TPR Hausa

TPR Hausa The Pulse Report Hausa| Shafin gidan jarida da zai mayar da hankali kan kawo labarai da wayar da kan al'umma kan lamurran yau da kullum

I've just reached 5K followers! Thank you for continuing support. I could never have made it without each one of you. 🙏🤗...
08/01/2026

I've just reached 5K followers! Thank you for continuing support. I could never have made it without each one of you. 🙏🤗🎉

KWANKWASO: Babu jam'iyyar da ta kai NNPP tsari a Najeriya.Tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma jagoran jam'iyyar NNPP, Sanata ...
21/12/2025

KWANKWASO: Babu jam'iyyar da ta kai NNPP tsari a Najeriya.

Tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma jagoran jam'iyyar NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya bugi ƙirji cewa jam'iyyarsu ta NNPP ita ce jam'iyyar siyasa mafi tsari da natsuwa a faɗin Najeriya a halin yanzu.

Kwankwaso ya yi wannan furucin ne a ranar Juma'a a Abuja, yayin taron kwamitin zartarwa na ƙasa (NEC) na jam'iyyar, gabanin babban taron gangamin da za su yi a jiya Asabar.

Ya yi kira ga 'ya'yan jam'iyyar da su cigaba da nuna haɗin kai da ladabi, yana mai jaddada cewa zaman lafiyar NNPP shi ne mabuɗin nasararsu a zaɓen 2027 mai zuwa.

Shin dan aka yi la'akari da rigingimun da ke cikin manyan jam'iyyun Najeriya (APC da PDP) a yanzu, shin kuna ganin Kwankwaso ya faɗi gaskiya cewa NNPP ce jam'iyya mafi tsari ko kuwa?

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar kimiyyar lafiya ta Azare zuwa sunan Sheikh Dahiru Bauchi.A wani mataki na karrama gagaruma...
21/12/2025

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar kimiyyar lafiya ta Azare zuwa sunan Sheikh Dahiru Bauchi.

A wani mataki na karrama gagarumar gudunmawar da ya bayar ga addini da zaman lafiya, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince da sauya sunan Jami’ar Kimiyyar Lafiya ta Tarayya da ke Azare (FUHSA) a Jihar Bauchi.

To amma shin ko me za ka ce kan wannan mataki?

Anthony Joshua ya lallasa Jake Paul a ranar Juma'a, lamarin da ya girgiza duniya.A daren ranar Asabar, 20 ga watan Disam...
21/12/2025

Anthony Joshua ya lallasa Jake Paul a ranar Juma'a, lamarin da ya girgiza duniya.

A daren ranar Asabar, 20 ga watan Disamba, duniyar wasanni da shafukan sada zumunta sun ɗauki zafi bayan ɗan damben asalin Najeriya, Anthony Joshua (AJ), ya lallasa fitaccen ɗan YouTube, Jake Paul a ranar juma'a.

Wasan, wanda aka dade ana cece-kuce a kansa, ya zo ƙarshe ne a zagaye na shida (Round 6) yayinda Anthony Joshua ya yi laga-laga da tamaula da Jake Paul, inda ya bar shi kwance magashiyan batare da sanin inda yake ba.
Wannan nasara ta kasance babban abin farin ciki ga 'yan Najeriya da masoya dambe a faɗin duniya, waɗanda ke ganin AJ ya kare martabar damben ƙwararru daga rainin wayon chalin-chalin kafafen sada zumunta.

Tuni shafukan Twitter da TikTok s**a cika da bidiyon nasarar, inda ake yaba wa AJ kan nuna gogewa da kuma "ba da darasi" ga ɗan YouTube ɗin.

To amma shin ko kai me za ka ce a kai?

Shin wai a ina aka tsaya ne kan Rikicin Masarautar Kano?Al'ummar jihar Kano sun ƙosa su san wannan muhimmiyar amsar, wai...
20/12/2025

Shin wai a ina aka tsaya ne kan Rikicin Masarautar Kano?

