24/05/2025
LABARIN YUSHA'U NARIMI DUTSE BAKA FARGABA.
Littafi: Magana Jarice 2
Mawallafi: Margayi Alhaji Abubakar Imam
Da, an yi wani yaro wanda Allah ya nufa da wata irin zuciya sai ka ce dutse, don rashin fargaba. Saboda ganin haka sai ya rika alfahari, yana cewa shi duk duniyan nan bai ga wani abin da zai bashi tsoro ba har ya kadu. ’Yan’uwansa yara su kan kulla abubuwa da yawa yadda za su sa ya kadu, amma duk a banza. Saboda haka har s**a sa masa suna ‘Dutse.’ Da sun gan shi sai su rika yi masa kirari suna cewa, “Yusha’u Na-Narimi, dutse-ba-ka- fargaba.”
Da kakansa ya ji haka, sai ya ce shi lalle sai ya ba shi tsoro har ya kadu. Yusha’u kuwa duk bai san abin da a ke ciki ba. Ran nan da tsakad dare sai ya tafi hira wata unguwa, ya raba dare bai dawo ba. Da kakan nan nasa ya ji haka sai ya tashi, ya sami karare, ya daura wani mutum-mutumi dogo, ya sa masa farar riga, shi kuma ya sa wa kansa fara. Sai ya tashi ja dauki mutum- mutumin nan ya dora bisa kansa, ya tafi hanyar da yaron nan zai biyo, ya maqe.
Can zuwa tsakad dare, duk ba wani mahaluki mai motsi, sai ya ji yaron nan tafe yana waka. Da jinsa sai ya fito daga inda ya ke boye, ya tasam masa haikan. Da Yusha’u ya ga ya nufo shi sai ya ce, “Kai tsololo, in aljani ne kai, lalle Allah bai halicce ka da tsari ba, ga ka tsololo, amma dan kai sai ka ce kodago. Ko kuwa fatalwa ce? In kuwa fatalwa ce, na so in gan ta sa’ad da ta ke da rai. Zotori!”
kakansa dai bai ce uffan ba, ya dai nufo shi har ya taka wa yaron nan kafa. Sai yaron ya tsaya, ya ce, “A’a! Shakiyancin nan na aljannu da fatale har ya kawo gare ni? Kai tsololo, mene ne na taka ni? To, ko da ya ke tsawona bai kai ın mareka ba, ai ka sha kulki!” Sai ya dunkula hannu, ya kaiwa kakan bugu, tim!
Ya sake dagawa zai kara, sai kakan ya yad da karan, ya ce, “Kai, kai, kai, ni ne kakanka Narimi, kada ka buge ni.”
Yaron ya yi murmushi ya ce, “Kaka, me ya sa ka yi mini haka, ga shi har ka sa na buge ka?”
Narimi ya ce, “Mutane na ke ji suna cewa, ai wani abin da za a yi maka har ka kadu, shi ya sa na yi wannan dabara wai ko na sa ka ji tsoro. Ashe dai gaskiyarsu. Gobe kuwa sai na tafi na gaya wa Sarki jaruntakan nan taka.”
Yaro ya ce, "Shin kaka, mene ne tsoro ne? Ni ban san abin da a ke kira hakanan ba. Ashe yanzu nan duniya har akwai abin da zai sa In kadu?” Kakan ya yi murmushi, ya korna gida.
Gari na wayewa sai kakan ya tafi ya gaya wa Sarki, ya ce yana da jika wanda ba abin da za a yi masa ya kadu. In Sarki yana so ya gani, ya kirawo shi ya gwada shi. Fadawa s**a ce, “Allah ya ja zamaninka, wannan yaron ai sananne ne a kan rashin tsoro, ai tun da ya ke babu abin da ya taba sa shi ya kadu.”
Sarki ya ce, “To, madalla, gobe, ku zo da shi mu gani. Ai inda ba kasa a ke gardamar kokawa.”
Da gari ya waye kakan ya kira yaro, ya gaya masa abin da s**a yi da Sarki; Yaro ya ce, “To, sai mu tafi, in shakka ya ke yi.”
Da aka yi sallar azahar, da yaro da kakansa s**a tafi gidan Sarki. S**a tarad da fada ta cika, kowa na fadin albarkacin bakinsa. S**a fadi s**a yi gaisuwa. Dogarawa s**a ce, “An gaishe ku.”
Sarki ya dube su, ya ce, “Kun taho”
Kakan ya ce, “I, Allah ya ba ka nasara, ga yaron.”
Sarki ya dubi jama’a ya ce, “Kun ga yaron da aka ce bai ta6a kaduwa ba don tsoro. Ina so in gwada shi, amma ku shaida, ln aljannu s**a halaka shi, ko kuwa s**a zauta shi, kada a zarge ni. Zan sa shi ya kwana cikin dakin gindin tsamiyan nan ta gunki. In ya tashi lafiya gobe, ba a ji ya yi kuwwa ba, ko wata firgita, zan ba shi ’yata aure.”
