Hausa Novels Cinema

  • Home
  • Hausa Novels Cinema

Hausa Novels Cinema Welcome To Hausa Novels Fans Page Of Hausa Cinema.

Hausa Novels Cinema - Fauziya D Sulaiman Novels, Hausa Novels Complete Documents, Gidan Uncle Hausa Novels, Free Hausa Novels Groups And Audio Hausa Novels.

Na Taso Cikin Rayuwar Ƙunci Da Ba Kowacce Yarinya Ke Fuskanta Ba. Mahaifina Ya Rasu Tun Ina Shekara Goma Sha Ɗaya, Mahai...
28/07/2025

Na Taso Cikin Rayuwar Ƙunci Da Ba Kowacce Yarinya Ke Fuskanta Ba. Mahaifina Ya Rasu Tun Ina Shekara Goma Sha Ɗaya, Mahaifiyata Ta Biyo Bayansa Shekara Biyu Bayan Rasuwar Sa. Daga Wannnan Lokaci Rayuwata Ta Canza Gabadaya. Ba Domin Rashin Iyaye Kadai Ba, Har Ma Da Yadda Duniya Ta Fara Juya Min.

Ina Zaune A Gidan Kawuna Allah Bai Bashi Haihuwa Ba, Tare Da Wata Yar Yafendona Maimuna A Unguwar Da Gabadaya Marasa Karfi Ne A Wajen. Akwai Wani Matashi A Unguwar, Sunansa Sameer, Farin Mutum Tsiriri, Da Idanu K**ar Na Zaki. Ko Wace Yarinya A Unguwar Tana Masa Kallon Zinari, Kowa Sha'awarsa Take Saboda Kyawu Da Kwarjininsa. Amma Ni Ban Taɓa Zaton Zan Iya Faɗawa Tarkonsa Ba… Har Sai Da Hakan Ta Faru.

Na Fara Lura Da Shi Ne A Lokacin Da Yake Wucewa Kofar Gidanmu Kullum Yakan Yi Min Murmushi. Daga Baya Ya Fara Tsayawa Yana Tambayata, Ko Kuma Yace Na Kawo Masa Ruwa, Daga Baya Ya Nemi Lambar Waya Na Domin Yana So Mu Ringa Gaisawa Idan Ya Tafi Kasuwa. Na Fara Jin Wani Abu Daban A Zuciyata, Wani Yanayi Da Ban Taɓa Fahimta Ba. Maimuna Ta Sha Fadamin Na Lura Da Irin Wadannan Mazajen, Amma Nace Mata “Wanda Bai Da Wata Manufa A Kanmu Tayaya Zai Cutar Damu?”

A Hankali Na Fara Mantawa Da Gargaɗinta, Ina Faɗawa Cikin Duniyar Da Ban Sani Ba. Na Fara Tsayawa Ina Bata Lokaci Mai Tsayi Tare Dashi Muna Hira, Yana Jefo Min Kalaman Kwantar Da Hankali Da Zance Irinsu "Kin Fi Kowacce Mace Mutunci Da Kima", Da Kuma "Ban Taɓa Ganin Mace K**ar Ki Ba", Har Da "Da Zan Samu Mace Irin Ki, Da Babu Abinda Zai Hana Ni Aure Nan Bada Jimawa Ba."

Watarana Da Dare Bayan Sallah, Sai Ya Kira Ni A Waya Ya Ce Zai So Muyi Magana Sosai, Face To Face, Inda Ba Mai Jinmu. Na Ce Masa To. A Lokacin Maimuna Ta Sake Min Gargadi Na Kula Da Kyau Kar Na Kuskura Na Barshi Ya Fara Min Ɗabi'ar Da Zanzo Ina Da-Na-Sani Wato Ya Taɓa Jikina Ko Mak**ancin Haka. Na Yarda, Na Wuce Wajen Da Muka Shirya Haɗuwa.

Muka Hadu A Bayan Wani Tsohon Shago, Inda Fitilar Solar Ke Aiki. A Nan Ya Dube Ni Cikin Ido Yace:

"Ina Son Ki… Ba Don Ke Marainiya Bace. Ni Da Gaske Nake, Kuma Ina Jin Kece Maacen Da Zata Iya Zama Matata."

Na Ji K**ar Sama Zata Fashe. Wannnan Shi Ne Karo Na Farko Da Wani Ya Furta Min Irin Wannnan Magana Kuma Cikin Tausasawa, Kulawa Da Girmamawa. Na Yarda Da Shi Da Zuciyata, A Lokacin Naji Na Faɗa Sabuwar Duniya.

Bayan Kwana Biyu Ya Roƙe Ni Da Na Zo Gidansa Saboda Bashi Da Lafiya, Kuma Ba Shi Da Kowa A Kusa. Da Farko Na Ki, Amma Kalamansa S**a Ja Ni. Mukayi Magana Da Yar Uwata Maimuna Na Fice Ta Katanga A Sulale Ba Tare Da Kowa Ya Sani Ba.

Na Wuce Inda Yake Kwana, Ina Shiga, Na Tarar Da Gidan A Tsaftace, Ya Buɗe Min Kofa Da Murmushi, Yana Sanye Da Kayan Bacci. Na Zauna. Sai Ya Fara K**ar Kuka, Yana Cewa Yana Jin Tsoro Kar Na Barshi, Babu Abinda Zai Same Ni. Na Dube Shi Cike Da Tausayi Nace "Ba Zan Taba Barinka Ba." Wannnan Shine Lokacin Da Komai Ya Canza Min Nayi Alkawarin Da Yafi Ƙarfi Na.

Ya Matso Kusa Dani, Yana Kokarin K**a Hannaye Na. Nikuma Na Janye Ina Kallon Gefe. Ya Saki Miko Hannunsa Kan Kafaduna A Hankali Na Ji Hannunsa Yana Yawo A Jikina, Da Yana Ambaton "Ki Yarda Dani, Wallahi Ina Sonki Ne, Banida Da Yadda Zanyi, Ke Tawa Ce Har Abada". Na Juya Na Kalle Shi Har Cikin Idanu Yana Kallona, Muka Jima A Haka, Sa'annan Ya Turo Bakinsa A Hankali Ya Fara Sumbata Ta.

Abin Da Ya Faru Daga Nan Ba Zan Iya Cewa Komai Ba. Amma A Wannnan Rana Na Sadaukar Da Komai, Jikina Da Amincina, A Daren Nan Don Kawai In Tabbatar Da Soyayyata A Gare Shi.

Washegari, Na Farka Da Hasken Rana Yana Haskawa Kofar Dakin. Na Juyo, Na Same Shi Yana Shiryawa. Bai Ce Min Komai Ba, Ba Tare Da Ya Kalli Inda Nake Ba Yace “Ki Koma Gida Kafin A Fara Neman Ki.” Babu Abinda Ya Kara Faɗa. Haka Na Tashi Na Koma Gida Zuciyata Gabadaya Tayi Nauyi.

Bayan Kwana Biyu… Na Kira Wayarsa Bai Ɗauka Ba. Na Aika Masa Da Text, Bai Amsa Ba. Na Aiko Maimuna Ta Leƙa Gidansa, Tace Min Ya Tafi Abuja Tun Shekaranjiya.

