Arewa Media

Arewa Media Arewa Media is a credible online news medium that focuses mainly on truthful, objective, fair and balance journalism.

We are always committed to bringing reliable information to our large and diverse subscribers from all parts of Nigeria and even beyond.

"Bai kamata a haɗa Malam Haruna Ɗorayi cikin zugar mutane 3,000 da aka yiwa auren gata ba. Kyanta a yi ma sa aure na mus...
09/08/2026

"Bai kamata a haɗa Malam Haruna Ɗorayi cikin zugar mutane 3,000 da aka yiwa auren gata ba. Kyanta a yi ma sa aure na musamman, saboda ƙaddarar da ta same shi ta musamman ce. Amma sai ga shi an siyasantar da shi har da jar hula mai ɗauke da tambarin Omologo."- In ji Yakubu M Kumo.

Me za ku ce?

‎ILIMI KOGI: "Ƙarya ne zargi ba ya kashe aure. Wannan magana babu ita a addini. Babu abin da ke kashe aure sai saki. Akw...
09/08/2026

‎ILIMI KOGI: "Ƙarya ne zargi ba ya kashe aure. Wannan magana babu ita a addini. Babu abin da ke kashe aure sai saki.

Akwai sahabin da ya zo ya sami Manzon Allah S.A.W ya ce masa matata tana bin maza kuma ba shakka na tabbatar da hakan, sai Manzon Allah S.A.W Ya ce masa sake ta sai ya ce ina son ta, sai Manzon Allah S.A.W ya ce riƙe abar ka. Shi ba ma zargi yake ba ya tabbatar. Dan haka maganar zargi yana kashe aure ba nassi ba ne magana ce ta molanka da ake faɗa a ƙasar Hausa". In ji shaik Lawan Triumph.

Me zaku ce?

Bode George Har Yanzu Yana Fushi Ne Kan Rashin Zama Shugaban PDP, Sannan Tunda Aka Koma Mulkin Siyasa A 1999 Bai Taba Ka...
09/08/2026

Bode George Har Yanzu Yana Fushi Ne Kan Rashin Zama Shugaban PDP, Sannan Tunda Aka Koma Mulkin Siyasa A 1999 Bai Taba Kawowa Jam'iyyar Wata Nasara Ba A Zabe A Jiharsa Ta Legas, Inji Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya ce Cif Bode George, tsohon Mataimakin Shugaban Jam’iyyar PDP na Ƙasa, har yanzu yana fushi ne saboda an hana shi zama Shugaban Jam’iyyar PDP na Ƙasa.

Wike ya ce ba ya nadamar matakin da aka ɗauka na dakile burin Bode George na shugabancin jam’iyyar, yana mai cewa an hana shi ne saboda lokacin baiwar shugabancin ya koma yankin Kudu maso Kudu.

Ministan ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da Babban Mataimakinsa na Musamman kan Sadarwar Jama’a da Kafofin Sadarwar Zamani, Lere Olayinka, ya fitar ranar Asabar.

Wike ya ce rashin gamsuwar Bode George ta ƙara tsananta ne sakamakon fitowar Deji Doherty a matsayin wani jigo mai tasiri a shugabancin PDP a Jihar Legas, wanda a cewarsa Bode George ba ya son ganin yana jagorantar jam’iyyar a jihar.

Ya kuma bayyana cewa bayan babban taron jam’iyyar PDP na ƙasa, lokacin yana gwamnan Jihar Rivers, ya ziyarci gidan Bode George da ke Maitama, Abuja, domin sasanta tsakaninsu.

Wike ya ce duk da irin mukamai da tasirin da Bode George ya samu a cikin PDP, bai iya samar wa jam’iyyar wata gagarumar nasara a zaɓe a Jihar Legas ba tun shekarar 1999.

Ministan ya yi amfani da sakamakon zaɓukan 2019 da 2023 a matsayin misali, yana mai cewa a rumfar zaɓe ta Bode George a zaɓen shugaban ƙasa na 2019, APC ta samu ƙuri’u 84, yayin da PDP ta samu 40. A shekarar 2023 kuwa, ya ce PDP ta samu ƙuri’u huɗu a rumfar da aka danganta da shi.

Wike ya jaddada cewa shugabancin jam’iyyar siyasa bai kamata ya dogara da suna, mukami ko kasancewa cikin waɗanda s**a kafa jam’iyya ba, sai dai abin da mutum zai iya kawo wa jam’iyyar musamman wajen samun nasarar zaɓe.

A halin da ake ciki, reshen PDP na Jihar Legas ya mayar wa Wike martani, inda ya soki kalaman nasa kan Bode George tare da zarginsa da tsoma baki cikin harkokin jam’iyyar a jihar.

