Allah ya jaddada Rahma

Kotun ta ce nan da kwanaki 60 a daura wa Ashiru da sahibarsa aure. Kotun ta kuma umurci hukumar tace fina-finai ta jihar...
20/10/2025

Kotun ta ce nan da kwanaki 60 a daura wa Ashiru da sahibarsa aure. Kotun ta kuma umurci hukumar tace fina-finai ta jihar kano da ta sa ido don ganin an daura wannan auren.

Mene ne fatanku gare su?

Hoto: Ashiru FB

10/10/2025

*TALLA TALLA TALLA*

*GURU NA FAMILY PLANING.*

Amincin Allah Su Tabbata Agareku Dafatan kuna Lafiya Cikin Amincin ALLAH.

Albishirinku Yan Uwa Masu Girman Daraja Da Albarka,A Yau Munzo Muku Da Guru Na Tazarar Haihuwa.

Wannan Guru Ne Na Tazarar Haihuwa,Idan Mace Ta Ɗaura Wannan Guru A ƙugunta Yayi Kwana Ɗaya A Jikinta Sai Tayi Shekara Ɗaya Bata Haihu Ba, Haka Nan Idan Yayi Kwana Biyu a Jikinta Shekara Biyu Zatayi Bata Haihu Ba.

Ma'ana Duk Adadin kwanakin Da Wannan Guru Yayi A Jikinta Shine Shekarun Da Zatayi Bata Haihu Ba.

-ABINDA ZA'A KIYAYE SHINE:-

Matar Da Zata Ɗaura Wannan Gurun Ta Tabbata Be tsinke Ba a Lokacin Da take Ɗaura Shi,Sannan Ta kiyaye Karya Kunce Har Sai Tayi Adadin kwanakin Da take Buƙata.

Sannan Ta Nisanci Kusanta(Saduwa) a Lokacin Da Take Ɗaure Dashi a ƙugunta.

Ga Wanda Suke Da Buƙata Sai Su Tuntuɓemu a Wannan Number:-

-07066778330

Dan Asalin Jihar Katsina Injiniya Ibrahim Lawal Dankaba Ya Kera Motar Sulke Domin Kare Al'umma Rubutun Katsina TimesWani...
06/10/2025

Dan Asalin Jihar Katsina Injiniya Ibrahim Lawal Dankaba Ya Kera Motar Sulke Domin Kare Al'umma

Rubutun Katsina Times

Wani ɗan asalin Katsina, Injiniya Ibrahim Lawal Dankaba, ya ƙera wata mota ta zamani mai sulke wadde aka sanya mata suna “Begua” kalmar Hausa da ke nufin dabba wadda take da ƙashin kariya a jikin ta.

A cikin tattaunawar da Majiyar Accuracy News Hausa "Katsina Times" ta yi da matashin Injiniya Dankaba ya bayyana cewa, aikin wata hanya ce ta tsaron al’umma domin ƙara ƙarfin rundunonin tsaro na Gwamnati da kuma dawo da kwarin gwuiwar jama’a a yankunan da matsalar tsaro ta addaba.

“Mun zaɓi wannan suna ne saboda ma’anarsa. Begua ba ta fara farmaki sai an cuce ta. Idan aka kawo mata hari ne kawai take kare kanta. Haka nan wannan mota ba don tada rikici aka yi ta ba, sai don kariya idan aka kawo wa al’umma hari,” in ji shi.

Motar Begua ta bambanta da sauran motocin sulke da ake gani a kasuwa saboda tana amfani da taya-trak (tracked APC) maimakon taya na al’ada. A cewar Injiniya Dankaba, hakan ya fi dacewa da yanayin ƙasar nan da kuma buƙatun tsaro na karkara.

Za ta iya shiga gonaki, dazuzzuka da ƙasa mai laka.

Ba ta cika makalewa a cikin caɓo ko hanya mara kyau ba.

Tana bayar da kariya mai ƙarfi ga mutanen da ke cikinta.

Dankaba ya ce aikin ya wuce matakin zane a takarda, yanzu haka ana kan gwajin samfurin farko. Ya ƙara da cewa an fara tunanin aikin tun kusan shekaru biyu da s**a wuce a lokacin da hare-haren ’yan ta’adda da ’yan bindiga s**a ƙaru a arewacin Najeriya.

