GY Times Hausa

GY Times Hausa Idan rana ta fito, tafin hannu baya kareta, GY Times Hausa ta shirya domin sanar daku zafafan Labaran duniya , wasanni, nishadi, kimiyya da fasaha.

Domin sanin halin da duniya ke ciki,kasance da wannan shafin jarida na A.M.T Hausa TV ..

Ina Sake Jaddada Tsayuwa Ta Da Ci gaba Da Bada Hadin Kai Da biyayya Ga Tafiyar Darikar Kwankwasiyya -Maryam A HamisuNi, ...
31/12/2025

Ina Sake Jaddada Tsayuwa Ta Da Ci gaba Da Bada Hadin Kai Da biyayya Ga Tafiyar Darikar Kwankwasiyya -Maryam A Hamisu

Ni, Maryam A. Hamisu, shugabar gidauniyar (CEO) Maryam A. Hamisu Development Foundation, yar asalin karamar hukumar Garun Malam a jihar Kano ina sake bayyana duniya a fili kuma ba tare da shakka ba tsayin daka na, hadin kai na, da cikakkiyar biyayya ta ga tafiyar siyasar Kwankwasiyya da kuma jagora, Mai Girma Dr. Rabiu Musa Kwankwaso, wanda nake dauka a matsayin jagorana kuma uban gidana a siyasa.

Shiga ta cikin tafiyar Kwankwasiyya ya samo asali ne daga akida da manufofi na adalci, ci gaban al’umma, inganta ilimi, da kula da talakawa wadannan duk suna da nasaba ta kai tsaye da hangen nesa da manufofin jin kai na gidauniyata.

Ina sake tabbatar da cewa ina tsaye daram tare da Dr. Rabiu Musa Kwankwaso, ba tare da la’akari da duk wani sauyin siyasa, matsin lamba, ko wani hali da zai taso ba. Biyayya ta da goyon baya na gare shi ba za su gushe ba, ba yau ba, ba gobe ba. Ban fice ba, kuma ba ni da niyyar ficewa daga darkar Kwankwasiyya a kowane lokaci.
Wannan matsaya ta fito ne daga zuciyata da akidata, ba don anfani na wucin gadi ba; daga amanna da biyayya, ba don yanayi ba; kuma daga gaskiya, ba tare da sulhu ko sassauci ba.

Ina tare da Kwankwasiyya cikin hadin kai, manufa, da jajircewa, kuma zan ci gaba da bayar da gudummawa mai kyau domin cimma muradun tafiyar, don ci gaban Jihar Kano da kasa baki daya.
A bayyane yake cewa tafiyata ta siyasa ba ta canza ba, kuma biyayya ta na nan daram. Kwankwasiyya har abada.

Wayannan sune sarakai a kowanne fannin Wasanni. 1. 🇺🇸 Michael Jordan - Basketball  2. 🇺🇸 Muhammad Ali - Boxing  3. 🇯🇲 Us...
14/12/2025

Wayannan sune sarakai a kowanne fannin Wasanni.

1. 🇺🇸 Michael Jordan - Basketball
2. 🇺🇸 Muhammad Ali - Boxing
3. 🇯🇲 Usain Bolt - Athletics
4. 🇨🇦 Wayne Gretzky - Ice Hockey
5. 🇺🇸 Michael Phelps - Swimming
6. 🇺🇸 Babe Ruth - Baseball
7. 🇨🇭 Roger Federer - Tennis
8. 🇺🇸 Joe Montana - American Football
9. 🇺🇸 Tiger Woods - Golf
10.🇺🇸 Bruce Lee - Martial Arts
11.🇺🇸 Tom Brady - American Football
12. 🇦🇺 Donald Bradman - Cricket
13.🇬🇧 Daley Thompson - Decathlon
14.🇺🇸 John Cena - Wrestling
15. 🇺🇸 Serena Williams - Tennis
16. 🇺🇸 Simone Biles - Gymnastics
17.🇺🇸 Tony Hawk - Skateboarding

Wa zamu saka a matsayin Sarkin Kwallon kafa?

