Arewa Media

Arewa Media Arewa Media is a credible online news medium that focuses mainly on truthful, objective, fair and balance journalism.

We are always committed to bringing reliable information to our large and diverse subscribers from all parts of Nigeria and even beyond.

YANZU-YANZU: Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, Yanzu Haka Isa Fadar Shugaban Ƙasa Domin Ganawa Da Shugaba Tinubu Me zaku ce?
21/07/2025

YANZU-YANZU: Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, Yanzu Haka Isa Fadar Shugaban Ƙasa Domin Ganawa Da Shugaba Tinubu

Me zaku ce?

Tsohuwar ministar Jinƙai da Walwalar Al'umma Hajiya Sadiya Umar Farouk kenan a lokacin da ta fashe da kuka a wurin taron...
21/07/2025

Tsohuwar ministar Jinƙai da Walwalar Al'umma Hajiya Sadiya Umar Farouk kenan a lokacin da ta fashe da kuka a wurin taron addu'a ta musamman da aka shirya wa marigayi tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari a masallacin Ansaruddeen da ke unguwar Maitama a Abuja a jiya Lahadi.

TIRƘASHI: Gwamnan jihar Imo, Hope Uzodinma ya yi subutar baki a wajen jawabinsa inda ya yi kuskuren fadar "Allah ya jika...
21/07/2025

TIRƘASHI: Gwamnan jihar Imo, Hope Uzodinma ya yi subutar baki a wajen jawabinsa inda ya yi kuskuren fadar "Allah ya jikan tsohon shugaban kasa Bola..." kafin yayi sauri tunawa ashe "Buhari" zai fadi...

Lamarin ya faru ne a wajen wani taron bita kan kundin tsarin mulki da aka yi a Owerri. Ayau News ta ruwaito wannan subutar baki ya jawo wasu mahalarta taron s**a fashe da dariya.

Me zaku ce?

MUHAWARA: Kana Ɗaya Daga Cikin Waɗanda Zasu Sake Zaɓar Shugaba Tinubu Domin Yin Tazarce A Zaɓen 2027 ?
20/07/2025

MUHAWARA: Kana Ɗaya Daga Cikin Waɗanda Zasu Sake Zaɓar Shugaba Tinubu Domin Yin Tazarce A Zaɓen 2027 ?

DAƊUMI-ƊUMI: Ana shirin gudanar da zazzafar Zàñga-zàñgar nuna goyon baya ga 'yãɲ sanda a Shelkwatar 'yan sanda ta ƙasa.A...
20/07/2025

DAƊUMI-ƊUMI: Ana shirin gudanar da zazzafar Zàñga-zàñgar nuna goyon baya ga 'yãɲ sanda a Shelkwatar 'yan sanda ta ƙasa.

A cewar fitaccen ɗan Jarida, Omoyele Sowore, za'a gudanar da Zàñga-zàñgar ne a safiyar ranar Litinin a Shelkwatar 'yan sanda ta ƙasa dake Abuja, don yaƙi da take haƙƙin jami'an 'yan sanda.

Shin zaku shiga cikin zánga-zángár nuna goyon baya ga 'yan sanda a gobe ?

YANZU-YANZU: Gwamnan Katsina ya yi hadari a hanyar Daura zuwa Katsina  Rahotanni na nuna cewa ayarin motocin Gwamnan Jih...
20/07/2025

YANZU-YANZU: Gwamnan Katsina ya yi hadari a hanyar Daura zuwa Katsina

Rahotanni na nuna cewa ayarin motocin Gwamnan Jihar Katsina Umaru Dikko Radda sun gamu da hadarin mota a hanyarsu ta komawa Katsina daga Daura bayan ya kammala karbar gaisuwar margayi Buhari.

DA DUMI-DUMI: An garzaya da tsohon Gwamnan Kano Abdullahi Ganduje zuwa wani asibiti a birnin London ?Mai magana da yawun...
20/07/2025

DA DUMI-DUMI: An garzaya da tsohon Gwamnan Kano Abdullahi Ganduje zuwa wani asibiti a birnin London ?

