Jaridar Dala

Jaridar Dala Sahihan labarai, Ilmantarwa, Nishadantarwa, kimiya da fasaha! A kasa najeriya da sauran fadin duniya!

Anyi kira ga Hisba da su k**a wani matashi me izgili da mutuwa!Gidauniyar Grassroot Care and Aid Foundation (GCAF) ta yi...
07/10/2025

Anyi kira ga Hisba da su k**a wani matashi me izgili da mutuwa!

Gidauniyar Grassroot Care and Aid Foundation (GCAF) ta yi kira ga hukumar Hisba a ƙarƙashin jagorancin Imam Dr. Muhammad Aminu Ibrahim Daurawa da kuma hukumar tace fina-finai ta jihar Kano, wato Kano State Censorship Board, ƙarƙashin Abba Almustapha, da su ɗauki matakin gaggawa kan wani matashi da ya wallafa bidiyo na rashin tarbiyya a kafafen sada zumunta.

A cewar shugaban gidauniyar, Amb. Auwalu Muhammad Danlarabawa, bidiyon na nuna matashin cikin makaranta yana yin isgili, yana sanya likafani, tare da tsayawa a gaban wuta yana rawa da waka da ke nuna rashin natsuwa da rashin kunya.

Gidauniyar ta bayyana damuwa kan irin wannan bidiyo, tana mai cewa hakan na iya cutar da tunanin yara da matasa masu tasowa, wadanda ka iya ɗaukar irin wannan hali a matsayin abin koyi.

Ta kuma roƙi manyan malamai da hukumomi irin su Hisba da Censorship Board su tabbatar da hana irin wannan bidiyo kafin su bazu cikin al’umma.

Tinubu Ya Ba Da Umarnin Rage Kuddin Hajjin 2026 Cikin GaggawaShugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayar da umarnin a sake ...
06/10/2025

Tinubu Ya Ba Da Umarnin Rage Kuddin Hajjin 2026 Cikin Gaggawa

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayar da umarnin a sake duba farashin aikin Hajjin shekarar 2026 nan take.
A cewar umarnin shugaban ƙasan, Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON) ta tattara sabon tsari na farashin cikin kwanaki biyu.

Wannan umarni na zuwa ne bayan korafe-korafe daga al’umma kan tsadar farashin aikin Hajjin bana, inda ake fatan sabuwar duba za ta taimaka wajen rage nauyin da ake ɗora wa mahajjata.

Shettima: Nigeria gaba ta ke da PENGASSAN da ma kowa!  Mataimakin Shugaban Ƙasa Ya Yi Kira Da A Sasanta Rikicin Dangote ...
06/10/2025

Shettima: Nigeria gaba ta ke da PENGASSAN da ma kowa! Mataimakin Shugaban Ƙasa Ya Yi Kira Da A Sasanta Rikicin Dangote Da Ƙungiyar Ma’aikata

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ya yi kira ga Ƙungiyar Ma’aikatan Man Fetur da Gas (PENGASSAN) da su nuna dattako da kishin ƙasa wajen magance sabanin da suke da shi da Kamfanin Dangote Refinery.

Shettima, yayin wata tattaunawa da manema labarai, ya bayyana cewa Alhaji Aliko Dangote ba mutum ɗaya ba ne, amma “cibiyar tattalin arzikin Najeriya”, wanda jarinsa ya taka muhimmiyar rawa wajen bunƙasa tattalin arzikin ƙasar.

“Idan ya zuba jarinsa a Microsoft ko Amazon, da yanzun yana da darajar dala biliyan 70 zuwa 80. Amma ya zaɓi ya zuba a ƙasarsa — don haka wajibi ne mu kare shi,” in ji Shettima.

Ya kuma gargadi ma’aikata da masu masana’antu da su guji daukar matakan da za su haifar da cikas ga ci gaban ƙasa, yana mai cewa:

“Ba lamarin da zai sa a rike ƙasa gaba ɗaya a matsayin garkuwa saboda ƙaramin rikicin ƙwadago. Najeriya ta fi PENGASSAN girma. Najeriya ta fi kowa girma.”

Shettima ya yi kira da a nemi hanyar sulhu da fahimtar juna tsakanin ɓangarorin biyu domin kare sha’anin tattalin arzikin ƙasa.

