G2 Times Hausa

G2 Times Hausa A WANNAN SHAFI ZAKU SAMI SAHIHAN LABARAI DA SHIRIN BINCIKE (FACT-CHECKING) CIKIN HARSHEN HAUSA https://whatsapp.com/channel/0029VbDLbZi60eBeN33Cgz3q

Mayaƙan Houthi na Yemen sun ce sun kai harin jirgin sama mara matuƙi kan wata matatar man fetur ta Saudiyya da ke gaɓar ...
09/08/2026

Mayaƙan Houthi na Yemen sun ce sun kai harin jirgin sama mara matuƙi kan wata matatar man fetur ta Saudiyya da ke gaɓar Bahar Maliya.

Kakakin rundunar sojin ƙungiyar, Yahya Saree, ya ce harin da aka kai kan matatar man fetur ta Aramco da ke Jazan, martani ne kan kutsen da Saudiyya ke yi a arewa maso yammacin Yemen.

Ma'aikatar makamashi ta Saudiyya ta ce jami'an kashe gobara sun yi nasarar kashe gobarar da ta tashi a wurin.

Mayaƙan Houthi sun sanar da kafa katanga ta ruwa kan Saudiyya a watan da ya gabata, lamarin da ya sake rura wutar rikicin tare da ƙara matsin lamba kan samar da makamashi a duniya, wanda yaƙin Iran ya haifar.

A gefe guda kuma, babbar hukumar tsaron Iran ta yi gargadin cewa ba za a bude mashigar ruwan Hormuz ba har sai Amurka ta amince da wasu bukatu guda shida, ciki har da sassauta takunkuman da aka ƙaƙaɓawa Iran, biyan diyya kan barnar yakin, da kuma kawo karshen katangar da aka sanya wa tashoshin jiragen ruwa na Iran.

゚viralシ

Gwamnatin Trump ta sanar da cewa za ta kashe dala biliyan uku a ayyukan haƙar ma’adanai masu muhimmanci da kuma samar da...
08/08/2026

Gwamnatin Trump ta sanar da cewa za ta kashe dala biliyan uku a ayyukan haƙar ma’adanai masu muhimmanci da kuma samar da batura.

Wannan na cikin wani ɓangare na zuba jari da nufin taimakawa wajen sake cike rumbunan makamai na Amurka bayan yaƙin da aka yi da Iran.

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaito cewa sojojin Amurka sun yi amfani da adadi mai yawa na makamai masu linzami da kuma makamai masu linzami na kare sararin samaniya yayin yaƙin da s**a shafe watanni biyar suna yi da Iran.

Jami’an tsaro da ’yan majalisar dokokin Amurka sun yi gargadin cewa zai iya ɗaukar shekaru kafin a maye gurbin wasu daga cikin waɗannan makamai, saboda ƙalubalen da ake fuskanta wajen samar da su cikin gaggawa.

Ana amfani da wasu ma’adanai kamar rare earth, tungsten, germanium da scandium wajen kera makamai masu linzami masu bin sahihin manufa, jiragen yaƙi, motocin sulke da kuma ingantattun na’urorin soji.

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Najeriya (Immigration) ta ce sabon tsarin da ta bullo da shi na mayar da buga fasfo a A...
07/08/2026

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Najeriya (Immigration) ta ce sabon tsarin da ta bullo da shi na mayar da buga fasfo a Abuja bai shafi karɓa ko yin rijistar fasfo a jihohi ba.

Hukumar ta ce rahotannin da ke cewa za a ɗauke cibiyoyin gudanar da fasfo daga Kano ba gaskiya ba ne, kuma mutane sun yi kuskuren fahimtar abin da ake nufi.

Bayanin na zuwa ne yayin da ake ci gaba da cece-ku-ce kan wata takarda da ta nuna cewa an mayar da wasu cibiyoyin buga fasfo daga wasu jihohin zuwa Abuja kaɗai.

Jami'in hulɗa da jama'a na hukumar a jihar Kano, DSI Muhammad Auwal, ya shaida wa BBC cewa sabon tsarin ya fara aiki tun farkon shekarar nan, kuma an aiwatar da shi a wasu jihohin a rukuni-rukuni.

"Ba wai za a daina rijistar fasfo ko kuma karɓarsa a jihohi ba ne. Buga fasfo ne aka mayar zuwa Abuja," in ji shi.

Ya ƙara da cewa, an fara aiwatar da tsarin ne a jihohin Nasarawa, Kogi, Borno da Yobe, kuma za a ci gaba da faɗaɗa shi zuwa sauran jihohi.

Rundunar Ƴan Sandan Jihar Sokoto ta ce ta yi nasarar daƙile hare-haren ƴanbindiga guda biyu a ƙananan hukumomin Shagari ...
07/08/2026

Rundunar Ƴan Sandan Jihar Sokoto ta ce ta yi nasarar daƙile hare-haren ƴanbindiga guda biyu a ƙananan hukumomin Shagari da Rabah, inda ta ƙwato dabbobi sama da 450 da maharan s**a kwashe.

