Jaridar Dala

Jaridar Dala Sahihan labarai, Ilmantarwa, Nishadantarwa, kimiya da fasaha! A kasa najeriya da sauran fadin duniya!
(1)

Hantavirus wasu ƙwayoyin cuta ne masu haɗari da ɓeraye da sauran danginsu ke yaɗawa zuwa ga mutane. Ana kamuwa da cutar ...
11/05/2026

Hantavirus wasu ƙwayoyin cuta ne masu haɗari da ɓeraye da sauran danginsu ke yaɗawa zuwa ga mutane.

Ana kamuwa da cutar ne galibi idan mutum ya shaƙi iska mai ɗauke da ƙwayoyin cutar daga busasshen kashin ɓera, fitsarinsu ko yawunsu, musamman a wuraren da s**a daɗe ba a tsaftace ba k**ar ɗakunan ajiya, rumbuna ko gidajen da ɓeraye s**a mamaye.

Masana lafiya sun bayyana cewa cutar na iya haifar da matsananciyar lalacewar huhu ko koda, kuma a wasu lokuta tana iya kaiwa ga mutuwa idan ba a gano ta da wuri ba.

Alamomin cutar Hantavirus:
Zazzabi mai tsanani
Ciwon kai da ciwon jiki
Gajiya da kasala
Tari ko wahalar numfashi
Tashin zuciya ko amai
Ciwon ciki
A wasu mutane, cutar kan rikide zuwa matsalar numfashi mai tsanani da ke bukatar kulawar gaggawa a asibiti.

Hanyoyin kariya:
A rika tsaftace wuraren da ɓeraye ke shiga cikin kulawa
A guji share busasshen kashin ɓera kai tsaye ba tare da jika wurin da maganin kashe ƙwayoyin cuta ba
A rufe abinci yadda ya k**ata
A toshe ramukan da ɓeraye ke bi su shiga gida
A wanke hannu bayan hulɗa da wuraren da ake zargin akwai ɓeraye
Hukumar lafiya ta duniya ta ce hana yawaitar ɓeraye da tsaftar muhalli na daga cikin manyan hanyoyin kariya daga cutar Hantavirus.

Wani sabon bincike da aka wallafa a mujallar lafiya ya bayyana cewa yawan shan energy drink na iya haddasa matsananciyar...
11/05/2026

Wani sabon bincike da aka wallafa a mujallar lafiya ya bayyana cewa yawan shan energy drink na iya haddasa matsananciyar lalacewar koda (Acute Kidney Injury).

Rahoton ya fito ne daga wani bincike da likita Ahmet Murt ya gudanar, inda aka bayyana yadda wani matashi ɗan shekara 21 ɗan ƙasar Turkiyya ya kamu da matsalar koda bayan ya shafe kusan wata guda yana shan lita biyu na energy drink a kullum.

Matashin ya je asibiti ne da alamun tashin zuciya, amai da kuma kasala. Bayan gwaje-gwaje, likitoci sun gano cewa kodarsa ta samu matsananciyar matsala har matakin “Stage 3 Acute Kidney Injury”.

Rahoton ya ce matashin ba shi da wata cuta ko tarihin amfani da magunguna, abin da ya sa likitoci s**a danganta matsalar kai tsaye da yawan shan energy drink.

An bayyana cewa sinadaran da ke cikin irin waɗannan abubuwan sha — musamman caffeine da sauran stimulants — na iya cutar da koda idan aka sha su ba tare da kima ba.

Sai dai bayan an dakatar da shi daga shan energy drink, kodarsa ta dawo daidai cikin kusan makonni biyu ba tare da an yi masa dialysis ba.

Masana lafiya sun yi gargadin cewa mutane su rika kula da yawan energy drink da suke sha, musamman matasa da masu amfani da su domin ƙara kuzari ko yin aiki na dogon lokaci.

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa Alhaji Atiku Abubakar ya gargadi jam’iyyun adawa cewa su daina tunanin tura tikitin shug...
11/05/2026

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa Alhaji Atiku Abubakar ya gargadi jam’iyyun adawa cewa su daina tunanin tura tikitin shugaban ƙasa zuwa Kudu a 2027, yana cewa hakan zai taimakawa Tinubu ya ƙara karfi a zabe.

Ya ce ai siyasa ba tausayi ba ce, “lissafi ne da dabaru,” kuma ya tambaya: *yaya dan Kudu zai kayar da shugaban Kudu?*

Atiku ya kuma ce Kudu ya riga ya yi dogon lokaci a mulki a Jamhuriya ta Hudu, don haka hujjar zoning na iya zama mai rauni.

