Jaridar Dala

Jaridar Dala Sahihan labarai, Ilmantarwa, Nishadantarwa, kimiya da fasaha! A kasa najeriya da sauran fadin duniya!

Tiƙar rawa ba zai hana ni suburbuɗo mu ku aiki ba! Gwamna Adeleke Gwamnan Osun, Ademola Adeleke, ya ce duk wanda ke s**a...
10/12/2025

Tiƙar rawa ba zai hana ni suburbuɗo mu ku aiki ba! Gwamna Adeleke

Gwamnan Osun, Ademola Adeleke, ya ce duk wanda ke s**ar rawarsa a bainar jama’a yana bata lokaci, saboda rawa ba ta hana shi gudanar da aikinsa ko kaɗan.

Ya ce: “Na riga na kasance mai farin ciki tun kafin na zama gwamna. Rawa ba matsala ba ce ba zai hana inyi aiki ba!”

JANYE ƳANSANDA BA FASHI!Shugaba Tinubu ya sake tabbatar da cewa ba za a fasa janye ’yan sanda daga tsaron manyan mutane ...
10/12/2025

JANYE ƳANSANDA BA FASHI!

Shugaba Tinubu ya sake tabbatar da cewa ba za a fasa janye ’yan sanda daga tsaron manyan mutane ba. Ya ce an horar da Civil Defence ne domin wannan aiki.

Ya umurci NSA Nuhu Ribadu da Isfeto Janar Egbetokun su tabbatar an aiwatar da umarnin na sa ba tare da wasa ba.

Matakin na nufin ƙara yawan ’yan sanda a unguwanni da yankunan karkara da ke cikin haɗari.

Can na jiyo wani na faɗin wai an ci jakk....Du wanda ya ƙarasa ba da yawun JaridarDala ba 🫣
10/12/2025

Can na jiyo wani na faɗin wai an ci jakk....

Du wanda ya ƙarasa ba da yawun JaridarDala ba 🫣

An hangi Shugaban Amurka Donald trump na sharɓar bacci Lokacin da yake ganawa da muƙarraban gwamnatinsa.
10/12/2025

An hangi Shugaban Amurka Donald trump na sharɓar bacci Lokacin da yake ganawa da muƙarraban gwamnatinsa.

Hedkwatar Tsaro ta ba da umarnin rusa dukkan roadblocks da checkpoints marasa muhimmanci a fadin Najeriya, ciki harda Ab...
10/12/2025

Hedkwatar Tsaro ta ba da umarnin rusa dukkan roadblocks da checkpoints marasa muhimmanci a fadin Najeriya, ciki harda Abuja zuwa Kano!

Hedkwatar ta ce yawaitar shingaye marasa izini na hana zirga-zirga cikin jindadi Sannan kuma ta na rage ingancin aiki hakan kuma na jefa jami’ai cikin hadari.

Wannan umarni na cikin wata takardar sanarwa ta cikin gida, wanda aka aike ranar 5 ga Disamba, kuma Brig. Janar A. Rabiu ya rattaba wa hannu “don CDS”, sanarwar ta nuna cewa Hedikwatar Tsaro ta lura da yawaitar shingayen sojoji marasa mahimmanci da dama daga cikin manyan hanyoyi.

Sanarwar ta lissafo wasu daga cikin manyan hanyoyin da abin ya fi shafa, ciki har da:

Abuja–Lokoja–Ajaokuta–Idah–Otukpa–Obollo Afor–Enugu

Abuja–Lokoja–Obajana–Kabba–Omuo–Ekiti–Ikole Ekiti

Abuja–Lokoja–Okene–Okpella–Auchi–Benin

Abuja–Kaduna–Kano

Lagos–Ore–Benin–Asaba–Niger Bridge

Daga yanzu, za a koma mobile patrols da tsauraran dabarun leken asiri.

Shin wannan mataki zai inganta tsaro?

Yan Bindiga Sun yi Garkuwa da Jami’an EFCC akan Hanyar K**a Wani mai laifi a Jihar KwaraWasu jami’an Hukumar Yaki da mas...
10/12/2025

Yan Bindiga Sun yi Garkuwa da Jami’an EFCC akan Hanyar K**a Wani mai laifi a Jihar Kwara

Wasu jami’an Hukumar Yaki da masu yiwan tattalin arziki zagon ƙasada (EFCC) sun fada cikin tarkon ƴan bindiga.
Ƴan bindiga sunyi garkuwa da su a kan hanyarsu ta zuwa jihar Kwara domin k**a wani da ake zargi da zamba ta yanar gizo.