Daga Nan Ne Zuciyata Ta Fara Girgiza K**ar Girgizar Kasa.

Na Fara Jefowa Kaina Tambayoyi Shin Ya Cutar Da Ni Ne Kawai Don Ya Biya Bukatarsa? Ko Kuwa Wani Abu Ne Ya Faru Da Bai Sanar Da Ni Ba?...

✍️ Cigaban Labarin Zaizo Bayan Kunyi Mana Sharing 100 😊 Da Comments ✊ Muje Zuwa

Labarin Yaƙi Da Soyayya Da Cin Amana A Filin Gasa (Complete)A Tsakiyar Birnin Bhab, Yan Kallo Sama Da Dubu Goma Sun Taru...
27/07/2025

Labarin Yaƙi Da Soyayya Da Cin Amana A Filin Gasa (Complete)

A Tsakiyar Birnin Bhab, Yan Kallo Sama Da Dubu Goma Sun Taru, Filin Gasa Ya Cika Da Ihu Da Shewar Jama’a. A Wannan Ranan, Jarumi Salisu, Ya Fuskanci Dan’uwansa Jamilu, Wanda Ya Zama Abokin Gaba Saboda Cin Amana Da Soyayya Ta Raba Su.

Salisu, Wanda Zuciyarsa Take Ɗauke Da Soyayyar Gimbiya Hafsat, Yana Jin Haushin Jamilu Wanda A Da Ya Kasance Abokinsa, Ya Ci Amanarsa. Jamilu Ya Hada Kai Da Sarkin Bhab, Wato Sarki Bature, Don Ya Ƙwace Nasarar Salisu A Filin Gasa. Sarki Bature, Wanda Yake Jin Tsoron Ƙarfin Salisu Da Tasirinsa, Ya Amince Da Jamilu, Ya Ba Shi Wani Laƙani Na Sihiri Wanda Zai Kanannade Salisu A Lokacin Yaƙi.

Da Gari Ya Waye, Sai Filin Gasa Ya Rude Da Murna, Jama’a Na Ta Kirari Ga Salisu, Saboda Suna Ji Da Shi. Amma Gimbiya Hafsat, Da Take Zaune A Kan Karagar Alfarma, Tana Jin Tsoro A Zuciyarta, Domin Ta Ji Labarin Cin Amanar Da Jamilu Yayi Masa. Ita Kuwa Gimbiya Zainab, ‘Yar Sarkin Bature, Ta Ji Daɗin Wannan Gasar, Saboda Tana Son Jamilu, Kuma Ta San Cewa Idan Salisu Ya Fadi, Jamilu Zai Iya Samun Matsayi.

Koda Jarumai Biyu S**a Tsaya A Filin Gasa, Sai Jamilu Ya Zaro Takobinsa, Wanda Yake Ɗauke Da Sihiri Na Tsafi, Ya Fara Kai Wa Salisu Hari Da Ƙarfi. Salisu, Duk Da Ƙarfinsa, Ya Ji Wata Guguwar Sihiri Ta Kanannadeshi, Tasa Ya Kasa Matsawa. Jama’a S**a Tsorata, S**a Fara Ihu, Amma Babu Mai Sanin Abin Da Ke Faruwa Sai Sarki Bature Da Shi Kanshi Jamilu.

A Wannan Lokacin, Gimbiya Hafsat Ta Mike Tsaye, Zumbur! Ta Kai Hannu A Kan Kirjinta, K**ar Zata Kwallara Ihu. Ta Ji Zafin Soyayyar Salisu A Zuciyarta, Amma Ba Ta San Yadda Zata Ceto Shi Ba. Sai Ta Hango Sarkin Tsafi, Mai Suna Gurama, Wanda Yake Zaune A Gefen Filin, Yana Kallon Gasar Da Guntun Murmushi. Gurama, Wanda Yake Da Labarin Soyayyar Salisu Da Hafsat, Ya Ji Haushi Da Cin Amanar Da Jamilu Yayi, Saboda Shi Ma A Da Ya Ji Raɗaɗin Irin Wannan Cin Amana A Soyayya.

Cikin Saurin Gaske, Gurama Ya Ɗaga Hannunsa, Ya Karanta Wata Kalmar Tsafi, Nan Take Guguwar Da Ta Kanannade Salisu Ta Bace. Salisu, Da Ya Samu ‘Sarari, Ya Sunkuya, Ya Kaucewa Harin Jamilu, Nan Take Cikin Wani Ihu Mai Ƙarfi, Ya Soka Takobinsa A Cikin Jamilu. Takobin Ya Shiga Gadon Bayan Jamilu, Ya Fito Ta Cikinsa, Sai Jamilu Ya Kwallara Ihu, Ya Faɗi Ƙasa, Jini Na Zuba.

Filin Gasa Ya Cika Da Shewa, Yan Kallo S**a Kaure Da Murna, Suna Kirari Ga Salisu. Gimbiya Hafsat Ta Daka Tsalle, Murna Ta Lullube Fuskarta, Amma Ta Hango Sarki Bature, Wanda Fuskarsa Ta Murtuke Saboda Takaici. Gimbiya Zainab Kuwa, Ta Sunkuya Da Kanta, Hawaye Na Zuba Saboda Rashin Nasarar Jamilu.

Sarki Bature, Ya Ji Kunya Da Rashin Nasarar Sihirinsa, Nan Take Ya Tashi Daga Karagarsa, Ya Fice Daga Filin, Ba Tare Da Ya Ce Komai Ba. Salisu, Duk Da Raunin Da Ya Ji, Ya Tsaya Tsaye, Ya Ɗaga Takobinsa Sama, Yana Nuna Nasararsa. Gimbiya Hafsat Ta Ruga Zuwa Filin, Ta Rungume Salisu, Ba Tare Da Ta Ji Kunyar Yan Kallo Ba.

Amma A Gaban Filin, Sarki Gurama Ya Tsaya Yana Kallon Salisu, Yana Guntun Murmushi. Ya San Cewa Soyayya Ta Fi Ƙarfin Cin Amana, Kuma Ya Ji Daɗin Cewa Ya Taimaka Wa Salisu Ya Yi Nasara. A Nan, Jama’a S**a Cika Da Murna, Suna Rera Waƙar Salisu, Wanda Ya Zama Jarumin Kwarai.

Idan Kaji Daɗin Labarin Kayi Sharing Domin Naci Gaba Da Kawowa Kullum ✍️😊

Daga Lokacin Da Ya Buɗe Min Ƙofar Ɗakin Naji Wani Sanyi, Na Ji Numfashina Ya Tsaya. Cikin Gidan K**ar Tsohon Gidan Tsafi...
26/07/2025

Daga Lokacin Da Ya Buɗe Min Ƙofar Ɗakin Naji Wani Sanyi, Na Ji Numfashina Ya Tsaya. Cikin Gidan K**ar Tsohon Gidan Tsafi. Babu Furniture Da Ado Irin Na Normal Gida. Ƙasan Gidan Katako Ne, Daga Sama Kuma Duhu Ne Da Ƙamshin Wuta Da Hayakin Turare. Mutumin Ne Yake Zaune Kan Kujera Jibgege, Ya Zuba Idanu K**ar Wani Ɓarawo.