‘Yanbindiga sun kirƙiro wata fasaha ta musamman don kauce wa bibiyar su -  Ministan sadarwa Ministan sadarwa, kirkire-ki...
14/12/2025

‘Yanbindiga sun kirƙiro wata fasaha ta musamman don kauce wa bibiyar su - Ministan sadarwa

Ministan sadarwa, kirkire-kirkire da tattalin arzikin zamani, Bosun Tijani, ya ce ‘yan bindiga na amfani da “wani irin fasaha ta musamman” wajen yin kira da kuma kauce wa sa-ido daga hukumomin tsaro.

Ministan ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa da Seun Okinbaloye a shirin Politics Today na tashar Channels TV a daren Juma’a.

Tijani ya ce sa-ido kan kiran wayoyin ‘yan bindiga domin tattara bayanan leƙen asiri ya fi “na fasaha” fiye da yadda yawancin ‘yan Najeriya ke zato.

Ya ce masu laifin kan tura kiran waya daga hasumiya zuwa wata da dama domin rikitar da jami’an tsaro da ke bibiyar hanyoyin sadarwarsu.

“Dalilin da ya sa shugaban ƙasa ya matsa lamba mu zuba jari a hasumiyoyin sadarwa a waɗancan yankuna shi ne mun gano cewa akwai wata fasaha ta musamman da su [‘yan bindiga] ke amfani da ita wajen yin kira,” in ji Tijani.

“Ba sa amfani da hasumiyoyin sadarwa na yau da kullum; suna amfani da kira daga hasumiya zuwa hasumiya da dama. Shi ya sa suke jin daɗin zama a yankunan da ba su da haɗin sadarwa.”

Tijani ya ƙara da cewa gwamnatin tarayya na aiki kan inganta tauraron dan adam (satellites) na ƙasar da ke sararin samaniya domin ƙarfafa sa-idon tsaro.

“Domin idan hasumiyoyinmu ba sa aiki, tauraron dan adam ɗinmu zai yi aiki,” in ji shi.

Ministan ya ce wannan hali ya nuna buƙatar “zuba jari mai yawa” a harkar sadarwa.

“Idan ka je ƙasar China, suna da sama da hasumiyoyin 5G miliyan huɗu. Jimillar hasumiyoyin da muke da su a Najeriya ba su wuce kusan 40,000 ba,” in ji Tijani.

~ Daily Nigerian

An shiga wasan ɓuya tsakanin Fasto da mabiyansa, bayan ya ce za a yi ambaliyar ruwan tashin Al-ƙiyama a 25 ga DisambaA w...
14/12/2025

An shiga wasan ɓuya tsakanin Fasto da mabiyansa, bayan ya ce za a yi ambaliyar ruwan tashin Al-ƙiyama a 25 ga Disamba

A watannin baya ne dai Shahararren Fasto a ƙasar Ghana, Fasto Ebo ya bayyana cewa an yi masa wahayin za a yi ambaliyar ruwan tashin Al-ƙiyama a ranar 25 ga watan Disamba.

Inda yasa aka haɗa manyan jiragen ruwa, a cewarsa duk wanda bai shiga ba zai halaka.

Sai dai bayan daruruwan mabiyan nasa sun fara sayar da kaddarori da ajiye aiki bisa dakon wannan rana, an ga sabon bidiyon Faston, inda ya bayyana cewa bai ce kowa ya sayar da kaddarorinsa ba, hasalima bai ambaci shekarar da wannan ambaliyar za ta faru ba.

Hakan ya sanya wasu zargin yana son janye maganarsa ne, bayan dayawa sun ajiye aiki, wasu sun sayar da kaddarorinsu, a hasashen su wannan shekarar ne abin zai faru. Masu karatu mene ne ra'ayoyin ku?

Daga Usman Umar Katsina.

14/12/2025
KA JI KAM: IRAN Ta Nuna Sabbin Makaman Rokoki Wajen Bikin Tunawa Da Ranar Da Matasan Iran S**a Fatattaki Jakadun Amurka ...
05/11/2025

KA JI KAM: IRAN Ta Nuna Sabbin Makaman Rokoki Wajen Bikin Tunawa Da Ranar Da Matasan Iran S**a Fatattaki Jakadun Amurka a Iran.

A ranar Talata, dubban Iraniyawa ne s**a fito kan titunan birnin Tehran domin bikin tunawa da 13 ga watan Aban, rana mai matuƙar tarihi a Iran wadda ake tunawa da mamayar da matasan Iran s**a yi wa ofishin jakadancin Amurka a shekarar 1979. Wannan rana ce da ta zama alamar tsayin daka da ƙin amincewa da mulkin zalunci da tsoma bakin Amurka cikin harkokin ƙasashen duniya.

