11/08/2026
Gwamnatin Kano Ta Umarci Masu Sayar da Dafaffiyar Masara Su Samar da Kwandunan Zuba Shara
Gwamnatin Jihar Kano ta umarci masu sayar da dafaffiyar masara da sauran masu sana’o’i a gefen tituna da su samar da kwandunan zuba shara domin tattara bawon masara, kwanson masara da sauran tarkacen da sana’o’insu ke samarwa.
Arewa Updates ta rawaito cewa, Jami’in Hulɗa da Jama’a na Hukumar Kwashe Shara ta Jihar Kano, REMASAB, Malam Abubakar Ahmad, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin, 10 ga Agusta, 2026.
Shugaban Hukumar, Dr. Muhammad Salisu Khalil, ya ce umarnin ya shafi masu sana’o’i musamman waɗanda ke gudanar da harkokinsu a t**in Gidan Zoo, France Road, Katsina Road, Maiduguri Road da t**in zuwa Zaria.
Ya kuma gargadi masu sana’o’in da su daina zubar da shara a kan tituna da kuma cikin magudanan ruwa, domin hakan na iya haifar da toshewar magudanan ruwa da kuma ƙara matsalar muhalli.
Hukumar ta ce ta gudanar da zagaye domin wayar da kan masu sana’o’i daban-daban da ke gefen t**i, ciki har da masu sayar da gyaɗa mai gishiri, yogurt, shinkafa da wake, ’yan bunburutu, masu sayar da dabino, yalo da ɗata da sauran masu sana’o’i.
REMASAB ta bayyana cewa ana samun wasu daga cikin masu sana’o’in suna sake zubar da shara a wuraren da ma’aikatan hukumar s**a riga s**a share, lamarin da ke ƙara haddasa taruwar datti da toshewar magudanan ruwa.
Hukumar ta jaddada cewa za ta ci gaba da aiwatar da dokokin tsaftar muhalli, tare da ɗaukar matakin doka kan duk wanda aka samu yana zubar da shara a wuraren da doka ta haramta.
Ta ce matakan za su iya haɗawa da gurfanar da waɗanda s**a karya dokar a gaban Kotun Tsaftar Muhalli.
Me za ku ce game da wannan umarni?
Zayyanu Suraj Yahya Maigari ✍️