Jannat Online TV

Jannat Online TV Domin samun labarai da dumi duminsu ziyarci shafin Jannat Online TV

25/02/2026
KARAMOMI GOMA DA HON. BAFFA BABBA DANAGUNDI YAKE DASU, WADANDA YAWAN ‘YAN SIYASA S**A RASAIdan ana maganar shirya taro c...
19/02/2026

KARAMOMI GOMA DA HON. BAFFA BABBA DANAGUNDI YAKE DASU, WADANDA YAWAN ‘YAN SIYASA S**A RASA

Idan ana maganar shirya taro cikin tsari, tsafta, natsuwa da mutunta jama’a, tare da girmama baki da abokan zama ba tare da hayaniya ko rashin da’a ba, to babu shakka Baffa Babba Danagundi ya zama abin koyi. Ga kaɗan daga cikin karamomin da Allah Ya h**e masa:
1. Yakan tsara duk wani abu tun da wuri, ya ajiye shi a muhallinsa da tsari mai kyau.
2. Duk wani saƙo ko aiki, musamman na kuɗi, baya jinkirin ba wa wanda ya yi masa aiki hakkinsa.
3. Ba a yarda da wargi, iskanci ko raini a wajen tarurrukansa.
4. Babu damar yin kazafi ko rashin kunya ga manyan da aka gayyata, ko da mutum bai shirya da su ba.
5. Shi kaɗai ne ke tanadar mazubai na zuba shara a duk inda ake taronsa, domin tabbatar da tsafta da tsari.
6. Taronsa baya rikicewa; babu damar zuwa wurin manya ana bara ko katsalandan yayin magana.
7. Ba ya yarda a lalata kayansa ko a ɗauke su da wasa ko sakaci.
8. Yana mutunta ‘yan jarida matuƙa – “duka dauka kawai” a wajensa alama ce ta girmamawa.
9. Yakan kula da lokaci sosai, yana daraja muhimmancin bin jadawali.
10. Yaransa suna mutunta duk wanda s**a san yana kaunarsa, kuma hakan na nuna tarbiyya da kyakkyawar shugabanci.

Hakika, waɗannan halaye darussa ne ga ‘yan siyasa da masu jagoranci, domin cigaban al’umma yana bukatar tsari, mutunci da adalci.

Marubuci:
Abdulwahab Ahmad Sa’id

Congratulations Oga
10/02/2026

Congratulations Oga

Kuce Romooo ! Kuce Romooo !! Kuce Romooo !!!Romoooo yana dab da Sauka…..              JANZAKARA
09/02/2026

Kuce Romooo ! Kuce Romooo !! Kuce Romooo !!!

Romoooo yana dab da Sauka….. JANZAKARA

A yammacin wannan ranar Talata, Tsohon Gwamnan jihar kano kuma tsohon Shugaban jam'iyyar Apc na ƙasa Dr. Abdullahi Umar ...
05/02/2026

A yammacin wannan ranar Talata, Tsohon Gwamnan jihar kano kuma tsohon Shugaban jam'iyyar Apc na ƙasa Dr. Abdullahi Umar Ganduje tare da fitaccen malamin addini Kuma Shugaban Darikar Khadiriyya na Afirka Sheikh Kariballah Sheikh Muhammad Nasiru Kabara, da kuma Babban Daraktan Cibiyar Kula da Nagartar Ayyuka ta Ƙasa (NPC),
Hon. Dr. Baffa Babba Dan’agundi NIM,
sun kai ziyara Babban Masallaci da Islamic Centre da tsohon Shugaban jam'iyyar yake ginawa a birnin tarayya Abuja.

Ziyarar ta kasance domin duba yadda aikin ginin da kuma samun cikakken bayani kan yadda aikin ke tafiya, kasancewar wannan gagarumin masallaci da cibiyar addinin Musulunci na daga cikin muhimman ayyukan da Dr. Abdullahi Umar Ganduje ke Aikatarwa a loko da sako na ƙasar nan da nufin bunƙasa harkokin addini, ilimi da tarbiyya a ƙasa baki daya.

A yayin ziyarar, Sheikh Kariballah Sheikh Muhammad Nasiru Kabara ya bayyana jin daɗinsu kan irin hidimar da yakewa Addini, tare da yi masa addu'a ta musamman kan irin Wadannan Ayyukan Alherin da Gandujen yake gudanarwa.

Ayuba Jarimi
SSA MEDIA TO THE DG NPC
TUESDAY 3RD FEBRUARY 2026.

31/01/2026

Bayan Ganawar Sirri, Mai Girma Gwamna Ya Gayyaci D.G na NPC Zuwa ABU Zaria Domin Halartar Bikin Yaye Dalibai

Bayan wata ganawar sirri da aka gudanar a ofishinsa, Mai Girma Gwamna ya gayyaci Babban Daraktan Cibiyar Kula da Nagartar Ayyuka ta Ƙasa (NPC),
Hon. Dr. Baffa Babba Dan’agundi NIM,
zuwa Jami’ar Ahmadu Bello (ABU) Zaria domin halartar bikin yaye dalibai (Convocation Ceremony) na jami’ar.

Gayyatar ta nuna irin girmamawa da amincewa da Mai Girma Gwamna ke da ita ga D.G na NPC, tare da jaddada kyakkyawar alaka da ke tsakanin shugabannin wajen bunkasa ilimi da ci gaban ƙasa baki ɗaya.

Ana sa ran halartar taron zai kara karfafa hadin kai da kuma nuna goyon baya ga harkokin ilimi da cigaban matasa a Najeriya.

Ayuba Jarimi
SSA MEDIA TO THE DG NPC
SATURDAY 31st JANUARY 2026.

LABARIN ZIYARAR AIKILaraba 28-01-2026.Babban Daraktan Cibiyar Kula da Nagartar Ayyuka ta kasa NPC           Hon. Dr. Baf...
28/01/2026

LABARIN ZIYARAR AIKI

Laraba 28-01-2026.

Babban Daraktan Cibiyar Kula da Nagartar Ayyuka ta kasa NPC
Hon. Dr. Baffa Babba Dan’agundi NIM
Yakai ziyarar aiki Ofis din Babban Daraktan Hukumar Kula da Sayen Kayayyaki da Ayyuka ta Gwamnati (Public Procurement), Dr. Adebowale Adedikun,

Ziyarar ta mayar da hankali ne kan muhimman batutuwa da s**a shafi inganta tsarin sayen kaya da aiwatar da ayyukan gwamnati, tare da ƙarfafa gaskiya, adalci da bin ka’idoji kamar yadda doka ta tanada.

A yayin ganawar, Dr. Adebowale Adedikun ya jaddada kudirin hukumar na tabbatar da nagarta, inganci da rikon amana a dukkan matakan sayen kaya da ayyuka, domin cimma burin ci gaban kasa.

Ziyarar ta gudana cikin yanayi na fahimtar juna da musayar ra’ayoyi masu amfani, inda aka bayyana aniyar ci gaba da hadin gwiwa domin bunkasa ayyukan gwamnati da kyautata wa al’umma

Ayuba Jarimi
SSA MEDIA TO DG NPC
Wednesday 28th January 2026.

25/01/2026

Dan Allah kuyi haquri,
afadi alkhairi ko ayi shiru
mu mazauna unguwar chiranci bama Jin dadi

DAN ALLAH 🙏🙏🙏🥺🥺

Address

Kano

Telephone

8135460004

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jannat Online TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share