Rahotanni daga majiyoyi sun bayyana cewa lamarin ya faru ne a kan wata hanya mai nisa da ke karkara, inda tsagerun s**a tare hanya, s**a bude wuta kan motar jami’an hukumar, s**a kuma kwashe su zuwa cikin dajin da ke yankin.

Wannan mummunan lamari ya tayar da hankalin hukumomin tsaro, inda aka fara wani gagarumin aikin ceto tare da hadin gwiwar rundunoni daban-daban domin gano inda aka kai jami’an.

Majiyoyi na tsaro sun ce ana amfani da bayanan sirri da na’urori domin bibiyar tafiyar ’yan bindigar, tare da fatan ganin an kubutar da jami’an cikin koshin lafiya.

Ban yafewa Buhari ba, na bar shi da Allah -ElZakzakyElzakzaky Ya yi alhini a lokacin Tunawa da Shekaru 10 Da Arangamar Z...
10/12/2025

Ban yafewa Buhari ba, na bar shi da Allah
-ElZakzaky

Elzakzaky Ya yi alhini a lokacin Tunawa da Shekaru 10 Da Arangamar Zariya Da Ta Hadar da Sojoji da ’Yan Kungiyar IMN

A yayin tunawa da cika shekaru goma da aukuwar rikicin Zariya, wani fitaccen malamin na Shia ya sake waiwaya irin tashin hankalin da ya faru tsakanin sojojin Najeriya da mabiya Sheikh Ibrahim Zakzaky a shekarar 2015.

Wannan tunawa ta zo ne a daidai lokacin da ake cika shekaru 10 da sojojin Najeriya s**a bude wa mabiyan ƙungiyar wuta a sak**akon arangama da ta barke a garin Zariya, Jihar Kaduna.

Rahotanni a wancan lokaci sun bayyana cewa rikicin ya samo asali ne bayan da aka zargi mabiya Zakzaky da toshe wa tawagar shugaban rundunar sojin Najeriya na wancan lokaci, Laftanar Janar Tukur Buratai, hanya yayin da yake wucewa.

Lamarin dai ya rikide zuwa babbar arangama, wadda daga bisani ta jawo asarar rayuka da dama tare da tayar da kura a tsakanin hukumomi da kungiyoyin kare hakkin bil’adama.

A cikin jawabinsa na yau, malamin ya ce tunawar shekaru 10 ya k**ata ta zama darasi ga bangarorin da abin ya shafa, tare da kira da a rika bi da irin wadannan matsaloli ta hanyar fahimta da ladabi, domin inganta zaman lafiya a kasa.

BA'A YI MANA ADALCI BA!Sanata Abdul Ningi ya koka kan cire masa Dogarin dansanda!A zaman majalisar dattawa na yau Laraba...
10/12/2025

BA'A YI MANA ADALCI BA!
Sanata Abdul Ningi ya koka kan cire masa Dogarin dansanda!

A zaman majalisar dattawa na yau Laraba, an ga fushin sanatoci bayan Sanata Abdul Ningi ya tayar da batun cire masa ɗansanda guda ɗaya, duk kuwa da cewa wasu manyan jami'an gwamnati da ’ya’yansu da ’yan kasuwa har da mawaka suna ci gaba da amfani da ’yan sanda masu dauke da mak**ai a matsayin tsaro.

Sanata Ningi, yayin amfani da Order 42, ya zargi cewa an yi amfani da umarnin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na 23 ga Nuwamba wanda ya bukaci a maida ’yan sanda zuwa ayyukan su na asali — don a muzgunawa ƴanmalisar, yayin da wasu manyan mutanen ke ci gaba da jan dogayen ayarin tsaro.

“Na ga ministoci biyu jiya da dogayen ayarin tsaro. Na ga ’yan kasuwa, ’ya’yan manyan masu mulki, har ma mawaka suna da tsaro. Amma ni Sanata mai aiki shekaru da dama — ɗan sandana guda ɗaya aka janye min,” in ji Ningi.

Ya ce ya amince da sabuwar manufar gwamnati kan tsaro, amma sai an aiwatar da ita daidaito ba tare da nuna bambanci ba.

A cikin martaninsa, Mataimakin Shugaban Majalisa, Sanata Jibrin Barau, ya tabbatar da cewa shugabancin majalisar ya tattauna batun tun ranar Talata, kuma an ɗauki matakin da zai dawo da orderlyn Sanata Ningi.

Ya kuma ba da umarni ga Kwamitin Harkokin ’Yan Sanda ya binciki yadda wasu mawaka, ’yan kasuwa da ’ya’yan manyan jami’an gwamnati ke ci gaba da gudanar da ayarin tsaro duk da umarnin Shugaba Tinubu.

