Radio Kano

Radio Kano Wannan Shi ne Shafin Gidan Rediyon Kano. Za ku iya turo mana sakonnin Ra'ayoyinku da Shawarwarinku.
(7)

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf yanada Mai Martaba Sarkin Gaya Alh. Dr Aliyu Ibrahim a matsayin Amirul Hajj na jiha...
12/05/2026

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf yanada Mai Martaba Sarkin Gaya Alh. Dr Aliyu Ibrahim a matsayin Amirul Hajj na jihar Kano awannan Shekara.

Zayyanu Suraj Yahya Maigari ✍️

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan’adam ta Amnesty International ta buƙaci Gwamnatin Najeriya ta binciki harin jirgin yaƙi da aka ...
12/05/2026

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan’adam ta Amnesty International ta buƙaci Gwamnatin Najeriya ta binciki harin jirgin yaƙi da aka kai a kasuwar Tumfa da ke Zurmi a jihar Zamfara, wanda rahotanni s**a ce ya kashe fararen hula sama da 100.

Ƙungiyar ta ce jiragen soji sun yi shawagi a saman kasuwar tun da rana kafin daga bisani su kai harin bama-bamai. Daraktan Amnesty a Najeriya, Isa Sanusi, ya bayyana cewa bayanan da s**a tattara sun nuna yawancin waɗanda s**a mutu fararen hula ne.
Ya kuma ce an samu irin waɗannan hare-hare a baya a jihohin Borno, Yobe da Niger, inda mutane da dama s**a rasa rayukansu ciki har da yara.

A cewarsa, dole ne gwamnati ta tabbatar da cewa ayyukan yaƙi da ta’addanci ba su jawo mutuwar mutanen da ba su ji ba su gani ba, domin dokokin ƙasa da ƙasa sun hana kai hari ga fararen hula.

Ghaliya Sadiq maisikeli.
Radio Kano

Fifita Adalci Akan Matsin Lamba - Salon Jagorancin Alhaji Murtala Sule GaroAn bayyana Mataimakin Gwamnan Jihar Kano, Alh...
12/05/2026

Fifita Adalci Akan Matsin Lamba - Salon Jagorancin Alhaji Murtala Sule Garo

An bayyana Mataimakin Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Murtala Sule Garo, a matsayin shugaba mai gudanar da mulki bisa adalci da hakuri da kuma gaskiya wajen tafiyar da al’amuran jama’a.

Bayanin hakan na kunshe ne a cikin wani rubutu da Jami'ar Hulda da Juma'a ta Ofishin Mataimakin Gwamnan, Na'ima Musa Umar ta wallafa kan salon jagoranci da sabon Mataimakin Gwamnan ya zo da shi.

Rubutun ya yi nuni da cewa a yayin da wasu shugabanni matsin lamba da tasirin ra’ayoyin jama’a ke sauya musu akalar jagoranci, Mataimakin Gwamnan na ci gaba da nuna natsuwa da hukunci cikin daidaito, tare da kokarin sauke nauyin da ke wuyansa, musamman ga waɗanda yake aiki tare da su.

Rubutun, wanda Wakilinmu na Ofishin Mataimakin Gwamna, Idris Muhammad Dawakin Kudu ya fassara, ya fito da wata gaskiya cewa, jagoranci bai tsaya ga iya jawabai ko nuna iko kawai ba, amma yana nuna iya binciko gaskiya kafin yanke hukunci da kare martabar jama’a da kuma gudanar da al’amura bisa adalci maimakon zato ko son rai.

Rahoton ya kara jaddada cewa halayen jagoranci irin na Alhaji Murtala Sule Garo na nuna tawali’u da kamun kai, wadanda su ne siffofi masu wuyar samu a harkokin mulkin jama’a a wannan zamani.

Rubutun ya karkare da cewa ko da yake muk**ai da shugabanci na iya gushewa bayan lokaci, ana ci gaba da tunawa da shugabanni ne saboda adalci da mutuntaka da kuma girmamawar da suke nunawa mutane a lokacin jagorancinsu.

Hukumar Lafiya ta Duniya  ta fitar da bayanan ƙasashen da aka tabbatar ko ake zargin mutanensu sun kamu da cutar hantavi...
12/05/2026

Hukumar Lafiya ta Duniya ta fitar da bayanan ƙasashen da aka tabbatar ko ake zargin mutanensu sun kamu da cutar hantavirus bayan ɓarkewar cutar a cikin wani jirgin yawon buɗe ido na MV Hondius.

A cewar WHO da hukumomin lafiya na wasu ƙasashe, an tabbatar da mutum shida masu rai sun kamu da cutar, yayin da ake zargin mutum guda da kamuwa da ita.

Haka kuma, mutum uku sun rasu, inda biyu daga cikinsu aka tabbatar sun mutu sak**akon cutar ta hantavirus, yayin da ɗaya ake zargi.