“A cikin ’yan makonni masu zuwa, za mu gayyaci jama’a da manema labarai domin kallo da shaida yadda Begua za ta yi aiki,” in ji shi.

Ya jaddada cewa aikin ba zai maye gurbin jami’an tsaro ba, sai dai ƙarfafa musu guiwa.

“Wannan aikin haɗin kan al’umma ne domin tallafawa gwamnati da hukumomin tsaro. Muna son haɗin kai tsakanin jama’a, gwamnati da masu ruwa da tsaki domin kare rayukan mutane,” ya bayyana.

Ga mazauna yankunan da ke fuskantar matsalolin tsaro, Injiniya Dankaba ya ce:

“Mun san irin fargaba da damuwar da jama’a ke ciki. Saƙonmu shi ne muna ɗaukar matakai na zahiri don taimaka musu. Duk da cewa gwamnati da jami’an tsaro su ne ginshikin tsaro, al’umma da kirkire-kirkiren cikin gida ma suna da rawar da za su taka. Begua wani ɓangare ne na wannan gudummawa,” in ji shi.

Katsina Times za ta kawo muku cikakkiyar tattaunawa da aikin Begua ta kafafenmu na Katsina Times TV (YouTube), Katsina City News (Facebook), da sauran shafukanmu na sada zumunta.

Hoto: Katsina City News

Mahaifiyar Attajirin Dan Kasuwa Alh Aliko Dangote, Wato Mariya  Sunusi Ɗantata, Kuma ƴar Wan Hamshaƙin Attajirin Wanda Y...
06/10/2025

Mahaifiyar Attajirin Dan Kasuwa Alh Aliko Dangote, Wato Mariya Sunusi Ɗantata, Kuma ƴar Wan Hamshaƙin Attajirin Wanda YaRasu Kwana Nan, Alh Aminu Alasan Ɗantata {Amin-Dogo}

Da yawa mutane ba su san wacece Mariya Sanusi Dantata ba, kawai dai suna kallon tacne a matsayin mahaifiyar shahararren Attajirin nan na Afrika Aliko Dangote.

Cikakken sunanta shine, Uwar Marayu da Marasa Gata, Domin idan zan yi maka ta babban mahaukaci zan iya rantse maka, duk fadin Afrika babu wanda ke ciyar da al'umma abinci tare da agazawa talakawa sama da ita, wallahil azim, ko Gwamnati ba za ta iya abinda wannan baiwar Allah take yi na ciyar da bayin Allah ba, saboda idan kazo gidan Mariya, sai ka tausayawa kudi, duk jihar Kano, duk Nijeriya, duk Afrika babu inda kudi suke kuka da ihu sama da gidan Mariya Sanusi Dantata, domin Mariya wani kamfani ta kafa na musamman domin ciyar da Bayin Allah tare da farantawa rayuwarsu.

Idan ka je kofar gidanta ka ga yadda ake ciyar da mutane kamar a wasan kwaikwayo, na san duk tsananin kiyayyar ka da Mariya Sanusi Dantata sai ka ce Ubangiji ya gafartawa Mariya.

Gidan Mariya ya zama wata inuwa wacce talakawa suke zuwa su huta, Mariya ta zama wata katanga wacce al'umma ke jingina da ita su sami saukin rayuwa. Abokina Sadik Abdullahi Koki
Tunda a unguwarku take ai zaka bada sheda akanta.

Malam ka zo jihar Kano kofar gidan Mariya a sannan za ka san wacece ita.

Akalla talakawa sama da dubu hamsin kullum suna cin abinci tun daga safe har zuwa dare a jikin Mariya domin da yawansu ba su da wata hanyar samun abinci sai a gidan Mariya.

Kullum ciyarwa ake yi gidan Mariya.

Abincin asibiti daban
Abincin gidan nakasassu daban.

Abincin Alumma na gari daban.

Banda wanda take rabawa mutane ba tare da an kirga ba.

Akalla Mariya tana da ma'aikan da take baiwa albashi sama da mutum dubu a karkashinta, wadanda ta ajiye saboda kawai kula da ciyar da Bayin Allah.

Daga Cikin ma'aikatanta akwai.

