12/08/2026
Hukumomi a Sudan ta Kudu sun tabbatar da mutuwar fiye da mutane 60, yayin da wasu sama da 50 s**a jikkata a wasu hare-haren da matasa masu ɗauke da mak**ai s**a kai a jihar Warrap, a tsakiyar ƙasar.
An ce hare-haren, waɗanda ake zargin suna da nasaba da rikicin ƙabilanci, sun shafi yankunan Tonj North da Akok.
Rahotanni sun ce an kuma sace dabbobi tare da wawure wasu kadarori.
Hukumomin jihar sun ce mutane 17 daga cikin waɗanda s**a jikkata sosai an tura su Wau domin samun ƙarin kulawar lafiya, yayin da sauran ke karɓar magani a cibiyoyin kiwon lafiya na yankin.
Rikicin ƙabilanci da hare-haren ramuwar gayya na ci gaba da zama babbar barazana ga zaman lafiya a Sudan ta Kudu, duk da ƙoƙarin da ake yi na aiwatar da yarjejeniyar zaman lafiya.