A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, DSP Ahmad Rufa'i, ya fitar, ya ce harin na farko ya faru ne da misalin ƙarfe 7:20 da yammacin ranar 4 ga Agusta, lokacin da ƴanbindiga ɗauke da makamai s**a kai hari ƙauyukan Horo Birni da Marake a ƙaramar hukumar Shagari.

Sanarwar ta ce bayan samun kiran gaggawa, jami'an rundunar da sojoji s**a iza zuwa wurin, inda s**a yi musayar wuta da maharan.

Ya ce maharan sun tsere zuwa cikin daji bayan sun sha ƙarfinsu, tare da barin dabbobin da s**a kwashe, waɗanda s**a haɗa da shanu 195, tumaki 84 da raƙuma biyu.

Sai dai mutum biyu daga cikin mazauna yankin sun samu raunukan harbin bindiga, kuma an kai su asibiti domin samun kulawa.

Mahukuntan Kuwait sun ba da umarnin rufe makarantar ƴan Iran guda ɗaya tilo da ke ƙasar, bayan hare-haren da Iran ta kai...
06/08/2026

Mahukuntan Kuwait sun ba da umarnin rufe makarantar ƴan Iran guda ɗaya tilo da ke ƙasar, bayan hare-haren da Iran ta kai wa Kuwait a lokacin yaƙin Gabas ta Tsakiya.

Wata majiya daga Ma'aikatar Ilimi ta Kuwait ta shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa an bayar da umarnin rufe makarantar, sai dai ba ta bayyana takamaiman dalilin matakin ba.

Kuwait na cikin ƙasashen yankin Tekun Fasha da Iran ta kai wa hare-hare a lokacin yaƙin, saboda kasancewar sojojin Amurka a ƙasar.

Takardar umarnin Ma'aikatar Ilimi, wadda AFP ta gani, ta ce: "Ministan Ilimi ya yanke shawarar soke lasisin makarantar mai zaman kanta ta Iran tare da rufe ta."

Bisa wannan umarni, an dakatar da karɓar sabbin ɗalibai domin shekarar karatu mai zuwa, yayin da aka buƙaci iyaye su mayar da ƴaƴansu zuwa wasu makarantu.

゚viralシ

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya sake nanata cewa ƙasarsa ba ta fuskantar ƙarancin makamai.A wani saƙo da ya wallafa a ...
06/08/2026

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya sake nanata cewa ƙasarsa ba ta fuskantar ƙarancin makamai.

A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Truth Social, Trump ya soki rahotannin da ke cewa makaman Amurka sun ragu, yana mai cewa ƙasar na da "tarin makamai da harsasai", sai dai bai bayyana nau'o'in da yake magana a kansu ba.

Ya ƙara da cewa kamfanonin tsaro na ƙasar na ci gaba da samar da makamai cikin sauri, tare da gina sabbin masana'antu da cibiyoyin kera makamai mafi yawa a tarihin Amurka.

A cewarsa, za a ci gaba da tura makamai zuwa inda ake buƙatarsu a duk lokacin da bukatar hakan ta taso.

A baya dai jaridar Washington Post ta ruwaito cewa Trump ya tambayi Sakataren Tsaron Amurka, Pete Hegseth, bayani kan rahotannin ƙarancin harsasai a wani taron majalisar ministoci da aka gudanar a Camp David a ranar Juma'ar da ta gabata.

Jaridar, wadda ta ambato wasu majiyoyi biyu da ba ta bayyana sunayensu ba, ta ce Trump ya shaida wa Hegseth cewa yana tunanin an riga an warware matsalar ƙarancin makaman.

Sai dai a saƙonsa na ranar Alhamis, Trump ya yi kakkausar s**a ga waɗanda s**a fitar da bayanan, yana mai cewa an fara gurfanar da su a gaban shari'a, kuma za su fuskanci hukuncin ɗaurin shekaru masu yawa a gidan yari.

Ma'aikatar Tsaron Rasha ta ce dakarunta sun kakkabo jiragen marasa matuƙa 605 na Ukraine a hare-haren da ta kai cikin da...
06/08/2026

Ma'aikatar Tsaron Rasha ta ce dakarunta sun kakkabo jiragen marasa matuƙa 605 na Ukraine a hare-haren da ta kai cikin daren Laraba.

A cewar ma'aikatar, an daƙile hare-haren ne a yankuna da dama, ciki har da Moscow da Yaroslavl, inda ɗaya daga cikin manyan matatun man Rasha, Slavneft-Yanos, take.

Rahotanni sun ce an ga baƙin hayaƙi mai yawa na tashi sama a birnin Yaroslavl bayan harin da jiragen marasa matuƙa da Ukraine s**a kai.

Gwamnan yankin, Mikhail Evraev, ya ce wannan shi ne hari mafi girma da yankin ya taɓa fuskanta, kumaan lalata jirage marasa matuƙa 92 a yankin kaɗai.

