31/12/2025
Ina Sake Jaddada Tsayuwa Ta Da Ci gaba Da Bada Hadin Kai Da biyayya Ga Tafiyar Darikar Kwankwasiyya -Maryam A Hamisu
Ni, Maryam A. Hamisu, shugabar gidauniyar (CEO) Maryam A. Hamisu Development Foundation, yar asalin karamar hukumar Garun Malam a jihar Kano ina sake bayyana duniya a fili kuma ba tare da shakka ba tsayin daka na, hadin kai na, da cikakkiyar biyayya ta ga tafiyar siyasar Kwankwasiyya da kuma jagora, Mai Girma Dr. Rabiu Musa Kwankwaso, wanda nake dauka a matsayin jagorana kuma uban gidana a siyasa.
Shiga ta cikin tafiyar Kwankwasiyya ya samo asali ne daga akida da manufofi na adalci, ci gaban al’umma, inganta ilimi, da kula da talakawa wadannan duk suna da nasaba ta kai tsaye da hangen nesa da manufofin jin kai na gidauniyata.
Ina sake tabbatar da cewa ina tsaye daram tare da Dr. Rabiu Musa Kwankwaso, ba tare da la’akari da duk wani sauyin siyasa, matsin lamba, ko wani hali da zai taso ba. Biyayya ta da goyon baya na gare shi ba za su gushe ba, ba yau ba, ba gobe ba. Ban fice ba, kuma ba ni da niyyar ficewa daga darkar Kwankwasiyya a kowane lokaci.
Wannan matsaya ta fito ne daga zuciyata da akidata, ba don anfani na wucin gadi ba; daga amanna da biyayya, ba don yanayi ba; kuma daga gaskiya, ba tare da sulhu ko sassauci ba.
Ina tare da Kwankwasiyya cikin hadin kai, manufa, da jajircewa, kuma zan ci gaba da bayar da gudummawa mai kyau domin cimma muradun tafiyar, don ci gaban Jihar Kano da kasa baki daya.
A bayyane yake cewa tafiyata ta siyasa ba ta canza ba, kuma biyayya ta na nan daram. Kwankwasiyya har abada.