09/08/2026
Mayaƙan Houthi na Yemen sun ce sun kai harin jirgin sama mara matuƙi kan wata matatar man fetur ta Saudiyya da ke gaɓar Bahar Maliya.
Kakakin rundunar sojin ƙungiyar, Yahya Saree, ya ce harin da aka kai kan matatar man fetur ta Aramco da ke Jazan, martani ne kan kutsen da Saudiyya ke yi a arewa maso yammacin Yemen.
Ma'aikatar makamashi ta Saudiyya ta ce jami'an kashe gobara sun yi nasarar kashe gobarar da ta tashi a wurin.
Mayaƙan Houthi sun sanar da kafa katanga ta ruwa kan Saudiyya a watan da ya gabata, lamarin da ya sake rura wutar rikicin tare da ƙara matsin lamba kan samar da makamashi a duniya, wanda yaƙin Iran ya haifar.
A gefe guda kuma, babbar hukumar tsaron Iran ta yi gargadin cewa ba za a bude mashigar ruwan Hormuz ba har sai Amurka ta amince da wasu bukatu guda shida, ciki har da sassauta takunkuman da aka ƙaƙaɓawa Iran, biyan diyya kan barnar yakin, da kuma kawo karshen katangar da aka sanya wa tashoshin jiragen ruwa na Iran.
゚viralシ