Babbar Kotun Tarayya da ke Maitama a Abuja ta bayar da umarnin kamo tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, bayan ...
12/05/2026

Babbar Kotun Tarayya da ke Maitama a Abuja ta bayar da umarnin kamo tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, bayan ya gaza halartar zaman shari’ar da ake yi masa kan zargin almundahana ta Naira biliyan 31.

Rashin halartar kotun da Saleh Mamman ya yi a ranar Litinin ya sa Mai Shari’a Maryanne Anenih, ta ɗage shari’ar zuwa ranar Alhamis.

Wannan ne karo na biyu cikin kwanaki kaɗan da kotu ke bayar da umarnin k**a shi, bayan wata kotu a Abuja ta same shi da laifin karkatar Naira biliyan 33.8 a wani shari’ar ta daban a ranar 7 ga watan Mayu.

Rahotanni sun bayyana cewa tsohon kocin Real Madrid, José Mourinho, ya bukaci a cika masa wasu sharudda biyu kafin ya am...
12/05/2026

Rahotanni sun bayyana cewa tsohon kocin Real Madrid, José Mourinho, ya bukaci a cika masa wasu sharudda biyu kafin ya amince da komawa kungiyar.

Mourinho na son a ba shi damar bayyana guraben da kungiyar ke bukatar ƙarfafawa wajen daukar sababbin ‘yan wasa.

Sannan kuma ya nemi a ba shi cikakken iko kan harkokin ‘yan wasa ba tare da tsoma bakin wasu jami’an kungiyar ba.

✍️ Muhammad areeze

Gwamnatin jihar Kano na shirin zamanantar da asibitoci ta hanyar fasahar zamaniTa karkashin ma’aikatar fasahar sadarwa t...
12/05/2026

Gwamnatin jihar Kano na shirin zamanantar da asibitoci ta hanyar fasahar zamani
Ta karkashin ma’aikatar fasahar sadarwa ta jihar Kano Wato kano state information and technology Agency (KASITDA)

Domin samar da tsarin fasahar zamani ga asibitoci da bayanan marasa lafiya a faɗin jihar

wajen ƙarfafa tsarin gudanar da harkokin lafiya, inganta sarrafa bayanan marasa lafiya, da ƙara inganci a cibiyoyin lafiya a faɗin jihar.

Annur Abdullahi Makula✍️
Radio Kano

12/05/2026

SAHER Boutique

The Director-General of the Kano State Information and Communication Technologies Development Agency, Dr. Bashir Abdu Mu...
12/05/2026

The Director-General of the Kano State Information and Communication Technologies Development Agency, Dr. Bashir Abdu Muzakkari, says transitioning to the use of modern digital technology is no longer optional, considering its importance in improving government operations and public service delivery in Kano State.

Dr. Abdu Muzakkari stated this during a working visit to the Kano State Ministry of Health to discuss ways of expanding the use of modern technology in healthcare and administration.

He said the visit is part of the implementation plans of the Kano State Digital Transformation Agenda for 2025 to 2030, introduced by the administration of Abba Kabir Yusuf to improve government activities through the use of modern technology.

During the meeting, the Director-General emphasized the importance of using modern technology to improve healthcare administration, data management, and support effective decision-making in the health sector.

He also explained that they would collaborate with the Ministry of Health to ensure easier and more transparent service delivery through the use of modern technology in meeting the needs of the people.

Officials of the Ministry of Health commended KASITDA for its efforts in promoting innovation and development within the public sector, while also expressing their readiness to work together toward the successful implementation of modern digital healthcare transformation in Kano State.

Gwamnatin Tarayya ta amince da maki 150 a matsayin mafi ƙarancin makin da za a karɓi ɗalibai da shi a jami’o’in gwamnati...
11/05/2026

Gwamnatin Tarayya ta amince da maki 150 a matsayin mafi ƙarancin makin da za a karɓi ɗalibai da shi a jami’o’in gwamnati da masu zaman kansu a faɗin ƙasar nan domin shekarar karatu ta 2026.

An sanar da wannan mataki ne a ranar Litinin daga bakin Ministan Ilimi, Tunji Alausa, yayin taron tsara manufofin shiga jami’o’i na shekarar 2026 wanda Joint Admissions and Matriculation Board (JAMB) ta shirya a Abuja.

Haka kuma, wannan sabon tsarin ya shafi makarantun koyon aikin jinya (Nursing Colleges), inda aka amince da maki 150 a matsayin mafi ƙarancin makin shiga.

Annur Abdullahi Makula✍️
Radio Kano

11/05/2026

Labaran AM da FM tare da Hauwa Muhd

Address

No. 1 Ibrahim Taiwo Road, Gidan Bello Dandago
Kano
700234

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Radio Kano posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Radio Kano:

Share