Jaridar Dala

Jaridar Dala Sahihan labarai, Ilmantarwa, Nishadantarwa, kimiya da fasaha! A kasa najeriya da sauran fadin duniya!
(1)

Hukumomi a Sudan ta Kudu sun tabbatar da mutuwar fiye da mutane 60, yayin da wasu sama da 50 s**a jikkata a wasu hare-ha...
12/08/2026

Hukumomi a Sudan ta Kudu sun tabbatar da mutuwar fiye da mutane 60, yayin da wasu sama da 50 s**a jikkata a wasu hare-haren da matasa masu ɗauke da mak**ai s**a kai a jihar Warrap, a tsakiyar ƙasar.

An ce hare-haren, waɗanda ake zargin suna da nasaba da rikicin ƙabilanci, sun shafi yankunan Tonj North da Akok.

Rahotanni sun ce an kuma sace dabbobi tare da wawure wasu kadarori.

Hukumomin jihar sun ce mutane 17 daga cikin waɗanda s**a jikkata sosai an tura su Wau domin samun ƙarin kulawar lafiya, yayin da sauran ke karɓar magani a cibiyoyin kiwon lafiya na yankin.

Rikicin ƙabilanci da hare-haren ramuwar gayya na ci gaba da zama babbar barazana ga zaman lafiya a Sudan ta Kudu, duk da ƙoƙarin da ake yi na aiwatar da yarjejeniyar zaman lafiya.

12/08/2026
Dakarun Operation Enduring Peace (OPEP) na Sashen 9 sun kashe wasu da ake zargin 'yan ta'adda biyu tare da kwato bindiga...
11/08/2026

Dakarun Operation Enduring Peace (OPEP) na Sashen 9 sun kashe wasu da ake zargin 'yan ta'adda biyu tare da kwato bindigar AK-47 da harsasai a ƙauyen Nwur da ke Ƙaramar Hukumar Langtang North a Jihar Filato.

Rahotanni sun bayyana cewa an gudanar da wannan samame ne a ranar Litinin, 10 ga Agustan 2026, bayan k**a wani da ake zargin ɗan bindiga a Shendam, inda binciken da aka yi masa ya sa ya bayyana wurin da ya ɓoye bindigarsa.

Majiyar soji ta ce dakarun sun tafi tare da wanda ake zargin domin gano makamin, sai dai suna isa yankin s**a fuskanci harin wasu 'yan ta'adda, lamarin da ya haifar da musayar wuta.

A yayin artabun, dakarun sun kashe mutum biyu, ciki har da wanda ake zargin ɗan bindigar da ke jagorantar su zuwa wurin da aka ɓoye makamin. Ba a samu asarar rai ko jikkata daga ɓangaren sojojin ba.

Bayan kammala fafatawar, dakarun sun ci gaba da binciken yankin inda s**a kwato bindiga ƙirar AK-47 guda ɗaya, mujallar bindigar guda ɗaya da kuma harsasai biyu masu girman 7.62mm Special.

Majiyar ta ƙara da cewa mutanen da aka kashe 'yan asalin yankin ne, kuma ana zarginsu da hannu a hare-haren da s**a addabi al'ummar yankin. A cewarta, a lokuta da dama ana ɗora alhakin irin waɗannan hare-hare kan Fulani masu garkuwa da mutane, alhali wasu daga cikin masu aikata laifukan 'yan yankin ne.

A halin yanzu, dakarun na ci gaba da sintiri da bincike domin kamo ko hallaka sauran mambobin ƙungiyar da s**a tsere.

Gwamnatin Tinubu ta ce ta gyara gadoji sama da 10 a kowace jiha cikin shekaru uku.Gwamnatin Tarayya ta ce ta sake ginawa...
10/08/2026

Gwamnatin Tinubu ta ce ta gyara gadoji sama da 10 a kowace jiha cikin shekaru uku.

Gwamnatin Tarayya ta ce ta sake ginawa tare da gyara gadoji sama da 10 a kowace jiha cikin shekaru uku na mulkin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Ministan Ayyuka, Sanata Dave Umahi, ne ya bayyana hakan a ranar Lahadi yayin wani taron tuntubar masu ruwa da tsaki da kuma kaddamar da wasu ayyukan hanyoyi a jihar Legas.