Kotun Majistare ta aika da ɗan Tiktok “Maiwushirya” gidan gyaran hali!An same shi da laifin wallafa bidiyo da hotunan fi...
06/10/2025

Kotun Majistare ta aika da ɗan Tiktok “Maiwushirya” gidan gyaran hali!

An same shi da laifin wallafa bidiyo da hotunan fitsara tare da wata Wada.
Mai shari’a Halima Wali ta ce irin wannan dabi’a tana lalata tarbiyyar matasa.

Wata sabuwa!💥Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche Nnaji, ya amince da kansa cewa Jami’ar Nsukka (UNN) ba ta taba ba shi shed...
06/10/2025

Wata sabuwa!💥

Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche Nnaji, ya amince da kansa cewa Jami’ar Nsukka (UNN) ba ta taba ba shi shedar kammala digiri ba!

Rahoton Premium Times ya tabbatar da cewa duk takardun da ya gabatar lokacin da Shugaba Tinubu ya nada shi minista – ciki har da takardar digiri da NYSC – ana zargin bogi ne!

Jami’ar ta tabbatar da cewa Nnaji bai kammala karatu ba kuma ba ta da wani shaida da ke nuna cewa ya taɓa karɓar takarda daga gare ta.

Tambayar yanzu: Idan UNN ba ta ba shi digiri ba, daga ina ya samo takardar da ya gabatar wa gwamnati?

ASUU za ta shiga yajin aikin Gargaɗi sati mai zuwa: Idan Gwamnati Ta Gaza!Kungiyar Malam Jami'a ASUU ta baiwa gwamnati w...
06/10/2025

ASUU za ta shiga yajin aikin Gargaɗi sati mai zuwa: Idan Gwamnati Ta Gaza!

Kungiyar Malam Jami'a ASUU ta baiwa gwamnati wa’adin kwanaki 14 ta cika alkawuran da aka yi tun Fabrairu 2025, in ba haka ba za ta tafi yajin aiki na makonni biyu!

Shugaban ƙasa na ASUU, Farfesa Christopher Piwuna, ya ce gwamnati ta yi burus da mu, duk da an sanar da ita batun.
Yanzu ASUU ta ce lokaci ya ƙure — dole gwamnati ta sanya hannu kan yarjejeniyar da aka kulla da ita, ko kuma su tafi yajin aikin gargadi na sati biyu, cikin satin mai zuwa.

“Na nemi Uwargidan Shugaban Ƙasa ta zama uwata” — Gwamna MutfwangGwamnan Filato, Caleb Mutfwang, ya bayyana cewa ya nemi...
06/10/2025

“Na nemi Uwargidan Shugaban Ƙasa ta zama uwata” — Gwamna Mutfwang

Gwamnan Filato, Caleb Mutfwang, ya bayyana cewa ya nemi Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta karɓe shi a matsayin ɗanta.

Ya faɗi haka ne a jana’izar mahaifiyar shugaban jam’iyyar APC, Farfesa Nentawe Yilwatda, inda ya yabawa Oluremi bisa ƙaunar da take nuna wa Jihar Filato.

“Tun kafin Nentawe ya kira kansa ɗan farko na shugaban ƙasa, ni ma na riga da na nema in zama ɗa. Ita uwa ta ce,” in ji Mutfwang.

Ya kuma gode wa Uwargidan Shugaban Ƙasa bisa tallafi da kulawar da take ba jihar.

Gwamnatin Jihar Kano ta gargadi wasu malamai daga wajen jihar da su daina tsoma baki ko yin sharhi da zai iya kawo cikas...
05/10/2025

Gwamnatin Jihar Kano ta gargadi wasu malamai daga wajen jihar da su daina tsoma baki ko yin sharhi da zai iya kawo cikas ga aikin da kwamitin shura ke gudanarwa kan zargin da ake yi wa Malam Lawan Abubakar Shu’aibu Triumph.

Sakataren kwamitin, Shehu Wada Sagagi, ne ya bayyana hakan yayin taron manema labarai da aka gudanar a ranar Lahadi.

Sagagi ya ce gwamnati ta lura da yadda wasu malamai daga jihohi daban-daban ke shiga cikin batun kafin kammala binciken, abin da ya bayyana cewa na iya kawo tangarda ga aikin kwamitin.

