Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria FREEDOM RADIO (Muryar Jama’a)
(455)

An indigenous private radio station established in Kano a historic city, the commercial nerve center of the sub-Saharan Africa and perhaps Nigeria’s political melting pot...

13/08/2026

Zuwan Kwamishinan kasa Hon. Abduljabbar Umar Garko ne aka tsaftace harkar yanka filaye, tare da yin maganin 'yan kasa ta Allah ce - Ibrahim Soja Kantin Kwari

13/08/2026

Muna rokon Gwamna ya shiga al'amarinmu, a bar mana filayenmu na Rimin Zakara Gabas - Mukhtar Idris Bature.

Tun daga shekarar 1999, duk lokacin da wani sabon shugaban Ƙaramar Hukumar Kabo ya zo, sau da yawa mutane kan ce: “Wanda...
13/08/2026

Tun daga shekarar 1999, duk lokacin da wani sabon shugaban Ƙaramar Hukumar Kabo ya zo, sau da yawa mutane kan ce: “Wanda ya tafi ya fi na yau.” Amma zuwan Comr. Lawan Najume Kabo ya sa wannan magana ta fara samun sabon salo.

Yanzu abin da ake cewa shi ne: “Kabo na buƙatar shugabanni irin su Lawan Najume.”

Wannan ba magana ce ta son rai kawai ba. Shugabanci ana auna shi ne da irin tasirin da yake yi a rayuwar al’umma. A lokacin mulkinsa, an samu shirye-shiryen tallafa wa jama’a, inganta ilimi, tsaftar muhalli da bunƙasa tattalin arzikin al’umma. Rahotanni sun kuma bayyana wasu daga cikin ayyukan, ciki har da tallafin kuɗi ga ɗaruruwan mazauna Kabo da sauran shirye-shiryen jin daɗin jama’a.

Saboda haka, Lawan Najume ya kafa tarihi ta hanyar salon shugabancinsa da kusancinsa da jama’a. Abin da ya kamata mu yi shi ne mu yaba wa duk wani shugaba da yake ƙoƙarin sauƙaƙa wa talaka rayuwa, ba tare da raina abin da ya gabata ba.

Kabo na buƙatar shugabanci mai sauraron jama’a, mai tausayi, mai aiki, kuma mai barin abin tunawa.

Lawan Najume — Tarihi Ya Rubuta!
Kabo na buƙatar irin ku. 🇳🇬

Daga Smart Hussain.

Cikin Hotuna: Koken al’ummar Garin Gurin Gawa dake Kumbotso a Kano. Al’ummar yankin Gurin Gawa dake Karamar Hukumar Kumb...
13/08/2026

Cikin Hotuna: Koken al’ummar Garin Gurin Gawa dake Kumbotso a Kano.

Al’ummar yankin Gurin Gawa dake Karamar Hukumar Kumbotso na kira ga Gwamnan Jihar Kano, Dan Majalisar Tarayya na Jihar da Shugaban Ƙaramar Hukumar Kumbotso, da sauran masu ruwa da tsaki, da su kawo ɗauki kan matsalar rashin hanya a wannan gari.

Al’ummar sun kara da cewa a halin yanzu, hanyar shigo wa garin tana cikin mummunan hali, har ta kai ga wasu mutane suna ajiye ababan hawansu a gefen t**i, sannan su shigo da ƙafa saboda rashin kyawun hanyar.

Saboda haka, suke kira ga hukumomin da abun ya shafa da su duba wannan matsala cikin gaggawa, domin samar da hanya mai kyau don sauƙaƙa wa jama’ar yankin zirga-zirga.

13/08/2026

WASIKA: Korafin al'ummar Tudun Yola da kewaye kan rashin ingancin aikin t**in da ake musu, da ya tashi daga Rafin Dannana zuwa karshen t**in Northwest.

13/08/2026

Kamfanin Wassee Investment dake garin Abuja da Kano ya muku tanadin kayatattun kayayyaki masu kyau da inganci a farashi mai sauki, ku dai kawai ku garzaya shagunansu dake jihar Kano ko Abuja.

A madadin Zababben Kansilan Mazabar Tudun Wada kuma Majority Leader na Majalisar Karamar Hukumar Nassarawa, Hon. Sani Su...
13/08/2026

A madadin Zababben Kansilan Mazabar Tudun Wada kuma Majority Leader na Majalisar Karamar Hukumar Nassarawa, Hon. Sani Sule Tudun Wada (Ingila), muna mika godiya ta musamman ga Gwamnan Jihar Kano, Engr. Abba Kabir Yusuf, bisa wannan kyakkyawar manufa ta bai wa matasa filaye a fadin Jihar Kano, musamman a Karamar Hukumar Nassarawa da Mazabar Tudun Wada.

Muna matukar jin dadin wannan namijin kokari da Gwamna ya yi wajen tallafa wa matasa da kuma samar musu da damar mallakar filaye domin bunkasa rayuwarsu da harkokin ci gaba.

Daga cikin matasan Mazabar Tudun Wada da s**a amfana da wannan shiri akwai:

1. Abdulaziz Tasiu Tudun Wada (Na’zi)
2. Auwal Idris Tudun Wada (Auwalu Magus)

Da sauran matasa daga Karamar Hukumar Nassarawa da Jihar Kano baki daya.