Cikin Sanyin Murya Yace: “Ki Matso, Ki Zauna Kusa Da Ni.”

Karfin Jikina Ya Ƙare Gabadaya. Bani Da Wani Ƙuzari. Sai Na Zauna A Hankali. Na Sauƙe Kaina, Na Kulle Bakina. Amma Zuciyata Na Faɗa Mini Cewa Lafiya. Wannan Mutumin Ba Zai Kyaleni Ba.

Na Juyo, Na Hango Wasu Hotuna A Jikin Bango — Hotunan Ƴan Mata, Wasu Fuskarsu Tayi Jaa. Na Sake Kafewa Gam Cikin Tsoro. Sannan Na Hango Katuwar Tabarya Da Take Tattare Da Jini. Na Rungume Kafafuwana Cike Da Tsoro, Jikina Ya Fara Ɓari K**ar Mai Jin Sanyi. Na Fara Tuna Gida, Na Tuna Mahaifiyata, Na Tuna Da Mahaifina. Na Ce A Zuciyata:

“Allah, Idan Har Wannan Ne Karshena, Ya Allah Ka Yi Mini Rahama.”

Lokacin Da Ya Matso Kusa Da Ni, Yana Mim Murmushi K**ar Ba Komai, Ya Janyo Da Wani Tulu, Na Ji Ƙamshin Wani Abin Da Ba Zan Iya Faɗa Ba. Yana Ƙoƙarin Shafa Ni, Na Miƙe Cikin Rawar Murya Na Ce: “Don Allah… Don Allah… Ni Ba Zan Iya Ba… Kawai Muyi Abinda Ya Kawo Mu”

Ya Yi Murmushin K**ar Na Rashin Jin Daɗi, Ya Ce:

“Karki Damu, Wannan Duk A Cikin Haɗin Ne. Kuma Ina Da Tabbacin Zakiyi Farin Ciki Sosai, Daga Yau Zaki Ji Ki Rass.”

Ban San Me Wannan Yake Nufi Ba, Amma Na San Ba Za'a Gama Lafiya Ba.

Sai Da Na Tsaya, Na Sake Hada Ido Wani Katon Wuri Da Ke Da Wani Karamin Ƙofa Mai Firgitarwa. A can Na Hango Wani Ɗan Jariri A Tsakar Kwalba, Jikinsa K**ar Na Mace. Na Dafe Kijina, Na Fara Hawaye Ina Ja Da Baya.

Yana Ƙoƙarin Rufe Ƙofar, Na Jefa Masa Tulu Daya Da Ke Tsakar Ɗakin, Na Bugeshi A Kai. Bai Ɓata Lokaci, Ya Yi Wani Atishawa Mai Ƙarfi Sa'annan Ya Faɗi Ƙasa. Na Buɗe Wata Ƙaramar Ƙofa Da Ke Gefen Falon, Na Bude Cikin Tsoro, Na Saka Kai Na Fita.

Titin Duhu Gabadaya Ta Ko Ina, Ko Hasken Wata Babu, Ina Ta Gudu Da Ƙafafuna Bansan Ma Inda Nake Jefa Ƙafafuna Ba. Babu Takalmi A Ƙafata. Nayi Ta Gudu, Har Na Hauro Babban Hanya Ina Kaucewa Motoci, Na Cire Guntun Gyale Na Ina Ƙoƙarin Ɗaurawa A Kuguna.

Na Fita Har Kan Titin Nsukka, Na Koma Gefen Daji. Gashi Ban Da Kuɗi, Ban Da Waya A Hannuna, Kuma Gashi Dare Yayi Babu Wanda Zai Tsaya Ya Taimake Ka.

Na Fara Tafiya Cikin Rashin Sa Rai, Da Kafa, Ban San Ina Nake Ba. Idan Na Ji Mota Ma Sai Na Ɓuya. Daga Nan Na Fara Jin Numfashi Na Yana Yankewa. Cikin Kuka, Na Ce:

“Ya Allah Ka Sa In Isa Gida... Wallahi Na Gane Kuskure Na.. Ta Tuba, Wallahi Ba Zan Sake Ba, Zan Samu Miji Ko Wanene Na Zauna Mu Rufawa Kanmu Asiri Nayiwa Iyayena Biyayya.” Na Ƙarasa Maganar Ina Kuka Kaina Na Min Ciwo.

Wannan Tafiya Ce Da Ta Fi Duk Wahalar Da Na Taɓa Fuskanta. Gajiya, Yunwa, Tsoro, Ciwon Kai, Duk Sun Hadu Min Lokaci Guda A Wannan Daren.

____

👉 Saura Shafi Uku ✍️ Idan Kana Jin Daɗin Labarin Kayi Like, Da Sharing Koda Sau Ɗaya Ne Domin Mu Tabbatar Ana Tare 😘

Ban Manta Ranar Da Na Yanke Shawarar Barin Gida Ba. Da Yamma, Rana Na Fadi, Lokacin Ina Cike Da Sha’awar Sabuwar Rayuwa....
25/07/2025

Ban Manta Ranar Da Na Yanke Shawarar Barin Gida Ba. Da Yamma, Rana Na Fadi, Lokacin Ina Cike Da Sha’awar Sabuwar Rayuwa. Kawata Maryam Ce Ta Zo Gida Ranar, Ta Zauna Ta Ce Min:

“Zarah, Wallahi Enugu Rayuwa Ce Ta Jin Daɗi. Kuɗaɗe Kam Akwai Su, Domin Har Na Bude Boutique. Gaskiya Ba Irin Wannan Rayuwa Ce Ta Dace Dake Ba. Ki Biyo Ni Mu Huta Da Wahalar Nan, Ki Dubi Fa Yadda Kika Lalace Kika Rame Gabadaya, Kyawunki Yana Ƙoƙarin Gushewa, Ki Dubi Fa... Wane Irin Mai K**e Shafawa Ne.”

Maganganunta Sun K**a Ni. Lokacin Muna Fama Da Matsin Rayuwa A Gida. Mahaifina Ya Yi Ritaya, Mahaifiyata Kuma Kayan Miya Take Sayarwa A Kasuwa. Kuɗi Ba Su Da Yawa, Kullum Ga Jinya Da Biyan Albashi. Hakan Ne Yasa Na Ga Mafita A Maganar Ta, Sai Nace Mata.

“Idan Haka Ne Sai Na Shirya Kawai Mu Tafi.”

Bani Da Babbar Waya A Hannuna Lokacin, Ta Bani Naira Dubu Goma Da Lambarta. Na Yi Shiru Ba Tare Da Na Faɗawa Iyaye Na Komai Ba. Bayan Ta Tafi Da Kwana Biyu, Na Hau Mota Na Gudu.

Zuciyata Tana Cike Da Fatan Sabuwar Rayuwa, Amma Ban San Cewa Zan Shiga Makarkashiyar Da Ba Zan Mantu Da Ita Har Abada Ba.

Lokacin Da Muka Iso Enugu,..

