G2 Times Media

G2 Times Media A WANNAN SHAFI ZAKU SAMI SAHIHAN LABARAI DA SHIRIN BINCIKE (FACT-CHECKING) CIKIN HARSHEN HAUSA

Gamayyar kungiyoyin Matasa a Arewacin Najeriya sun kai ziyara ta musamman ga shugaban kamfanin SAGAMA Construction Ltd, ...
31/08/2025

Gamayyar kungiyoyin Matasa a Arewacin Najeriya sun kai ziyara ta musamman ga shugaban kamfanin SAGAMA Construction Ltd, SAGAMA Homes(Baban kamfanin gine gine da dlilacin gidace a tarayyar na Najeriya) Alhaji Ali Nuhu, a jihar Kano.

Ziyarar ta gudana kar kashin Jagorancin Comr. Aliyu Abdul Garo, da Fatima Joel Ajemasu, inda kungiyoyin s**a mika shaidar girmamawa da yabo bisa irin gudunmawar da Alh. Ali Nuhu ke bayarwa wajen tallafawa matasan Arewacin Najeriya.

Shugabannin gamayyar kungiyoyin sun bayyana cewa manufar wannan ziyara ita ce nuna godiya da yabo bisa irin kokarin da shugaban kamfanin SAGAMA Homes ke yi wajen karfafawa matasa ta hanyar samar da ayyukan yi, horas da Matasa, da kuma inganta ci gaban tattalin arziki a yankin Arewa.

Sun kuma bayyana cewa irin wannan jajircewar 'Yan kasuwa masu kishin kasa yana da matukar tasiri wajen gina al’umma mai karko, tare da karfafa zumunci da hadin kai tsakanin shugabanni da matasa.

Kungiyoyin sun yi addu’ar Allah ya kara daukaka kamfanin SAGAMA Construction tare da ba shi ikon ci gaba da gudanar da ayyukan alheri da taimako ga matasan Arewacin Najeriya da kasa baki daya.

Hukumar gudanarwar Azama TV ta naɗa Aminu Shehu Dauda wanda aka fi sani da Aminu S.D. Hotoro a matsayin sabon General Ma...
30/08/2025

Hukumar gudanarwar Azama TV ta naɗa Aminu Shehu Dauda wanda aka fi sani da Aminu S.D. Hotoro a matsayin sabon General Manager na tashar. Wannan nadin wani muhimmin mataki ne na tabbatar da ingantaccen shugabanci da kyakkyawan gudanar da harkokin tashar.

Aminu S.D. Hotoro gogaggen ɗan jarida ne mai ƙwarewa a harkokin talabijin. Ya yi aiki a sassa daban-daban ciki har da Sashen Fasaha, Sashen Shirye-shirye, Sashen Labarai da kuma Sashen Gudanarwa, lamarin da ya ba shi cikakkiyar fahimta kan dukkan ɓangarorin aikin gidan talabijin.

Hukumar Gudanarwar Azama TV ta bayyana wannan nadi a matsayin wani babban mataki na tabbatar da hangen nesan tashar. Haka kuma ta yi kira ga sabon GM ɗin da ya yi amfani da ƙwarewarsa wajen kawo ci gaba mai dorewa ga tashar.

“Mun yi imanin cewa kwarewar Aminu S.D. Hotoro da hangen nesansa za su taka muhimmiyar rawa wajen ɗaga matsayin Azama TV zuwa matsayi na farko a matsayin tashar talabijin da ke yin shirye-shirye cikin harshen Hausa tare da ingantattun ƙa’idojin duniya,” in ji hukumar gudanarwar Azama TV.

Azama TV sabon gidan talabijin ne da ke yada shirye-shiryensa a harshen Hausa a kan AMOS-17 Satellite, Frequency 11719, Symbol Rate 30000. Tashar ta kuduri aniyar kawo shirye-shiryen da s**a haɗa da labarai sahihai, al’adu, nishaɗi da ilimi, tare da mai da hankali kan al’ummar Arewacin Najeriya da kuma masu kallo a sassan Afirka baki ɗaya.