A yayin gudanar da wannan biki, sojojin Iran sun nuna sabbin makaman rokoki, drones, da injinan sarrafa makamashin nukiliya (centrifuges) a gefen gangamin domin nuna ƙarfin fasaha da ci gaban tsaronsu.

Masu lura da lamurra na ganin wannan nuni a matsayin sakon ƙarfafa gwiwa ga al’umma, da kuma gargadi ga abokan gaba cewa Iran na da cikakken iko da karfin kare kanta daga duk wata barazana daga waje, musamman daga Amurka da Isra’ila.

A cikin jawabinsa, jami’in gwamnati ya bayyana cewa, “13 ga watan Aban, Ba kawai ranar tarihi ba ce, rana ce ta tunatar da duniya cewa Iran ba za ta taɓa miƙa wuya ga zalunci ko matsin lamba daga kowace ƙasa ba.”

Wannan Ranar ta kasance ɗaya daga cikin ranakun siyasa mafi muhimmanci a kalandar Iran, wacce ake kira da “Ranar Yaƙi da Girman Kai da Zaluncin Amurka.”

Me Zaku Ce?

05/11/2025
Ƴan Yahoo matasa ne masu kaifin basira da ke buƙatar jagoranci ba la’ana ba - Obi Tsohon dan takarar shugaban kasa na ja...
26/10/2025

Ƴan Yahoo matasa ne masu kaifin basira da ke buƙatar jagoranci ba la’ana ba - Obi

Tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party (LP), Peter Obi, ya bayyana cewa wasu daga cikin masu damfara ta yanar gizo da ake kira Yahoo boys matasa ne masu basira da za su iya taimakawa ci gaban kasa idan aka shiryar da su ta hanyar da ta dace.

Obi ya bayyana haka ne a yayin taron “Golden Health” da aka gudanar a Onitsha, jihar Anambra, inda ya ce “basira da jarumtakar wasu daga cikin ‘yan Yahoo’ na iya zama ginshikin kirkire-kirkire da ci gaban kasa idan aka tsara su yadda ya kamata.”

Ya ce ya dawo daga Birtaniya domin halartar taron, wanda ya mayar da hankali kan gyaran halin matasa da shugabanci na gaskiya. Obi ya gargadi cewa Najeriya ba za ta ci gaba ba muddin tana yabawa da rashawa da rashin gaskiya.

A cewarsa, “kudi ba shi ne ainihin dukiya ba,” domin dukiya ta gaskiya tana gina mutum da al’umma ta hanyar ilimi, rage talauci, da samar da damammaki ga wasu.

Obi ya kuma shawarci matasa da su rungumi aiki tukuru da gaskiya, yana mai cewa kasashe ba sa ginuwa da mu’ujiza, sai da mutane masu aiki da hangen nesa.

Ya kammala da kiran gwamnati da shugabanni su tabbatar da adalci da gaskiya, yana mai cewa ci gaban kasa yana bukatar hadin kai ba tare da nuna kabilanci ko addini ba.

Dalilin da ya sa mu ka soke batun auren Mai Wushirya da Ƴarguda - Hisbah Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa ta...
26/10/2025

Dalilin da ya sa mu ka soke batun auren Mai Wushirya da Ƴarguda - Hisbah

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa ta soke batun auren jarumin Tiktok din nan Ashiru Idris Mai Wushirya da Abashiyya Yarguda bayan sun tabbatar da cewa babu soyayya a tsakanin su.

Idan za a iya tunawa dai a kwanakin baya ne, wata kotun Majistiri ta umarci hukumar Hisbah ta shirya kan auren jaruman biyu bayan an same su da laifin wallafa hotuna da bidiyoyi na badala.

Sai dai, a wata sanarwa da mataimakin Babban Kwamandan hukumar Hisbah ta jihar Kano, Dakta Mujahideen Aminudeen ya aiko wa jaridar Daily Nigerian Hausa ya bayyana cewa bayan an gudanar da gwaje-gwaje, Mai Wushirya da 'Yar Guda sun tabbatar wa da hukumar cewa "Content Creation" kawai suke yi ba wai soyayya ba.