Masu saran itacen girki.
Masu nikan garin tuwo.
Masu dauko Itace.
Masu cefane daban.
Masu girki daban.
Masu rabon Abinci daban.
Masu markade daban.
Masu tuka mota

Yakamata kowacce mace ta karanta wannan labarin.Sunan labarin Zalincin Turawa lokacin bauta da samun ilimin cutukan mata...
06/10/2025

Yakamata kowacce mace ta karanta wannan labarin.

Sunan labarin Zalincin Turawa lokacin bauta da samun ilimin cutukan mata: Labarin Anarcha, wacce a yau ake kira da Mahaifiyar Ilimin Cututtukan Mata.

Anarcha Westcott baiwa ce a garin Alabama a shekarun 1840s. Tana 'yar shekara 16 aka mata ciki, tana yar shekara 17 ta fara naƙuda, ta yi naƙuda na kwana uku wanda ya bar ta da cutar fistula—wata cuta mai tsanani da ke haifar da zubar jini da mutuwar ɗan da yake cikin.

Wani azzalumin Likita mai suna J. Marion Sims ya yi mata tiyata daban daban sama da sau 30 ba tare da maganin kashe zafi ba. Haya ya dinga yaga mata gabanta yana dinkewa, duk wata kalar tiyata sai da ya gwada ya koya a kanta. Tana ihu tana ƙaraji amma babu mai taimakonta saboda ita baiwa ce, batada ƴanci ko mutuwa tayi babu damuwa.

A tsakanin 1845 zuwa 1849. Ya yi amfani da ita da sauran bayi mata biyu—Betsy da Lucy—don gwada hanyoyin tiyatar gaba. Sun sha azaba mai yawa. Haka akadinga yi musu ciki ana gwajin aiki akansu.

A lokacin da yayi mata wannan rashin imanin, ta kamu da wani ciwo a gaban ta. Ku yi tunani, ga zafin yagu sama da talatin duk a gabanta, ga kuma wani irin ciwon sanyi da ta kamu dashi. A ƙarshe, ya yi nasara wajen warkar da ciwon data kamu da shi.
Sims ya zama mashahurin "Uban Ilimin Cututtukan Mata" kuma ya sami dukiya mai tarin yawa da lambobin girmamawa da yawa. Amma Anarcha ba ta sami komai ba—ba 'yanci, ba ko sisi, ba yabo.

Yau, ana kiranta "Mahaifiyar Ilimin Cututtukan Mata" saboda sadaukar dole da ta yi. Labarin ta yana tunatar da mu cewa yawancin ci gaban kimiyya yana zuwa ne akan azabtar da mutane da ba su da zaɓi. Amma yanzu tunda an daina bauta, a koma yin gwaji akan ɓeraye.

Anarcha ta cancanci a tuna da ita—ba a matsayin abar gwaji ba, a matsayin mace mai ƙarfi wadda azabarta da ita da akayi ya taimaki mata miliyoyin mata da s**a zo bayanta.

A duk lokacin da kika zo haihuwa, ki tuna azabar da Anarcha ta sha domin ku samu damar haihuwa cikin sauki.


✍️ Copied
Yahuza Rabiu Garba

Wannan  hoto akwai karatu cikin sa, wannan fa shahararren maikudin nan ne wanda a yanzu yake riqe da lamba ta biyu a zun...
25/09/2025

Wannan hoto akwai karatu cikin sa, wannan fa shahararren maikudin nan ne wanda a yanzu yake riqe da lamba ta biyu a zun-zurutun malu masu gidan rana a wannan qasa tamu ta yan war waso, shine yake durqushe a gaban babban yayayn sa kuma magajin uba Khalifa Alh Nafiu Ishaqa Rabiu,

Shin ya kakewa wanda s**a girmeka a gidan ku saboda tunanin cewa ka mallaki yan kudin da basu fi na ce fane ba, ko kuma Ilimin da bai zamar maka jagora ba.

Ko kuma ma abin takaici kake jin ka samu wayewar da bata wuce Sanin kasuwar garin ku ko kauyen ku ba, ko kake jin kafi shi iya sa rigar da bata wuce ayi wa doki kwalliya da yadin da ka saka ba.

To ina gaya mana mu bi duniya a sannu, mazajen da s**a riga ka kwana to tuni sun riga ka tashi, kar wata baiwa taka da ka samu tasa ka rena halittar ALLAH.

