Amintacciya

Amintacciya Amintacciya
(9)

Zaku iya aiko mana da sahihan Labarai daga ko ina a fadin Duniya, ko wani saƙo da kuke son isarwa ta wannan number 👉07012613017 ko ta Email dinmu ✉️ 👉[email protected]

12/08/2026

Meye asalin hukuncin aikata istim'nai ?

Yanzu shima Alhaji Badamasi duk kuɗinshi saida yabi tafiyar masu dattin ƙwalƙwalwa ta Triple R. Ina mutumin nan yake so ...
11/08/2026

Yanzu shima Alhaji Badamasi duk kuɗinshi saida yabi tafiyar masu dattin ƙwalƙwalwa ta Triple R. Ina mutumin nan yake so yakai abun duniya ne!

~ inji Mamuda Wappah

Fuskokin wasu jaruman kenan daga taron kungiyar nan dake goyon bayan tazarcen Tinibu wato Triple R
11/08/2026

Fuskokin wasu jaruman kenan daga taron kungiyar nan dake goyon bayan tazarcen Tinibu wato Triple R

Mutum ɗaya tilo da yan Arewa s**a amincewa shiga kungiyar Triple R Kannywood Tanimu Akawu ya yalarci taron kungiyar.An h...
11/08/2026

Mutum ɗaya tilo da yan Arewa s**a amincewa shiga kungiyar Triple R Kannywood Tanimu Akawu ya yalarci taron kungiyar.

An hango shi ya haɗe ƙafa ɗaya kan ɗaya

An kammala musabaqar Al-qur'ani mai girma ta mazabar Mariri mai suna "PPS Dr Sani Danjuma Mariri Ward Inter -Polling Uni...
11/08/2026

An kammala musabaqar Al-qur'ani mai girma ta mazabar Mariri mai suna "PPS Dr Sani Danjuma Mariri Ward Inter -Polling Unit Qur'anic Competition "

A ranar lahadin data gabata 9-8-2026 aka kammala gagarumar musabaqar Al-qur'ani mai girma wanda aka gwabza tsakanin makarantun islamiyu guda 14 dake cikin mazabar Mariri inda aka gudanar da ita akan izu 2, 5,da 10, dakuma 20.

"Sakataran kwamatin Musabaqar, Umar Saleh Zara ya baiyyana mana cewa yan takarkaru guda 56 ne s**a shiga musabaqar yayin da yan takara 12 s**ayi nasarar samun mataki na 1 da 2 dakuma 3 a matakan Izu , 2,5,10 dakuma 20 haka kuma yakara da cewa wannan musabaqa ce daba'ataba, gudanar da irin taba a Mazabar"

Bayan kammala tattara Alkaluma
Alkalin alkalan musabaqar, Gwani Malam Ashiru Abubakar Hassan, ya baiyyana sak**ako k**ar haka:

Izu Biyu 2
Idiris Umar daga makarantar Bilkis Memorial Academy Gerawa shi yazo na daya (1)da maki 92 ,yayin da Fatima Abubakar daga makarantar Ahlulbaiti Rasulilah Farawa tazo ta biyu (2) da maki 89 inda kuma dalibi Muhammad Jidda daga Tajdidul islam sabuwar Zara yazo na uku( 3) da maki 88.

Izu biyar( 5)
Rabi'a Murtadha daga makarantar Bilkis Memorial Academy Gerawa itace tazo ta daya (1) da maki 93 inda Khidir Mu'az daga makarantar Tajdidul islam yazo na biyu (2) da maki 89,Aisha Abdulrazak daga makarantar Subulasalam Mariri Gado tazo ta uku (3) da maki 86 da rabi.

Izu 10
Hauwa'u Usman daga makarantar Subulusalam Mariri Gadon Arewa tazo na daya (1) da maki 95 sai Abubakar Kamal daga Tajdidul islam yazo na biyu(2) da maki 94 inda Mu'utasim Sanusi daga Ashabul Hadith Mariri yazo na uku( 3)da maki 92 da rabi.