Al'ummar jihar Kano sun ƙosa su san wannan muhimmiyar amsar, wai shin wanene sarkin Kano?.

amsar da kowa ya ke da ta sa ta daban, wasu su ce Sarki Aminu Ado shine sarkin Kano, wasu kam su kan ce Sarki Muhammad Sunusi II shine sarkin Kano, kuma dai ba bu wanda za ka ce amsarsa ba haka ta ke ba.

To amma shin kai mecece amsarka? Sannan a ganinka wanne kalar tasiri wannan rikici na Masarautar Kano ke haifarwa a jihar, ta fannin tattalin arziki, tsaro da kuma raya al'adu?

A ranar Juma'a, Shugaba Bola Tinubu ya gabatar da kasafin kuɗin shekarar 2026 mai jimillar Naira Tiriliyan 58.18 a  gaba...
20/12/2025

A ranar Juma'a, Shugaba Bola Tinubu ya gabatar da kasafin kuɗin shekarar 2026 mai jimillar Naira Tiriliyan 58.18 a gaban Majalisar Dokoki ta Ƙasa.

Sai dai, jam'iyyar adawa ta PDP ta yi watsi da kasafin nan take. A martaninta, ta yi wa kasafin kirari da kasafin cigaba da "Ɗanɗanawa al'ummar Najeriya kuɗa"

Jam'iyyar ta PDP ta bayyana cewa, maimakon sauƙi, wannan kasafin zai ƙara wa talakawa wahalar rayuwa ne kawai.

Wannan kasafin kuɗi dai shi ne mafi girma a tarihin Najeriya, kuma ya janyo zazzafar muhawara kan makomar tattalin arzikin ƙasar.

To amma shin kai me za ka ce kan wannan lamari?

Ana ta magana kan naɗa Rarara a matsayin "Sarkin Waƙar Ƙasar Hausa" a Daura. Wanda wannan lamari ya janyo muhawara da ce...
20/12/2025

Ana ta magana kan naɗa Rarara a matsayin "Sarkin Waƙar Ƙasar Hausa" a Daura.

Wanda wannan lamari ya janyo muhawara da cece-kuce a kafafen sada zumunta tsakanin magoya baya da masu s**a kan ko ya cancanci wannan babban matsayi fiye da sauran mawaka.

To amma shin kai a na ka ɓangaren menene ra'ayinka? Ko rarara ya cancanci wannan matsayi?

Shugaban hukumar kula da harkokin man fetur ta NMDPRA a Najeriya Farouk Ahmed ya yi murabus.Biyo bayan rikita-rikitar da...
17/12/2025

Shugaban hukumar kula da harkokin man fetur ta NMDPRA a Najeriya Farouk Ahmed ya yi murabus.

Biyo bayan rikita-rikitar da ke tsaka da gudana da Farouq Ahmad, tsakanin sa da mai kuɗin Afrika, Aliko Dangote yau ya yi ritaya.

Shin ko me za ka ce a kai?

14/12/2025

Sponsored:

Kai har yanzu kana shiga mota ƙafa da ƙafa har zuwa Kano kawai don ka yi siyayya? 😅

⏩Ga asarar kuɗin mota da abinci
⏩Ga gajiyar hanya
⏩ Idan shago ne da kai sau da yawa sai ka rufe shagon nan kawai don ka zo Kano yin siyayya.

Zamanin nan ya wuce fa!