🖊️ Sadiq Quraysh

ƘARIN BAYANIShi wannan gunki na Tsumburbura (mace ce) ta dade ana bauta masa a duniya. An ce hatta Fir'aunonin Masar sun...
16/09/2025

ƘARIN BAYANI
Shi wannan gunki na Tsumburbura (mace ce) ta dade ana bauta masa a duniya. An ce hatta Fir'aunonin Masar sun same ta sunyi ta'ammuli da ita. Sune ma s**a gina mata Dutsen Dala. Dutsen Dala ba wai dutse bane, irin dalar nan ne na Egypt da aka sani wato Pyramid. Dama ko a Egypt din wuraren bauta ne.

Masana tarihi sunce Allah (SWT) Ya ambaci gunkin Tsumburbura a Qur'ani cikin manya manyan gumaka inda Yayi hani da bauta musu.

_Wa qalu la tazarunna Wuddan wala Suwa'a , wala Yagusa wa Ya'uƙa wa Nasra._

Wudda
Suwa'a
Yagusa
Ya'uka
Nasra

Dukkan su gumaka ne a fadin duniya da ake bauta musu. To YA'UƘA shine gunkin Tsumburbura dake Kano.

Br.Magashi

TARIHIN TAKUTAHA DA LOKACIN DA AKA FARA YIN YA A KANO TUN ƘARNI NA 13TH MILADIYYA. Hawan Dala da ake da  Mauludi a Tarih...
16/09/2025

TARIHIN TAKUTAHA DA LOKACIN DA AKA FARA YIN YA A KANO TUN ƘARNI NA 13TH MILADIYYA.

Hawan Dala da ake da Mauludi a Tarihin Kano shin yaushe aka soma

Asali, kusan shekaru dubbai da s**a gabata, Kano ba gari bane da ke da Tsarin mulki ba, Shirayi(mazauni) ne kawai, kamar yadda marubucin wakar Bagauda ta Kano ya bayyana. Birnin Kano a wannan lokaci ya shahara ne a matsayin wurin bauta, dake cike da addinai kalakala. Wadanda s**a hada da ; masu bautar ruwa, wadanda ke zaune a Bakin Ruwa, kuma asalinsu sun taso daga kasar Gaya ne. Wadannan suke ke bautar ruwan jakara. Kuma sun amince shine yake tsaresu daga dukkan wani balai da zai taso musu, ko kuma ya taso ma garinsu.

Wani nau'in addinin shine Adzna ko Arna. Wadanda ke Gwabron Dutse. Su wadannan sune masu bautar Ubangiji. Wato wani Allahnsu ne da suke bautawa, Wanda a zatonsu yana ko ina. Haka kuma suna da gumaka da suke bautawa a matsayin wakilan Shi wannan ubangiji. Ita wannan kalma, ita ce malaman musulunci s**a amsheta, s**a nuna cewa ba Wanda ya cancanci wannan siffa ta ubangiji in banda Allah (domin shine yake ko ina, ilminsa ya game komai).

Addinin da yafi kowanne karfi da shahara, kuma manyan sarakunan kasar Kano dake da helikwata a Santolo suke bi, shine addinin maguzanci. Wanda babban wurin bautarsu ke kan Dutsen Dala. Masu bin wannan addini su ake kira Maguzawa, Farfesa Murray Last a kasidarsa maitaken : Historical Metaphor in the history of Kano ya bayyana cewa asalin sunan, ya samo ne daga "Majus " wato majusawa. Wadannan bayin Allah na bautar iskokai ne, wato aljannu. Musamman wata aljanna da ake kira Tsumburbura, ko kuma Danko. Malam Adamu na Maaji ya bayyana a littafinsa I'lan bi Tarikh Kano cewa, asalin wannan aljan ana bauta mata tun zamanin Annabi Nuhu, inda ya tabbatar da cewa ita ce 'Yaquqa ' da aka fada a alqurani, cikin suratul Nuh.

Akwai kuma masu bautar Bishiya da aka fi sani da Gazargawa, wanda sheikh AbdurRahman Zagaiti ya sha fama da su. Sune ke zaune a Shirawa, akwai cikakken bayani akan wannan rigima a kundin nan maisuna: Waraqa makatuba, fiha asl al wangariyun ".

Akwai sauran addinai da dama wanda Malam Nasiru Kabara ya yi dogon bayani akan su, a wani kaset na waazinsa da ya Maida martani ga malaman Izala akan gudunmowar sufaye a wurin yada addinin musulunci a Kasar Kano. (Abin bakin ciki na nemi kaset din na rasa).