09/08/2026

TIRƘASHI: Duk Wanda Yake Son Ya Hadu Da Allah Lafiya, Rufin Asirinsa Shine Ya Zabi Tinubu Ya Zarce ~ Cewar Shugaban Annahadatul Kadiriyya Al-Muhammadiyya, ~Imam Sadiqu Inuwa

Me zaku ce?

‎"Ko Kana So Ko Ba Ka So Kano Ita Ce Jigo; A Duk Najeriya A Kano Ne Kaɗai Za Ka Ga Mutane Bayan Sallar Asuba Sun Fita Su...
08/08/2026

‎"Ko Kana So Ko Ba Ka So Kano Ita Ce Jigo; A Duk Najeriya A Kano Ne Kaɗai Za Ka Ga Mutane Bayan Sallar Asuba Sun Fita Suna Zikiri A Kan Hanyarsu Ta Zuwa Kasuwa. Allah Ya Yi Wa Garin Wata Albarka Ta Daban", In Ji Sadiq Sani Sadiq A Cikin Shirin Podcast Na Dokin Ƙarfe TV.

Me zaku ce?

‎Alummar Jihar Nasarawa sunyi murna da ayyukan Shugaba Tinubu na Raya Kasa.‎‎Tinubu na shirin Sauya tsarin arewa daga Du...
08/08/2026

‎Alummar Jihar Nasarawa sunyi murna da ayyukan Shugaba Tinubu na Raya Kasa.

‎Tinubu na shirin Sauya tsarin arewa daga Duhu zuwa Haske.

‎ A yayin da ake ci gaba da bayyana ayyukan raya ƙasa da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke aiwatarwa a sassan Najeriya, wasu wakilan kafafen yaɗa labarai sun isa Jihar Nasarawa domin ganin ayyukan da idonsu tare da tantance yadda suke tasiri ga rayuwar al’ummar jihar.

‎Ziyarar ta bai wa wakilan kafafen yaɗa labarai damar zagayawa wasu muhimman wurare da ake aiwatar da manyan ayyukan more rayuwa, da wakilan Fadar Shugaban kasa, Karkashin Hadimin Shugaba Tinubu, Bayo Onanuga, da Hadimin Shugaba Tinubu a bangaren kafafen yada labarai, Abdulaziz-abdulaziz, da Dada Olusegun, da sauran tawagar su.
‎A ziyarci masana’antun bunƙasa sana’o’in hannu a ƙarƙashin gwamnatin Shugaba Tinubu, tare da haɗin gwiwar gwamnatin Jihar Nasarawa ƙarƙashin jagorancin Gwamna jihar, Injiniya Abdullahi A. Sule.

‎Manyan ayyukan more rayuwa
‎Daga cikin wuraren da tawagar ta ziyarta akwai katafariyar Sakatariyar Gwamnatin Jihar Nasarawa, wadda ke daga cikin manyan gine-ginen dgwamnati da ake amfani da su wajen inganta ayyukan gudanar da mulki da samar da yanayi mai kyau ga ma’aikatan gwamnati da al’umma.

‎Haka kuma, tawagar ta duba wasu manyan hanyoyi, ciki har da hanyar Shabu, wadda ke da muhimmiyar alaƙa da zirga-zirgar jama’a da harkokin kasuwanci zuwa wasu sassan jihar da kuma hanyar Taraba.

‎Wadannan ayyuka, a cewar mazauna yankin, suna taimakawa wajen rage wahalhalun sufuri tare da buɗe ƙofofin kasuwanci da zuba jari.

‎Wata muhimmiyar cibiyar da tawagar ta ziyarta ita ce wuraren koyar da walda da sauran sana’o’in hannu, waɗanda aka samar domin bai wa matasa damar samun sana’a da dogaro da kansu.

An bayyana cewa irin waɗannan shirye-shirye na da matuƙar muhimmanci wajen rage zaman kashe wando da kuma bai wa matasa damar zama masu amfani ga kansu, iyalansu da al’umma.

Shugaba Tinubu, tare da haɗin gwiwar gwamnatin Jihar Nasarawa, na ƙoƙarin ganin an ƙara saka jari a fannin ƙarfafa matasa da samar da hanyoyin dogaro da kai.

Tawagar ta kuma kai ziyara wasu yankunan da ambaliyar ruwa ta taɓa, inda aka gudanar da ayyukan gyaran manyan kwalbatin ruwa da magudanan ruwa domin rage barazanar ambaliya da kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Daga cikin wuraren da aka duba akwai yankin Hanyar Lafiya zuwa Doma, da kuma Gadar Kilema a cikin birnin Lafiya, inda ake ganin ayyukan gyaran ababen more rayuwa sun taimaka wajen inganta zirga-zirga da sauƙaƙa rayuwar mazauna yankin.

‎Mazauna yankunan da tawagar ta ziyarta sun bayyana farin cikinsu kan ayyukan da ake gudanarwa, inda s**a ce inganta hanyoyi, magudanan ruwa, samar da sana’o’i da sauran ayyukan more rayuwa na taimakawa wajen sauƙaƙa rayuwarsu.

