GY Times Hausa

GY Times Hausa Idan rana ta fito, tafin hannu baya kareta, GY Times Hausa ta shirya domin sanar daku zafafan Labaran duniya , wasanni, nishadi, kimiyya da fasaha.

Domin sanin halin da duniya ke ciki,kasance da wannan shafin jarida na A.M.T Hausa TV ..

01/06/2025

Nan da 'yan kwanaki kaɗan ne alhazai za su fara aikin Hajji bana - kuma yayin da mahajjata a duk faɗin duniya ke shirye-shiryen tafiya zuwa fara fita wuraren ibadun a Saudiyya, kusan abu ɗaya ne a zuciyar kowa: yaya zafi zai kasance a wannan shekara, kuma me za a iya yi don sauƙaƙa wa mahajjata?

Shekaru da dama kenan aikin Hajji yake zuwa dai-dai da lokacin tda ake tsananin zafi a kasar Saudiyya, kuma wannan shekarar ma haka lamarin yake. Kamfanin dillancin labaran Saudiyya ya rawaito cibiyar kula da yanayi ta kasar, ta yi hasashen yanayi mai tsananin zafi a wurare masu tsarki a bana, inda za a iya samun zafi tsakanin ma'auni 40 ° C zuwa 47 ° C.

A bara yanayin zafin ya kai ma'auni 51.8°C, wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane sama da 1,000, k**ar yadda alƙaluman Saudiyya s**a nuna.

Yayin da ake sa ran za a sake yin zafi a Hajjin 2025, ga yadda jami'an Saudiyya ke ƙoƙarin kare mahajjata daga tsananin zafin da ake yi a wannan lokaci.

Kungiyar 'Yan Jaridu ta Arewa Online Journalists Forum Ta Zabi Alhaji Sani Ahmed a Matsayin Sakataren ƘasaKungiyar 'yan ...
01/06/2025

Kungiyar 'Yan Jaridu ta Arewa Online Journalists Forum Ta Zabi Alhaji Sani Ahmed a Matsayin Sakataren Ƙasa

Kungiyar 'yan jaridu ta Arewa mai suna Arewa Online Journalists Forum (AOJF) ta sanar da zaben Alhaji Sani Ahmed a matsayin sabon Sakataren Ƙasa na kungiyar.

Zaben Alhaji Sani Ahmed ya biyo bayan amincewa da kwarewarsa da jajircewarsa wajen ganin kafafen yada labarai na yanar gizo a Arewa suna tafiya bisa gaskiya, rikon amana da ingantaccen bincike.

Shugaban kungiyar, Malam Barrah Almadany, ya bayyana cewa zaben Alhaji Sani Ahmed wani bangare ne na sabbin matakan da kungiyar ke dauka domin ƙarfafa tafiyar da shirye-shiryen da s**a shafi horar da matasa, yaƙi da labaran ƙarya, da kuma inganta martabar aikin jarida a yankin Arewa da ma Najeriya baki ɗaya.

Alhaji Sani Ahmed ya gode wa mambobin kungiyar bisa amincewa da shi, inda ya sha alwashin yin aiki tukuru tare da sauran shugabannin domin dorewar cigaba da bunkasar kungiyar.

Arewa Online Journalists Forum ta kasance daya daga cikin kungiyoyin jaridu na yanar gizo da ke taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da sahihanci da gaskiya a harkar yada labarai a Arewacin Najeriya.

01/06/2025

Jan Hankali ga rundunar yansandan Nigeria

Daga Nasiru Salisu Zango

Wannan hoto da kuke gani dake nuna wasu matasa biyu da yansandan Nigeria ke Neman su ruwa a jallo ba kayan kowa s**a sata ba kuma basu yiwa kowa komai ba, Babban laifin su bai wuce kasancewar su jajirtattun matasa Masu neman abin kan su ba ta hanyar da dokar Nigeria ta tanada, sai kuma watakila dan sun kasance Masu karamin karfi da s**a ki yadda wani babban kamfani yazo har kasar su yana kokarin murkushe su ba.

Fiye da shekara kenan wani babban kamfani na yan asalin India yayi karar Wadannan matasa wadanda sune Suke da mallakin kamfanin ganyen shayin Y and Z kan cewar sun Satar masa samfurin ganyen shayin su( k**ar yadda Coca Cola s**a taba yin karar Pop Cola)

amma da aka bincika a ofishin trade mark sai aka tabbatar da cewar Y and Z sun bi duk Wata ka’ida hasali Ma hukumar ce ta basu raiista da wannan suna da tambarin da suke amfani da shi

amma abin takaici Wadannan indiyawa wadanda ke ganin suna da karfi suna ta biye biye kan lallai sai sun ci zarafin Wadannan matasa idan har basu Yi saranda sun daina wannan Sana’a ba.

