16/05/2026
WANE ABU BILAL AL-MAINUKI?
Abu Bilal al-Mainuki, wanda ake kuma kira Abubakar Mainok ko Abu Mainok, wanda ya fito daga jihar Borno Nigeria. Lakabin “al-Mainuki” yana nuna cewa asalinsa daga garin Mainok ne da ke ƙaramar hukumar Kaga a jihar Borno. Ya kasance ɗaya daga cikin manyan shugabannin ƙungiyar ta’addanci ta ISWAP (Islamic State West Africa Province), wacce ta samo asali daga Boko Haram.
Kafin ya shiga cikin manyan shugabannin ISWAP, an yi imanin cewa ya kasance cikin tsoffin mayaƙan Boko Haram a zamanin Abubakar Shekau. Bayan rarrabuwar kai tsakanin Shekau da reshen ISIS a Afirka ta Yamma, Abu Bilal ya koma bangaren ISWAP, inda ya samu ƙarin matsayi saboda gogewarsa, dabarunsa, da alaƙarsa da manyan shugabannin ƙungiyar.
A cikin shekarun baya, ya zama jagora mai muhimmanci a sashen da ake kira al-Furqan, wani sashe da ke kula da hulɗa da hedikwatar ISIS da ke wajen Afirka. A shekarar 2023, gwamnatin Amurka ta sanya shi cikin jerin “Specially Designated Global Terrorists,” wato manyan ‘yan ta’adda da ake nema a duniya saboda rawar da yake takawa wajen shirya hare-hare da jagorantar mayaƙa.
An danganta shi da ayyukan ta’addanci a yankin Tafkin Chadi, wanda ya haɗa da arewacin Najeriya, Nijar, Chadi, da Kamaru. Ana zargin ya taka muhimmiyar rawa wajen kai hare-hare kan jami’an tsaro da fararen hula, da kuma haɗa kai tsakanin ISWAP da sauran rassan ISIS a yankin Sahel.
A watan Afrilu 2024, Hedikwatar Tsaro ta Najeriya ta sanar da cewa an kashe shi a wani farmaki. Sai dai daga baya rahotanni s**a nuna cewa ko dai bayanin bai tabbata ba ko kuma ya tsira daga harin.
A ranar 16 ga Mayu 2026, kawai sai akaji gwamnatocin Najeriya da Amurka sun sanar da cewa an kashe Abu Bilal al-Mainuki a wani farmaki na haɗin gwiwa da aka kai a Metele, jihar Borno. Rahotanni sun bayyana cewa an kashe shi tare da wasu manyan mataimakansa, kuma an bayyana hakan a matsayin babbar nasara a yaƙin da ake yi da ta’addanci a Afirka ta Yamma.
Abu Bilal al-Mainuki ya kasance ɗaya daga cikin fitattun shugabannin ta’addanci da s**a fito daga Najeriya, kuma ya kai matsayi mai girma sosai a tsarin ISIS na duniya. Tarihinsa ya nuna yadda rikicin Boko Haram da ISWAP ya haifar da shugabanni masu haɗari da s**a jawo asarar rayuka da dukiyoyi a yankin arewa maso gabashin Najeriya da maƙwabtanta.