Mai magana da yawunsa Salihu Yakasai ya tabbatar da cewa labarin da ake yadawa cewa tsohon Gwamnan yana cen yana jinya a wani asibiti dake London ba gaskiya bane.

Ana dai ta cece-kuce game da tsohon Gwamnan bayan rashin ganinsa a bainar jama’a ciki har da rashin halartar jana'iza ko gaisuwar margayi Buhari sannan kuma sai ziyarar da Shugaba Tinubu ya kai jihar Kano anan din ma ba a ga Ganduje ba lamarin da ya jawo ake rade-radin bashi da lafiya.

Me zaku ce?

JIN RA’AYIN JAMA’A: Idan kana ɗaya daga cikin ƴan Najeriya masu goyon bayan Tinubu ya saki Abba Kyari wanda gwamnatin Bu...
20/07/2025

JIN RA’AYIN JAMA’A: Idan kana ɗaya daga cikin ƴan Najeriya masu goyon bayan Tinubu ya saki Abba Kyari wanda gwamnatin Buhari ta tsãre a gidan Yari, (Prison), ka rubuta Free Abba Kyari a (Comment Section).

A Kafta....

Yariman Saudiyya da ya shafe shekaru 20 ya na bacci ya rãṣuBayan shafe sama da shekaru 20 ya na bacci sakamakon dogon su...
20/07/2025

Yariman Saudiyya da ya shafe shekaru 20 ya na bacci ya rãṣu

Bayan shafe sama da shekaru 20 ya na bacci sakamakon dogon suma da ya yi bayan wani mummunan hatsarin mota da ya yi, Yarima Alwaleed bin Khalid bin Talal, wanda mutane su ka fi sani da "Yariman Barci" ya rasu.

Mahaifin marigayin Yarima Khaled bin Talal bin Abdulaziz ne ya tabbatar da rasuwan ɗan nasa a shafukansa na sada zumunta.

Yarima Al-Waleed ya yi fama da matsalar zuban jini a kwakwalwarsa a shekarar 2005 bayan wani hatsarin mota da ya yi a lokacin da yake karatu a kwalejin soji da ke Landan.

Bayan afkuwar hatsarin, an kwantar da shi a asibitin “King Abdulaziz Medical City” da ke birnin Riyadh inda ya kasance a cikin dogon suma.

Iyayensa sun shafe shekaru 20 cikin addu'o'i tare da rashin karaya, da kuma ƙaunarsa har zuwa lokacin da Allah ya ɗauki rayuwarsa.

Karon Farko babban ɗan marigayi Dakta Idris Abdulaziz Dutse Tanshi, ya hau Munbarin mahaifinsa, shima yana da matakin Da...
20/07/2025

Karon Farko babban ɗan marigayi Dakta Idris Abdulaziz Dutse Tanshi, ya hau Munbarin mahaifinsa, shima yana da matakin Dakta, ana kiransa da suna Dakta AbdulAziz Dakta Idris Abdul Aziz.

Wane fata za ku yi masa?

Ina kira ga Tinubu ya taka wa ɗansa Seyi burki, ya daina zaƙewa kan harƙoƙin mulki, domin shekaru 8 na mulkin Buhari ban...
19/07/2025

Ina kira ga Tinubu ya taka wa ɗansa Seyi burki, ya daina zaƙewa kan harƙoƙin mulki, domin shekaru 8 na mulkin Buhari ban taɓa jin Yusuf ya yi magana ba sai bayan rasuwar mahaifinsa, Inji Farfesa Usman Yusuf

Me zaku ce ?

An Fara Aikin Samar Da Lantarki Mai Amfani Da Hasken Rana (Solar) A Fadar Shugaban ƘasaGwamnatin Tarayya ta fara aikin g...
19/07/2025

An Fara Aikin Samar Da Lantarki Mai Amfani Da Hasken Rana (Solar) A Fadar Shugaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya ta fara aikin gina tashar wutar lantarki (solar mini-grid) wanda darajarsa ta kai Naira biliyan 10 domin samar da wadataccciyar wutar lantarki ga fadar shugaban ƙasa da ke Asokoro.

Me zaku ce?

Address

Kano

Telephone

+2348101029115

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Media posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share