Tun wancan lokaci ake ta kai kawo har sun fara gajiyar da matasan, amma abin mamaki wai kare da tallan tsire jami’ai na ta basu kariya da kokarin muzgunawa Wadannan matasa ta hanyar Yi musu barazana irin wannan.
Kun san dai yadda me Karfi ke fin kwarjin a idon galiban Mahukuntan kasar Nan

Ina rokon Babban sufeton yansandan kasar nan IGP Kayode Egbetokun da ya shiga maganar nan da Kansa domin tabbatar da adalci da kaucewa yin amfani da karfin iko wajen muzgunawa Masu karamin karfi.

Nayi mamakin ganin yadda Jami’an yansanda s**a Yi uwa da makarbiyya cikin wannan lamari tare da yada hotunan Wadannan matasa kai kace abokan Turji ne, kullum Kira ake ga matasa su k**a Sana’a amma kuma babu wani cikakken tsari na kare mutumcin ka,Ban sani ko dan matasan yan arewa ne tun da dai wani lokacin an fi mai da su karkatacciyar kuka.

Ina Kira ga mai girma DSP Barau I Jibril da sauran yan majalisu da ma duk wani me hali da yayi amfani da matsayin sa wajen taimakon Wadannan matasa yan Kano.

Idan baku mance ba k**ar yadda na faro a farko kamfani Pop Cola ma ba Dan Masu shi gwaskaye ba ne da yanzu Suma Ana Fama da su, domin yanzu ko kana da gaskiya Akan iya amfani da iko wajen muzguna maka har kaji cewar Ma ka hakura da kasuwnacin ka kawai saboda wani yana ganin cewar baka isa kayi irin nasa ba.
Dan Allah yan uwa ku taimaka da Neman hakkin wadannan matasa ta hanyar Kira ga IGP da Majalisun kasar nan da su shiga maganar domin Neman halak ba laifi bane.

With Adam A Zango – I just got recognised as one of their top fans! 🎉
01/06/2025

With Adam A Zango – I just got recognised as one of their top fans! 🎉

Arewa Online Journalists Forum Za Ta Ƙaddamar da Yaƙi da Yaɗuwar Labarun Ƙarya a ArewaƘungiyar Arewa Online Journalists ...
31/05/2025

Arewa Online Journalists Forum Za Ta Ƙaddamar da Yaƙi da Yaɗuwar Labarun Ƙarya a Arewa

Ƙungiyar Arewa Online Journalists Forum ta bayyana shirinta na ƙaddamar da gagarumin aiki na yaƙi da yaɗuwar labarun ƙarya a yankin Arewa da ma Najeriya baki ɗaya. Wannan mataki na zuwa ne domin kare sahihancin labarai da kuma tabbatar da aikin jarida mai inganci da amana.

Shugaban ƙungiyar, Malam Barrah Almadany, ya bayyana cewa yaɗuwar labarun ƙarya ta zama barazana ga zaman lafiya, haɗin kan al'umma, da sahihancin kafafen watsa labarai. “Labarun ƙarya suna haddasa ruɗani, rikici da rashin amincewa da kafafen jarida. Wannan shi ya sa muka ɗauki alhakin ɗaukar matakin da ya dace,” in ji shi.

Shirin da za a ƙaddamar nan gaba kaɗan zai haɗa da:

Taron bita da horo na musamman ga ƴan jarida, musamman matasa da masu aiki a kafafen yanar gizo,

Wayar da kan al’umma game da illolin yaɗa labarun ƙarya,

Haɗin gwiwa da ƙungiyoyi masu zaman kansu da hukumomin gwamnati don ƙarfafa gaskiya a cikin labarai,

Fadakarwa ta amfani da harsunan gida domin isar da sahihan bayanai cikin sauƙi.

Malam Barrah ya ce Arewa Online Journalists Forum za ta tsaya tsayin daka wajen ganin an kawar da yaɗuwar ƙarya, tare da horar da mambobinta yadda za su rika tantance gaskiyar labarai kafin watsawa.

A karshe, ya yi kira ga duk masu ruwa da tsaki a fannin jarida da su mara wa wannan yunƙuri baya, domin tabbatar da cewa al’umma na samun bayanai masu inganci da aminci.