Barau ya yi nuni da cewa manufar Shugaban ƙasa na janye ’yan sanda daga manyan mutanen an yi ta ne domin ƙarfafa aikin rundunar cikin gida, yana mai cewa majalisa na goyon bayan gwamnati akan haka, amma dole a yi komai bisa ka’ida da adalci.

TURJI YA SHIGA TSAKA MAI WUYA: Sojojin Najeriya sun kashe babban yaronsa a sokotoSojoji sun kashe Kachalla Kallamu, babb...
10/12/2025

TURJI YA SHIGA TSAKA MAI WUYA: Sojojin Najeriya sun kashe babban yaronsa a sokoto

Sojoji sun kashe Kachalla Kallamu, babban na hannun daman Bello Turji, a wani samame da Runduna ta 8 ta kai a Sabon Birni!

Rahotanni sun tabbatar da cewa an kashe shine tare da wani babban mai samar wa Turji mak**ai a kauyen Kurawa.

Mutanen Sabon Birni sun yi murna matuƙa da jin labarin.

Hukuma ta ce: “Kashe Kallamu babban rauni ne ga cibiyar Turji.”

LABARI CIKIN HOTUNA: An sace ma mota ko an ƙwace ma ita?Yan Sanda sun gano motoci 7 da aka sata a Kano tare da cafke bar...
09/12/2025

LABARI CIKIN HOTUNA: An sace ma mota ko an ƙwace ma ita?

Yan Sanda sun gano motoci 7 da aka sata a Kano tare da cafke barayin da ke da hannu a fashi da makami!
Motocin sun haɗa da RAV4, Corolla, Matrix, Yaris da manyan motoci biyu!

CP Bakori ya yaba wa jami’ansa, ya kuma gode wa mutanen Kano kan haɗin kai.
Ga jerin Motocin wasu ma harda Plate Number ɗinsu

1. Toyota RAV4 Ruwan Toka

2. jar Peugeot 406 plate number Kebbi GWN 335 AM

3. Baƙar Toyota Corolla Lagos APP 538 DJ

4. Toyota Yaris mai plate number Gombe 121 AH

5. Babbar mota

6. Farar Toyota Matrix mai lambar Lagos EKY 978 GU

7. Forland Truck fara mai plate lamba– GAK 701 XA

Kano na samun sauƙin tsaro, kuma bincike ya ci gaba!

👉 Ku yi sharing – a faɗa wa mutane ko Allah zai sa a dace !

KA JI RABO KO! 🎷Sarkin Daura ya sa ranar da zai naɗa RARARA a matsayin sarkin wakar ƙasar hausa!Sarkin Daura, Alhaji Far...
09/12/2025

KA JI RABO KO! 🎷
Sarkin Daura ya sa ranar da zai naɗa RARARA a matsayin sarkin wakar ƙasar hausa!

Sarkin Daura, Alhaji Faruk Umar Faruk, shi zai yi nadin Ranar Asabar, k**ar yanda RARARA ya wallafa a shafinsa na sada zumunta. Ga abinda ya rubuta:

"Ina gayyatar kowa da kowa zuwa bin wajen nadin sarautata, mai taken 'Sarkin Wakar Kasar Hausa,' sarautar da mai alfarma sarkin Daura yayi min. "Za’ayi nadin a fadar mai martaba sarkin Daura a ranar Asabar, 13 ga Disamba, 2025, Insha Allah."

Sai dai cece-kuce ya tashi, in da masoyan Buhari su ke nuna rashin jin daɗinsu akan haka, in da su me cewa ba su goyi bayan a ba Rarara wannan sarautar!

Shin kuna ganin RARARAn ya dace da sarautar ta Sarkin Wakar ƙasar Hausa?

NAJERIYA WASA CE!Burkina Faso ta saki Jirgin yaki da sojojin Najeriya 11 da ta tsare bayan jirgin sojojin ya yi saukar g...
09/12/2025

NAJERIYA WASA CE!
Burkina Faso ta saki Jirgin yaki da sojojin Najeriya 11 da ta tsare bayan jirgin sojojin ya yi saukar gaggawa ba tare da izini ba!

Gwamnatin Najeriya ta ce matsalar na’ura ce ta tilasta saukar, yanzu an warware komai lafiya, jirgin na shirin tashi daga ƙasar ta burkina fason.

Sai dai wannan lamarin ya sake haskaka yanda yanayin tsaro da diflomasiyya a yankin Sahel ke a dagule a tsakanin maƙotan ƙasashen.

Me kuke ganin ya jawo rashin jituwa a tsakanin ƙasashen yankin?

Address

Kano

Telephone

+2348133260813

Website

http://jaridardala.com.ng/, http://jaridardala.com.ng/

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jaridar Dala posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share