Ya tabbatar da cewa kwamitin na gudanar da aikinsa cikin gaskiya, adalci da tsoron Allah, tare da tabbatar da cewa duk wani rahoto da za a fitar zai kasance bisa hujjoji da shaidu na gaskiya.

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari a Sakaba, Jihar KebbiA yau Asabar, 4 ga Oktoba, 2025, rahotanni sun tabbatar da cewa wasu ƴan b...
04/10/2025

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari a Sakaba, Jihar Kebbi

A yau Asabar, 4 ga Oktoba, 2025, rahotanni sun tabbatar da cewa wasu ƴan bindiga sun kai farmaki a ƙaramar hukumar Sakaba ta jihar Kebbi.

Shaidun gani da ido sun bayyana cewa mazauna yankin sun shiga tsananin firgici yayin da maharan s**a mamaye wasu sassan ƙauyuka, inda harbe-harbe s**a yi ta tashi na tsawon lokaci.

Duk da cewa har yanzu hukumomin tsaro ba su fitar da cikakken bayani ba, an ce akwai yiwuwar asarar rayuka da raunuka a cikin lamarin.

Ana sa ran rundunar ƴan sanda da sauran jami’an tsaro za su fitar da sanarwa cikin lokaci kan halin da ake ciki, da kuma matakan da ake ɗauka domin dawo da zaman lafiya a yankin.

Akpabio ya ce mahaifiyar shugaban APC Nentawe “ta zaɓi lokaci mafi dacewa” ta rasu 😮A yau a Jos, Shugaban Majalisar Datt...
04/10/2025

Akpabio ya ce mahaifiyar shugaban APC Nentawe “ta zaɓi lokaci mafi dacewa” ta rasu 😮

A yau a Jos, Shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio ya halarci jana’izar Mama Lydia Yilwatda, mahaifiyar shugaban jam’iyyar APC na ƙasa.

Ya yaba da rayuwarta, ya kuma ce gadonta na ci gaba da bayyana a rayuwar ɗanta.
Ya yi godiya ga Shugaba Tinubu kan haɗa kan shugabanni da jama’a a jihar Filato.

AKWAI YIWUWAR A SAMU RAGI A KUƊIN HAJJIN BAƊINAHCON ta ce ta samu nasarar rage Naira biliyan 19 daga farashin Hajjin 202...
03/10/2025

AKWAI YIWUWAR A SAMU RAGI A KUƊIN HAJJIN BAƊI

NAHCON ta ce ta samu nasarar rage Naira biliyan 19 daga farashin Hajjin 2025!

👉 Wannan na nufin an samu saukar sama da N200,000 ga kowanne mahajjaci daga cikin kujeru 66,910 da aka ware wa Najeriya.

Shugaban NAHCON, Prof. Abdullahi Usman, ya ce wannan ragi ya zo ne bayan tattaunawa da hukumomin Saudiyya – kuma ya yi daidai da manufofin gwamnatin Tinubu na rage nauyin al’umma.

Kotun Shari’a ta Fagge ta yankewa ɗan sanda na bogi hukuncin shekara 1 a kurkukuKotun Upper Shari’a Court da ke Fagge, J...
03/10/2025

Kotun Shari’a ta Fagge ta yankewa ɗan sanda na bogi hukuncin shekara 1 a kurkuku

Kotun Upper Shari’a Court da ke Fagge, Jihar Kano, ta yanke wa wani mutum mai suna Nasiru Sh*tu Kofar Dawanau hukuncin shekara 1 a gidan gyaran hali ko kuma ya biya tarar ₦50,000, bisa k**a shi da laifin sanya kansa ɗan sanda na bogi.

Mai magana da yawun rundunar ƴan sanda a Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya tabbatar da faruwar lamarin. A cewarsa, an k**a wanda ake zargin ne bayan samun bayanan sirri kan yadda yake damfara mutane da sunan jami’in tsaro.

Kotun ta bayyana cewa wannan hukunci na zama darasi ga sauran jama’a da ke shiga irin wannan ta’asar.

Address

Kano

Telephone

+2348133260813

Website

http://jaridardala.com.ng/, http://jaridardala.com.ng/

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jaridar Dala posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share