Al'adun Hausawa a Da,da Yanzu.

Al'adun Hausawa a Da,da Yanzu. AN BUDE WANNAN SHAFI NE,SABODA TUNATAR DA KAWUKAN MU
BISA KYAWAWAN AL'ADUMMU NA HAUSA,

WADAN DA AYA Mungode

Dan Bunkasa Harshen Hausa da Al'adunsa,
Muna Maraba da shawarwarinku Domin wannan shafi naku ne.

A Shekarun Baya Na Yi Tashen Da Babu Irin Abinda Ban Mallaka Ba A Masana'antar Fim, Amma Yanzu Har Gudun Saka Ni A Fim A...
25/07/2025

A Shekarun Baya Na Yi Tashen Da Babu Irin Abinda Ban Mallaka Ba A Masana'antar Fim, Amma Yanzu Har Gudun Saka Ni A Fim Ake Yi Saboda Ana Kallo Na Da Kuskuren Da Na Yi A Baya, Cewar Ummi Nuhu

Ummi Nuhu ta kara da cewa duk da cewa tana kaunar harkar fim har yanzu, amma koda ta je neman a saka ta a fim, sai a ki saka ta, saboda ana waiwayar kuskuren da ta yi a baya.

Cikin kuka Ummi, ta ce a yanzu ba ta da wata sana'a da ta iya illa harkar fim gashi kuma an daina yi da ita, kuma tana fama da rashin lafiya wanda ya k**ata a ce ana saka ta a fim domin ta kula da kanta.

Tsohuwar jarumar dai ta bayyana hakan ne a hirar ta da Hadiza Gabon a shorinta na 'Gabon Talk Shaw', k**ar yadda Rariya ta nakalto.

KO BA MUTUWA AKWAI TSUFA.Wannan baiwar Allah ita ce Hajiya indo Musawa Wacce Mamman  Shata  yayi wa waƙa. A cikin waƙar ...
17/07/2025

KO BA MUTUWA AKWAI TSUFA.

Wannan baiwar Allah ita ce Hajiya indo Musawa Wacce Mamman Shata yayi wa waƙa.

A cikin waƙar yana cewa, "wata 'yar yarinya, mai kyaun diri da kyaun tsari, mai kyaun zama da kyaun tafiya ga alkawari k**ar tawada, ga dadin riko k**ar chasbi Indon Musawa."

Ance a lokacin su, duk garin Musawa babu mai kyaun ta.

from Muktar Maigamo shafin zinariya.

Tarihin Kabilar Da Ta Fi Ban-Tsoro A Duniya Kabilar North Sentinel Dake Rayuwa A Kan Tsibiri.mutanen kabilar North senti...
17/07/2025

Tarihin Kabilar Da Ta Fi Ban-Tsoro A Duniya Kabilar North Sentinel Dake Rayuwa A Kan Tsibiri.

mutanen kabilar North sentinel Island. Kabilar da tafi kowacce ban tsoro da kuma kebewa daga cikin al’umma.

A zanen taswira, North sentinel Island yana yanayi ne da sauran gurare na indian Ocean wanda yake kewaye da kwawar teku masu daukar hankali. North Sentinel Island yana nan ne a bakin tekun Bengal dake Andaman archipelago.

Shi dai North Sentinel Island ba k**ar sauran gurare na bakin ruwa bane da aka sani domin kuwa a kan kwatanta ko misalta shi da waje mafi wahala mafi muni sannan kuma wajen da ya fi ko wane waje tsoro yayin ziyara, sannan kuma guda ne ga mutanen da s**a fi kowannen mutane kadaita ko kuma ware kansu daga sauran mutanen duniya.

Wannan abu na abin mamaki da ake dangata wadannan mutane da shi ba zai iya misaltuwa ko aunawa a ma’auni ba kai tsaye, amma mafi yawan gaskiyar ita ce, a kiyasi na k**ar shekara 60,000 North Sentinel Island ya kasance gida ne ga kabila masu cin gashin kansu kuma suke ki' suna hana sauran mutanen duniya kusantar su karfi da yaji.

Idan aka hango North Sentinel Island daga sama k**ar yadda tauraron dan’Adam na European Space Agency ta labarta.

Kabilar “Sentineli” sun kai hari ga kusan duk wani mahaluki da ya shiga yankinsu. a shekarar 1896 sun soki wani dan Indiya wanda ya gudo daga birninsu har ya kasance cewa ruwa ya kawo shi zuwa bakin gabar ruwan da suke har lahira, a shekara ta 1974, sun yi wa wadansu ‘yan daukar fim ruwan masu, (kwari da baka) shekara ta 2004 kuwa daya daga cikin mutanen kabilar ne ya saita sannan ya harbo wani jirgin sama mai saukar ungulu wanda yake shawagi a sararin Subhaana sak**akon tura shi da aka yi ya duba ko akwai wadanda suke a raye har zuwa lokacin' bayan an sami yanayi na girgizar kasa, a baya bayannan ma a shekarar 2006 mutanen sun kashe wasu masu ‘su’( masu kamun kifi) wadanda s**a fada kogin yankinsu bisa kuskure

Tsuguno dai bata kare ba, domin kuwa bayan an tura jirgin sama mai saukar ungulu akan ya je ya taho da gawarwakin wadanda s**a kashe din kuwa, mutanen sun sake kai hari ne wa shi kansa jirgin.