Da kakan yaron nan ya ji haka sai idonsa s**a yi kwal-kwal. Fadawa kuma duk s**a dube su, s**a yi dariya. Kowa ya san tsamiyan nan akan kwankwamai. Nan ne kuwa fadar Sarkin aljannu. In mutum ya bari magariba ta yi masa, ko kuwa rana ta take yana kusa da wurin, sai wani ba shi ba. Wannan abu ba ko camfi ba ne, an ga haka ba daya ba, ba biyu ba. Saboda yawan aljannu har a ke kiranta “Mutuwa kusa.”
Da kakan yaro ya ji haka sai ya ce, “Ranka ya dade in dai wannan za a gwada shi, ba ya iyawa, kwarinsa bai kai haka ba.”
Yusha’u ya yi wuf ya ce, ‘Me ya sa ka ce haka? Cikin duniyan nan ashe har akwai wani abin da zai sa ni in kadu ma, b***e har a ce in yi ihu? Haba, ranka ya dade, ko ba ka san labarina ba ne? Ni ne fa Dutse Na—Narimi ba ka fargaba. Allah ya kai mu magariba.”
Kakansa ya yi, ya yi, ya hana shi, ya tsaya shi sai ya kwana. Narimi ya gaji, ya ce, “Jeka, ai mai rabon shan duka ba ya jin kwabo, sai ya sha.” S**a sallami Sarki, s**a tafi gida, duk Narimi ’na zulumin abin, yana cewa, "Lalle baki dai shi ke yanka wuya,”
Magariba na yi sai yaron nan ya dauki ’yar tabarmarsa, ya tafi gindin tsamiyan nan, ya shige dakin ya yi shimfida, ya kunna fitila, ya kwanta, ya bar ta tana ci. Aka zo aka gayawa Sarki. Sai ya sa wadansu malamai su hudu, s**a sami wani wuri can nesa da gindin tsamiyar, s**a buya. S**a tsayâ daidai da inda za su iya hanğen duhun yaron nan cikin daki; don kada ya fito.
Yana nan kwance sai ya ga wani aljanni ya keto bangon dakin ya fito, duk tsawonsa bai fi kamu guda ba. Amma kansa, duk inda tulu ya kai da girma ya fi hakanan. Da fitowarsa sai ya zauna gindin fitila tare da yaron, ya yi masa kuri da ido. Sai Yusha’u ya ce masa, “Me ka ba ni ajiya ne. har ka dame ni da kallo haka? Ko kuwa kana da wani da ne k**ata wanda ya bace?” Aljannin nan dai bai ce masa uffan ba, sai lashe-lashen bakinsa ya ke yi. Yaro ya ce, “Kurwata kur, ka ci kanka, ka sha bakin ruwa!” Aljanni dai bai ce masa kome ba.
Suna nan zaune, sai ga cinyar mutum ta fado kasa tim, har da jini. Yusha’u ya dubi cinyar, ya ce, “Kai, mai wannan cinya lalle kafin ya mutu an yi kato! Shinkici! Amma irin kattan nan galibi ba su kan yi karfi ba. Bari in jinjina cinyar, in ji in da alamar karfi.” Ya tashi ya ciccibi cinyan nin ya ji ta sakwat, ba nauyi. Sai ya ce, “Allah wadai, yau ga katon kwabo! Ashe duk katancin nan ta gina ne ba ta shiga ba.” Sai ya yar da ita waraf, ya korna kusa da gajeren nan na tsugune. Ya zauna ke nan, kuma sai wata cinyar ta fado kusa da ta fari. Kafin a yi haka kuma sai ga hannuwa sun fado. Yaro dai bai ce kome ba sai dariya ya ke yi musu. Can kuma sai ga gangar jiki ta fado tirim. Ko wace gaba ta like ga ’yar’uwata, sai ga mutum ya tashi ya nufo su, amma ba kai. Yaron nan ya ce, “Kai, wannan huhun ma’ahu ya faye doki! Tsaya mana tukun kanka ya fado sa’an nan ka zo, in hira za mu yi.”
Aljani dai bai ce kome ba, sai ya zo wurin wancan dan gajeren nan da ya fara zuwa, ya danne shi, ya k**a hannunsa guda ya kakkarya shi rugu-rugu, ya bar shi nan yana kuka. Ya zabura zai gudu sai ga wadansu aljannu guda biyar sun tsago kasa sun fito. Da ganin abin nan da ya faru, sai s**a yi cacukwi da wannan da ya karya dan uwansu, s**a ce, “A’a, a, a! Kai Kururrumi, kai ka karye Dandagizge? Wallahi yau in Sarkin Aljannu ya zo, bari ta kai, ko da mutumin nan mai fitala da ke nan aka yi abin, kashinsa ya bushe!”
Sai yaron nan ya ce, “Kai, in kuna shiriritarku ku bar gamawa da ni. Ka ga ’yan nema masu manyan kunnuwa! Kashina ya bushe! Halama ni na kashe shi?”
Kai, in-gajarce muku labari dai, aljannun nan s**a yi ta ba shi tsoro iri iri har gari ya waye, amma Yusha’u bai razana ba, b***e ya kadu.