Sai dai ya ce Kudu maso Gabas na da damar shugabanci amma a hanya mai tsari, ba kawai “kyautar siyasa” ba.

Wannan magana ta tayar da kura a siyasar Najeriya!

KANO: ’Yan sanda sun k**a mutane 3 bisa amfani da ƙananan yara wajen tallata maganin gargajiya da furta kalamai marasa d...
11/05/2026

KANO: ’Yan sanda sun k**a mutane 3 bisa amfani da ƙananan yara wajen tallata maganin gargajiya da furta kalamai marasa dacewa.

SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce rundunar ba za ta bari a riƙa amfani da yara wajen abubuwan da s**a saɓa wa tarbiyya da doka ba.

Ana ci gaba da bincike domin kamo sauran masu hannu a lamarin.

An k**a wata matar uba mai suna Ogechi John bisa zargin dukan ‘yar mijinta mai shekara 9 har ta rasu a jihar Enugu.Rahot...
11/05/2026

An k**a wata matar uba mai suna Ogechi John bisa zargin dukan ‘yar mijinta mai shekara 9 har ta rasu a jihar Enugu.

Rahotanni sun ce yarinyar mai suna Ogechi Amanda ta dade tana fama da cin zarafi daga wajen matar uban nata kafin wannan mummunan lamari.

Gwamnatin Enugu ta ce ba za ta lamunci cin zarafin yara ba, tare da alkawarin tabbatar da an yi wa yarinyar adalci.

Wata Babbar Kotu a Abuja ta sake bayar da sammacin k**a tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, bayan ya kasa gurf...
11/05/2026

Wata Babbar Kotu a Abuja ta sake bayar da sammacin k**a tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, bayan ya kasa gurfana a gaban kotu a ranar Litinin.

Wannan ne karo na biyu cikin mako guda da kotu ke bayar da umarnin k**a tsohon ministan saboda rashin bayyana a zaman shari’a.

Rahotanni sun ce kotun ta dauki matakin ne domin tabbatar da cewa an gabatar da shi domin ci gaba da sauraron karar da ake yi masa.

Ana sa ran hukumomin tsaro za su aiwatar da umarnin kotun domin gurfanar da shi a gaba.

Gwamnatin Tarayya ta ce za ta fara tilasta gwajin miyagun ƙwayoyi ga sabbin dalibai da masu ci gaba da karatu a makarant...
11/05/2026

Gwamnatin Tarayya ta ce za ta fara tilasta gwajin miyagun ƙwayoyi ga sabbin dalibai da masu ci gaba da karatu a makarantun sakandare domin yaƙi da shaye-shaye a tsakanin matasa.

Yayin da wasu ke yabawa da matakin, wasu na tambayar yadda za a kare sirrin ɗalibai da haƙƙinsu.

Shin kana goyon bayan wannan tsari?

Gwamnatin Tarayya ta sanar da cire sharadin rubuta jarabawar JAMB ga daliban da ke neman shiga Kwalejojin Ilimi (College...
11/05/2026

Gwamnatin Tarayya ta sanar da cire sharadin rubuta jarabawar JAMB ga daliban da ke neman shiga Kwalejojin Ilimi (Colleges of Education) a Najeriya.

Ministan Ilimi, ne ya bayyana hakan a ranar Litinin yayin taron tsara manufofin daukar dalibai na jarabawar JAMB ta shekarar 2026 da aka gudanar a Abuja.

A cewarsa, duk dalibin da ya samu akalla credit hudu a darussan da s**a dace zai iya neman gurbin karatu a Kwalejojin Ilimi ba tare da ya rubuta jarabawar UTME ba.

Matakin na zuwa ne yayin da gwamnati ke kokarin kara yawan masu shiga bangaren horas da malamai tare da bunkasa ilimi a fadin kasar nan.

Sai dai har yanzu JAMB da Ma’aikatar Ilimi ba su fitar da karin cikakkun ka’idojin yadda tsarin zai fara aiki ba.

Wani matashi mazaunin Zariya mai suna Ahmad Sa’idu, wanda aka fi sani da Abba, ya bayyana dalilin da ya sanya ya rike ri...
11/05/2026

Wani matashi mazaunin Zariya mai suna Ahmad Sa’idu, wanda aka fi sani da Abba, ya bayyana dalilin da ya sanya ya rike rigar Kakakin Majalisar Wakilai ta Tarayya, Rt. Hon. Abbas Tajudeen, yayin wani taron siyasa da aka gudanar a filin Idi na Mallawa da ke Zariya.

