Radio Kano

Radio Kano Wannan Shi ne Shafin Gidan Rediyon Kano. Za ku iya turo mana sakonnin Ra'ayoyinku da Shawarwarinku.
(4)

Wani matashi mai shekaru 18, Abdullahi Aminu, ya rasu bayan  ya faɗa wani kududdufi a Kofar Gabas dake ƙaramar hukumar D...
12/08/2026

Wani matashi mai shekaru 18, Abdullahi Aminu, ya rasu bayan ya faɗa wani kududdufi a Kofar Gabas dake ƙaramar hukumar Danbatta a nan jihar Kano.

Hukumar Kashe Gobara ta jihar nan ta tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa ta bakin Jami'in Hulɗa da Jama'arta, Saminu Yusuf Abdullahi, inda ta ce jami’anta sun samu fito da matashin daga cikin ruwa ba ya cikin hayyacinsa, amma daga bisani aka tabbatar da rasuwarsa, sannan aka miƙa gawarsa ga Sakataren Dagacin Danbatta, Alhaji Baba Ado Sarkin Bai.

Hukumar ta jajantawa iyalan marigayin, tare da yin kira ga jama’a da su ƙara taka-tsantsan a kusa da wuraren ruwa, musamman a wannan lokacin na damina.

Shahararren dan wasan kwallon kafa na Portugal, Cristiano Ronaldo, da masoyiyarsa Georgina Rodriguez, sun zama ma’aurata...
11/08/2026

Shahararren dan wasan kwallon kafa na Portugal, Cristiano Ronaldo, da masoyiyarsa Georgina Rodriguez, sun zama ma’aurata a hukumance.

Ronaldo ya wallafa hotunan zoben aure, lamarin da ya kara tabbatar da wannan sabon babi na rayuwarsu.

Muna taya Cristiano Ronaldo da Georgina murnar wannan babban mataki na rayuwa, muna musu fatan zaman lafiya da soyayya.

Muhammad Bello Galadanchi ✏️

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya karɓi bakuncin takwaransa na Jihar Yobe, Mai Mala Buni, a ofishinsa a ya...
11/08/2026

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya karɓi bakuncin takwaransa na Jihar Yobe, Mai Mala Buni, a ofishinsa a yau Talata, 11 ga watan Agusta, 2026.

Mai Mala Buni ya kai wa Gwamnan Kano ziyarar girmamawa, inda Gwamnonin biyu s**a tattauna kan batutuwan da s**a shafi al’amuran gwamnati da haɗin gwiwa tsakanin jihohin Kano da Yobe.

Mai Rahoto
Muhammad Bello Galadanchi

11/08/2026

Labarai Da Rahotanni tare da Mu'azzam Abdullahi Gwale.

Gwamnatin jihar Kano ta Gyara Ofishin Hukumar Kididdiga ta Jihar KanoGwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya gyaran ofi...
11/08/2026

Gwamnatin jihar Kano ta Gyara Ofishin Hukumar Kididdiga ta Jihar Kano

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya gyaran ofishin Hukumar Kididdiga ta Jihar Kano (Kano State Bureau of Statistics – KSBS), domin inganta yanayin aiki da samar da ingantaccen muhalli ga ma’aikatan hukumar.

Aikin gyaran na daga cikin matakan da ake dauka wajen inganta cibiyoyin Gwamnati da kuma samar da kyakkyawan yanayin gudanar da ayyukan ma’aikata.

Hukumar Kididdiga ta Jihar Kano na da muhimmiyar rawa wajen tattara, sarrafawa da samar da bayanan kididdiga da ake amfani da su wajen tsara manufofi da shirye-shiryen ci gaban jihar.

Takardun kasafin kudin Jihar Kano sun kuma nuna cewa gwamnatin jihar ta tanadi ayyuka da s**a shafi samarwa da gyaran gine-ginen ofisoshin gwamnati, ciki har da aikin da ya shafi ofishin Bureau of Statistics a Audu Bako Secretariat.

Ana sa ran inganta kayan aiki da muhallin ofisoshin hukumar zai taimaka wajen kara ingancin ayyukan kididdiga, tare da samar da sahihan bayanai da za su taimaka wajen yanke shawarar da ta dace kan ci gaban Jihar Kano.

Wannan na daga cikin kokarin gwamnatin Abba Kabir Yusuf na inganta ababen more rayuwa da cibiyoyin Gwamnati domin kara ingancin ayyukan da ake gudanarwa ga al’ummar jihar.