Acewar Dakta Mujahideen, daman sharadi ne a addini cewa sai Amarya da Ango sun amince da junansu kafin a kai ga daura aure.

"Tun kafin a zo maganar Sadaki ma, s**a nuna gaskiya baza su iya ba, mai girma babban kwamanda ya yi la'akari da cewa, a Musulunci Shari'a ake karewa , kuma a shari'a ba a auren dole".

Ya kara da cewa tunda ba soyayya tsakanin Haruna Tiktok din kuma na akwai bambancin halitta tsakanin su, to ta tabbata cewa za a iya rasa wannan batu na aure domin za a iya samun matsaloli bayan auren.

"Mu kuma a Hisbah, so mu ke yi aure ya zama mutu-ka-raba, ba wai a rika samun matsaloli har ta kai ga cin zarafi ba," innji Dakta Mujahideen

Haka kuma, ya ce Hisbah za ta mayar da su gaban kotu domin daukar mataki na gaba.
Daily Nigerian Hausa

25/10/2025

Labaran Duniya.

Ziyarar tsoffin ‘yan wasan Barcelona shaida ce ta samuwar tsaro da zaman lafiya - Ministan Tsaron NijeriyaMinistan tsaro...
25/10/2025

Ziyarar tsoffin ‘yan wasan Barcelona shaida ce ta samuwar tsaro da zaman lafiya - Ministan Tsaron Nijeriya

Ministan tsaron Nijeriya, Dr. Bello Muhammad Matawalle, ya bayyana ziyarar tsoffin ‘yan wasan ƙungiyar kwallon kafa ta Barcelona zuwa Nijeriya a matsayin tabbacin dawowar zaman lafiya, tsaro da kwanciyar hankali a Nijeriya.

A wata sanarwa da mataimakinsa na musamman kan yaɗa labarai, Ahmad Dan-Wudil, ya fitar a Abuja ranar Juma’a, Matawalle ya ce ziyarar ta nuna yadda ƙasashen duniya ke sake samun kwarin gwiwa kan ƙoƙarin da gwamnatin Nijeriya ke yi wajen magance matsalar tsaro.

A cewar Matawalle, ziyarar tsoffin ‘yan wasan Barcelona zuwa Nijeriya hujja ce ta ci-gaban da ƙasarmu ta samu wajen farfaɗo da tsaro da zaman lafiya.

Hakazalika, ya ƙara da cewa wannan lamari ya nuna Nijeriya ta zama kasar da ke jan hankalin ƙasashen duniya sakamakon jajircewar jami’ai da hukumomin tsaron kasar.

Matawalle ya bayyana wasan sada zumunci da tsoffin ‘yan wasan Barcelona za su buga da tsoffin taurarin ‘yan wasan Afirka a ranar Asabar, 25 ga watan Oktoba 2025, a filin wasa na Moshood Abiola da ke Abuja, a matsayin nasara ga gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu wajen tabbatar da zaman lafiya da samuwar yanayi mai kyau domin gudanar da wasannin kasa da kasa.

Daga karshe, Matawalle ya kuma yi wa tawagar tsoffin ‘yan wasan maraba a madadin gwamnatin Nijeriya da ma ‘yan Nijeriya, da fatan natsuwa da nishadi a lokacin da za su shafe a Nijeriya.

Hukumar Kula da Gidajen Yari ta Najeriya (NCoS), reshen Jihar Kano, ta bayyana cewa fursunoni 68 sun yi nasara a jarraba...
23/09/2025

Hukumar Kula da Gidajen Yari ta Najeriya (NCoS), reshen Jihar Kano, ta bayyana cewa fursunoni 68 sun yi nasara a jarrabawar kammala sakandire ta NECO na shekarar 2025. Wannan nasara na nuna irin ƙoƙarin da ake yi wajen bai wa fursunoni damar samun ilimi da gyaran rayuwa a cikin gidan yari. Hukumar ta ce ilimi na daga cikin manyan hanyoyin sake fasalin rayuwar fursunoni, domin ba su damar samun makoma mai kyau bayan kammala wa’adin da aka yanke musu. Wannan mataki ya kuma nuna cewa gidan yari ba wai wurin hukunta mutane kawai ba ne, har ma wurin gina su don sake komawa cikin al’umma da amfani.

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when GY Times Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share