Manu Fagge

Manu Fagge Writer
Content Creator
Blogger
Graphic Designer
(2)

Cikin wannan dare Minista Hon Yusuf Abdullahi Ata ya ziyarci gidan Hon Sageer Abba Fagge domin tausasa shi da kara kwant...
16/05/2026

Cikin wannan dare Minista Hon Yusuf Abdullahi Ata ya ziyarci gidan Hon Sageer Abba Fagge domin tausasa shi da kara kwantar masa da hankali bisa rashin nasara da yayi akan MB Shehu Fagge dan majalisar tarayya mai wakiltar karamar hukumar Fagge.

16/05/2026
16/05/2026

Innalillahi'Wainnailairrajiun.

Wallahi na tausayawa bawan Allah nan, sabida kwarfiyar da aka masa a karamar hukumar Fagge.yayi mugun kashe kudi a sabgar nan, wallahi ko yau sai da na amfana da aikin sa.

Kwarfiya kwarfiya kwarfiya, Allah ya mana tsari dake.

Amma bawan Allah nan aikin da yayi a Fagge wallahi ko Tukur bai ba.

Sagir Abba Allah ya hakurkuntar da kai.
MB Shehu Allah ya ida nufi.

Zan iya haɗa mata hudu na aure ba tare da damuwa ba, tun daga kan Izala, Shi'a Dariƙa har dama Kirista.  Sai dai banda b...
16/05/2026

Zan iya haɗa mata hudu na aure ba tare da damuwa ba, tun daga kan Izala, Shi'a Dariƙa har dama Kirista.

Sai dai banda burin auren mace sama da ɗaya.

Dawanne dan Dambe Kuke Ganin yakamata a Hadashi ?
16/05/2026

Dawanne dan Dambe Kuke Ganin yakamata a Hadashi ?

Dandazon Jama'a A Garin Nguru Sun Yi Wa Engr. Mustapha Maihaja Kyakkyawar Tarba
16/05/2026

Dandazon Jama'a A Garin Nguru Sun Yi Wa Engr. Mustapha Maihaja Kyakkyawar Tarba

Kana kabilanci dan kare kabilanka, kuma daga gefe kana s**ar masu Kabilanci irinka dan bawa tasu kabilar kariya.Shin mah...
16/05/2026

Kana kabilanci dan kare kabilanka, kuma daga gefe kana s**ar masu Kabilanci irinka dan bawa tasu kabilar kariya.

Shin mahaukacin ina kai?

WANE ABU BILAL AL-MAINUKI?Abu Bilal al-Mainuki, wanda ake kuma kira Abubakar Mainok ko Abu Mainok, wanda ya fito daga ji...
16/05/2026

WANE ABU BILAL AL-MAINUKI?

Abu Bilal al-Mainuki, wanda ake kuma kira Abubakar Mainok ko Abu Mainok, wanda ya fito daga jihar Borno Nigeria. Lakabin “al-Mainuki” yana nuna cewa asalinsa daga garin Mainok ne da ke ƙaramar hukumar Kaga a jihar Borno. Ya kasance ɗaya daga cikin manyan shugabannin ƙungiyar ta’addanci ta ISWAP (Islamic State West Africa Province), wacce ta samo asali daga Boko Haram.

Kafin ya shiga cikin manyan shugabannin ISWAP, an yi imanin cewa ya kasance cikin tsoffin mayaƙan Boko Haram a zamanin Abubakar Shekau. Bayan rarrabuwar kai tsakanin Shekau da reshen ISIS a Afirka ta Yamma, Abu Bilal ya koma bangaren ISWAP, inda ya samu ƙarin matsayi saboda gogewarsa, dabarunsa, da alaƙarsa da manyan shugabannin ƙungiyar.

A cikin shekarun baya, ya zama jagora mai muhimmanci a sashen da ake kira al-Furqan, wani sashe da ke kula da hulɗa da hedikwatar ISIS da ke wajen Afirka. A shekarar 2023, gwamnatin Amurka ta sanya shi cikin jerin “Specially Designated Global Terrorists,” wato manyan ‘yan ta’adda da ake nema a duniya saboda rawar da yake takawa wajen shirya hare-hare da jagorantar mayaƙa.