Enugu Garin Manya Ne, Wasu Wuraren Gwanin Sha'awa, Mutane Da Daban-Daban Ana Hada-Hada, Wurin Da Ba Kowa Ke Gane Kowa Ba. Sai Da Muka Je Wani Hotel Mai Hawa Sama Da Ƙasa. Akwai Ƴan Mata Da Dama. Kowa Na Sanye Da Kaya Masu Sheƙii Da Turare

Na tambayi Maryam:

“To Boutique Ɗin Fa?” Ta Yi Dariya Kawai Ta Ce: “Zarah, Komai Sai A Hankali. Ba Haka Ake Farawa Ba, Kema Zaki Samu Boutique.”

Cikin Kwanaki Uku, Na Gane Abin Da Ake Yi. Karuwanci. Harkar Zin-a. Harkar Masu Bin Masu Kuɗi. Bidirin Duniya. Za'a Shirya Ki, A Baki Kaya, A Zuba Miki Kwalliya, A Sa Ki A Motar Wani Tsoho Ko Matashi, Ki Tafi Ki Yi Abin Da Ba Zaki Iya Faɗa Ba. Sannan Ki Zo Ki Karɓi Naki Rabon.

Na Fara Rawar Zuci, Na Nemi Ficewa, Amma Maryam Ta Ce:

“Duk Abincin Da K**e Ci Ba Kyauta Bane, Kuma Babu Wata Mafita Da Ta Wuce Wannan.”

Wannan Shine Abin Da Ya Fara Rushe Min Duk Wani Shiri Na. Na Sha Kuka A Cikin Daki. Ban San Wanda Zan Kira Ba, Saboda Ban Faɗa Wa Iyaye Na Inda Na Je Ba. Na Kulle Kaina Na Rungume Ƴar Jakata, Babu Yadda Zan Yi Yanzu Illa Nayi Haƙuri Na Ga Abinda Zai Faru.

Wata Rana, Aka Ce Min Akwai Wani Mai Kuɗi Ne Ya Zo Daga Abuja. Zai Zabi Sabuwar Yarinyar Gida. Ba Wanda Ya Amince In Je Face Ni, Saboda Na Fi Kowa Kyau. Maryam Ta Tabbatar Min Cikin Daɗin Baki

“Kada Kiyi Wasa. Wallahi Zai Miki Kyauta, Ko Wayar iPhone 13 Pro Max.”

Wannan Ne Abinda Mukayi. Da Daddare Aka Sa Ni Cikin Mota, Aka Kai Ni Gidan Wani Matsakaicin Gini A Ƙarshen Garin Nsukka. Cikin Gidan K**ar Babu Abu Mai Rai, Wutar Gidan Tayi Low. Wani Dogon Bature Mai Baƙin Fata Ne Ya Buɗe Mini Ƙofa, Idanunsa Alamun Mara Gaskiya Da Yadda Yake Kallon Mu.

Ya Kalli Idanu Na, Cikin Sanyin Murya:

“Welcome. Just Relax.”

Na Fara Jin Tsoro. Amma Zuciyta Tace Zai Wuce.

Ashe Wannan Kawai Shi Ne Farkon Bala’in Da Zan Fara Shiga Rayuwata.
____

👉 Zan Cigaba, Amma Ku Tabbatar Kunyi Like Da Sharing 💔

23/07/2025

Labarin Soyayyar Nan Zai Baka Tausayi... Gajeren Labari...

Tace "Na Tsinci Kaina Cikin Soyayyar Da Bani Da Ikon Fita Daga Ciki, Ashe-Ashe..."

Watarana Fatima Tana Zaune A Gaban Madubi, Tana Murza Idanunta Sanye Da Kayan Bacci, Tana Murmushi K**ar Wacce Aka Yi Wa Bushara Da Shiga Aljannah. Sai Ta D**o Kai Cikin Nutsuwa Ta Ce Da Kanta:

“Wallahi Har Yanzu K**ar Da Gaske Nake Ji…”

Labarin Ya Fara Ne Ranar Da Ta Fara Ganinsa A Gidansu Su Rahma. Wani Bawan Allah Ne Yana Da Tsabta, Kyakkyawa Da Sanyin Halitta. K**ar Dai Namijin Novel, Sunan Sa Khalid.

Tun Farkon Ganin Sa, Fatima Ta Ji K**ar Wani Abu Ya Soki Zuciyarta. Ba Tayi Magana Ba, Amma A Idanunsu Sunyi Ta Wasa Da Junan Su. Khalid Ya Kalli Fatima Cikin Sanyin Murya Ya Ce:

'Kinyi Shiru K**ar Ba’a Gidan Ku K**e Ba. Idan Kuma A Wani Gidan K**e Fa?'

Fatima Ta Kasa Amsawa, Amma Ta San Zuciyarta Ta Tsunduma Cikin Wani Abu Da Ta Dade Ta Kasa Ganewa, (Soyayya).

Bayan Wannan Rana, Khalid Ya Zame Mata Tamkar Jinin Jikinta. Su Kan Yi Hira A Waya, Su Tattauna Har Zuwa Dare. Zuciyar Fatima Na Cike Da Farin Ciki. Khalid Ya Cika Mata Duniyarta Da Farin Ciki, Kalamansa Kaɗai Sun Isheta, Lallai Sai Yanzu Ta Fahimci Asalin Soyayya.

“Fatima, Ina Son Ki. Kuma Ina Mafarkin Yin Rayuwa Tare Da Ke Na Har Abada.”

Ta Mayar Masa Da Amsa “Nima, Baka San Yadda Ka Shige Min Zuciya Ba Khalid... Bana Tunanin Zan Iya Rayuwa Ba Tare Da Kai Ba”

Kwana Biyu Baya, Khalid Ya Zo Gidansu Da Manyan Kaya. Ya Ce Ya Zo Neman Izini. Mahaifiyar Fatima Ta Karɓe Shi Hannu Bibbiyu, Kowa Ya Ji Dadi. Aka Sa Rana, Aka Fara Shirye-Shiryen Biki.

A Ranar Daurin Aure, Fatima Na Zaune Gaban Mai Shafa Mata Lalle, Ta Na Tunanin Rayuwa Da Khalid. Sai Ta Lumshe Idonta Ta Cika Da Murmushi...

Innanillahi, Kwatsam Cikin Daren Nan Ta Tashi Da Hawaye...

“Ina Khalid? Ina Lallen Aure? Ina Rigunan Amarya?”

Ta Kalli Hannunta — Babu Lalle.
Ta Dubi Dakin — Inda Take Kwanciya Ne..
Ta Leka Waje — Babu Komai.

Ta Rike Kanta Tana Jin Haushi. Ashe Duk Wannan A Mafarki Take Yi...

Fatima Ta Zauna, Ta Kalli Kanta A Madubi. Tana Kuka Da Murmushi A Lokaci Guda.

Wace Shawara Zaku Baiwa Fatima? ☺️

21/07/2025

Cigaban Labarin Abinda Ya Faru Da Jamila, 👉 A Ranar Jamila Ta Koma Gida Cike Da Tunanin Abubuwan Da Ta Gani Da Saurara. Ta Saka Wayarta A Flight Mode, Ta Rufe Kanta A Daki, Bata Iya Bacci Ba. Hoton Mahaifinta Da Alhaji Ya Nuna Mata Yana Cigaba Da Zagayawa A Idanunta, Cike Da Tsoro, Da Tambayoyi.