Izu 20
Zainab Muhammad Sani daga Ahalulbaiti Rasulilah Farawa tazo na daya( 1) da maki 95 da rabi yayin da Idiris Ahmad Idiris daga Tajdidul islam yazo na biyu (2) da maki 90 inda Rukaiyya Muhammad daga makarantar Abuhuraira T/Zara malesiya tazo ta uku (3) da maki 83 da rabi.

Taron musabaqar yasamu hallatar daruruwan mutane da manyan malamai daga wurare daban daban.

Idan aka matsa ni saina fara kuran sunan mutanen da suke fada mana zasu bamu Saudiyya da sunan karya.Duk masu yanon Anna...
11/08/2026

Idan aka matsa ni saina fara kuran sunan mutanen da suke fada mana zasu bamu Saudiyya da sunan karya.

Duk masu yanon Annabi suna filuskamtar haka, kawai k**a cikin majalisi wani zai ce ya biya maka Madina ko yace kai da yaranka, kuyi ta murna karshe ku gane karya yake domin ya birge mutane.

Irin wadannan mutanen basa kyautawa wlh.

Inji Zaki Dan Yaya

Ni bana goyon bayan yin Auren gata da Gwamnonin jihohi ke yi Inji mawaki Ali Jita
11/08/2026

Ni bana goyon bayan yin Auren gata da Gwamnonin jihohi ke yi

Inji mawaki Ali Jita

Neman ALBARKA Yadda mawaki Rarara ke sharewa mahaifiyar sa wajan da zata zauna
10/08/2026

Neman ALBARKA

Yadda mawaki Rarara ke sharewa mahaifiyar sa wajan da zata zauna

innalillahi wa'inna ilaihi raji'un,Allah yayiwa mamammu rasuwa Hadiza Ismail, yanzu mahaifiya ga Alh. zakari Ismail kasu...
10/08/2026

innalillahi wa'inna ilaihi raji'un,

Allah yayiwa mamammu rasuwa Hadiza Ismail, yanzu mahaifiya ga Alh. zakari Ismail kasuwa masara Pambegua,

Allah yaji kanta da rahama amen.😭😭😭😭

~ Mustapha

Kaga ikon Allah sai Zumɗen wannan matashin sukeyi saboda kawai yayi Aure.Amma da Tsintso Shi s**ayi a shafin kiyawa yayi...
10/08/2026

Kaga ikon Allah sai Zumɗen wannan matashin sukeyi saboda kawai yayi Aure.

Amma da Tsintso Shi s**ayi a shafin kiyawa yayiwa wata Under Age wani Abu da yanzu iyayen iyayensa ma basu Daina shan zagi da Tsinuwa ba.

Bai Ɗauki kayan kowa ba.
Bai yi lalata da yar kowa ba.
Ba shaye-shaye yake ba.
Bai koma Gidan matan banza ya tare ba.

Lefinsa kawai meyasa zaiyi Aure yana matashi? Saboda su masu Zumɗen nasa Gidadawa ne har sun Gama yanke hukuncin bazai iya Riƙe Auren ba. A k**a matashi k**ar wannan Da wani lefi A Tsine masa shine burin wasu Hegun, bawai Asamu matashi k**arsa da kamun kai ba.

Allah ya zaɓe shi ya fifita shi kuma yasamu rabon yin Aure ba zaman Dadiro ba, bai zama Wanda zai ƙwaci kayan mutane ya siyar ya tafi gidan matan banza ba, yayi Aure Don ya kame kansa Amma bai Tsira Daga sharrin Gidadawa ba.

Shekarun sa sun kai yaji yana son mace da Aure, ƙaiminsa yakai yayi maganar Auren, Hankalinsa yakai ya nemi Auren, Rabonsa ya cika A Ɗaura masa Auren to wane Lefi kuma yayi?

Muma da muke zaune a haka bamuyi Auren ba wallahi Bahaka mukaso ba Duk ranar da Allah yakawo lokacin mu Aurenmu zamuyi lafiya ƙalau mu tafi mu zauna da iyalinmu Wanda baiso haka ba Dan kwatamar Ubansa Ya zauna ya bushe.

Daga Shehu Tijjani Sherif

Address

Kano

Telephone

+2347012613017

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Amintacciya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share