TPR Hausa

TPR Hausa The Pulse Report Hausa| Shafin gidan jarida da zai mayar da hankali kan kawo labarai da wayar da kan al'umma kan lamurran yau da kullum

Mun kai hari ne kan hukumar leƙen asirin sojin Isra'ila ne ba asibiti ba in ji Iran.Gwamnatin Iran ta bayyana cewa hare-...
19/06/2025

Mun kai hari ne kan hukumar leƙen asirin sojin Isra'ila ne ba asibiti ba in ji Iran.

Gwamnatin Iran ta bayyana cewa hare-haren da ta kai a safiyar Alhamis sun nufi cibiyoyin leƙen asirin soja na Isra’ila a kudancin ƙasar, ba asibiti ba kamar yadda wasu kafafen yaɗa labarai s**a bayyana.

Kamfanin dillancin labarai na IRNA ya ce an kai harin ne kan hedikwatar rundunar sadarwa da kuma wata cibiyar leƙen asiri, sai dai fashewar bam ɗin ta shafi wani asibiti a kusa da wurin.

A gefe guda kuma, Isra’ila ta kai hari kan matatar ruwa ta Arak da ke Iran, amma an kwashe ma’aikata kafin faruwar lamarin.

Jagoran Iran ya gargaɗi Amurka inda ya bayyana cewa "Kowanne hari kan Iran yana da mummunan sakamako.Jagoran juyin juya ...
19/06/2025

Jagoran Iran ya gargaɗi Amurka inda ya bayyana cewa "Kowanne hari kan Iran yana da mummunan sakamako.

Jagoran juyin juya halin kasar Iran ya bayyana cewa duk wani hari da Amurka za ta kai wa Iran mummunan martani zai biyo bayansa daga Iran.

Wannan jawabi na zuwa ne a daidai lokacin da rikici ke ƙara ƙamari tsakanin Iran da Isra’ila, tare da yiwuwar shiragr Amurka ƴakin gaba ɗaya.

Jagoran ya nanata cewa Iran ba za ta zauna tana gani ana cin zarafinta ba, kuma za ta kare kanta da ƙarfinta gaba ɗaya idan aka tsallaka layi.

Trump ya amince da shigarwa Israel yaƙin, tare da kai hari ga Iran nan ba da jimawa ba, matukar ba ta bi abinda su ke so...
19/06/2025

Trump ya amince da shigarwa Israel yaƙin, tare da kai hari ga Iran nan ba da jimawa ba, matukar ba ta bi abinda su ke so ba.
- Majiyoyin sirri.

Shugaban Amurka Donald Trump ya amince da shirye-shiryen kai hari ga Iran, domin shigarwa Israel yaƙin da ake fafatawa, biyo bayan gargaɗi da ya yi wa ƙasar ta Iran,amma ta yi kunnen uwar shegu da shi.

Amma dai har zuwa yanzu, bai yanke shawarar karshe ba kan lokacin da Amurka za ta fara kai hare-haren, kamar dai yadda wata majiyar sirri ta jaridar CBS News ta sanar.

Majiyoyin sun ce Trump ya ɗan dakata da shawarar kai harin ne domin ba wa Iran damar janyewa daga yaƙin, da kuma dakatar da shirin nukiliyarta.

“Ni na fi son yanke shawara kwatsam, minti ɗaya kafin lokacin kai hari ya yi, saboda abubuwa na iya canzawa, musamman idan ya shafi yaƙi,” in ji Trump a wata tattaunawa da yayi manema labarai, ya kuma ƙara da cewa “Zan iya fara shiga yaƙin, ko kuma in ƙi. Babu wanda ya san me zan yi.”

Duk da mutane da yawa sun tsaneni kamar yadda su ka tsani shiga wuta, amma dai duk da haka, ni ne dai shugaban Nijeriya ...
18/06/2025

Duk da mutane da yawa sun tsaneni kamar yadda su ka tsani shiga wuta, amma dai duk da haka, ni ne dai shugaban Nijeriya in ji Tinubu.

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa koda yake mutane da dama sun tsane shi kamar mutuwarsu, hakan bai hana shi kasancewa zababben shugaban kasar Najeriya ba.

A Yayin ziyararsa a Jihar Benue don jaje da kuma duba yanayin tsaron jihar ta Benue, biyo bayan harin ta'addanci a jihar, shugaba Tinubu ya jaddada cewa kalubalen da ya ke fuskanta na kiyayya da kuma s**ar ƴan Adawa abu ne da ya zama dole ga duk wanda ya riƙe wani shugabanci na siyasa.