Bayan Kwana Biyu, Alhaji Mukhtar Ya Aiko Da Motar Dauko Ta Zuwa Wani Wurin Da Ya Ambata “Cibiyar Sirri.” Wurin Yana Gefen Gari A Wata Daji, Amma Cikin Ginin Alfarma Wanda Babu Wanda Zai Yi Tunanin Akwai Irinsa A Wurin.

A Cikin Cibiyar, Ta Tarar Da Wasu Matasa Irinta Su Bakwai. Wasu ‘Yan Sanda Ne Da Aka Kora, Wasu ‘Ya’yan ‘Yan Siyasa Ne Da Aka Kashe Su, Wasu Kuma Irin Wadanda Rayuwa Ta Yiwa Juyin Masa. Kowa Na Da Dalilin Da Ya Sa Yake So Ya Ɗauki Fansarsa.

Malam Lawan, Shugaban Cibiyar, Ya Ce, “Wannan Wurin Na Da Tsari. Zamu Horar Daku A Harkar Tsaro, Leken Asiri, Fashin Baya, Harsuna, Kwamfuta, Harma Da Sarrafa Hankalin Mutane. Amma Kafin Wannan, Sai Mun Fahimci Zukatan Ku. Wane Ne Kuke So Ku Zama?”

Da Sauri Jamila Ta Ce, “Ni Ina So Na San Gaskiyar Abin Da Ya Faru Da Mahaifina. Ina So Na Dawo Da Darajarsa. Kuma Ina So Na Ga Idanun Wadanda S**a Hallaka Shi, In Saka Su Kuka Da Nadama.”

Malam Lawan Ya Dube Ta K**ar Ya Gane Wani Abu Cikin Zuciyarta. “Zaki Ga Duk Wannan. Amma Dole Ki Sa A Ranki Cewa, Bashi Da Sauƙi. Zaki Koyi Abubuwan Da Ba Kowacce Mace Ke Iya Yi Ba.”

Cikin Watanni Uku, Jamila Ta Canza. Ta Koyi Gudu, Tsalle, Fasa Lambobi, Karanta Harsuna, Da Yadda Za Ta Yi Amfani Da Hankali Fiye Da Tunaninku. Amma Abinda Bata Sani Ba Shine, Wani Matashi Daga Cikin Su, Wato Haris, Wanda Yafi Kowa Shiru Kuma Wanda Yake Da Hankali Da Lura, Shine Ɗan Mutumin Da Ya Kashe Mahaifinta.

Yayin Da Horon Ke Tafiya, Jamila Da Haris S**a Kulla Alaka. S**a Fara Fara Fahimtar Juna, Suna Jin Dadin Kasancewa Tare. Amma Haris Na Da Wani Sirrin Da Baya Son Kowa Ya Sani. Shi Aka Baiwa Aikin Lura Da Duk Wani Motsinta.

Ranar Da Zasu Tafi Aikin Farko, Malam Lawan Ya Tattauna Da Haris A Sirrance. Ya Ce, “Karka Manta Da Umurni Na. Idan Ta Gano Gaskiyar Kawai.., Ka Gama Da Ita.”

Haris Ya Kalle Shi, Yana Girgiza Kai Ya Ce, “Na Fahimta.”

Amma Ranar Da S**a Fara Aiki, S**a Je Wani Wurin Da Aka Ajiye Takardun Sirrin Wadanda S**a Kashe Mahaifin Jamila, Itace Ta Farko Da Ta Fara Fitar Da Bayanai. Tayi Bincike Cikin Natsuwa, Sannan Ta Dubi Haris Har Cikin Ido.

Ta Ce, “Na Fara Fahimtar Abin Da Ke Faruwa... Menene Kake Boye Min?”

Haris Ya Yi Shiru. Ya Kalli Takardar Dake Hannunta, Ya Ce, “Kin Riga Kin Fara, A Yanzu Babu Ja Da Baya, Idan Kika Bayyana Abin Da Ki Ka Gani, Zaki Bi Mahaifinki.”

Jamila Ta Kalli Haris Cike Da Mamaki. Shiru Ya Biyo Bayan Maganar. Sai Murya Haris Cike Da Ciwon Rai Yace Ce: “Ni Ne Na Kashe Shi... Amma Ba Da Niyya Ba... Na Fara Nadama Ranar Da Na Gano Waye Shi.”

Jamila Ta Rike Hannunsa, Idonta Cike Da Kuka. 😭😭

Wannan Labarin Ya Faru A Cikin Garin Gombe, Anguwa Mai Suna Malam Kuri, Wurin Da Kowa Yake Rayuwa Cikin Tsananin Tsaro. ...
20/07/2025

Wannan Labarin Ya Faru A Cikin Garin Gombe, Anguwa Mai Suna Malam Kuri, Wurin Da Kowa Yake Rayuwa Cikin Tsananin Tsaro. A Cikin Wannan Anguwa Ce Wata Yarinya Mai Suna Jamila Ke Zaune, ‘Yar Shekara Ashirin Da Uku, Kyakkyawa Ta Ɗauki Hankalin Kowa. Amma Bayan Wannan Kyawu, Tana Dauke Da Wani Sirri A Rayuwarta Wanda Ko Ita Kanta Bata San Mecece Ba.

Jamila Ta Girma Baya Da Iyaye, Tana Zaune Ne Da Goggonta Wato Inna Salamatu, Matar Da Ta Dawo Daga Maiduguri Bayan Rikicin Boko Haram Ya Kwace Mata Komai. A Rayuwa, Jamila Bata San Komai Ba Sai Gida Da Makaranta, Ita Da Littafinta Su Kadai Ne. Amma Komai Ya Sauya Ranar Da Ta Gane Cewa Wani Dattijo Mai Kudi, Alhaji Mukhtar, Yana Bibibiyarta Bata Sani Ba.

Ranar Juma'a, Bayan Ta Idar Da Sallah, Ta Hango Wani Mota Black Jeep Da Ke Tsaye Kusa Da Masallacin Anguwa. Wani Tsoho Ya Sauko Daga Motar Yana Sanye Da Farar Riga Da Hula Mai Tsada, Yana Dubanta Cikin Wani Iri Na Kallo. Bayan Ta Wuce, Taji An Kirata Da Sallama. Ta Juyo A Hankali.

"Ke Ce Jamila Ko?" Ya Tambaya Cikin Muryar Da Take Da Dadi Amma Cike Da Sanyayawa.

Ta Ce, "Eh Ni Ce." Tana Ɗauke Da Takaici A Muryarta.

"Sunana Alhaji Mukhtar. Na Jima Ina Bibibiyar Ki Tun Lokacin Da Ki Ka Yi Speech A Wajen Graduation Dinku. Ina So Na Zama Aboki A Gareki Dan Allah Idan Ba Zaki Damu Ba."

Jamila Ta Yi Murmushi Cikin Sanyin Jiki, Amma Cikin Ranta Tsoro Ya Fara Shiga. Tayi K**ar Ba Komai, Ta Ce, "To Alhaji, Nagode. Amma Bana Bukatar Komai."