An danganta shi da ayyukan ta’addanci a yankin Tafkin Chadi, wanda ya haɗa da arewacin Najeriya, Nijar, Chadi, da Kamaru. Ana zargin ya taka muhimmiyar rawa wajen kai hare-hare kan jami’an tsaro da fararen hula, da kuma haɗa kai tsakanin ISWAP da sauran rassan ISIS a yankin Sahel.

A watan Afrilu 2024, Hedikwatar Tsaro ta Najeriya ta sanar da cewa an kashe shi a wani farmaki. Sai dai daga baya rahotanni s**a nuna cewa ko dai bayanin bai tabbata ba ko kuma ya tsira daga harin.

A ranar 16 ga Mayu 2026, kawai sai akaji gwamnatocin Najeriya da Amurka sun sanar da cewa an kashe Abu Bilal al-Mainuki a wani farmaki na haɗin gwiwa da aka kai a Metele, jihar Borno. Rahotanni sun bayyana cewa an kashe shi tare da wasu manyan mataimakansa, kuma an bayyana hakan a matsayin babbar nasara a yaƙin da ake yi da ta’addanci a Afirka ta Yamma.

Abu Bilal al-Mainuki ya kasance ɗaya daga cikin fitattun shugabannin ta’addanci da s**a fito daga Najeriya, kuma ya kai matsayi mai girma sosai a tsarin ISIS na duniya. Tarihinsa ya nuna yadda rikicin Boko Haram da ISWAP ya haifar da shugabanni masu haɗari da s**a jawo asarar rayuka da dukiyoyi a yankin arewa maso gabashin Najeriya da maƙwabtanta.

Fatan nasara Gina Carano
15/05/2026

Fatan nasara Gina Carano

A samomin fiya wata a jikamin bayana, zan rufe bakins kamar ina kuka, mai kyamara dawo daga gefe. Akshin, Ƙyarass.
15/05/2026

A samomin fiya wata a jikamin bayana, zan rufe bakins kamar ina kuka, mai kyamara dawo daga gefe. Akshin, Ƙyarass.

NAMAN SALLAH Naman Sallah layya shi ne naman dabbar da alummar Musulmai ke yankawa domin ibadar Babbar Sallah (Eid al-Ad...
15/05/2026

NAMAN SALLAH

Naman Sallah layya shi ne naman dabbar da alummar Musulmai ke yankawa domin ibadar Babbar Sallah (Eid al-Adha). Wannan ibada tana tuna wa da biyayyar Annabi Ibrahim (Alaihis Salam) lokacin da Allah Ya umarce shi da ya yi hadaya, sannan Allah Ya fanshe Annabi Isma'il da rago. Saboda haka, Musulmi masu hali suna yanka dabba kamar rago, akuya, saniya ko raƙumi domin neman kusanci ga Allah.

Ana son a ci daga cikin naman layyar, a ba dangi da maƙwabta, sannan a sadaka ga talakawa da masu buƙata. Malamai sun fi so a raba shi gida uku: kashi ɗaya iyali su ci, kashi ɗaya a kyautata wa dangi da abokai, kashi ɗaya kuma a bai wa mabukata. Duk da haka, idan mutum ya ci mafi yawansa ko ya ba da mafi yawansa, ya halatta.

Naman layya yana da matuƙar muhimmanci a rayuwar al’umma, domin yana haɗa zumunci, yana faranta ran iyali, kuma yana sa talakawa su samu abin ci a lokacin Sallah. A ƙasashen Hausa, ana amfani da naman layya wajen yin miya, tuwo, gashashshe, soyayye da kuma busasshen nama har ma dana sawa a kakile domin a adana shi na tsawon lokaci.

Layya ibada ce mai girma, kuma naman da ake samu daga gare ta alama ce ta godiya ga Allah, taimakon mabukata, da kuma ƙarfafa soyayya da haɗin kai tsakanin al’umma. Allah Ya karɓi layyarmu da sauran ibadunmu baki ɗaya, nima da ban taɓa yi ba Allah ya bani ikon yi, tare da sauran Al'umma Ameen.

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Manu Fagge posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share