Arewa Media

Arewa Media Arewa Media is a credible online news medium that focuses mainly on truthful, objective, fair and balance journalism.

We are always committed to bringing reliable information to our large and diverse subscribers from all parts of Nigeria and even beyond.

"A lokacin da lauyoyina s**a je wajen shugaban EFCC domin neman a bada ni beli, ya ce sai na kawo waɗanda za su tsaya mi...
14/08/2025

"A lokacin da lauyoyina s**a je wajen shugaban EFCC domin neman a bada ni beli, ya ce sai na kawo waɗanda za su tsaya min. Na ce su koma su gaya masa na taɓa zama kakakin majalisa, na yi wa’adin gwamna har sau biyu, kuma yanzu ina majalisar dattawa, don haka ina iya tsayawa kaina domin belin kaina." Inji Aminu Waziri Tambuwal

Me zaku ce?

Gwmanan Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya dauki hutun aiki na tsawon mako Uku domin zuwa duba lafiyarsa Hutun zai far...
14/08/2025

Gwmanan Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya dauki hutun aiki na tsawon mako Uku domin zuwa duba lafiyarsa

Hutun zai fara daga 18 ga Agusta 2025, Ayau News ta ruwaito Gwamnan ya nada Mataimakinsa, Faruk Lawal rikon kwarya har zuwa lokacinda zai dawo. Gwamnan Ya gode wa jama’a bisa addu’o’i tare da tabbatar da cewa ayyukan gwamnati za su ci gaba da gudana ba tare da tsaiko ba.

A kwanakin baya ne dai Gwamnan ya yi hatsarin mota

Me zaku ce?

Kar Ku Yarda Mahandama Ƴan Kasuwar Biyan Buƙata Su Yaudare Ku, Gargaɗin Wonosikou Ga Masu Zaɓe A Garin GanyeA daidai lok...
14/08/2025

Kar Ku Yarda Mahandama Ƴan Kasuwar Biyan Buƙata Su Yaudare Ku, Gargaɗin Wonosikou Ga Masu Zaɓe A Garin Ganye

A daidai lokacin da guguwar siyasa ke ci gaba da kaɗawa kan zaɓen da za a gudanar a ƙaramar hukumar Ganye, Jihar Adamawa, mai taimaka wa gwamna Fintiri kan harkokin yaɗa labarai, Humwashi Wonosikou, ya gargaɗi masu zaɓe da su kula kar su yarda mahandama na jam'iyyar APC ƴan kasuwar biyan buƙata su yaudare su har su zaɓe su.

Da yake zanta wa da manema labarai a birnin Yola, Wonosikou ya zargi jam'iyyar APC da neman yin amfani da ɗan lokacin da ya rage domin neman jama'a su mara musu baya. Ya bayyana aikin gyaran hanyar da aka fara a yankin a matsayin wata yaudara irin ta siyasa ta nuna ci gaba na ƙarya.

"Jam'iyyar APC ta ga zaɓe ya zo ta kawo kayan aiki tana neman tausayawar mutane bayan da ta yi watsi da mutanen na Ganye tsawon shekaru, kar ku yarda su yaudare ku". Inji shi.

A cewarsa, jam'iyyar ta APC ta gaza taɓuka komai kan manyan ayyukan raya ƙasa kamar: ayyukan titunan gwamnatin tarayya na Jalingo zuwa Numan da ta Numan zuwa Gombe, a daidai lokacin da gwamna Fintiri ya baza ƴan kwangila su fara aikin titin Ganye zuwa Mbulo, "Mutane ba wawaye ba ne".

Wonosikou ya kuma ƙara kira ga al'umma da su ƙarfafa imaninsu, kar su yarda ƴan kasuwar buƙata su yaudare su, "Gwamnatin Fintiri tana da kykkyawan tarihi na shinmfiɗa tituna, samar da asibitoci, gyara makarantu da ba wa matasa damammaki na dogaro da kai. Dan haka, ina kira ga al'ummar Ganye su fito su yi zaɓensu cikin kwanciyar hankali da lumana ba tare da wata fargaba ba. Jam'iyyar PDP za ta ci gaba da kasancewa gwamnati mai tafiya tare da kowa gami da samar da ayyukan raya ƙasa". Inji shi

DA ƊUMI-ƊUMI: Dan Bello Ya Samu Sarautar Sarkin Yakin Talakawan NijeriyaMajalisar Malamai Mahaddata Kur'ani ne s**a ba s...
14/08/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Dan Bello Ya Samu Sarautar Sarkin Yakin Talakawan Nijeriya

Majalisar Malamai Mahaddata Kur'ani ne s**a ba shi wannan sarauta

Wane fata zaku yi masa?

DA ƊUMI-ƊUMI: Har yanzu bamu kãma kaŝurģumiɲ ɗan ta'ãḍḍã Bello Turji ba kuma muna nemansa ruwa a jallo -inji Hedikwatar ...
14/08/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Har yanzu bamu kãma kaŝurģumiɲ ɗan ta'ãḍḍã Bello Turji ba kuma muna nemansa ruwa a jallo -inji Hedikwatar tsaron Najeriya

Me zaku ce?

