Arewa Media

Arewa Media Arewa Media is a credible online news medium that focuses mainly on truthful, objective, fair and balance journalism.

We are always committed to bringing reliable information to our large and diverse subscribers from all parts of Nigeria and even beyond.

Gwamna Fintiri Ya Yi Alhinin Rasuwar Masu Yi Wa Ƙasa Hidima (NYSC) Da Jami’in Soja Ɗaya Waɗanda S**a Rasa Rayukansu A Ha...
07/06/2026

Gwamna Fintiri Ya Yi Alhinin Rasuwar Masu Yi Wa Ƙasa Hidima (NYSC) Da Jami’in Soja Ɗaya Waɗanda S**a Rasa Rayukansu A Hatsarin Mota

Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ya bayyana alhininsa kan wani mummunan hatsarin mota da ya yi sanadin mutuwar wasu membobin hukumar masu yi wa ƙasa hidima, (NYSC) da wani jami’in soja a jihar.

A cikin wata sanarwa da Kakakin Gwamnan, Humwashi Wonosikou, ya fitar ranar Juma’a, Fintiri ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici da raɗaɗi, yana mai cewa mamatan sun rasa rayukansu ne yayin da suke yi wa ƙasarsu hidima, kamar yadda Arewa Media ta ruwaito.

Gwamnan ya miƙa saƙon ta’aziyya ga iyalan mamatan, Hukumar NYSC, da gwamnatin da al’ummar JiharnKaduna, inda aka ce wasu daga cikin masu yi wa ƙasa hidimar s**a fito.

Ya ce sadaukarwar da matasan da jami’in sojan s**a yi wajen bautawa ƙasa ba za a manta da ita ba, tare da tabbatar da cewa gwamnatin Adamawa tana tare da waɗanda wannan rashi ya shafa.

Fintiri ya kuma yi addu’ar Allah Ya gafarta wa mamatan tare da bai wa iyalansu da sauran masu alaka da su juriyar jure wannan babban rashi. Haka kuma ya umarci hukumomin da abin ya shafa su haɗa kai da NYSC da hukumomin soji domin ba iyalan mamatan duk tallafin da ya dace.

"Wayata ce kuma data ta ce, dan haka na dakata da tallan Tinubu tunda ni ba mahaukaci ba ne."- In ji Abdullahi Junaid Ad...
07/06/2026

"Wayata ce kuma data ta ce, dan haka na dakata da tallan Tinubu tunda ni ba mahaukaci ba ne."- In ji Abdullahi Junaid Adam.

Me za ku ce?

MUHAWARA: Tsakanin mulkin Buhari da na Tinubu, wanne ne talaka ya fi samun saukin rayuwa?
07/06/2026

MUHAWARA: Tsakanin mulkin Buhari da na Tinubu, wanne ne talaka ya fi samun saukin rayuwa?

Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Barista Nyesom Wike, tare da matarsa,  Babbar Mai Shari’a Suzzette Nyesom-Wike, su...
06/06/2026

Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Barista Nyesom Wike, tare da matarsa, Babbar Mai Shari’a Suzzette Nyesom-Wike, sun halarci bikin yaye dalibai karo na 36 na Jami’ar Port Harcourt, inda ya gabatar da lacca, a yau Asabar.

Ministan ya yi amfani da wannan dama wajen bayyana manyan ayyukan ci gaban ababen more rayuwa da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta aiwatar.

INNALILLAH WA'INNA ILAIHI RAJI'UN Allah Ya yi wa Alhaji Adamu Ibrahim Getso, tsohon MD na gidan Radio Kano rasuwa. Allah...
06/06/2026

INNALILLAH WA'INNA ILAIHI RAJI'UN

Allah Ya yi wa Alhaji Adamu Ibrahim Getso, tsohon MD na gidan Radio Kano rasuwa.

Allah Ya gafarta masa.

A Zaɓen 2027 za mu zazzaga wa Tinubu ruwan ƙuri'u a Arewa Maso Gabas a matsayin sakayya kan aikin titin Gombe zuwa Biu d...
06/06/2026

A Zaɓen 2027 za mu zazzaga wa Tinubu ruwan ƙuri'u a Arewa Maso Gabas a matsayin sakayya kan aikin titin Gombe zuwa Biu da ya amince a yi mana, In Ji Sanata Muhammad Ali Ndume.

SUBHALALLAH: Babban Malami a Najeriya, Sheikh Muhammad Nuru Khalid ya na fama da rashin lafiya a kasar Saudiyya bayan ka...
05/06/2026

SUBHALALLAH: Babban Malami a Najeriya, Sheikh Muhammad Nuru Khalid ya na fama da rashin lafiya a kasar Saudiyya bayan kammala aikin hajjin bana na 2026.

Al'ummar Musulmai a saka Malam cikin addu'a.

"Yadda komai ya tabarbare a kasar nan, yan Najeriya daga ko wane bangare s**a fusata, ina kyautata zaton Tinubu na uku z...
05/06/2026

"Yadda komai ya tabarbare a kasar nan, yan Najeriya daga ko wane bangare s**a fusata, ina kyautata zaton Tinubu na uku zai zo a zabe mai zuwa" In ji Barrista Abba Hikima.

Me za ku ce?

Ku Haɗa Kuɗi Ku Sayi Makamai Domin Kare Kanku Daga Harin Ƴan Bindiga, Saƙon Sarkin Kebbin Argungu Ga Al'ummarsaMe zaku c...
05/06/2026

Ku Haɗa Kuɗi Ku Sayi Makamai Domin Kare Kanku Daga Harin Ƴan Bindiga, Saƙon Sarkin Kebbin Argungu Ga Al'ummarsa

Me zaku ce?

Address

Zoo Road
Kano
700224

Telephone

+2348101029115

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Media posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share