07/06/2026
Gwamna Fintiri Ya Yi Alhinin Rasuwar Masu Yi Wa Ƙasa Hidima (NYSC) Da Jami’in Soja Ɗaya Waɗanda S**a Rasa Rayukansu A Hatsarin Mota
Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ya bayyana alhininsa kan wani mummunan hatsarin mota da ya yi sanadin mutuwar wasu membobin hukumar masu yi wa ƙasa hidima, (NYSC) da wani jami’in soja a jihar.
A cikin wata sanarwa da Kakakin Gwamnan, Humwashi Wonosikou, ya fitar ranar Juma’a, Fintiri ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici da raɗaɗi, yana mai cewa mamatan sun rasa rayukansu ne yayin da suke yi wa ƙasarsu hidima, kamar yadda Arewa Media ta ruwaito.
Gwamnan ya miƙa saƙon ta’aziyya ga iyalan mamatan, Hukumar NYSC, da gwamnatin da al’ummar JiharnKaduna, inda aka ce wasu daga cikin masu yi wa ƙasa hidimar s**a fito.
Ya ce sadaukarwar da matasan da jami’in sojan s**a yi wajen bautawa ƙasa ba za a manta da ita ba, tare da tabbatar da cewa gwamnatin Adamawa tana tare da waɗanda wannan rashi ya shafa.
Fintiri ya kuma yi addu’ar Allah Ya gafarta wa mamatan tare da bai wa iyalansu da sauran masu alaka da su juriyar jure wannan babban rashi. Haka kuma ya umarci hukumomin da abin ya shafa su haɗa kai da NYSC da hukumomin soji domin ba iyalan mamatan duk tallafin da ya dace.