Wannan muguwar dabi’a ta mutanen North Sentinel Island ne ya sanya aka kasa sanin wani abu mai yawa game da wannan kabila, abin da aka sani kawai shi ne suna da mak**ai musamman irin danginsu kwari da baka, sannan kuma suna amfani da raga irin ta kamun kifi, suna amfani da kwale-kwale, su kan yi kamun kifi, su shiga daji domin samun ganyayyaki na daji, amma babu wani labari na noma ko kiwo ko kuma wani abu da ya danganta su da kunna wuta ko da kuwa irin ta ita ce ce, mutane su kan yada jita- jitar cewa mutanen Sentinel su kan jira ne har sai an yi tsawa sannan kafin ta hura musu wuta a jikin gunguma-gunguman itatuwan da s**a hada wanda za su yi ta amfani da shi har na tsawon wani lokaci.

Sanannen abu ne cewar kabilar sentinel su ne mutane na karshe dake rayuwa a duniyar nan wanda ya kasance cewar ba wanda yake taba su ko kuma zuwa kusa da su da abin da ya danganci zamani.

mutane sun yi kokarin bincike akan kabilar sentinel inda wasu s**a yi nasarar samun wadansu bayanai kalilan.

A shekarar 1771 wani mai binciken yanayi na kasar Birtaniya mai suna John Ritchie ya wuce ta wannan waje, ya ce daga bangaren Kudu maso Yammacin Andaman akwai gabar wani kogi mai kyau wanda yake rufe da bishiyoyi yana da girma da tsawo sannan kuma idan za mu yanke hukunci daga yawan hàske da ake iya hanga daga wajen za mu iya cewa wuri ne da ya dace da rayuwa, 'jirgin na ruwa ya yi ta shawagi har tsawon wasu shekaru yana kewayawa yana komawa har na tsawon shekara 100, amma ba’a sami wani abu na dorar wa game da mutanen ba.

A shekarar 1869 jeremiah Homfray, mutumin da ke da alhakin kula da Andamanese ya yi tafiya zuwa Sentinel Island domin binciko wadansu masu laifi wadanda s**a kubuta daga penal Colony a Port Blair.

Da fara isarsu, Homray wanda yake tafe da rakiyar ‘yan sanda da da kuma wadansu daga cikin Andamanese s**a hango wadansu mutane su goma zaune a bakin tekun ‘tsirara ’suna da dogon gashi rike da ‘kwari da baka’ suna harbin kifi.

Daga nan dai mutanen na Sentinel s**a nemi waje s**a boye bayan sun hango wannan jirgi na su Homray. Mutanen na Andamanese da s**a kasance cikin firgici tsoro da kuma faduwar gaba yayin da s**a hango abin da ke faruwa, sun gargadi Homfray da kakkausar muraya a kan hatsarin da ke tattare da wadannan mutane, amma sai ya yi bitis da gargadin na su ya kuma sanya wa ransa cewar ya isa wannan waje inda kuma hari ne ya biyo baya daga wadannan mutane.

A wannan shekarar kuma wata tawaga ta ‘yan kasuwa daga indiya sun fado wannan waje sak**akon jirginsu na kasuwanci da ya farfashe a cikin kogi har ya wanko su zuwa North Sentinel bayani ya nuna cewa mutane 86 daga cikin wadanda s**a rayu cikin fasinjan jirgin da kuma mutum 20 daga cikin masu kula da jirgin sun sauka lafiya a bakin tekun.

A kwana na uku da saukarsu ne kuwa ‘yan kabilar Sentinel s**a kawo masu hari. Kyaftin din jirgin ya ce: mutanen suna zamane a tube ma’ana tsirara, suna da guntun gashi da kuma hanci ja, sannan suna bude bakunansu domin fitar da wata irin kara k**ar na namun daji, suna amfani da baka wanda s**an yi tsinin bakinsa da karfe, kyaftin din ya ce ya kubuta ne daga hari wadan nan mutane ta kan burbushi jirgin yayin da kuma aka kawo masa agaji kwanaki da dama bayan ya kubuta ta hanyar wasu matafiya da hanya ta wuto da su ta wajejen inda daga baya kuma aka tura jirgin ruwa irin na yaki domin ceton sauran wadanda s**a rayu wanda s**a samu s**a gudu daga tekun Sentinel da taimakon duwatsu da itatuwa.

Bayan wannan ruguntsimi kuwa, an share sama da shekaru goma 13 ba tare da wani ya sake waiwayar wadannan mutanen ba.

A Janairu na shekarar 1880 ne kuma wasu mayakan Britaniya s**a sami nasarar sauka a tsibirin na North Sentinel, mayakan, karkashin jagorancin Maurice Bidal Portman dan shekaru 20 sun shiga tsibitin neman wadan nan kabila inda s**a s**a ci karo da hanyoyi ma banbanta da kuma sababbin kauyuka wadanda aka yi watsi da su.

Portman ya ce yanayin girki da sarrafa abinci na mutanen Sentinel ya yi k**a da na mutanen Onges, ba irin na aborigin da mutanen Andaman ba. A lokacin wannan zagaye Portman ya ce bai gamu da ko mutum kwaya daya ba na daga wannan kabila duk sun watse cikin daji.