Wasu daga cikin mazauna yankin sun ce suna fatan ayyukan za su ci gaba da yaɗuwa zuwa sauran sassan jihar domin ƙarin jama’a su amfana.
‎Arewa na fuskantar sabon salo na ci gaba?

Abin da tawagar ta gani a yayin ziyarar ya nuna cewa wasu yankunan Arewa na samun ƙarin ayyukan more rayuwa da shirye-shiryen bunƙasa tattalin arziki.

Masu goyon bayan gwamnatin Shugaba Tinubu na kallon waɗannan ayyuka a matsayin wani ɓangare na shirin sabunta abubuwan more rayuwa da ƙarfafa tattalin arzikin yankunan Arewa, yayin da suke bayyana burin ganin Arewa ta samu ci gaba mai ɗorewa har ta kai matsayin manyan biranen duniya.

A Nasarawa, abin da ya fi bayyana shi ne yadda haɗin gwiwar gwamnatin tarayya da gwamnatin jihar ke ƙoƙarin mayar da wasu muhimman ayyukan raya ƙasa zuwa abubuwan da jama’a za su iya gani da idonsu.

MAHAIFIN GWARZON DAN KWALLON DUNIYA, LIONEL  MESSI YA RAȘU A YAUJorge Messi, mahaifin fitaccen ɗan wasan ƙwallon ƙafa Li...
08/08/2026

MAHAIFIN GWARZON DAN KWALLON DUNIYA, LIONEL MESSI YA RAȘU A YAU

Jorge Messi, mahaifin fitaccen ɗan wasan ƙwallon ƙafa Lionel Messi kuma wakilinsa na tsawøɲ lokaci, ya rãșu yana da shekaru 68.

YANZU-YANZU: Hadimi Na Musamman Ga Isah Ali Pantami Ya Watsar Da Tafiyar Pantami Ya Koma Tsagin Jamilu Isyaku Gwamna, ‎‎...
08/08/2026

YANZU-YANZU: Hadimi Na Musamman Ga Isah Ali Pantami Ya Watsar Da Tafiyar Pantami Ya Koma Tsagin Jamilu Isyaku Gwamna,

‎Hon. Muhammad Buhari Ɗalhatu, mai ba Farfesa Isa Ali Pantami shawara kan jagorancin matasa da hulɗa da al’umma, ya yi murabus daga muƙaminsa tare da bayyana goyon bayansa ga ɗan takarar gwamna na APC a Gombe, Dr. Jamil Isyaku Gwamna.

‎Ɗalhatu ya ce zai ci gaba da kasancewa cikin APC tare da goyon bayan jam’iyyar a zaɓen 2027, kamar yadda Arewa Media ta ruwaito.

‎Matakin nasa ya zo ne bayan wasu jiga-jigan da aka bayyana a matsayin makusantan Pantami, ciki har da Affan Buba Abuya, Sunusin Gombe da Ɗahiru Saidu Nafaɗa, sun koma goyon bayan Jamil Gwamna.

‎Mai magana da yawun Gwamna, Ibrahim Sani Shawai, ya ce sauye-sauyen na nuna canjin yanayin siyasar Gombe yayin da ake tunkarar zaɓen 2027.

‎Jamilu Gwamna ya yi maraba da Ɗalhatu, yana mai cewa makomar jihar na buƙatar haɗin kai, ƙwarewa da gogewa.

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN:Wannan Baiwar Allah Mai Suna Walida Ta Rãșu Wajen Haihuwa, Inda Ita Da Ƴan Biyun Da T...
08/08/2026

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN:

Wannan Baiwar Allah Mai Suna Walida Ta Rãșu Wajen Haihuwa, Inda Ita Da Ƴan Biyun Da Ta Haifa Duk Sun Rãșu

Allah Ya gafarta mata.

DAƊUMI-ƊUMI: Shugabannin Ɗariƙar Tijjaniyya na wasu ƙasashen Afirka da s**a haɗa da: Najeriya, Aljeriya da Senegal sun z...
07/08/2026

DAƊUMI-ƊUMI: Shugabannin Ɗariƙar Tijjaniyya na wasu ƙasashen Afirka da s**a haɗa da: Najeriya, Aljeriya da Senegal sun ziyarci Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja a wannan rana ta Juma'a, kamar yadda Arewa Media ta ruwaito.

Tawagar ta haɗa da: Sheikh Ibrahim Ɗahiru Bauchi, Babban Khalifan Tijjaniyya na Aljeriya Sheikh Ali Al-Arabi, da malamin addinin Musulunci daga Senegal, Sheikh Muhammad Al-Mahy.

Address

Zoo Road
Kano
700224

Telephone

+2348101029115

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Media posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share