"Mu Akùýòyin Kwankwaso Ne, Duk Inda Ya Ķada Mu Nan Za Mu Yi, -A Cewar Masoyinsa, Dan DumurmurMe za ku ce?
14/08/2025

"Mu Akùýòyin Kwankwaso Ne, Duk Inda Ya Ķada Mu Nan Za Mu Yi, -A Cewar Masoyinsa, Dan Dumurmur

Me za ku ce?

AREWA NA BUƘATAR MANUFA KAMAR YADDA INYAMURAI DA YARBAWA SUKE DA MANUFADAGA Bashir Abdullahi El-bash A fahimtata, mataki...
14/08/2025

AREWA NA BUƘATAR MANUFA KAMAR YADDA INYAMURAI DA YARBAWA SUKE DA MANUFA

DAGA Bashir Abdullahi El-bash

A fahimtata, matakin farko na samun mafita da ci gaba a Arewa shi ne samar wa yankin manufa kamar yadda Yarbawa da Inyamurai suke da manufa.

Yarbawa da Inyamurai ba sa tafiya kara zube irin yadda muke tafiya kara zube a Arewa. A tsarinsu duk shugaban ƙasar da ya zo sai sun ɗauki kundin manufofi da buƙatunsu sun ba shi, amma mu ko shugaban ƙasa za a gani a Arewa sai dai a kai masa s**a da gulmace-gulmacen su wane ba sa sonka ko su wane maƙiyansa ne. Ba wai buƙatun yankin ba.

Ko lokacin da aka yi jin ra'ayin ƙasa kan gyaran kundin tsarin mulki lokacin Jonathan, Yarbawa da Inyamurai sun gabatar da manufofinsu amma mu Arewa ba mu yi hakan ba saboda ba mu da wata manufa a kasa.

Idan muka yi duba da ayyukan tituna da ake mana, Yarbawa da Inyamurai ba za su yarda da irin wannan jinkiri kan ayyukansu ba. Namu ya shafe shekaru 8 ba a iya kammala mana aikin titin Kaduna, Kano, Abuja ba. Ba a kammala aikin ruwa na Baro ba, ba a kammala aikin wuta na Mambila ba. Tare da rufe boda, Yarbawa ba za su yarda da wannan tsari ba.

Amma mu Arewa ba manufa babu haɗin-kai, matasa ba haɗin-kai malamai, ƴan siyasa, sarakuna, duk ba haɗin-kai. Sai hassada, kin juna da rigingimu. Yau a matsayinka na matashi ko kai ne ba ka da manufa ba ka da tsari ba wanda zai kula ka ko ya karɓi abin da kake yi.

Dole idan ana son a ga daidai a Arewa sai an samu haɗin-kai da tsari, da manufa da kuma jagora wanda in ya ce a yi Gabas za a yi gabas, in ya ce a yi Yamma za a yi Yamma, in ya ce a yi Kudu za a yi Kudu, in ya ce a yi Arewa za a yi Arewa, kamar yadda Yarbawa suke da hakan.

INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN: Fatima Rabi'u Lawal Ta Rãșu Sakamakøɲ Haihuwa'Yan uwanta sun bukaci jama'a da su yi...
14/08/2025

INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN: Fatima Rabi'u Lawal Ta Rãșu Sakamakøɲ Haihuwa

'Yan uwanta sun bukaci jama'a da su yi mata addu'ar samun rahama.

WATA SABUWA: Dalilai biyu ne zasu hana Shugaba Tinubu lashe zaben shekarar 2027, ko dai a soke zabe a Najeriya ko Kuma d...
13/08/2025

WATA SABUWA: Dalilai biyu ne zasu hana Shugaba Tinubu lashe zaben shekarar 2027, ko dai a soke zabe a Najeriya ko Kuma da kan shi ya ce ba zai tsaya takarar ba; inji Ali Modu Sheriff

Shin Kun yarda da maganar sa?

YANZU-YANZU: Shugaban Tinubu ya tattauna ta wayar tarho da firaministan ƙasar Netherlands, H.E Dick Schoof a fadar gwamn...
13/08/2025

YANZU-YANZU: Shugaban Tinubu ya tattauna ta wayar tarho da firaministan ƙasar Netherlands, H.E Dick Schoof a fadar gwamnati.

13/08/2025

Shugaba Tinubu Kenan A Lokacin Da Ya Shigo Wurin Taron Majalisar Zartawa A Yau Laraba

YANZU-YANZU: Majalisar dokokin jihar Kano ta dakatar da shugaban ƙaramar hukumar Rano, Muhammad Naziru Ya'u, na tsawon w...
13/08/2025

YANZU-YANZU: Majalisar dokokin jihar Kano ta dakatar da shugaban ƙaramar hukumar Rano, Muhammad Naziru Ya'u, na tsawon wata 3.

Address

Zoo Road
Kano
700224

Telephone

+2348101029115

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Media posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share