Cikin sa’a ne bayan wasu kwanaki masu dama ana bincike sai kuwa s**a ci karo da mutum shida daga cikin Kabilar Sentinel wadanda s**a kunshi mata da miji dattijai da s**a manyanta sai kuma ‘ya’yansu guda hudu inda s**a k**a su, s**a tattarasu s**a mai da su Port Blair.

TAƘAITACCEN TARIHIN IBRAHIM YARO YAHAYA (1944–1995)Tattarowa da rubutawa Abubakar S Sabiu (Sarki).......Ibrahim Yaro Yah...
07/07/2025

TAƘAITACCEN TARIHIN IBRAHIM YARO YAHAYA (1944–1995)

Tattarowa da rubutawa Abubakar S Sabiu (Sarki).......

Ibrahim Yaro Yahaya (1944–1995) ya kasance mashahurin masani a marubuci a fannin harshen Hausa. Yahaya ya bayar da gudunmawa wajen rubuta litattafai a ɓangaren harshe da adabin Hausa.

Rayuwa da Ilimin Ibrahim Yaro Yahaya.

An haifi Ibrahim Yaro Yahaya a shekarar 1944. Ya yi karatu a Jami'ar Bayero da ke Kano, inda ya kware a fannin Hausa da adabin gargajiya. Ya kasance malami a Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya (Centre for the Study of Nigerian Languages) a Jami'ar Bayero, inda ya taka muhimmiyar rawa wajen koyarwa da bincike kan harshen Hausa da adabinsa.

Yahaya ya rubuta littattafai da dama da s**a taimaka wajen bunƙasa ilimin Hausa, kaɗan daga ciki sun haɗa da:

Ga jerin wasu daga cikin litattafan da Ibrahim Yaro Yahaya ya rubuta, waɗanda s**a shahara a fannin harshen Hausa da adabinsa:

1. "Hausa a Rubuce: Tarihin Rubuce-Rubuce Cikin Hausa" (1988)
Wannan littafi yana bayani kan tarihin rubuce-rubuce cikin harshen Hausa, tare da jerin littattafan da aka wallafa daga 1930 zuwa 1980.

2. "Labarun Gargajiya"
Wannan littafi ya ƙunshi tatsuniyoyi na gargajiya da ke koyar da darussa da nishaɗi.

3. "Da Koyo A Kan Iya" (1975)
Littafi na uku a jerin karatun Hausa, wanda aka wallafa a 1975.

4. Tatsuniyoyi da Wasanni: Littafi na Shida
Wannan littafi ya ƙunshi tatsuniyoyi da wasannin gargajiya na Hausa.

5. "Sunayen Hausawa na Gargajiya da Ire-Iren Abincin Hausawa" (1979)
Littafi da ke bayani kan sunayen gargajiya da nau'o'in abincin Hausawa.

6. "Jagoran Nazarin Hausa: Don Makarantu"
Littafi da ke taimakawa wajen koyar da harshen Hausa a makarantu.

7. "Darussan Hausa: Don Manyan Makarantun Sakandare: Littafi na Daya"
Littafi na farko a jerin darussa na Hausa don manyan makarantu.

8. "Darussan Hausa: Don Manyan Makarantun Sakandare: Littafi na Biyu" (1996)
Waɗannan su ne wasu daga cikin litattafan da Yahaya ya wallafa

A matsayinsa na malami da marubuci, Yahaya ya kasance ginshiƙi wajen bunƙasa harshen Hausa da adabinsa. Ya kuma taka rawa wajen shirya tarukan ƙasa da ƙasa kan harshen Hausa, k**ar taron farko na ƙasa da kasa kan Hausa da adabinta da aka gudanar a Jami'ar Bayero a shekarar 1978.

Ya rasu a shekarar 1995, amma har yanzu ana jin tasirinsa a fannin Hausa da adabin gargajiya.
Muna roƙon Allah Ya gafarta masa amin.

Abubakar S Sabiu (Sarki)
7 July, 2025

Rashin Marigayi Alh Aminu Dantata ba karamin Rashi bane a duniya.Allah ya gafarta masa.
29/06/2025

Rashin Marigayi Alh Aminu Dantata ba karamin Rashi bane a duniya.

Allah ya gafarta masa.

Alhaji Alhassan Dantata, hamshakin dan kasuwa kuma dan kasuwa ya kasance mafi arziki a yammacin Afirka a wajen shekarun ...
29/06/2025

Alhaji Alhassan Dantata, hamshakin dan kasuwa kuma dan kasuwa ya kasance mafi arziki a yammacin Afirka a wajen shekarun 1940.

Ya gina dala na Groundnut Kano wanda kowanne dala yana da buhuna sama da 15,000 da aka cika. Ya kuma yi aiki tare da kolanuts kuma ya kasance mai ba da kayayyaki ga kamfanonin kasuwanci na Burtaniya.

British Bank Of West Africa (yanzu First Bank) ya bude reshensu na farko a Kano a shekarar 1929, ya zama dan kasuwa na farko da ya fara saka kudi a bankinsu kuma ya fara yin haka a duk wani banki a Najeriya yana ajiye kaya na rakuma 20 na tsabar Azurfa.