Dokar kasar Kano a wannan lokaci shine: tunda kasa ce mai tsarki ta gamayyar addinan Hausawa, da suke aikin hajji duk shekara acikinta, kuma malamnsu da limamansu duk na ciki, to baa yadda kayi noma acikinta ba, ba kuma a yadda kayi farauta acikinta ba. Duk yayi wannan to zaiyi fuskantar fushin Allolinsu ko kuma ya fuskanci yaki daga Sarakan Kasar dake zaune a Santolo (wato Tsakuwa kenan dake karamar hukumar Dawakin Kudu a yau). Wannan dalilin ne ya sanya Shi kansa limaminsu mafi shahara (Barbushe), yake tafiyar wuni domin ya farauto nama. Saboda ba damar yin farauta a garin Kano da kewaye. Hakan ta sanya kqbilar Doma s**a bar gari saboda mafarauta ne, s**a koma Kazaure, karkashin jagorancin shugabansu maisuna Kazaure.

Yunkurin Bagaudawa;

Farkon Wanda s**a fara yunkurin rusa wannan addinai sune Abagayawa, asalinsu makera ne da manoma, s**an kuma taba farauta. A wannan lokaci saboda bukatar sabon wurin noma da kuma neman karfe domin kara fadada sanaarsu, ta sanya dole su fara neman sabon wuri, inda zasu samu kasa mai yalwa, da kuma isasshen karfe. Ba kuma inda yake da wannan abubuwa in ba Kano ba. Gashi kuma ba a noma a kasar Kano, kuma baa farauta, ba kuma dama a haki ma'adanan ta. To amma fa, dan wuya ba za a bar dadi ba.

Zuwan Bagauda Kano ya tabbatar da shi fa yaga, domin yaga akwai karfe a kasa, ga kuma kasar noma mai albarka, sannan ga dabbobi kala kala. Don haka ya yanke shawarar Shi fa, sai dai ayi wacce zaayi, amma dole a barsu, su cigaba da rayuwa a kasar Kano. Kuma dole su noma kasa, dole su hako karfe, dole kuma a barsu suyi farauta, don ba zasu bar nama a banza ba.

Wannan yunkuri na Bagauda da mutanensa, ya jawo musu tsangwama daga sarakunan Santolo da kuma tofin Allah tsine daga manyan limaman Kano. Koda yake da farko Bagauda ya keta doka yayi yanda yake so, amma ba a jima ba Santolo ta zo da runduna mai karfi ta fatattake shi, inda ya sha da kyar, ya tattara yanasa-yanasa ya koma Sheme a kasar Kazaure, acan ya rasu!

Sai dai wannan fatattaka da akayi masa ya bar baya da kura, domin ya haifar da gadajjiyar gaba tsakanin Bagaudawa da manyan addinan Kano, inda s**a sha alwashin ko bajima, ko badade, sai sunga bayan wadannan addinai. Sun shafe kusan shekara 100 da doriya suna mulki a kasar garin sheme na Kazaure, kafin daga baya dama ta samu a zamanin Gijimasu su ka dawo su ka kafa gidan sarauta a birnin kano.

Bawani cikakkiyen bayani, akan ko ya akai s**a dawo, cikin Kano, domin kundin Tarikh Arbab bai bada wani bayani cikakke ba akan yadda s**ayi nasarar dawowa cikin garin Kano, da maido da masarautarsu, amma alamu na nuna cewa, a wannan lokaci karfin Santolo yayi rauni ainun! Kila ko saboda yake yake da ya addabe su, musamman da daulolin Tumbi da kuma Washa, ko kuma da Zazzau. Kila hakan ne ya sanya aka bar shirayin Kano ba wani tsayyayen tsaro da zai kareta, daga mamayar Bagaudawa.

Koda yake Bagaudaw sun dawo Kano, amma kuma sai ga shi basu samu yadda suke so, na murkushe tsoffin abokan gabarsu ba. Duk wani yunkuri da s**a yi na tabbatar da mulkinsu, abin yaci tura. Shi kansa Zamnagawa (usmanu) da yayi yunkurin farko, bai kare lafiya ba.