Yanzu Kano Direct Market ta kawo kasuwar Kano har kofar gidanka.
Ka siya komai cikin sauƙi tamkar kaine a kasuwa
Ba ƙurar hanya
Ba Turereniya.
Ba Asarar Kudin Mota.
Ka yi kasuwancinka kaitsaye daga Kano. 🚛
Yi mana magana yanzu

domin magana ta whatsApp [08140037061],
Domin kiran waya [07075969383]

Kirkirar bidiyo: Ibrahim Aliyu
Domin bidiyon tallace-tallacen kamfani ko sana'a irin wannan, za ka iya yi masa magana.
Kira ko Whatsapp [09129387379]

🚨 SCHOLARSHIP: KOYI CONTENT CREATION TA HANYAR AMFANI DA AI KYAUTA! 🚨Wata kila ka na yawan gani bidiyoyi da aka kirkira ...
05/12/2025

🚨 SCHOLARSHIP: KOYI CONTENT CREATION TA HANYAR AMFANI DA AI KYAUTA! 🚨

Wata kila ka na yawan gani bidiyoyi da aka kirkira da AI kuma hakan ya na burge ka, to ga dama ta samu, kai ma ka na da damar farawa daga yanzu, har ma ka yi amfani da shi don gina rayuwar ka da yin abubuwa masu amfani.

Me ka ke buƙata? Kwazo da dagewa kawai.

Ina neman mutane 100 masu kwazo da mayar da hankali, wadanda suke son koyon yadda ake hada Videos, Hotuna, sauti, waƙoki da kuma rubuce-rubuce masu inganci ta hanyar amfani da fasahar AI.
Wannan dama ce ta musamman don koyawa mutane sana'a kyauta don fara dogara da kan su.
🔥 Abinda za ku koya a wannan ajin ya haɗar da:

✅ Yadda ake hada Bidiyo domin content Creation da tallace-tallace cikin sauki kuma cikin kankanin lokaci.
✅ Yadda ake kirkirar Hotuna masu inganci da AI.
✅ Yadda ake ƙirƙirar waƙoki da AI.
✅ Da kuma mafi muhimmanci shine sirrin Content Creation ta hanyar amfani da AI, da kuma damarmakin da za ka iya samu a Content Creation.

Domin kasancewa cikin waɗanda za su amfana da wannan garaɓasar, ka yi maza ka yi joining.

📅 Ranar farawa: Gobe (Asabar) (6/11/2026)
📍 Wuri: WhatsApp Group

https://chat.whatsapp.com/I9rPJT71bOcFs0EX5gOgZ7?mode=wwt

💰 Kudin Shiga: KYAUTA (Free)

GARGADI: Ka tabbatar da cewa za ka iya halartar ajin, kuma za ka mayar da hankali don koyon abinda zai canza rayuwar ka.

KA YI SHARING WANNAN RUBUTU DON YA ISA WURIN MUTANE DA YAWA.

Hukumar ƴansanda ta Kano ta ayyana haramcin sana'ar acaɓa a Kano.Hukumar Yan sanda ta jihar Kano ta bayyana haramcin Aca...
01/12/2025

Hukumar ƴansanda ta Kano ta ayyana haramcin sana'ar acaɓa a Kano.

Hukumar Yan sanda ta jihar Kano ta bayyana haramcin Acaɓa a Kano, tare da ƙara tsaurara takunkumi kan aiki da keke-napep daga ƙarfe 10 na dare zuwa 6 na safe.

Wannan mataki ya biyo bayan ƙarin barazanar tsaro a jihar ta kano, da kuma kiraye-kirayen al'umma kan dakatar da hakan k**af yadda aka yi tun a shekarun baya, sak**akon hare-haren da ke faruwa a kan iyakar Kano da Katsina.

Hukumar ta ce za a aiwatar da dokar a kananan hukumomi tara da s**a hada da Kano Municipal, Gwale, Dala, Fagge, Nassarawa, Tarauni, Kumbotso, Ungogo da Dawakin Kudu. Masu karya doka za a k**a su.

01/12/2025

Kira ga Shugaba Bola Ahmad Tinubu da ya ayyana dokar ta ɓaci a jihar Kano a matsayin jihar da ke fama da matsalar tsaro a wasu kananan hukumomi da s**a hadar da Bagwai, Gezawa.

Shin ko me za ka ce kan wannan kira?

Address

4 Jos Road, Falgore, Doguwa Local Government
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when TPR Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share