Babban jikansa, Aliko Dangote a yanzu shi ne Bakar fata mafi arziki a duniya

SK PRESS TV
Alkanawey kano ❤️

SHEKARU FIYE DA 500 DON ALLAH DA ANNABINSA KU TAYANI DUBAWA!!!Kafin Tajdidin Addinin musulunci da Mujaddidi shehu Usman ...
12/06/2025

SHEKARU FIYE DA 500
DON ALLAH DA ANNABINSA KU TAYANI DUBAWA!!!

Kafin Tajdidin Addinin musulunci da Mujaddidi shehu Usman Dan Fodio ya jagoranta Fulani Torankawa( Futatoro) Sun shekara Fiye da 500 a kasar Hausa,tsakanin Shehu da Musa jokolo jagoran Toronkawa Hula Goma Sha Daya zuwa Sha biyu ne,

Amma yau ansami wasu bankadaddu karnukan farautar makiya,suna kokarin su nuna Wai ai su Fulani Baki ne a kasar Hausa,bakin uwar wa,dayawan wadanda suke zaune a kasar sunzo ne sun tarar da Fulani, jeka ka bincika zaka taras da babu wata kasar Hausa da babu fulani a cikin na tsawon wadancan shekaru,Kai Tarihi ya Tabbatar mafi akasarin Malamai da alkalai a kasar Hausa Fulani ne,

kai har a cikin Alkalawa Babban Birnin Gobir Fulani ne mafi akasarin Malamai da alkalansu,haka kabi da zamfara ko Malaman 'yandoto da ake ta wani Magana akansu da Fulani a cikinsu ko shi Sambo Dan Ashafa din Menene shi, bafullatani ne Kuma daga cikin Malaman 'yan doton ya fito, Haka ma Malaman Degel suke daga cikinsu Shehu ya fito, da wannan zaku iya fahimtar jihadin da Mujaddidi shehu Usman Dan Fodio,Kira ne na Tabbatar da Adalci a domin kuwa da aka kawar da Sarakunan Gargajiya har da tsarinsu aka kawar,

Kuma a cikin wadanda suke tafiyar da tsarin babu Wanda babu na daga Hausawa da fulani da Sauran mazauna kasar Hausa k**ar Arawa da Buzaye da Saurasu,Haka ma wadanda s**a Taimaki Shehu yada Addini da jaddada shi dukkansu sun fito ne daga bangarori daban daban na kasar Hausa da Makwabta, Kai in takaita Jawabi shine a kasar Anyi juyi juya Hali na Addinin musulunci Wanda Mujaddidi shehu Usman Dan Fodio ya jagoranci Mazauna kasar Haus a 'yan uwansa domin kawo sauyi Kuma yayi Nasara,

domin a shekaru 500 ba kawai sun mayar da Kai Dan wurin bane A'a kaima bangare ne ba wurin,A yau cikin wadannan Marasa Mutumcin babu Wanda zai iya lissafo hula na Bakwai na kakaninsa Hausawa ne,Amma tun zamanin jihadin Shehu Torankawa ke da tarihin Shekaru Fiye da 500 a kasar hausa, Hula Goma Sha Biyu, zuwa yanzu shekaru kusan 900 kenan hula kuwa ta Kai kusan 16 zuwa Sha Bakwai, to in basu zama Hausawa ba Ubanka ne zai zama Bahaushe da Ba zaka Iya Lissafo hula Bakwai na Asalinka ba a Yau kake karyar Tunkaho dashi!!!

Muhammad Rajab Muhammad

Kwafi...MUBAYA'AR SARKIN ZAZZAU ISIYAKU JATAU 1782/1802 GA MUJADDIDI SHEHU USMAN FODIO Sarki na 59 a  cikin Sarakunan Ha...
12/06/2025

Kwafi...

MUBAYA'AR SARKIN ZAZZAU ISIYAKU JATAU 1782/1802 GA MUJADDIDI SHEHU USMAN FODIO

Sarki na 59 a cikin Sarakunan Habe ya Mika mubaya'a ga Mujaddidi shehu Usman Dan Fodio a lokacin shehu yayi Hijira daga degel zuwa Gudu, wannan Mubaya'a da sarki sukutum na habe ya Mika Shehu,To itafa take karyata duk wata karya da za'a kirkiro ta yau ace mana Wai jihadin shehu fulatanci ne,shifa wannan sarki bada bakin takobi ya Amsa Kiran shehu ba A'a zunzurutun Gaskiya ya gani da Kuma Addinin Allah na Gaskiya,ba irin Wanda akeyi a kasar Hausa ba na cudanya Addini da bori da tsafi,Ganin himmar Shehu na tsarkake Addinin Allah daga gurbata da Kuma tsamo Al'umma daga duhun zalunci da jahilci yasa Sarki isiyaku Jatau ya Amsa Kiran Shehu ba tare da bata lokaci ba,Kuma ya dukufa wajen kyautata rayuwar Al'umma da sasu a tafarki na Gaskiya ,Al'umma Kuma s**a Amsawa sarkin su s**a bishi da Biyayya.

Wannan Dalilin yasa Shehu ya kyale Sarki Jatau batare da'an turo kowa zazzau ba haka tasa zazzau ta zama Darul Islam na farko a zamanin Jihadi karkashin jagorancin Sarki Jatau,haka aka ci gaba da tafiya har Allah yayi Masa Rasuwa.