Ya ce “Ba lallai sai kowa ya so ka a siyasa ba, mutane sun tsane ni kamar yadda su ka tsani mutuwar su, amma dai har yanzu ni ne shugaban kasa, na kuma sha alwashin kare rayukan kowanne ɗan ƙasa, bisa ga tsarin dimokuradiyya, kuma ko da masu zagi na ne.”

Shin kai a wannan ɓangaren ka ke?

PUTIN: Hare-haren Isra’ila sun ƙarfafa haɗin kai ga al'ummar Iran wajen goyon bayan shugabanninsu.Shugaban Rasha, Vladim...
18/06/2025

PUTIN: Hare-haren Isra’ila sun ƙarfafa haɗin kai ga al'ummar Iran wajen goyon bayan shugabanninsu.

Shugaban Rasha, Vladimir Putin, ya bayyana cewa hare-haren Isra’ila a kan Iran sun sa al’ummar Iran sun haɗa kai wajen goyon bayan shugabanninsu.

A cewarsa, yana da yiwuwar a sulhunta a tsakanin ɓangarorin biyu, wacce za ta tabbatar da tsaron Isra’ila daga muradun mallakar nukiliyar Iran.

Putin ya ce Rasha na da ma’aikata fiye da 200 a tashar nukiliya ta Bushehr da Rasha ta gina, sai dai shugaban Amurka Donald Trump ya ƙi amincewa tayin Putin na shiga tsakani, yana mai cewa ya fi dacewa Putin ya magance rikicinsa da Ukraine kafin ya shiga na wasu.

An gano hujjoji masu ƙarfi da ke nuna cewa da akwai mutane a Nahiyar Amurka tun kusan shekaru 23,000 da s**a gabata. A w...
18/06/2025

An gano hujjoji masu ƙarfi da ke nuna cewa da akwai mutane a Nahiyar Amurka tun kusan shekaru 23,000 da s**a gabata.

A wani binciken da aka gabatar a tsaunukan white Sands, da ke New Mexico, a gano sawun kafar ɗan adam da ke nuna hujjojin kasancewar ɗan adam a wannan wuri tun shekaru 23000 da s**a gabata.

Wannan ya ƙalubalanci tsohon ra'ayin masanin tarihi Clovis wanda ya ce mutane sun fara zuwa Amurka ne kimanin shekaru 13,000 da s**a gabata.

Hujjojin sun haɗar da gwaje-gwajen ƙasa da kwayoyin halitta waɗanda s**a nuna cewa lallai an fara zama a Amurka tun shekaru 23000 da su ka gabata.

Shin ko ka san bincike ya tabbatar da cewa ɗan Adam ya fara zama ne a Nahiyar Afirka?

Gwamnatin Sokoto ta shirya tsaf don zama da ‘Yan Bindiga domin neman sulhuGwamnatin Jihar Sokoto ta bayyana shirinta na ...
18/06/2025

Gwamnatin Sokoto ta shirya tsaf don zama da ‘Yan Bindiga domin neman sulhu

Gwamnatin Jihar Sokoto ta bayyana shirinta na sasantawa da ‘yan bindiga masu niyyar ajiye makamansu da komawa kyakkyawar rayuwa kamar sauran al'umma.

A cikin wata sanarwa da mai ba gwamna shawara kan tsaro, Col. Ahmed Usman (rtd), ya fitar, gwamnatin ta ce tarihi ya nuna cewa ba iya ta hanyar amfani da ƙarfin gwamnati ake samar da zaman lafiya ba, har ma ta hanyar tattaunawa da kuma fahimtar juna.

Gwamnatin ta godewa shugaba Tinubu da kuma ɗaukacin hafsoshin tsaron Najeriya bisa sadaukarwar su wajen kare yankin, har ila yau, ta goyi bayan shirin kafa ma'aikatan gandun daji a fadin yankin da gwamnatin Tinubu ta ke yi, domin dakile ayyukan ta’addanci.

An yi watsi da ƙarar da aka shigar tsohon Tsohon Shugaba ƙasa, Buhari da Emefiele dangane da canza fasalin kuɗin Naira a...
29/04/2025

An yi watsi da ƙarar da aka shigar tsohon Tsohon Shugaba ƙasa, Buhari da Emefiele dangane da canza fasalin kuɗin Naira a 2023

A ranar Litinin, 28 ga Afrilu, 2025, wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ƙarƙashin jagorancin mai shari’a Inyang Ekwo, ta yi watsi da wata kara da wani lauya mai suna Uthman Isa Tochukwu ya shigar a shekarar 2023, ƙarar ta shafi tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari da tsohon gwamnan CBN, Godwin Emefiele, saboda sabon tsarin canza Naira da s**a aiwatar.

