Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria FREEDOM RADIO (Muryar Jama’a)
(433)

An indigenous private radio station established in Kano a historic city, the commercial nerve center of the sub-Saharan Africa and perhaps Nigeria’s political melting pot...

13/01/2026

Me ku ke tunanin zai faru tsakanin tawagar kasar Moroco da Super Eagles a wasan gobe, na gasar cin kofin kasashen Arfica wato AFCON ?

13/01/2026

Yanzu-yanzu: Gobara ta tashi a gidan Man Wahida, dake Unguwar Rimin Kebe Karshen Kwalta a Karamar Hukumar Ungogo a Kano.

Al'ummar yankin dai na neman daukin gaggawa, sak**akon yadda gidan man ke kusa da gidajen mutane.

Tuni dai jami'an kashe gobara s**a isa wajen, kuma sun fara shawo kan gobarar.

Bidiyo daga Abubakar Umar da aka fi sani da Kawun Baba.

"Ga alama dai yau a  Kano an fadi ba nauyi, an gano farashin yan kungiya tun da sun ce aci dadi lafiya, mai girma Gwamna...
13/01/2026

"Ga alama dai yau a Kano an fadi ba nauyi, an gano farashin yan kungiya tun da sun ce aci dadi lafiya, mai girma Gwamna muna ma maraba da zuwa gidan nasara" - Abdulmajid Mustapha.

Kungiyar tsofaffin Kansiloli na Kano tin daga shekarar 1999,  karkashin jagorancin Barr. Kabiru Ibrahim Makoɗa ta yi kir...
13/01/2026

Kungiyar tsofaffin Kansiloli na Kano tin daga shekarar 1999, karkashin jagorancin Barr. Kabiru Ibrahim Makoɗa ta yi kira ga Gwamna Abba Kabir Yusuf ya shigo Jam'iyyar APC.

13/01/2026

Sponsored: Ƙungiyar tsofaffin Kansiloli na Kano tin daga shekarar 1999, ƙarƙashin jagorancin Barr. Kabiru Ibrahim Makoɗa da Sakatare Hon. Ibrahim Raboge Gobirawa, ta gudanar da taro na musamman domin kira ga Gwamna Abba Kabir Yusuf kan ya shigo Jam'iyyar APC, tare da yi masa godiya bisa biyansu haƙƙoƙinsu da ya yi tin daga lokacin da ya hau kujerar Gwamnan.

13/01/2026

Ba ma jin dadin yadda yaran Alh. Atiku Abubakar na kusa, ke kokarin raba mu da shi, duk da irin kyawawan aidunsa - Idris Jibrin Satatima.

"Jagora mun gode da ka amince mu tafi, Insha Allah za mu zamar maka wakilai na gari a cikin jam’iyyar APC" - Salisu Yaha...
13/01/2026

"Jagora mun gode da ka amince mu tafi, Insha Allah za mu zamar maka wakilai na gari a cikin jam’iyyar APC" - Salisu Yahaya Hotoro.

"Na sha fada, a wannan kasar ta Najeriya kar ka kuskura rashin lafiya ta k**a ka, saboda asibitocin sun koma wani waje d...
13/01/2026

"Na sha fada, a wannan kasar ta Najeriya kar ka kuskura rashin lafiya ta k**a ka, saboda asibitocin sun koma wani waje da za ka je da ciwon kai, ka dawo da ciwon kaba" - Prof. Sani Lawan Malumfashi.

"Wadannan su ne awakan da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya ba ni, gashi sun haifamin ɗa santalele, shi ma ya girma, zuri'a ta ...
13/01/2026

"Wadannan su ne awakan da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya ba ni, gashi sun haifamin ɗa santalele, shi ma ya girma, zuri'a ta fara yaduwa" - Yahya S. Ali Gidan-kaji.

13/01/2026

Ali Gyara Hausawa ya gyara k**ansa, bayan cece-ku-cen da s**a janyo a jiya.

Hukumar kula da asibitoci ta Kano, ta dakatar da likitocin da su ka yi wa marigayiya  Aishatu Umar aiki, har su ka manta...
13/01/2026

Hukumar kula da asibitoci ta Kano, ta dakatar da likitocin da su ka yi wa marigayiya Aishatu Umar aiki, har su ka manta almakashi a cikinta, tare da aike wa da su kwamitin da ke bincike kan yadda lamarin ya faru.

A sanarwar da kakakin hukumar Samira Suleiman ta fitar a yau, tace ko kadan, ba za su lamunci sakaci irin wannan ba, ta kuma kara mika sakon ta'aziyya ga iyalai da 'yan uwan Marigayiyar, tare da alkawarin dakile faruwar lamarin a nan gaba.

Shugabancin Jam’iyyar NNPP na Karamar Hukumar Tudun Wada ƙarƙashin jagorancin Hon. Salisu Yusha’u Soja, sun sake jaddada...
13/01/2026

Shugabancin Jam’iyyar NNPP na Karamar Hukumar Tudun Wada ƙarƙashin jagorancin Hon. Salisu Yusha’u Soja, sun sake jaddada cikakken goyon bayansu ga sabon Shugaban jam’iyyar NNPP na Jihar Kano, Hon. Abdullahi Zubairu Abiya.

Sun bayyana cewa wannan goyon baya na su, alama ce ta haɗin kai, da amincewa da jagoranci na gari da kuma fatan ganin jam’iyyar na cigaba da samun nasara a matakin jiha da ƙasa baki ɗaya.

Jam’iyyar NNPP a Tudun Wada ta tabbatar da cewa za ta ci gaba da marawa sabon shugaban baya da dukkan ƙoƙari na ɗorewar ci gaba da hadin kai a jam’iyyar.

Address

PHASE 1 SHARADA INDUSTRIAL Estate KANO
Kano
700234

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Freedom Radio Nigeria posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Freedom Radio Nigeria:

Share

Category