Daga baya aka Sami wani makakke waishi Makau inda ya Nemi sauya komai da mayar da Al'umma baya zuwa ga jahilcinsu da zalunci,haka tasa Shehu ya turo masu Jihadi zazzau domin Gyara Al'amurra Kamar yadda Sarki Jatau yabarsu,Sun tunkaro zazzau Makau ya so yayi fada dasu don an Dan fafata a wajen kasar makarfi ya ga ba dama fadan yafi karfinsa ya koma cikin Birnin Zaria a guje,daga nan shida 'yan Tsirarun Jama'ar dake tare dashi s**a fice s**a bar Zaria Kai har har kasar zazzau Baki Daya,

Masu Jihadi Karkashin Malam Muusa s**a shigo Zaria Jama'a s**a tarbe su , Al'amurra Kuma s**a daidata k**ar yadda Sarki Jatau ya barsu Kai Harma Fiye da haka.

ALHAMDULILLAH

09/06/2025

*Garin da babu Musulmi ko daya, kuma Musulmi bai isa ya shiga ba a Kano❗*

Back to Kanawa masu kurarin "Yaro ko dame kazo an fika." Suna can suna dagawa da kurarin iska, ana mummunan finsu da cinsu a cikin kasan nasu.

Ina kuma Malaman-Zamanin? Suna cike a cikin Kano, suna ta hayaniya da raba kan al'Ummah. Sun ƴale wannan mummunan lamarin na faruwa, don daman ba shine matsalar su ba kuma ba hakikanin Musuluncin be a gaban su ba, -daga abunda al'Ummah ke gani a tattare da su

Da sun baiwa hakikanin musulunci kadan daga karfin da suke bayarwa gojen raya kungiyanci, yaudara, raba kan al'Ummah da rikitar da ita, da ko kusa hakan bai faru ba.
Wannan kuma, haka yake a yawancin garuruwan Musulmi a yau.

Malaman-Zamani, sun rikitarda mu, sun sugultardamu da kawunannan, can kuma sun budawa makiyan addinin mu da mu, suna yakammu a saukake.

A zamanin Malaman baya, ba wanda ya isa, ya shigo cikin kasan Musulmi ya ci karen sa ba babbaka. Kuma sannu a hankali cikin ' _mau'izatul Hasana_ ' suke ta Musuluntar da maguzawan. Da Malaman-Zamani s**a bullo ne da aqiidun su, shine kome ya rikice mana.

Therefore, and obviously,
Malaman-Zamani, Malaman-Social,
Malaman-Hayaniya etc
Su s**a jaza mana f*k matsalolin nan!

FisabililLAHI, ina Malantan anan?

LABARIN YUSHA'U NARIMI DUTSE BAKA FARGABA.Littafi: Magana Jarice 2Mawallafi: Margayi Alhaji Abubakar ImamDa, an yi wani ...
24/05/2025

LABARIN YUSHA'U NARIMI DUTSE BAKA FARGABA.

Littafi: Magana Jarice 2
Mawallafi: Margayi Alhaji Abubakar Imam

Da, an yi wani yaro wanda Allah ya nufa da wata irin zuciya sai ka ce dutse, don rashin fargaba. Saboda ganin haka sai ya rika alfahari, yana cewa shi duk duniyan nan bai ga wani abin da zai bashi tsoro ba har ya kadu. ’Yan’uwansa yara su kan kulla abubuwa da yawa yadda za su sa ya kadu, amma duk a banza. Saboda haka har s**a sa masa suna ‘Dutse.’ Da sun gan shi sai su rika yi masa kirari suna cewa, “Yusha’u Na-Narimi, dutse-ba-ka- fargaba.”

Da kakansa ya ji haka, sai ya ce shi lalle sai ya ba shi tsoro har ya kadu. Yusha’u kuwa duk bai san abin da a ke ciki ba. Ran nan da tsakad dare sai ya tafi hira wata unguwa, ya raba dare bai dawo ba. Da kakan nan nasa ya ji haka sai ya tashi, ya sami karare, ya daura wani mutum-mutumi dogo, ya sa masa farar riga, shi kuma ya sa wa kansa fara. Sai ya tashi ja dauki mutum- mutumin nan ya dora bisa kansa, ya tafi hanyar da yaron nan zai biyo, ya maqe.

Can zuwa tsakad dare, duk ba wani mahaluki mai motsi, sai ya ji yaron nan tafe yana waka. Da jinsa sai ya fito daga inda ya ke boye, ya tasam masa haikan. Da Yusha’u ya ga ya nufo shi sai ya ce, “Kai tsololo, in aljani ne kai, lalle Allah bai halicce ka da tsari ba, ga ka tsololo, amma dan kai sai ka ce kodago. Ko kuwa fatalwa ce? In kuwa fatalwa ce, na so in gan ta sa’ad da ta ke da rai. Zotori!”

kakansa dai bai ce uffan ba, ya dai nufo shi har ya taka wa yaron nan kafa. Sai yaron ya tsaya, ya ce, “A’a! Shakiyancin nan na aljannu da fatale har ya kawo gare ni? Kai tsololo, mene ne na taka ni? To, ko da ya ke tsawona bai kai ın mareka ba, ai ka sha kulki!” Sai ya dunkula hannu, ya kaiwa kakan bugu, tim!

Ya sake dagawa zai kara, sai kakan ya yad da karan, ya ce, “Kai, kai, kai, ni ne kakanka Narimi, kada ka buge ni.”

Yaron ya yi murmushi ya ce, “Kaka, me ya sa ka yi mini haka, ga shi har ka sa na buge ka?”