Yunkurin Musulunci
Acikin wannan hali ne, a wata shekara zamanin sarkin Kano Yaji dan Tsamiya, wasu malaman Wangarawa karkashin jagorancin sheikh AbdurRahman Zaiti s**a zo, Kano, baya ga musulunci da kuma kasuwanci, suna kuma da sabbin makamai da dabarun yaki da baa san da su ba a Kano. Wannan ya sanya Bagaudawa s**a karbi musulunci, gami da neman samu hadin kan wadannan baki, su taimaka musu su yaki abokan gabarsu. Kwana daya da zuwansu Sarkin Kano Yaji ya karbi musulunci, ya kuma canjawa kansa suna zuwa Ali. Wanda hakan ke nuna, cewa , shirin yaki za'ayi dan tabbatar da Addinin Allah, domin ana cewa Ali bin Abu Talib shine sarkin yakin manzon Allah (saw).

A farkon watan Rabiul Awwal na wannan shekara, ne Yaji ya tara dukkan Hausawan da basu musulunta ba ya karanta musu dokar-ta-baci. Inda yace musu

"Ku sani, daga yau, ba komai tsakanina daku, sai yaki da tsinin mashi in har ku ka cigaba da yakar musulunci ba yaudara, bawani boye boye, domin ba mayaudari sai matsoraci, ku shirya gani nan zuwa gareku "

Mataki biyu s**a dauka, na farko sunyi kokarin bada cin hanci ga Sarki Yaji, amma yaki karba, yace a maida musu baya so. Na biyu, sai s**a koma ga Tsumburbura, domin neman nasara, amma ta gaya musu, cewa wannan yaki ba nasara, domin lokacin karshen addininsu a kasar Kano yazo.

Acikin watan dai, rundunar musulmi s**a fuskanci, rundunar mabiya addinin gargajiya,a gefen Dutsen Dala, inda s**a hadu, aka gwabza. A wannan lokacin ne, Jarmai Bajere ya samu nasarar Kutsa kai cikin shigifar Tsumburbura, inda ya samu wani halitta na tsaye, rike da maciji a hannunsa, ya daga mashi ya bugawa halittar nan, tayi kuwwa ta fito a guje wannan yaƙi ya faru ne a Ranar 19th ga Rabi'ul Awwal wanda kuma yayi dai-dai da Ranar bakwai ga haihuwar shugaba sallahu alaihi Wasallam. Bayan fitar wannan halitta sai Nan da nan s**a bita, inda ta nufi kofar liƙwai wato kofar ruwa a Yanzu, ta fada cikin ruwan Dankwai. Wannan Shi ya kawo karshen Tsumburbura, da kuma addinin gargajiya (maguzanci)a garin Kano a lokacin Mulkin Sarkin Musulmi Ali yaji ɗan Tsamiya a ƙarni na 13th.

Takutaha

Samuwar wannan Nasara, ba karamin abu bane a wurin musulman Kano. Wanda aka shafe sama da shekaru 100 ana nema. A dalilin haka ne, ya sanya musulman kanawa duk shekara, s**an taru su hau Dutsen Dala domin tunawa da wannan nasara da musulunci yayi akan Maguzanci. Su nunawa duniya cewa, addinin Allah yau ya shafe addinin kafirai. Domin kafin zuwan musulunci, ba mai hawa Dala in ba Babban limamin addinin ba. Amma zuwan musulunci, yanzu kowa ma sai ya hau, ya yi kashi ma aka. Wannan shine dalilin da ya sanya ake takutaha a duk shekara a Kano, Wanda wasu da basu san tarihin ba, ke ganin jahilci ne, ko kuma abu ne, da ya sabawa musulunci.

Allah ya sa mu dace

Allah Gwani | Tsokoki fiye da 600 ne a jikin mutum. Sai tsoka ta yunƙura ake samar da motsi har muhimman ayyuka su gudan...
09/09/2025

Allah Gwani | Tsokoki fiye da 600 ne a jikin mutum. Sai tsoka ta yunƙura ake samar da motsi har muhimman ayyuka su gudana kamar:

1. Harba jini da zuciya ke yi.

2. Numfashi da huhu ke yi.

3. Furuci da laɓɓa da harshe ke yi.

4. Tattauna abinci da haƙora ke yi.

5. Kallo ko jujjuyawar ƙwayar ido.

6. Haka nan, duk sauran motsi da mutum ke yi a ayyukan yau da kullum tun daga kwaciya zuwa zama, zama zuwa tsaiwa, tsaiwa zuwa tafiya, tafiya zuwa gudu, duka na buƙatar yunƙurawar tsokokin jiki.