Da rana ta fito ya dauki ’yar tabarmasa, ya nufi gidan Sarki, ya ce ya dawo. Mutane za su yi muşun bai kwana ba, sai malaman nan hudu s**a shaida ya kwana. Sarki ya rasa abin da ke masa dadi, ga shi ya yi alkawari ba damar warwarewa. Mutane s**a yi ta mamakin yaron nan, kakansa kuwa ya yi ta farin ciki da ya kubuta.
Sarki ya tashi, ya shige gida duk rai a bace, ya kira ’yar da uwarta, ya gaya musu wannan al’amari duka. Yarinyan nan ta ga ran iyayenta ya baci, sai ta ce,‘“Kada ku bata rayukanku a banza, na ce ko kaduwa ce ya ce bai ga abin da zai sa shi ya yi ba?”
Uban ya ce, “I, lalle ko gaskiyarsa, duk duniyan nan kuwa babu.”
Yarinya ta ce, “To, na ce ko kun gama naku na manya? Saura kuma mu mu yi kokarimmu na yara, mu gani.”
Uban ya yi dariya ya ce, “Wane kokari gare ku na yara ban da wauta?”
Yarinyar ta ce, “Ina so, in ka yarda, baba, ka je yanzu cikin taro, ka ce ka ba shi ni, amma da sharadi guda, shi ne daga yau har kafin rana wa ta yau, in wani abu ya sa shi ya kadu, baiko ya tashi.”
Uwar ta yi dariya ta ce, “Ka ji wautar tamu ta mata! Wanda ya kwanta dakin gunki bai ji tsoro ba, to, me zai tsorata shi a cikin gidansa?”
Uban ya ce, “Bari in je in fadi, kada mu rage mata hanzari.”
Sai ya korna zaure ya fadawa mutane haka, duk s**a shaida. Yusha’u ya yi dariya, ya sallami Sarki ya tafi gida, iyayensa s**a yi ta yi masa guda don murna. Yarinyan nan kuwa ta san tun da ya kwana dakin gunki jiya, lalle aljannu ba su bar shi ya runtsa ba, tun da abin ya ke haka kuwa, daren yau lalle in ya fara barci sai Allah. To, lokacin nan kuwa cikin tsakiyar dari ne muku-muku. Saboda haka da asuba sai yarinya ta tashi ta fadawa ubanta, ta sa ya aike aka tado Waziri da Alkali, da manyan malaman gari guda hudu wadanda Sarki ya sa su tsaron nan jiya da dare. Da s**a taru, sai yarinyar ta debo ruwa mai sanyi kwarai daga wani sabon tulu, ta ba Sarkin Zagi ya dauka, duk s**a dunguma zuwa gidan.
Da s**a isa kofar gida, ta ce kada kowa ya yi magana, ko wani babban motsi. Ta sa aka tafi sululu aka tado kakan yaron nan, ya fito waje ya tarad da su, kowa dai ya zuba wa ’yar yarinya ido ya ga abin da za ta yi. Sai ta ce kakan yaron ya shiga gaba ya nuna musu dakin jikansa, amma fa ba a ce in ya je ya ta da shi ba, ko motsi mai karfi ma kada kowa ya yi.
S**a isa, ta tarad da dakin rufe da asabari, ta sa hannu sannu a kan hankali ta cire, sai ga yaro kwance tim, daga shi sai durwar bante, barci ya sa har ya ture dan bargonsa bai sani ba. Sai ta karbi ruwan nan ta shiga cikin dakin sadadaf, sadadaf, ta watsa masa a jiki. Ko da ruwan nan ya zuba masa sai ya kadu, ya yi firgigi ya tashi, ya ce, ‘Wai!” Duk mutanen nan s**a yi tafi baki daya, s**a bushe da dariya, s**a ce, “A’ ya kadu, ya kadu!”
Da Yusha’u ya bude idonsa, ya gane makirci ne aka yi masa, sai kunya ta rufe shi. Don gudun jin kunya bai bari gari ya waye masa ba, sai da ya gudu ya bar garin. Mutane s**a yi ta mamakin wannan fasaha ta ’yar yarinya.
Da Sarki ya komo gida ya gaya wa uwar yarinyar abin da ya faru, duk sai s**a rungume ta don murna. Da gari ya waye Sarki ya nemi yaro, aka ce ai ya gudu. Sai ya sa mutane su bi shi. Kafin azahar aka komo da shi. Sarki ya nada shi Sarkin Yaki. Aka ba shi katon gida. Sarki ya aura masa ’yam mata biyu daga cikin ’ya’yan bayinsa. Da ma abin da ya tsana ya ba shi ’yar cikinsa, ga shi talaka. Sarki kuma ya yi wa kakan yaron nan kyauta mai yawa don jaruntakar jikansa. S**a yi ta cin duniyarsu a tsanaki. Kullum idan Sarkin Yaki ya tafi fada Sarki ya ce masa, “Yusha’u, Sarkin Yaki, Na-Narimi, dutse ba ka fargaba.” Shi kuma sai ya ce, “Lalle ba na fargaba sai na ruwa, Allah ya ba ka nasara.” Duk sai a yi ta dariya.