Kuma muna kira ga Matasa wadanda basu rabauta da Fili ba, suyi hakuri suma Insha Allah rabonsu na nan zuwa tare da abubuwan Alkairai na Musanman.

Muna sake mika godiya ta musamman ga Gwamna Engr. Abba Kabir Yusuf bisa wannan abin alheri. Allah Ya saka masa da alheri, Ya kara masa basira da ikon ci gaba da yi wa al’umma hidima.

Mungode Gwamna! Allah Ya maimaita maka kujerarka, tare da dukkan kujerun Jam’iyyar APC a zaben 2027.

Sponsored

Hon. Sani Sule Tudun Wada ( Ingila)
Zababben Kansilan Mazabar Tudun Wada kuma Majority Leader na Majalisar Karamar Hukumar Nassarawa.

Kamfanin jiragen sama na Air India ya sanar da cewa zai fara gudanar da gwajin shan ƙwayoyi na dole ga dukkan matuƙan ji...
13/08/2026

Kamfanin jiragen sama na Air India ya sanar da cewa zai fara gudanar da gwajin shan ƙwayoyi na dole ga dukkan matuƙan jiragensa, bayan da wani jirginsa ya ya rasa hanya yayin da yake sararin samaniya.

Daga baya, gwajin da aka yi wa matuƙin jirgin ya nuna cewa ya ha tabar wiwi gabanin tashin jirgin.

A ƙarƙashin dokokin da ake bi a yanzu, kamfanonin jiragen sama suna da wajibcin gudanar da gwajin miyagun ƙwayoyi ga aƙalla kashi 10 cikin 100 na ma’aikatan jirgi a kowace shekara.

Sai dai Air India ta ce sabon tsarin da za ta aiwatar zai bai wa fasinjoji ƙarin ƙwarin gwiwa da tabbacin tsaro yayin tafiye-tafiyensu.

Abdullahi Idris Said Gora daga karamar hukumar Madobi ya ce, KWANKWASIYYA ba siyasa bace ƙungiya ce ta siyasa wadda iyay...
13/08/2026

Abdullahi Idris Said Gora daga karamar hukumar Madobi ya ce, KWANKWASIYYA ba siyasa bace ƙungiya ce ta siyasa wadda iyayen mu s**a sadaukar da kansu wajen kafuwar ta, kuma yanzu dalili yasa s**a bar ta.

‎Don haka daga yau ya bar duk wani tsarin tafiyar siyasar Kwankwasiyya tare da jaddada goyon baya da mubayi'a ta ga Mai Girma Gwamna Alh. Abba Kabir Yusuf da Jam'iyyar APC ƙarƙashin Jagorancin Haj. Bilkisu Yakubu Indabo, wadda ke faɗi tashi ba dare ba rana wajen ziyarar gani da ido a ƙananan Hukumomi 44 dake Jihar Kano, don tallata ayyukan alkhairin Mai Girma Gwamna bisa jajircewa da ƙoƙarinta kan ayyukan Gwamna don tabbatar nasararsa a zaɓen 2027 da yardar ALLAH.
‎Abba 4+4 insha Allah

Jami'ar Iconic Open University Ta Sanar Da Bude Daukar Ma’aikata a Sabbin Cibiyoyin Bincike Da Ta KafaJami'ar Iconic Ope...
13/08/2026

Jami'ar Iconic Open University Ta Sanar Da Bude Daukar Ma’aikata a Sabbin Cibiyoyin Bincike Da Ta Kafa

Jami'ar Iconic Open University, wadda ke da lasisi, da Hukumar Jami'o'in Kasa (NUC), ta sanar da buɗe kofar daukar ma’aikatan bincike a sabbin cibiyoyin bincike guda uku da ta kafa a Arewacin Najeriya.

Jami'ar, ta hannun Daraktan Bincike, na Directorate of Research, Innovation and The Impossible (DRII), tana gayyatar ƙwararrun masu bincike domin fara gabatar da aiki a cibiyoyin bincike na musamman da aka keɓe a Jihohin Kano, Sakkwato, da Zamfara.

Cibiyoyin binciken, waɗanda aka tsara domin cike gibin da ke tsakanin binciken ilimi da ci gaban tattalin arziki da zamantakewa, sune:

1. Cibiyar Bincike da Ci gaban Noma da Ma'adinai, a Gusau, Jihar Zamfara - wanda za ta mayar da hankali kan sha’anin noma, sarrafa kaya da bunƙasa ma'adinan ƙasa.
2. Cibiyar Bincike da Ci gaban Farfaɗo da Masana'antu, a Kano - wanda za ta mayar da hankali kan farfaɗo da masana'antu, ƙirƙira sabbin masana'antu, da bunƙasa ƙananan masana'antu da matsakaitan masana'antu (SMEs).
3. Cibiyar Bincike da Ci gaban Lafiyar Al'umma, a Sakkwato, - wanda za ta mayar da hankali kan tsarin kiwon lafiyar al’umma, bincike kan cuttutuka, da samar da rigakafi.

Ga masu sha’awar cike gurabun neman aiki a wadannan cibiyoyi, za su iya ziyartar shafin yanar gizon jami’ar a www.iconicuniversity.edu.ng

Address

PHASE 1 SHARADA INDUSTRIAL Estate KANO
Kano
700234

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Freedom Radio Nigeria posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Freedom Radio Nigeria:

Share

Category