© Physiotherapy Hausa

Martha Kande Audu (nee Gowon), ita ce ma'aikaciyar gidan radiyon Kaduna ta farko da a ka fara jin muryarta a lokacin da ...
01/09/2025

Martha Kande Audu (nee Gowon), ita ce ma'aikaciyar gidan radiyon Kaduna ta farko da a ka fara jin muryarta a lokacin da aka bude gidan radiyo da talabijin na Kaduna (Radio Television Kaduna). Lokacin da aka budeshi a ranar 11 ga watan Maris 1962.

01/09/2025

*Ina Yan 70's da 80's ga sunayen Littattafan Hausa 200, Wanene kuka Kara ta a ciki?*👇👇👇👇👇👇👇👇

LITTAFAN HAUSA GUDA ƊARI Biyu (200)

1.Tafiya Mabuɗin Ilmi
2. Jiki Magayi
3. Hikayoyin Kaifafa Zuƙata
4. Ganɗoki
5. Labarun Gargajiya
6. Ai ga irinta nan
7. Uwar Gulma
8. Kulɓa Na Ɓarna
9. Karamin Sani Ƙunƙumi 1&2
10. Shaihu Umar
11. Zaman Duniya Iyawa ne
12. Dare Daya
13. Matar Mutum Kabarin sa
14. Magana Doki Ce
15. Matsolon Attajiri
16. Gangar Wa'azu
17. Ki Gafar Ce Ni
18. Turmin Danya
19. Suda
20. Namijin Duniya
21. Duniya Rumfar Kara
22. Kukan Kurciya
23. Dana Sani
24. Mallam In Kuntum
25. Ruwan Bagaja
26. Tsohon Najadu
27. So Aljannar Duniya
28. Alkalami A Hannun Mata
29. Turmi Sha Daka
30. Gogan Naka
31. Sidi Ya Shiga Makaranta
32. Yula
33. Dausayin Yara
34. Tatsuniyoyin Mace Mutum-1-3
35. Tatsuniyoyi Da Wasanni 1-6
36. Nagari Na Kowa
37. Yawon Duniyar Hajji Gaba
38. Kukan Kurciya
39. Mallam Mamman
40. Kitsen Rogo
41. Duniya Sai Sannu
42. Kyandir
43. Tsumangiyar Kan Hanya
44. Tabarmar Kunya
45. Hikayoyin Shehu Jaha
46. Mungo Park Mabuɗin Ƙwara
47. Kowa Ya Bar Gida
48. Labaru Na Da DaNa Yanzu
49. Iliya Ɗan Mai Ƙarfi
50. Labarin Dikko Ɗan Maichede Da Kada Mai Rikiɗa
51. Waƙoƙin Infiraji
52. Fasaha Aƙiliya
53. Kwasar Ganima
54. Jatau Na Kyallu
55. Komai Nisan Dare
56. Magana Jari ce 1,2&3
57. Soyayya Tafi Kuɗi
58. Sharri Kare Ne
59. Mallam Zailani
60. Abin Da Kamar Wuya
61. Bala Da Babiya
62. Dausayin Soyayya
63. Abinci Garkuwar Jiki
64. "Yar Tsana
65. Tarihin Fulani
66. Dare Dubu Da Ɗaya
67. Tatsuniyoyin Hausa
68. Wasannin Yara
69. Asan Mutum Akan Cinikin Da
70. Ikon Allah 1,2,3,4,&5
71. Ƙarshen Alewa Ƙasa
72. Musha Dariya
73. Gajerun Labarai
74. Amarzadan A Birnin Aljanu
75. Amarzadan Maraba A Farsiyas
76. Amarzadan Da Zoben Farsiyas
77. Rayuwa Bayan Mutuwa
78. Kimiyyar Sararin Samaniya
79- Kimiyya Da Al'ajaban Alqur'ani
80. Dabarun Rubuta Ƙagaggun Labarai
81. Jagoran Nazarin Waƙar Baka
82. Rubutun Wasiƙa A Dunƙule
83. Jagoran Nazarin Ƙagaggun Labarai
86. Ƙaidojin Rubutun Hausa
87. Gandun Dabbobi
88. Wasanni Tashe
89. Zamanin Nan Namu
90. Zaman Mutum Da Sana'arsa
91. Zaman Hausawa
92. Kowa Na Son Na Gari
93. Hannu Da Yawa
94. Jagoran Nazarin Hausa
95. Zuwan Turawa Nijeriya Ta Arewa