Narimi ya ce, “Mutane na ke ji suna cewa, ai wani abin da za a yi maka har ka kadu, shi ya sa na yi wannan dabara wai ko na sa ka ji tsoro. Ashe dai gaskiyarsu. Gobe kuwa sai na tafi na gaya wa Sarki jaruntakan nan taka.”

Yaro ya ce, "Shin kaka, mene ne tsoro ne? Ni ban san abin da a ke kira hakanan ba. Ashe yanzu nan duniya har akwai abin da zai sa In kadu?” Kakan ya yi murmushi, ya korna gida.

Gari na wayewa sai kakan ya tafi ya gaya wa Sarki, ya ce yana da jika wanda ba abin da za a yi masa ya kadu. In Sarki yana so ya gani, ya kirawo shi ya gwada shi. Fadawa s**a ce, “Allah ya ja zamaninka, wannan yaron ai sananne ne a kan rashin tsoro, ai tun da ya ke babu abin da ya taba sa shi ya kadu.”

Sarki ya ce, “To, madalla, gobe, ku zo da shi mu gani. Ai inda ba kasa a ke gardamar kokawa.”

Da gari ya waye kakan ya kira yaro, ya gaya masa abin da s**a yi da Sarki; Yaro ya ce, “To, sai mu tafi, in shakka ya ke yi.”

Da aka yi sallar azahar, da yaro da kakansa s**a tafi gidan Sarki. S**a tarad da fada ta cika, kowa na fadin albarkacin bakinsa. S**a fadi s**a yi gaisuwa. Dogarawa s**a ce, “An gaishe ku.”

Sarki ya dube su, ya ce, “Kun taho”

Kakan ya ce, “I, Allah ya ba ka nasara, ga yaron.”

Sarki ya dubi jama’a ya ce, “Kun ga yaron da aka ce bai ta6a kaduwa ba don tsoro. Ina so in gwada shi, amma ku shaida, ln aljannu s**a halaka shi, ko kuwa s**a zauta shi, kada a zarge ni. Zan sa shi ya kwana cikin dakin gindin tsamiyan nan ta gunki. In ya tashi lafiya gobe, ba a ji ya yi kuwwa ba, ko wata firgita, zan ba shi ’yata aure.”

Da kakan yaron nan ya ji haka sai idonsa s**a yi kwal-kwal. Fadawa kuma duk s**a dube su, s**a yi dariya. Kowa ya san tsamiyan nan akan kwankwamai. Nan ne kuwa fadar Sarkin aljannu. In mutum ya bari magariba ta yi masa, ko kuwa rana ta take yana kusa da wurin, sai wani ba shi ba. Wannan abu ba ko camfi ba ne, an ga haka ba daya ba, ba biyu ba. Saboda yawan aljannu har a ke kiranta “Mutuwa kusa.”

Da kakan yaro ya ji haka sai ya ce, “Ranka ya dade in dai wannan za a gwada shi, ba ya iyawa, kwarinsa bai kai haka ba.”

Yusha’u ya yi wuf ya ce, ‘Me ya sa ka ce haka? Cikin duniyan nan ashe har akwai wani abin da zai sa ni in kadu ma, b***e har a ce in yi ihu? Haba, ranka ya dade, ko ba ka san labarina ba ne? Ni ne fa Dutse Na—Narimi ba ka fargaba. Allah ya kai mu magariba.”

Kakansa ya yi, ya yi, ya hana shi, ya tsaya shi sai ya kwana. Narimi ya gaji, ya ce, “Jeka, ai mai rabon shan duka ba ya jin kwabo, sai ya sha.” S**a sallami Sarki, s**a tafi gida, duk Narimi ’na zulumin abin, yana cewa, "Lalle baki dai shi ke yanka wuya,”

Magariba na yi sai yaron nan ya dauki ’yar tabarmarsa, ya tafi gindin tsamiyan nan, ya shige dakin ya yi shimfida, ya kunna fitila, ya kwanta, ya bar ta tana ci. Aka zo aka gayawa Sarki. Sai ya sa wadansu malamai su hudu, s**a sami wani wuri can nesa da gindin tsamiyar, s**a buya. S**a tsayâ daidai da inda za su iya hanğen duhun yaron nan cikin daki; don kada ya fito.

Yana nan kwance sai ya ga wani aljanni ya keto bangon dakin ya fito, duk tsawonsa bai fi kamu guda ba. Amma kansa, duk inda tulu ya kai da girma ya fi hakanan. Da fitowarsa sai ya zauna gindin fitila tare da yaron, ya yi masa kuri da ido. Sai Yusha’u ya ce masa, “Me ka ba ni ajiya ne. har ka dame ni da kallo haka? Ko kuwa kana da wani da ne k**ata wanda ya bace?” Aljannin nan dai bai ce masa uffan ba, sai lashe-lashen bakinsa ya ke yi. Yaro ya ce, “Kurwata kur, ka ci kanka, ka sha bakin ruwa!” Aljanni dai bai ce masa kome ba.

