
07/10/2025
Anyi kira ga Hisba da su k**a wani matashi me izgili da mutuwa!
Gidauniyar Grassroot Care and Aid Foundation (GCAF) ta yi kira ga hukumar Hisba a ƙarƙashin jagorancin Imam Dr. Muhammad Aminu Ibrahim Daurawa da kuma hukumar tace fina-finai ta jihar Kano, wato Kano State Censorship Board, ƙarƙashin Abba Almustapha, da su ɗauki matakin gaggawa kan wani matashi da ya wallafa bidiyo na rashin tarbiyya a kafafen sada zumunta.
A cewar shugaban gidauniyar, Amb. Auwalu Muhammad Danlarabawa, bidiyon na nuna matashin cikin makaranta yana yin isgili, yana sanya likafani, tare da tsayawa a gaban wuta yana rawa da waka da ke nuna rashin natsuwa da rashin kunya.
Gidauniyar ta bayyana damuwa kan irin wannan bidiyo, tana mai cewa hakan na iya cutar da tunanin yara da matasa masu tasowa, wadanda ka iya ɗaukar irin wannan hali a matsayin abin koyi.
Ta kuma roƙi manyan malamai da hukumomi irin su Hisba da Censorship Board su tabbatar da hana irin wannan bidiyo kafin su bazu cikin al’umma.