A gefe guda kuma, jami'an Ukraine sun ce hare-haren Rasha sun kashe mutum uku a birnin Balakliya, yayin da wasu 12 s**a jikkata a yankin Sumy.

Gwamnatin jihar Kwara da ke arewa ta Tsakiyar Najeriya ta tabbatar da sako mutanen da aka yi garkuwa da su a yukan Woro ...
05/08/2026

Gwamnatin jihar Kwara da ke arewa ta Tsakiyar Najeriya ta tabbatar da sako mutanen da aka yi garkuwa da su a yukan Woro da Nuku da ke ƙaramar hukumar Kiama bayan wata shida a hannun ƴanbindigar.

A watan Fabrairin wannan shekarar ne dai wasu ƴanbindiga s**a kai hari ƙauyukan biyu tare da kashe fiye da mutum 75 da sace aƙalla mutum 175.

Cikin wata sanarwa da gwmanatin jihar ta fitar da tabbatar da sakin mutanen, sai dai ba ta yi ƙarin haske kan adadin wadanda aka sako ɗin ba.

Haka kuma sanarwar ba ta fayyace ko an biya kuɗin fansa kafin sakin mutanen ba.

Wani ɗan majalisar wakilai na yankin ya shaida wa BBC cewa yanzu haka mutanen da aka sako na hannun jami'an tsaro, inda suke samun kulawar likitoci, kafin sada su da iyalansu.

Harin da aka kai cikin watan Fabrairu lokacin sace mutanen, ya kasance ɗaya daga cikin munanan hare-haren da aka fi samun asarar rayuka a yankin cikin shekarun baya-bayan nan.

Hukumomi sun ɗora alhakin harin kan mayaƙa masu iƙirarin jihadi da ke cikin dazukan kusa da iyakar Najeriya da Benin.

Sakin mutanen ya zo ne makonni bayan sakin ɗalibai da malamai 44 da aka yi garkuwa da su a jihar Oyo, bayan sun shafe sama da makonni bakwai a hannun masu garkuwa da mutanen.

Najeriya na cewa tana kara ƙaimi wajen hare-haren soji kan ƙungiyoyin masu ɗauke da makamai, amma har yanzu ƙasar fuskantar ƙalubalen tsaro da dama, da s**a haɗa da hare-haren masu iƙirarin jihadi da garkuwa da mutane masu yawa.

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya bayyana cewa Falasɗinu na da matuƙar muhimmanci a manufofin harkokin wajen ƙa...
05/08/2026

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya bayyana cewa Falasɗinu na da matuƙar muhimmanci a manufofin harkokin wajen ƙasarsa.

Kafofin yaɗa labaran Iran sun ruwaito cewa shugaban ya faɗi hakan ne yayin wata tattaunawar wayar tarho da Khalil al-Hayyah, sabon shugaban ƙungiyar Hamas.

A yayin tattaunawar, Pezeshkian ya jaddada cewa Iran za ta ci gaba da bai wa batun Falasdinu muhimmanci a manufofinta na ƙetare.

Khalil al-Hayyah ya zama sabon shugaban ofishin siyasa na Hamas bayan da ƙungiyar ta fuskanci asarar shugabanni da dama sakamakon hare-haren Isra’ila da s**a biyo bayan harin 7 ga Oktoban 2023.

Tsohon shugaban Hamas, Ismail Haniyeh, ya mutu a wani hari da aka kai masa a Tehran shekaru biyu da s**a gabata yayin da ya je halartar bikin rantsar da Pezeshkian a matsayin shugaban ƙasar Iran.

Hamas na ci gaba da fuskantar matsin lamba da hare-hare daga Isra’ila a rikicin da ya daɗe yana ci gaba a yankin.
゚viralシ

Mataimakin Shugaban Hukumar KAROTA Hon. Auwalu Lawan Shaaibu ya bayyana kaɗuwarsa bisa mutuwar Muhammadu Buhari (kosan w...
05/08/2026

Mataimakin Shugaban Hukumar KAROTA Hon. Auwalu Lawan Shaaibu ya bayyana kaɗuwarsa bisa mutuwar Muhammadu Buhari (kosan waƙa).

Aranposu ya bayyana hakan ne ta cikin wani saƙon ta'aziyya da ya aikewa iyalan mawaƙin, wanda ya bayyana matsayin mai bayar da gudunmawa wajen ci gaban Al'ummar Najeriya.

Ta cikin sanarwa ya yi masa Addu'ar samun rahamar Allah tare da miƙa sakon ta'aziyarsa ga Mai girma Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf da iyalin mamacin.

Kosan waƙa dai ya riga mu gidan gaskiya bayan wata jinya da yayi fama da ita a asibiti a jihar Kano, wanda bayan rasuwar.

Address

NO. 80 ALI SHUGABA Street
Kano

Telephone

+2349027620636

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when G2 Times Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to G2 Times Hausa:

Shortcuts

Share