Suna nan zaune, sai ga cinyar mutum ta fado kasa tim, har da jini. Yusha’u ya dubi cinyar, ya ce, “Kai, mai wannan cinya lalle kafin ya mutu an yi kato! Shinkici! Amma irin kattan nan galibi ba su kan yi karfi ba. Bari in jinjina cinyar, in ji in da alamar karfi.” Ya tashi ya ciccibi cinyan nin ya ji ta sakwat, ba nauyi. Sai ya ce, “Allah wadai, yau ga katon kwabo! Ashe duk katancin nan ta gina ne ba ta shiga ba.” Sai ya yar da ita waraf, ya korna kusa da gajeren nan na tsugune. Ya zauna ke nan, kuma sai wata cinyar ta fado kusa da ta fari. Kafin a yi haka kuma sai ga hannuwa sun fado. Yaro dai bai ce kome ba sai dariya ya ke yi musu. Can kuma sai ga gangar jiki ta fado tirim. Ko wace gaba ta like ga ’yar’uwata, sai ga mutum ya tashi ya nufo su, amma ba kai. Yaron nan ya ce, “Kai, wannan huhun ma’ahu ya faye doki! Tsaya mana tukun kanka ya fado sa’an nan ka zo, in hira za mu yi.”

Aljani dai bai ce kome ba, sai ya zo wurin wancan dan gajeren nan da ya fara zuwa, ya danne shi, ya k**a hannunsa guda ya kakkarya shi rugu-rugu, ya bar shi nan yana kuka. Ya zabura zai gudu sai ga wadansu aljannu guda biyar sun tsago kasa sun fito. Da ganin abin nan da ya faru, sai s**a yi cacukwi da wannan da ya karya dan uwansu, s**a ce, “A’a, a, a! Kai Kururrumi, kai ka karye Dandagizge? Wallahi yau in Sarkin Aljannu ya zo, bari ta kai, ko da mutumin nan mai fitala da ke nan aka yi abin, kashinsa ya bushe!”

Sai yaron nan ya ce, “Kai, in kuna shiriritarku ku bar gamawa da ni. Ka ga ’yan nema masu manyan kunnuwa! Kashina ya bushe! Halama ni na kashe shi?”

Kai, in-gajarce muku labari dai, aljannun nan s**a yi ta ba shi tsoro iri iri har gari ya waye, amma Yusha’u bai razana ba, b***e ya kadu.

Da rana ta fito ya dauki ’yar tabarmasa, ya nufi gidan Sarki, ya ce ya dawo. Mutane za su yi muşun bai kwana ba, sai malaman nan hudu s**a shaida ya kwana. Sarki ya rasa abin da ke masa dadi, ga shi ya yi alkawari ba damar warwarewa. Mutane s**a yi ta mamakin yaron nan, kakansa kuwa ya yi ta farin ciki da ya kubuta.

Sarki ya tashi, ya shige gida duk rai a bace, ya kira ’yar da uwarta, ya gaya musu wannan al’amari duka. Yarinyan nan ta ga ran iyayenta ya baci, sai ta ce,‘“Kada ku bata rayukanku a banza, na ce ko kaduwa ce ya ce bai ga abin da zai sa shi ya yi ba?”

Uban ya ce, “I, lalle ko gaskiyarsa, duk duniyan nan kuwa babu.”

Yarinya ta ce, “To, na ce ko kun gama naku na manya? Saura kuma mu mu yi kokarimmu na yara, mu gani.”

Uban ya yi dariya ya ce, “Wane kokari gare ku na yara ban da wauta?”

Yarinyar ta ce, “Ina so, in ka yarda, baba, ka je yanzu cikin taro, ka ce ka ba shi ni, amma da sharadi guda, shi ne daga yau har kafin rana wa ta yau, in wani abu ya sa shi ya kadu, baiko ya tashi.”

Uwar ta yi dariya ta ce, “Ka ji wautar tamu ta mata! Wanda ya kwanta dakin gunki bai ji tsoro ba, to, me zai tsorata shi a cikin gidansa?”

Uban ya ce, “Bari in je in fadi, kada mu rage mata hanzari.”

Sai ya korna zaure ya fadawa mutane haka, duk s**a shaida. Yusha’u ya yi dariya, ya sallami Sarki ya tafi gida, iyayensa s**a yi ta yi masa guda don murna. Yarinyan nan kuwa ta san tun da ya kwana dakin gunki jiya, lalle aljannu ba su bar shi ya runtsa ba, tun da abin ya ke haka kuwa, daren yau lalle in ya fara barci sai Allah. To, lokacin nan kuwa cikin tsakiyar dari ne muku-muku. Saboda haka da asuba sai yarinya ta tashi ta fadawa ubanta, ta sa ya aike aka tado Waziri da Alkali, da manyan malaman gari guda hudu wadanda Sarki ya sa su tsaron nan jiya da dare. Da s**a taru, sai yarinyar ta debo ruwa mai sanyi kwarai daga wani sabon tulu, ta ba Sarkin Zagi ya dauka, duk s**a dunguma zuwa gidan.

Da s**a isa kofar gida, ta ce kada kowa ya yi magana, ko wani babban motsi. Ta sa aka tafi sululu aka tado kakan yaron nan, ya fito waje ya tarad da su, kowa dai ya zuba wa ’yar yarinya ido ya ga abin da za ta yi. Sai ta ce kakan yaron ya shiga gaba ya nuna musu dakin jikansa, amma fa ba a ce in ya je ya ta da shi ba, ko motsi mai karfi ma kada kowa ya yi.