Tochukwu ya bayyana cewa canza fasalin Naira ta sa ya fuskanci matsi, inda ya kasa samun kudinsa daga bankuna guda biyu tsawon watanni uku, sannan ya ce an tauye masa ‘yancinsa da dama, saboda haka, ya nemi kotu ta tilasta gwamnati ta biya shi diyya har Naira biliyan daya (₦1bn), ta kuma hana ci gaba da hana amfani da tsoffin takardun N200, N500, da N1000. Haka kuma, ya bukaci a buga masa hakuri a jaridu biyu manya a kasar.

Sai dai kotun ta kori karar saboda wanda ya shigar da karar da lauyansa sun gaza zuwa kotu tun shekara ta 2023.

Rasha za ta taimaka wa Najeriya wajen yaƙi da Ta’addanciGwamnatin Rasha ta bayyana cewa tana da niyyar tallafa wa Najeri...
29/04/2025

Rasha za ta taimaka wa Najeriya wajen yaƙi da Ta’addanci

Gwamnatin Rasha ta bayyana cewa tana da niyyar tallafa wa Najeriya da sababbin dabarun da ta kirkira wajen yaki da ta’addanci.

Wannan bayani ya fito ne daga bakin jakadan Rasha, Laftanar Janar Andrei Averianov, lokacin da ya kai ziyarar ban girma ga Babban Hafsan Tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, a Abuja.

Averianov ya bayyana cewa Rasha ta samu ƙwarewa ta musamman yayin da take gudanar da ayyukan tsaro a ƙasashe 39, kuma tana da niyyar yin amfani wannan gogewa waje. Taimakawa Najeriya wajen magance matsalolin Boko Haram da sauran ƙungiyoyin ta’addanci.

Janar Musa ya gode wa Rashar bisa wannan haɗin gwiwa, inda ya jaddada buƙatar kayan aikin zamani, horar da sojoji, da kuma gyaran na’urorin yaki na Rasha da ke Najeriya. Ya roki a samu ƙarin haɗin gwiwa a fannin leƙen asiri da musayar ƙwararru tsakanin ƙasashen biyu.

Wannan mataki zai ƙara ƙarfafa dangantaka tsakanin Najeriya da Rasha, tare da taimakawa Najeriya wajen cimma nasara a yaki da ta’addanci da rashin tsaro.

Shin ko ya ka ke ganin hakan?

Mai Gudanar da EPA na Shugaba Trump, Lee Zeldin, na Mayar da Hankali Kan Farashin Masana’antu don Rusa Hujjojin Kimiyya ...
29/04/2025

Mai Gudanar da EPA na Shugaba Trump, Lee Zeldin, na Mayar da Hankali Kan Farashin Masana’antu don Rusa Hujjojin Kimiyya na Dokokin Sauyin Yanayi

A cikin wata sabuwar dabara da ta janyo ce-ce-ku-ce, Lee Zeldin, wanda ke matsayin shugaban Hukumar Kare Muhalli ta Amurka (EPA) a karkashin Shugaba Donald Trump, ya mayar da hankali wajen duba tasirin farashin da dokokin sauyin yanayi ke yi wa masana’antu. Wannan mataki ya haifar da fargaba daga masana da masu fafutukar kare muhalli, wadanda ke ganin hakan a matsayin yunkurin rushe muhimman hujjojin kimiyya da ke bayan dokokin kariyar muhalli da sauyin yanayi.

Zeldin, wanda ke wakiltar ra'ayin gwamnati mai fifita ci gaban tattalin arziki fiye da tsauraran dokokin muhalli, ya bayyana cewa wajibi ne a tantance dokokin da ke haifar da nauyi ga masana’antu ba tare da cikakken amfani da ke nuna amfanin dokokin ba. Masu s**a sun bayyana cewa wannan salon na iya raunana matakan kariyar muhalli da kuma dagula kokarin duniya na dakile sauyin yanayi.

Gwamnatin Shugaba Donald Trump Ta Yi Barazanar Takaita Shigo da Dabbobi Daga Mexico Saboda Cutar New World ScrewwormA ra...
27/04/2025

Gwamnatin Shugaba Donald Trump Ta Yi Barazanar Takaita Shigo da Dabbobi Daga Mexico Saboda Cutar New World Screwworm

A ranar Asabar, gwamnatin Shugaba Donald Trump ta bayyana cewa za ta sanya takunkumi kan shigo da dabbobi daga kasar Mexico, matuƙar gwamnatin ƙasar ta gaza ƙara ƙaimi wajen yaki da wata mummunar cuta mai suna New World Screwworm. Wannan gargadi na zuwa ne sakamakon fargabar da gwamnatin Amurka ke nunawa dangane da yadda cutar ke iya barazana ga lafiyar dabbobi da tattalin arzikin kiwo a ƙasa

Address

4 Jos Road, Falgore, Doguwa Local Government
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when TPR Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share