Umahi ya kuma bayyana cewa gwamnati ta kammala ayyukan gyaran gaggawa sama da 260 a fadin Najeriya, wadanda kudinsu ya haura Naira biliyan 250.

Ya ce gwamnatin Tinubu ta bude ayyukan da take gudanarwa ga hukumar ICPC domin duba yadda aka bayar da kwangiloli da kuma yadda ake aiwatar da su, a wani mataki na tabbatar da gaskiya da rikon amana.

Game da Gadar Eko Bridge da ke Legas, ministan ya ce gadar na cikin wani hali da ya bukaci a rufe wani bangare nata domin gudanar da aikin gyara.

Ya ce an gano wata tsaga a gadar, amma binciken da ake gudanarwa akai-akai ya nuna cewa tsagar ba ta kara girma ba.

A cewarsa, aikin gyaran wucin gadi zai hada da sake kafa wasu turaku da kuma gyara bangaren da matsalar ta shafa, yayin da gwamnati ke shirin gudanar da cikakken gyaran gadar na dindindin domin tabbatar da dorewarta na tsawon shekaru.

KANO: BIRNI NA TARA A DUNIYA WAJEN YAWAN JAMA’A?.Alƙaluma sun bayyana cewa birnin Kano na daga cikin biranen da s**a fi ...
10/08/2026

KANO: BIRNI NA TARA A DUNIYA WAJEN YAWAN JAMA’A?.

Alƙaluma sun bayyana cewa birnin Kano na daga cikin biranen da s**a fi yawan jama’a a duniya, inda aka kiyasta cewa akwai kusan mutane miliyan 17 da rabi a cikin birnin.

Idan waɗannan alkaluma sun tabbata, menene tasirinsu ga ci gaban Jihar Kano?

👉 Ta yaya yawan jama’ar zai taimaka wajen bunƙasa tattalin arzikin jihar?

👉 Waɗanne damammaki ne wannan ɗimbin jama’a zai samar wa matasa da ‘yan kasuwa?

👉 Ta yaya gwamnati za ta yi amfani da wannan damar wajen samar da ayyukan yi, masana’antu, ingantaccen sufuri, lafiya da ilimi?

👉 Kuma ta yaya yawan jama’ar Kano zai iya zama wata babbar dama ga tattalin arzikin Najeriya baki ɗaya?

Ku aiko mana da ra’ayoyinku ta kafafen sada zumunta da kuka saba.

DA ƊUMI-ƊUMI: Shugaban NRS ya kare Tinubu kan zargin almubazzaranci.Shugaban Hukumar Haraji ta Najeriya (NRS), Zacch Ade...
10/08/2026

DA ƊUMI-ƊUMI: Shugaban NRS ya kare Tinubu kan zargin almubazzaranci.

Shugaban Hukumar Haraji ta Najeriya (NRS), Zacch Adedeji, ya ce Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ba ya rayuwar almubazzaranci duk da matsayinsa na shugaban ƙasa.

Adedeji ya bayyana hakan ne a wata hira da gidan talabijin na Channels, inda ya ce Tinubu kan yi tafiya da ƙafa daga gidansa zuwa ofis, sannan ya yi amfani da mota ne kawai idan zai je filin jirgin sama.

Ya kuma ce shugaban ƙasar na cin abinci sau ɗaya a rana, sannan a cikin watanni uku da s**a gabata bai yi wata tafiya zuwa ƙasashen waje ba.

Adedeji ya yi watsi da zargin cewa yawan motocin alfarma da ke cikin ayarin shugaban ƙasa na nuna almubazzaranci, yana mai cewa Tinubu yana da ikon mallakar irin waɗannan motocin.

Ya ƙara da cewa Tinubu na yawan kasancewa a ofis yana duba takardu da gudanar da ayyukan gwamnati, yana mai tambayar inda aka ga shugaban ƙasar yana shagulgula ko yawon buɗe ido a cikin 'yan shekarun da s**a gabata.

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jaridar Dala posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share