S**a isa, ta tarad da dakin rufe da asabari, ta sa hannu sannu a kan hankali ta cire, sai ga yaro kwance tim, daga shi sai durwar bante, barci ya sa har ya ture dan bargonsa bai sani ba. Sai ta karbi ruwan nan ta shiga cikin dakin sadadaf, sadadaf, ta watsa masa a jiki. Ko da ruwan nan ya zuba masa sai ya kadu, ya yi firgigi ya tashi, ya ce, ‘Wai!” Duk mutanen nan s**a yi tafi baki daya, s**a bushe da dariya, s**a ce, “A’ ya kadu, ya kadu!”

Da Yusha’u ya bude idonsa, ya gane makirci ne aka yi masa, sai kunya ta rufe shi. Don gudun jin kunya bai bari gari ya waye masa ba, sai da ya gudu ya bar garin. Mutane s**a yi ta mamakin wannan fasaha ta ’yar yarinya.

Da Sarki ya komo gida ya gaya wa uwar yarinyar abin da ya faru, duk sai s**a rungume ta don murna. Da gari ya waye Sarki ya nemi yaro, aka ce ai ya gudu. Sai ya sa mutane su bi shi. Kafin azahar aka komo da shi. Sarki ya nada shi Sarkin Yaki. Aka ba shi katon gida. Sarki ya aura masa ’yam mata biyu daga cikin ’ya’yan bayinsa. Da ma abin da ya tsana ya ba shi ’yar cikinsa, ga shi talaka. Sarki kuma ya yi wa kakan yaron nan kyauta mai yawa don jaruntakar jikansa. S**a yi ta cin duniyarsu a tsanaki. Kullum idan Sarkin Yaki ya tafi fada Sarki ya ce masa, “Yusha’u, Sarkin Yaki, Na-Narimi, dutse ba ka fargaba.” Shi kuma sai ya ce, “Lalle ba na fargaba sai na ruwa, Allah ya ba ka nasara.” Duk sai a yi ta dariya.

DALILIN DAYA SA BAHAUSHE KE KIRAN RIGA DA SUNA TAGUWA!Shekaru da dama da s**a wuce (tun kafin zuwan Fulani ƙasar Hausa) ...
05/05/2025

DALILIN DAYA SA BAHAUSHE KE KIRAN RIGA DA SUNA TAGUWA!

Shekaru da dama da s**a wuce (tun kafin zuwan Fulani ƙasar Hausa) an yi wani maƙeri mai suna Ado-guwa kuma yana sana'ar ƙira!
Wata rana matar sa ta aiko ɗansa domin yazo maƙerar mahaifinsa don ya ɗebo mata garwashi za ta hura wuta, to a lokacin guwa ya Riga da ya wanke bargonsa ya shanya shi a bisa ciyawa don ya bushe zuwan yaron keda wuya sai ya debi garwashi daga makerar mahaifinsa da nufin zai kaiwa mahaifiyarsa don tayi sanwa, abun ka da yarinta sai yaron yabi ta kan Bargon nan da mahaifinsa ya shanya! Allah cikin ikonsa kuwa sai garwashi daya ya fado tsakiyar bargon, nan take ya fara ci a hankali wurin nata kara fadi.
Chan! Sai hankalin guwa ya kai kan bargonsa ya lura garwashi ya fada tsakiyarsa har ya kone tsakiyar bargon.
Nan take ya tashi da sauri ya dauki bargonsa ya kakkafe wutar ya yanke inda ya kone! Gashi kuma lokacin sallar jumu'a yayi kuma wannan bargon ne kawai ya wanke da nufin ya laga yaje masallaci dashi! Daya rasa yadda zai yi (don gudun kada lokacin sallar ya wuce) sai ya dauki bargon daidai inda ya huje din ya Sanya a Kansa ya saki sauran bargon ya rufe duka jikinsa! Zuwansa masallaci ke da wuya sai kallo ya koma Kansa ana mamakin irin wannan shiga ta guwa!
Gama sallar ke da wuya sai wasu daga cikin hausawan wurin sunka dauki wuka mai kaifi s**a fara yanka bargunasu! Duk Wanda aka tambaya dalilin yanke tsakiyar bargonsa sai yace "yana so ne ya maida ita irin TAGUWA" Daga nan mutane s**a rika zuwa wurin madinka ana maida masu bargunansu irin TAGUWA!

WASA ƘWAƘWALWAWani mutum ne yake son tsallake rafi (kogi) a tare dashi kuma akwai ƙura, akuya da kuma dawa.Gashi kuma ba...
28/04/2025

WASA ƘWAƘWALWA

Wani mutum ne yake son tsallake rafi (kogi) a tare dashi kuma akwai ƙura, akuya da kuma dawa.
Gashi kuma baze iya tsallake rafin dasu a tare ba, sedai ya tsallakar dasu daya bayan daya!
Matsalar a nan shine:

1- Kunga idan ya ce ze fara tsallakar da ƙurar, to kafin ya tsallako ya dawo akuya zata cinye dawar!
2- Idan ya ce ze fara tsallakar da dawar kuma, kafin ya dawo ƙurar zata cinye akuyar.

Kuma gashi yana bukatar se ya tsallakar dasu dukkan su, to yaya za'ayi?

Aminu Kano

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Al'adun Hausawa a Da,da Yanzu. posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Al'adun Hausawa a Da,da Yanzu.:

Share