Daga Wannan Ranar, Alhaji Mukhtar Ya Fara Tura Mata Kudi A Banki, Duk Da Bata Taba Bashi Account Dinta Ba. Ya Aiko Mata Da Waya Sabuwar iPhone 14, Sai Kayan Leda Daga Abuja. Inna Salamatu Ta Fara Jin Dadi, Ta Ce, "Jamila Ki Fara Karbar Wannan Alhaji. Kila Rabon Allah Ne!"

Jamila Ta Kasa Fahimtar Yadda Wannan Dattijo Ke Da Dukiya Kuma Bai Da Wani Gida Ko Iyalai Da Aka Sani. Hakan Ya Zama K**ar Wani Abu Ne A Ɓoye, Waye Ya Sani.

Wata Rana Alhaji Ya Gayyace Ta Zuwa Gidan Sa Na Gwamnati. Da Ta Je, Ta Ga Gidan Ga Tsari Ga Tsada, Ga Abubuwan Alatu A Cikin Gidan Gabadaya. Amma Abinda Yafi Bata Mamaki Shi Ne Wani Hoton Babanta Da Ta Gani A Falon Alhajin, Hoton Mahaifinta Da Aka Ce Ya Mutu Tuni!

Ta Kalli Hoton Zuciyarta Na Tsinkewa. Ta Ce, "Wannan… Wannan Shine Baba Na!"

Alhaji Mukhtar Ya Kalle Ta Cikin Idanu, Yana Dariya K**ar Akwai Wani Abu. Sai Ya Ce, “Eh, Shine. Amma Kafin Ki Tambaya, Ki Zauna. Zaki Ji Komai.”

Jamila Ta Zauna, Jikinta Na Bari.

Alhaji Ya Ce: “Babanki Bai Mutu Ba, An Yi Masa Sharrin Da Har Yanzu Baya Da Dama Ya Ga Rana. Kuma Ni Ne Mutumin Da Aka Ce Shine Sanadin Mutuwarsa.”

Idanunta S**a Ciko Da Hawaye, Ta Ce, "Kayi Masa Sharrin?"

Ya Girgiza Kai. “A’a, Amma Na San Wa Ya Yi. Kuma Zaki Taimaka Min Ki K**a Su, Amma Saurari Wannan Labarin Daga Farko...”

Alhaji Ya Zare Wani Leda Cike Da Hotuna, Takardu Da Litattafai, Daga Ciki Tana Gani Ta Fara Kuka. Dukkan Takardun Sun Nuna Cewa Mahaifinta Ya Kasance Babban Injiniya A Wani Kamfani Na Gine-Gine, Kuma Ya Bankado Sirrin Wasu Tsofaffin Masu Mulki Da Attajirai Da S**a Saci Dukiyar Talakawa. S**a Yi Sharrin Kisan Akansa.

Jamila Ta Ce, “Amma Me Zanyi? Ni Kuma Ina Ruwana Da Wannan Rikicin Naku?... Ni Abbana Kawai Nakeso Dan Allah” Ta Ƙarasa Maganar K**ar Zatayi Kuka.

Alhaji Ya Kalle Ta Cikin Ido. “Zaki Zama ‘Yar Wata Makarantar Sirri Da Muke Da Ita. Zamu Horar Da Ke, Zaki Zama Mai Iko, Zaki Dauki Fansar Mahaifinki. Kuma Zaki Gano Duk Abinda K**e Nema!”

Jamila Ta Tashi Da Karfi, Ta Ce, “Zan Yi Komai In Dai Abbana Zai Dawo”

Sai Dai Bata San Cewa Daya Daga Cikin Mutanen Da Za A Horar Da Ita Tare Shi Ne Wanda Zai Sace Zuciyarta Ba, Kuma Shi Ne Mutumin Da Ya Ɗauki Nauyin Hallaka Mahaifinta...

To Me Zai Faru? Zata Cika Alkawari? Soyayya Ko Ramuwar Gayya Ce Zata Fi Karfi? Zan Ƙarasa Labarin Zuwa Anjima.

19/07/2025

Unveiling History: The 4,500-Year-Old Tunic at the Egyptian Museum"😱🥰😭😊

Treasures

19/07/2025

Labarin Hauwa'u (Hausa Video) Ku Saurara Zata Baku Tausayi

07/07/2025

Labarin Aisha Da Nasir, Yadda Ya Raba Auren Ɗan Uwansa Saboda Ya Auri Matar...

09/02/2025

Wanne Littafi Kuke Bukata Next?

05/11/2023

GIDAN UNCLE
Page Twenty One 25

❤️❤️❤️
❤️❤️
❤️

Juyowa s**ayi a tare cikin mamaki dukkansu suke kallon Hajiyan da tayi kicin² ta riqe Umaimah gam tare da qara daka masa tsawa tace “ka saketa nace Hameed wlh kaji na rantse gdannan yau dagani sai ku Daddynku baya qasar nan saboda haka dole ka saki Umaimah bazaka kashe marainiyar Allah ba Hameed tsine maka zanyi idan kaqi yimin biyayya"

Cikin tsananin tashin hankali ya zube a gurin muryarsa na wata irin karkarwa yace “na roqeki Hajiya kiyimin rai ki ceci rayuwata wlh inason matata ita kadai ta saura me tausayina a duniya Hajiya kada ki rabamu wlh nayi miki alqawarin bazan qara kusantar Umaimah ba har abada amma ki barmu tare Hajiya tana sona inasonta....” daukeshi da mari Hajiya tayi tace “bawai tausayinka ne banaji ba amma kaima kasan zamanka da Umaimah cutawa ne a gareka da ita kanta saboda haka dole anan ka saketa” miqewa yayi yana layi k**ar dan giya ya nufi qofa zai fice Umaimah tayi saurin riqoshi cikin kuka me ban tausayi tace.

“Kada ka fita cikin tsinuwar mahaifiyarka Uncle bawai saboda wannan dalilin ne kawai Hajiya takeson rabamu ba tanason rabamu ne saboda banida kowa banida gata don girman Allah Hameed kada ka sabawa umarnin Hajiya ka sakeni Hameed ka sakeni nace...” rufe mata baki yayi yana girgiza Mata kai Amma ya kasa cewa komai sai rawa da jikinsa yakeyi ya janyo Umaiman ya hadata da qirjinsa “Allah ya tsine....” da sauri Umaimah ta janye jikinta daga nasa ta cukumi wuyansa tace “wlh bazaka taba kasancewa cikin tsinuwar mahaifiyarka akaina ba dole ka sakeni Hameed” qara rufe mata baki yayi da sauri yana girgiza mata kai yana hawayen tausayin kansa cikin tashin hankali yace “Haj....” katseshi ta kuma yi tace “wlh saika saketa Hameed”

Cikin fitar hayyaci yace “shis.. shikenan na...na sakeki saki day....” bai ida qarasawa ba wani mugun jiri ya debeshi yayi baya kansa ya hadu da glass din qofar ya fadi tim tare da ballewar jini a kansa.