Lamarin dai ya faru ne lokacin da Abbas Tajudeen ya bayyana aniyarsa ta sake neman takara karo na biyar a Majalisar Wakilai, inda bidiyon yadda matashin ya rike rigar kakakin ya bazu sosai a kafafen sada zumunta.

Da yake zantawa da manema labarai a ranar Litinin, Ahmad Sa’idu ya ce yana fama da mummunan karaya a hannunsa na dama bayan wani hatsari da ya rutsa da shi, wanda ya karya hannun har wurare uku.

Ya bayyana cewa an fara duba lafiyarsa a Cibiyar Gyaran Karaya ta Gargajiya da ke Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ahmadu Bello (ABUTH), kafin daga bisani a tura shi zuwa Asibitin Sojoji na 44 Nigerian Army Reference Hospital da ke Kaduna domin ci gaba da jinya.

Sai dai ya ce matsalar rashin kudi ta hana shi ci gaba da samun magani bayan taimakon da wasu s**a rika ba shi ya tsaya.

“Ba mu iya ci gaba da biyan kudin magani ba bayan taimakon da ake mana ya tsaya,” in ji shi.

Ahmad Sa’idu ya kara da cewa bayan jin cewa Kakakin Majalisar zai halarci taron bayyana takara, sai ya je wajen da nufin neman taimako kai tsaye daga gare shi.

“A matsayina na daya daga cikin magoya bayan Kakakin Majalisar, na je wajen domin neman taimakonsa. Da na matsa kusa da shi sai na rike rigarsa ina kokarin nuna masa hannuna da ya karye, amma jami’an tsaro s**a janye ni,” ya bayyana.

Ya kuma nemi afuwar Abbas Tajudeen kan abin da ya faru, yana mai cewa bai taba nufin kunyata shi a bainar jama’a ba.

“Da ace na san abin zai jawo masa irin wannan abin kunya a kasa baki daya, da na hakura na ci gaba da zama da ciwon,” in ji shi.

Shi ma mahaifin matashin, Malam Sa’idu Ibrahim Abubakar, ya nemi afuwa ga Kakakin Majalisar tare da zargin cewa wasu ‘yan adawa na siyasa sun yi amfani da lamarin wajen yada bayanan karya.

Ya ce iyalinsu sun shafe sama da shekaru biyu suna fama da neman kudin maganin dan nasu a ABUTH da Asibitin Sojoji na 44 da ke Kaduna, amma kudin sun gagare su.

Sai dai ya yaba wa Abbas Tajudeen bisa amincewa da ya yi na daukar nauyin kudin maganin dan nasa duk da abin da ya faru a wajen taron.

11/05/2026

Mene ne ra’ayinku kan wannan furuci da Janar Ibro ya yi?

Rundunar Sojin Najeriya ta musanta rahotannin da ke cewa hare-haren sama da aka kai a wasu sassan jihar Neja sun yi sana...
11/05/2026

Rundunar Sojin Najeriya ta musanta rahotannin da ke cewa hare-haren sama da aka kai a wasu sassan jihar Neja sun yi sanadin mutuwar fararen hula.

A cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar, ta ce hare-haren sun kasance kan maɓoyar ƴan bindiga da masu aikata laifuka ne kawai, kuma an gudanar da su bisa sahihan bayanan sirri domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Sojojin sun bayyana cewa rahotannin da ke yawo a wasu kafafen sada zumunta na zargin kashe fararen hula “ba su da tushe”, tare da jaddada cewa rundunar na bin ƙa’idojin aikin soja da kare haƙƙin jama’a yayin gudanar da hare-hare.

Sanarwar ta ƙara da cewa hare-haren sun yi nasarar tarwatsa sansanonin ƴan bindiga da dama tare da kashe wasu daga cikin masu tayar da ƙayar baya da s**a addabi yankunan jihar.

Rundunar ta kuma yi kira ga jama’a da su riƙa tantance sahihancin labarai kafin yaɗawa, tana mai cewa wasu rahotanni na ƙoƙarin ɓata sunan jami’an tsaro da rage ƙwarin gwiwar yaƙi da matsalar tsaro.

A ƴan kwanakin nan dai ana ci gaba da kai hare-haren sama a wasu yankunan arewacin Najeriya domin daƙile ayyukan ƴan bindiga da ƙungiyoyin masu tayar da ƙayar baya.

Address

Kano

Telephone

+2348133260813

Website

http://jaridardala.com.ng/, http://jaridardala.com.ng/

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jaridar Dala posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share