Sa Hannu : Sakataren kungiya na kasa : Sani Ahmed

Rashin tsoron jahar katsina kaso 70% cikin 100% laifin Al'umma garine : Gwamna Umar Dikko Raddainda ya bayyana cewa bawa...
30/05/2025

Rashin tsoron jahar katsina kaso 70% cikin 100% laifin Al'umma garine : Gwamna Umar Dikko Radda
inda ya bayyana cewa bawai kawai Yan ta'adda bane matsala, Amma masu basu bayanan sirri dasuke zagaye da Al'umma acikin gari,

Yanxu matsalal bawai kawai mutanen dasuke cikin jeji bane, mutanen gari masu Basu bayanan sirri, Wanda suke kaiwa Yan ta'adda kayan abinci, maganun nuka, dasauran Abubuwan bukatu cikin daji,

Gwamna Dikko yakara dacewa idan bamuyi maganin masu bada bayanan sirri nacikin muba, bazamuyi nasara awannan fadan ba, Kuma nauyine daya rataya awuyan kowa domin muga mun bayyana masu irin wan nan hali acikin mu.
Kamar yadda jaridar ~ vanguard rawaito

Mayu 29: Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Arewa Online ta Aika Saƙon Gaisuwa ga Ƙasa, Ta Ƙara Jaddada Kudurinta ga Yankin ArewaYa...
30/05/2025

Mayu 29: Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Arewa Online ta Aika Saƙon Gaisuwa ga Ƙasa, Ta Ƙara Jaddada Kudurinta ga Yankin Arewa

Yayinda Najeriya ke bikin ranar Democracy Day da cika shekaru na mulkin farar hula a yau, 29 ga Mayu, Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Arewa (Arewa Online Journalists Forum - AOJF) ta aike da saƙon gaisuwa mai cike da ƙauna ga daukacin ‘yan ƙasa, musamman ga al’ummar Arewa.

A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Laraba, ƙungiyar ta yaba da juriyar ‘yan Najeriya, da haɗin kai da kuma ruhin dimokuraɗiyya da suke nunawa, tare da kira ga kowa da kowa da ya ci gaba da kasancewa da bege da kuma kishin ƙasa wajen gina Najeriya mai ɗorewa.

“Ranar 29 ga Mayu, ba kawai biki ba ne na dimokuraɗiyya; tana tunatar da mu nauyin da ya rataya a wuyar kowa wajen gina ƙasa mafi kyau. Muna girmama jaruntakar ‘yan Najeriya daga kowane yanki, musamman mutanen Arewa masu daraja, waɗanda ke ci gaba da tsayawa kan gaskiya, ɗa’a da kishin ƙasa duk da ƙalubale da dama,” in ji ƙungiyar.

Ƙungiyar ta kuma jaddada muhimmancin kafafen yaɗa labarai masu ‘yanci, aikin jarida na gaskiya, da kuma ƙarfafa ‘yan ƙasa wajen shiga cikin harkokin ƙasa, musamman a Arewa, a matsayin hanyoyi na sanya shugabanni su zama masU riko da gaskiya, da kuma ƙarfafa tushen dimokuraɗiyya a ƙasar.

“Muna sake tabbatar da kudurinmu na amfani da dandalinmu wajen inganta gaskiya, ba da dama ga marasa murya, da kuma tallafa wa ci gaba a Arewa da ma Najeriya baki ɗaya.”

Ƙungiyar ta kuma yi kira ga shugabanni a kowane mataki da su fifita tsaro, ilimi, ƙarfafa matasa, da bunƙasa tattalin arziki, musamman a cikin al’ummomin da ba su da isasshen kulawa a Arewacin ƙasar.

Yayinda ƙasa ke tunani kan tafiyar dimokuraɗiyya da ci gaban da aka samu, AOJF ta bukaci ‘yan Najeriya da su ci gaba da jajircewa wajen neman zaman lafiya, haƙuri da kuma shugabanci mai haɗin kai, tana mai jaddada cewa makomar Najeriya na hannun kowane ɗan ƙasa.

Sa Hannun : Sakataren kungiyar na Kasa : Sani Ahmed

Shugaba Tinubu ya ce sauye-sauyen tattalin arzikinsa suna tasiri a dai-dai lokacin da farashin kayan masarufi ke kara ts...
30/05/2025

Shugaba Tinubu ya ce sauye-sauyen tattalin arzikinsa suna tasiri a dai-dai lokacin da farashin kayan masarufi ke kara tsada a Najeriya.

A yayin da yunwa ke kara k**ari a Gaza, tarin mutane sun kutsa cikin wani rumbun kayan abinci na Majalisar Dinkin Duniya...
29/05/2025

A yayin da yunwa ke kara k**ari a Gaza, tarin mutane sun kutsa cikin wani rumbun kayan abinci na Majalisar Dinkin Duniya da ke Deir Al Balah domin daukar kayan tallafi. Hukumar Abinci ta Duniya (WFP) ta bayyana cewa an tanadi kayan ne domin rabawa, sai dai an ruwaito cewa aƙalla mutum biyu sun mutu yayin rububin dibar abincin, mutane da dama sun jikkata.

Wannan lamari yana nuna yadda halin jin kai ke kara tabarbarewa a Zirin Gaza, inda kusan kashi ɗaya cikin biyar na al'umma ke fuskantar yunwa da ka iya kashe rai, bayan makonni da dama da aka shafe ba tare da isasshen tallafi ba.

HOTO📸 The National

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when GY Times Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category