Nufarsa tayi da gudu tana sakin wata qarar tashin hankali tana cewa “shikenan kin kasheshi Hajiya mun shiga ukun mu...” riqo hanunta Hajiyan tayi cikin tashin hankali tace “kada ki tabashi babu aure tsakaninku" zubewa tayi a gurin tayi zaman tan bori kanta da kwakwalwar ta na juyawa jin abin take k**ar a mafarki “Hameed ya sakeni" ta fada a fili tare da miqewa tana dafa bango ta nufi dakinta tana shiga ta zube a qasa sai yanzu kukanta ya dawo sabo zuciyarta nayi mata suya kanta na juyawa “ Innanillahi wa innah ilaihir raji'un Allahummah ajjirni fi musibati wa'akalifni khairin minha”

Su taketa maimaitawa batare da tunanin mafita tafi awa daya a zaune a gurin batasan lkc ya tafi ba saida wayarta tayi qara sannan ta iya rarrafawa ta daukota sunan Sa'ud tagani ta daga ta kara a kunnenta tare da fashewa da kuka tace “Sa'ud Hajiya ta rabani da farin cikina na shiga ukuna Sa'ud zuciyata zata fashe Ina tunanin mutawa tace ta iskeni a wannan lkcn” salati Sa'ud ta dauka tace “ta rabaku Umaimah yanzu Ina Hameed din?” bata iya bata amsa ba saboda wata hardewa da numfashinta yakeyi saurin kashe wayar tayi inda Sa'ud ta miqe cikin fitar hayyaci ta dauki motarta ta nufi gdan Umaiman amma tana zuwa get man din ya sanar da ita kusan sati batanan da mugun gudu ta juya ta nufi Sokoto road tana zuwa ta fara doka horn megadin yazo ya bude parking tayi cikin tsananin firgici ta bude ko kashe motar batayi ba ta shiga cikin gdan.

A durqushe ta sameta riqe da cikinta tana ta murqususu tare da cije lebe tana hawaye shiga tayi da sauri ta ruqota tana cewa “Subhanallahi Umaimah kada ki mutu don Allah tashi maza tashi mubar musu gdansu Umaimah na yarda maraya bashi da gata a wannan zamanin wannan dalilin yasa na ware kaina saboda kunci da baqin cikin rayuwa ya isheni” tana fadin haka tana hadawa Umaimah kayanta a cikin handbag dinta tare da jan akwatunan kayanta guda biyu dake jingine a jikin bango ta fita da gudu² sauri² ta zuba a motar ta dawo ta dauki wayar Umaiman tare da magungunan ta ta dagota da iyakar qarfinta tana juya kai tana kuka tana komai tasata a mota ta shiga taja tare da zuge baqin glass din saboda gudun kada get man din ya gansu s**a fita unguwar Hotoro s**a nufa cikin wata hadaddiyar Unguwa me suna Farawa layout s**a shiga unguwar ganin yanda Sa'ud taga aminiyar tata tana riqe cikine yasata nufar wani babban asibiti da ake kiza Zeenat clernic and digonostic ta shiga tare da fita da sauri tayima likitocin bayani s**a nufo motar aka k**ata ranga² aka nufi cikin wani daki da ita s**a duqufa aikinsu.

Bincike s**ayi sosai akanta kafin su gano inda gizo yake saqar tashin hankalin da take cikine ya assasa mata hawan jini me tsanani wanda yayi tasiri wajan lalata cikin dake jikinta yakeson fita amma babu hali saboda haka s**a fara qoqarin ceto rayuwarta ta hanya cire mata cikin sannan s**a daura mata ruwa tare da neman jini kasancewar kafin zuwansu asibitin ta zubar da jini yafi leda biyu kallon likitan tayi tace “Dr indai akwai abamu mu siya sai nayi muku transfer bamu da kudi cash a hanun mu” bai wani damu ba yaje ya bincika yayi sa'a aka samu laida daya irin blood dinta ya maqala mata tare da rubuta mata magungunan qarin jini Sa'ud tayi musu transfer ta account dinta k**ar yanda ta fada masa naira na gugan naira har 140,00 saida aka mayar da Umaimah dakin hutu sannan Sa'ud ta samu ganinta lkcn har tayi sallah take gida ta dawo tana kwance a gadon idanunta a lumshe tayi wani fari ta dashe saboda rashin Isasshen jinin da take fama dashi.

K**a hanunta Sa'ud tayi cikin hawaye tace “Sannu bloody kiyi hqr ki daina kukan nan kowanne bawa baya wucce qaddararsa kinji” bude idonta ta rinqayi a hankali harta saukesu tar a fuskar Sa'ud idanunta naci gaba da malalar da hawaye tace “ina Uncle Hameed Sa'ud wanne hali yake ciki ya mutu ko?” kada mata kai tayi tace “yananan Umaimah bazai mutu ba insha Allahu" lumshe idonta ta kumayi daidai shigowar likitan ya fara dubata yace “alhmdllh jiki yayi kyau sai fatan Allah ya mayar dana aika” bude idonta tayi da sauri da tsananin mamaki tace “k**ar yafa ban gane ba?” shafa gashin goshinta Sa'ud tayi tace “damuwar da Hajiya ta jefaki a ciki ce tayi sanadin zubewar cikin jikinki Umaimah..." Miqewa tayi a tsorace tace “da gaske ya zube shima Innanillahi wa innah ilaihir raji'un shikenan farin cikin Uncle ya zube meyasa ya zube Dr inason cikina yanzu shikenan nayi biyu babu ba ubansa babushi”

Tausayinta ne ya cika zuciyar Sa'ud ta kamota ta miqe tace “insha Allahu komai zaizo qarshe Bloody nasan akwai ciwo a rabaka da mijinka batare da neman shawararka ba amma babu komai akwai Allah kuma Ina tabbatar miki Hameed bazai iya rabuwa dake ba saboda kece kadai zaki iya zama dashi ki biya masa buqata yanda yakeso kuma ya samu gamsuwa dake 💯 saboda haka karma ki wani damu tunda kinji qwari tashi mu qarasa gda kiyi wanka mu nemi abinda zamuci kinji” shidai likitan binsu kawai yakeyi da kallon mamaki “dama matan aurene ku?" Yakasa jurewa ya tambaya kallonsa s**ayi a tare Sa'ud ce tayi qarfin halin cewa “eh Hussaina tace am don Allah Dr mace da aka saketa da ciki kuma cikin ya zube matsayin iddarta yake a musulumci?"

Shafa kansa yayi sannan ya zauna yace “ma'anar iddah tana nufin tsarkin mahaifa tsarkin mahaifa kuwa shine yin jini bayan rabuwar aure to wacce aka saketa da ciki kinga bazatayi jini ba harsai ta haihu shiyasa iddarta take da wahala bayan ta haihun da zarar ta haihu to iddarta ta cika ko ranar zaa iya daura mata aure kinga kenan a shari'ance matar da aka saketa da ciki tayi bari koda a ranar da aka saketa ne to ita ta tsarkaka wannan shine amsarki a taqaice wallahu wa rasulihi aalam" yana fadin haka ya miqe ya fita tare da basu sallama Sa'ud ta k**a hanunta s**a fita a sanyaye jikin Umaimah yake ji takeyi dama zata iya mayar da cikinta jikinta jikinta yanzu shikenan ta fita daga sahun matar auren Abdulhameed?