96. Tarihin Islama
97. Hausawa Da Maƙwabtan su 1&2
98. Jagoran Nazarin Hausa
99. Wasiyyar Sarki Gambo Ga "ya"yanda
100. Gishirin Zaman Duniya
101. Dare Sha Biyu
102. Duniya Sai Sannu
103. Kowa Ya Yi Da Kyau
104. Tunaninka Kamannin
105. Asalin Hausawa
106. Rayuwa ta
107. Husufin Farin Ciki
108. Hausa A Rubuce
109. Amadi Na Malam Ama
110. Maraya
111. Jagoran Nazarin Wasan Kwaikwayo
112. Hausa A Dunƙule
113. Tsanin Hausa
114. Hausa Da Hausawa A Duniyar Intanet
115. Tsuntsu Duka Tsuntsu
116. Cikin Gida
117. Waka A Bakin Mai Ita
118. Idan So Cuta ne
119. Sanin Makamar Fassara
120. Jagoran Ilimi Walwalar Harshe
121. Sana'a Goma
122. Isharori 130
123. Albasa Bata Yi Halin Ruwan Ba
124. "Yan Matan Gaya
125. Jamila Da Jamila
126. Aure Mutuncin Samari
127. An Damu Kuwa
128. Gumakan Zamanin
129. Tarihin Annabi Da Halifofi
130. Rayuwar Mace
131. Zuma
134. Mu Fara Karatu
135. Taka Tsan-Tsan
136. Kwaryar Zuma
137. Nahawun Hausa
138. Wakokin Mu'azu Hadejia
139. Wakokin Sa'adu Zungur
140. Muhalli Sutura
141. Almajiranci Da Bata
142. Malam Zalimu
145. Balaguron Wawa
146. Sauna Jack
147. Wakar Furen Gero Da Tsarabar Madina
148. Auren Zobe
149. Tura Takai Bango
150. Auren Zobe
151. Hali Zancen Dutse
152. Abdulkadir Saladin
152. Jakar Magori
155. Kunne Ya Girmi Kaka
156. Karin Maganar Hausa
157. Marainiya Khairiyya "Yar Baba
158. Iska Sa Damina
159. Hasken Ilimi
160. Soyayya A Birnin Sarayebo
161. An Yanka Ta Tashi
162. Mutuwar Kasko
163. Labarin Saiful Milk
164. Batulu
165. Tarihi Da Wakokin Alhaji Mudai Spikin
166. Hausa A Yau
165. Hikayoyin Kyakyatawa
166. Wani Abu Akan Matar Sarki
167. Tsofafffi Da Sabbabbin Mudi Spikin
168. Dan Musulmi
169. Bakin Suri
170. Bori Da Rukayya
171. Ilimi Mabudin Tafiya
172. Tarihin Alhaji Haruna Uji
173. Soyayya A Harshen Ilimi
174. Soyayya Da Rayuwar Aure A Kasar Hausa
175. Turbar Tarabulus
176. Almajirai Ko Attajirai
177. Daurayar Gadon Fede Waka
178. Gobarar fushi
179. Aro Da Kirkira
180. Taskar Tatsuniyoyi
181. Fannin Falsafa A Ilmance
182. Wakokin Hausa
183. Dauloli A Kasar Hausa
184. Sunayen Hausawa
185. Damfara A Intanet
186. Fassara A Takaice
187. Damuwar Ruwan Sanyi
188. Tauraruwar Hamada
189. Tauraruwa Mai Wutsiya
190. Dabaru, Tunani Da Koyarwar Malam Aminu Kano
191. Wani Ganin Ga Allah
192. Diwanin Wakokin Baka
193. Daular Sakkwato
194. Dakikan Talatin
195. Birgimar Hankaka
196. Kaico
197. Da'u Fataken Dare
198. Mu Koyi Karatu
199. Wakokin Hikimomin Hausa
200. Wakar Nijeriya

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Al'adun Hausawa a Da,da Yanzu. posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Al'adun Hausawa a Da,da Yanzu.:

Share