Zayyanu Suraj Yahya Maigari ✍️

Gwamnatin Jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin  Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba  Kabir Yusuf, na sanar da gudanar da Bikin R...
11/08/2026

Gwamnatin Jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, na sanar da gudanar da Bikin Rarraba Takardun Bayar da Filaye ga Ƙungiyoyin Matasa daga Ƙananan Hukumomin Jihar Kano 44 — Kashi na Farko.

Za a gudanar da taron k**ar haka:

Rana: Laraba, 12 ga Agusta, 2026
Lokaci: 10:00 na safe
Wuri: Coronation Hall, Gidan Gwamnatin Jihar Kano
Masu Amfana: Matasa 1,000

Sameer Lukman Ibraheem
Mataimaki na Musamman ga Kwamishinan Ƙasa da Tsare-tsaren Birane na Jihar Kano

11 ga Agusta, 2026

Comr Sani Ibrahim
Radio Kano ✍🏻

An samu tashin gobara a reshen Access Bank da ke Dawanau, Ƙaramar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano.Wannan na cikin sana...
11/08/2026

An samu tashin gobara a reshen Access Bank da ke Dawanau, Ƙaramar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano.

Wannan na cikin sanarwar da Jami’in Hulɗa da Jama’a na Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano, ACFO Saminu Yusif Abdullahi, ya fitar a ranar Talata, 11 ga Agusta 2026.

Ya ce gobarar ta tashi ne da misalin ƙarfe 1:17 na rana, inda jami’an kashe gobara daga tashar Dawanau s**a isa wurin tare da shawo kan gobarar kafin ta bazu zuwa sauran sassan ginin bankin.

Sanarwar ta ce gobarar ta k**a injin janareta kirar Mikano da kuma taransifomar lantarki.

Hukumar ta ce har yanzu ana ci gaba da gudanar da bincike domin gano musabbabin tashin gobarar.

Zayyanu Suraj Yahya Maigari ✍️

Gwamnatin Kano Ta Umarci Masu Sayar da Dafaffiyar Masara Su Samar da Kwandunan Zuba SharaGwamnatin Jihar Kano ta umarci ...
11/08/2026

Gwamnatin Kano Ta Umarci Masu Sayar da Dafaffiyar Masara Su Samar da Kwandunan Zuba Shara

Gwamnatin Jihar Kano ta umarci masu sayar da dafaffiyar masara da sauran masu sana’o’i a gefen tituna da su samar da kwandunan zuba shara domin tattara bawon masara, kwanson masara da sauran tarkacen da sana’o’insu ke samarwa.

Arewa Updates ta rawaito cewa, Jami’in Hulɗa da Jama’a na Hukumar Kwashe Shara ta Jihar Kano, REMASAB, Malam Abubakar Ahmad, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin, 10 ga Agusta, 2026.

Shugaban Hukumar, Dr. Muhammad Salisu Khalil, ya ce umarnin ya shafi masu sana’o’i musamman waɗanda ke gudanar da harkokinsu a t**in Gidan Zoo, France Road, Katsina Road, Maiduguri Road da t**in zuwa Zaria.

Ya kuma gargadi masu sana’o’in da su daina zubar da shara a kan tituna da kuma cikin magudanan ruwa, domin hakan na iya haifar da toshewar magudanan ruwa da kuma ƙara matsalar muhalli.

Hukumar ta ce ta gudanar da zagaye domin wayar da kan masu sana’o’i daban-daban da ke gefen t**i, ciki har da masu sayar da gyaɗa mai gishiri, yogurt, shinkafa da wake, ’yan bunburutu, masu sayar da dabino, yalo da ɗata da sauran masu sana’o’i.

REMASAB ta bayyana cewa ana samun wasu daga cikin masu sana’o’in suna sake zubar da shara a wuraren da ma’aikatan hukumar s**a riga s**a share, lamarin da ke ƙara haddasa taruwar datti da toshewar magudanan ruwa.

Hukumar ta jaddada cewa za ta ci gaba da aiwatar da dokokin tsaftar muhalli, tare da ɗaukar matakin doka kan duk wanda aka samu yana zubar da shara a wuraren da doka ta haramta.

Ta ce matakan za su iya haɗawa da gurfanar da waɗanda s**a karya dokar a gaban Kotun Tsaftar Muhalli.
Me za ku ce game da wannan umarni?

Zayyanu Suraj Yahya Maigari ✍️

11/08/2026

Shirin Taskar Labarai Na Ranar Litinin 10/08/2026, Tare Da Aisha Sani Bala.

11/08/2026

Shirin Iya Ruwa Na Ranar Litinin 10/08/2026 Tare Da Mubrak Ubaye Kofar Wambai

Address

No. 1 Ibrahim Taiwo Road, Gidan Bello Dandago
Kano
700234

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Radio Kano posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Radio Kano:

Shortcuts

Share