Wasu hawaye masu zafin gaske s**a gangaro mata da haka s**a shiga motar s**a nufi cikin unguwar sunyi tafiya me dan tsayi sannan s**ayi parking jikin wani dan matsakaicin flat house me kyau saida Sa'ud ta tabata sannan ta dawo hayyacinta ta bude mata qofar ta fito tana daga qafarta daqyar ta nufi qofar da taji Sa'ud din na budewa ta bude mata ta shiga tanabin gdan da kallo wata qofar taga tasa key ta bude nanma Umaimah tasa qafarta ciki wani sanyi da qamshi me dadi ya daki hancinta ta lumshe idonta duk da zuciyarta babu dadi amma taji dadin qamshin ta bude idonta tanabin parlourn da kalloh yayi kyau sosai sai qofofi guda uku da suke a kulle, zubewa tayi a saman kujera tana sauke ajiyar zuciya tanabin parlourn da kallo amma gaba daya hankalinta na wajen Uncle dinta “ko wanne hali yake a ciki?" Abinda ta tambayi kanta kenan.

Tana zaune Sa'ud din ta shigo ta cire hijjab dinta tana murmushi tace “tashina kenan daga bacci kika kirani kinga ko rigar baccin ban cire ba na zari hijjab na fita" kawar da kanta tayi gefe saboda batason hayani ko surutu itama bata qara yimata mgnba ta bude daya cikin qofofin ta shiga bata jima ba ta fito ta bude dayan dakin tace “bloody ki shiga ki kwanta kafin na sama mana abinda zamuci nasan zuciyarki tana cike da zargi na da tarin tambayoyi akaina da kuma tunanin meyene yasa na daukoki na kawoki nan to kiyi hqr zan baki amsa nan da yan mintuna"

Tana gama fada mata haka ta riqo hanunta s**a shiga dakin data bude mata mamaki ne ya cika zuciyar Umaimah ganin dakin a shirye tsaf k**ar na matar aure gado wadroop madubi da bedsat komai dai akwai sai wata qofa da take nuna alamun bathroom ne qarewa dakin kallo tayi kafin ta zauna a gefen gadon ita kuma Sa'ud ta fita ta shiga daya qofar ta fara hada musu abinci.

*************************

Kusan awansu hudu da zuwa asibitin amma har yanzu bai farfado ba ko numfashi baya iyaye saida taimakon na'ura daga Hajiya har Aunty Zarah ba qaramin tashi hankalinsu yayi ba sun ma manta da baiwar Allah Umaimah da halin da zata iya shiga sai kaiwa da komowa sukeyi tare da likitocin a haka har dare yayi sai goma saura Zarah ta dubi Hajiya tace “Hajiya wai meye yayi coorsing din matsalar nan ne Ina matansa da banga kowacce a gurinnan ba?”
Gaban Hajiya ne ya fadi ta miqe da sauri tace “na shiga uku na Zarah amanar Allah wlh na manta da ita" tana fadin haka ta fita da sauri ta tari dan sahu ta nufi gdan tun daga parlourn ta fara ganin gdan a hargitse dakinta ta nufa tana qwala mata kira amma shiru tura kanta tayi a dakin ta fara dube² amma babu alamar mutum a gurin kunna light din dakin tayi idanunta ya sauka akan inda Umaiman ta zauna dazun taga yanda jini ya bushe a gurin da sauri ta shiga ta banka qofar bandakin amma babu wata alama ta an shiga toilet din sake fita tayi tana kalle² a parlourn sai yanzu idanunta ya kai kan Nihal da Maliha da suke kwance a qasa kan tiles suna bacci matsawa tayi da sauri gurinsu tana haskasu fuskarsu duk tayi jirwaye da alamun kuka s**aci har s**ayi bacci hankalinta ya dada tashi ta nufi wajen gdan ta fara qwalawa me gadi kira ya iso da gudu ya rusuna tace “ina Umaimah?"

Da sauri ya kalleta yace “banganta ba nidai bayan ansa yallabai a mota kun tafi naga wata motar tazo amma banga wanda ya ke ciki ba kuma bata dade ba ta fita...”bata tsaya bata lkcn sauraron shirme ba ta juya gdan tana safa da marwa itakam taga ta kanta da yaran daga nema musu sauqi ta jangwalo fitina yanzu ina Umaimah ta tafi wata sani a garin wa take dashi a garin bayan su da zata wajenshi ta zauna? Tambaya ce mara amsa Hajiya take yiwa kanta har tana runtuma tuntube saboda tashin hankali.
Debe yaran tayi ta kaisu dakinsu ta kwantar dasu ta kuma shiga dakin Umaiman itace leqe har qarqashin gado miqewa ta kumayi tana rarraba idanu ya shege a rabon gado sai yanzu ta lura ma duk wani abu da yake mallakin Umaimah babushi a dakin zubewa tayi a qasa tana karanto Innanillahi wa innah ilaihir raji'un kanta yana wata muguwar sarawa a fili tace.

“Na shiga uku ni Zulaiha yau naga bala'i me hakan yake nufi Baby ta gudu saboda na rabata da abinda zai cutar da ita? Allah ka sani bada wata muguwar manufa nayi hakan ba Allah naji tsoron kada yaron nan ya hallaka ta ne Allah ka fitar dani kunyar duniya ka jefa marainiyar ka hanu na qwarai” tana maganar tana kuka me ban tausayi wayewar garin yau tayi danasani tafi dari tilon danta yana kwance baisan inda kansa yake ba ga marainiyar Allah ta gudu “wallahi saboda ni bazaka rayu cikin tsinuwar mahaifiyar kaba Hameed ka sakeni saika sakeni Hameed ba wannan dalilin ne kadai yasa takeson ta rabamu ba akwai wani qulli a zuciyarta...” kalaman Umaiman ne s**a rinqa dawo mata tare dana Hameed din lkcn da yake kuka yana cewa “ki barni na rayu da farin cikina Hajiya nayi miki alqawarin bazan qara kusantar Umaimah ba har abada Hajiya ita kadai ta ragemin wadda takejin tausayina Hajiya kada ki rabamu tana sona kuma kema shaida ce inasonta babu wanda ya isa ya raba tsakanin hanta da jini…..”

A matuqar sanyaye ta miqe ta fita zuwa dakinta ta dauki wayarta ta fara kiran wayar Umaiman tun kiran farko aka fada Mata a kashe wayar take amma bata daina Kiran ba har saita charging wayar tata ya dauke ta koma ta kwanta zuciyarta tayi mata wani mugun nauyi daidai lkcn kiran Daddy ya shigo a tsorace Hajiya ta daga cikin rawar murya tace “hel...lo Daddy" bai iya amsawa ba yace “nakira wayar babana najita a kashe na kira ta Umaimatu itama a kashe nayi miki Miss call yafi ashirin baki daga ba Zarah ta kirani tacemin babana yana asibiti cikin mayuwacin halin da baisan wake a kansa ba meye yake faruwa ne".......

Address


Telephone

+2349070613079

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausa Novels Cinema posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Hausa Novels Cinema:

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share