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa reshen jihar kano ta tabbatar da k**a wani matashi da take zargi da...
25/08/2025

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa reshen jihar kano ta tabbatar da k**a wani matashi da take zargi da safarar kwayar Tramadol dubu 7 daga jihar legas zuwa kano.
Wannan na cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar ASN Sadiq Muhammad Maigatari ya aikewa G2Times media a safiyar litinin 25 ga watan Agustan 2025, a madadin kwamandan rundunar ta jihar Kano.
Sanarwar ta ce Jami’an hukumar dake kiru sun sami nasarar k**a wani matashi mai suna Adamu Yusuf dan shekara 29 a ranar 23 ga watan agusta a Kwanar Dangora akan hanyar sa ta shigowa Kano daga Legas dauke da kwayoyin.
Wanda ake zargin ya zuba kwayoyin da nauyin su ya kai kilogram 4.1, ne cikin wata jarkar Mai mai daukar lita 25, wannan ya nuna kokarin da hukumar ta ke na yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi a Nijeriya.
゚viralシfypシ゚viralシ

Hukumar KAROTA ta bayyana cewa dukkan wanda ta k**a da karya dokar tuƙi ta "One Way" za ta yi masa tarar Naira dubu 10.H...
22/08/2025

Hukumar KAROTA ta bayyana cewa dukkan wanda ta k**a da karya dokar tuƙi ta "One Way" za ta yi masa tarar Naira dubu 10.
Haka kuma sai ya yi gwajin ƙwaƙwalwa kafin a bashi abin hawansa.

Mataimakin Daraktan hukumar Hon. Auwal Aranposu ne ya bayyana hakan a wata wallafa da yayi a shafin sa na Facebook.

Kamar dai yadda dokar hukumar ta shekarar 2012 da aka yiwa gyaran fuska a shekarar 2022 ta bayyana baza a bawa dukkan wanda ya karya wannan doka abin hawansa ba har sai ya je asibiti ya yi gwajin kwakwalwa.

Me ne ra'ayin ku

Muna kira ga Mai Girman Gwamnan Kano ya Bawa Barrister Ibrahim Isah Aliyu muƙamin Kwamishinan Sufuri.Hon. Aliyu Adebayo ...
22/08/2025

Muna kira ga Mai Girman Gwamnan Kano ya Bawa Barrister Ibrahim Isah Aliyu muƙamin Kwamishinan Sufuri.

Hon. Aliyu Adebayo Gwagwarwa ya bayyana hakan ne yayin da yake ganawa da G2TIMES media, inda ya ce Barrister Ibrahim Aliyu yana kokarin taimakawa ƴan Jam'iyyar NNPP a karamar hukumar Nassarawa da jihar Kano.

Don haka yana da kyau Mai girma Gwamna ya duba wannan buƙata ta mu mu Al'ummar jihar Kano.

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya taya ƴanmatan nan uku da s**a nuna bajinta a wata gasa ta TeenEagle da aka yi a Birtan...
06/08/2025

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya taya ƴanmatan nan uku da s**a nuna bajinta a wata gasa ta TeenEagle da aka yi a Birtaniya.

Ƴanmatan Nafisa Abdullahi mai shekara 17 ta haskaka a gasar Turanci yayin da Rukayya Muhammad Fema mai shekara 15 ta fi kowa hazaƙa a muhawara da Hadiza Kashim Kalli ta lashe kyautar mafi fiƙira.

Cikin wata sanarwa da kakakin shugaban ƙasar, Bayo Onanuga ya fitar, Tinubu ya yaba wa matasan ƴan Najeriyar saboda bajintar da s**a nuna a gasar .

Ya kuma yaba wa makarantu da sauran cibiyoyin karatu inda ya ce irin waɗannan nasarori na bayyana yanayin ingancin da ilimi ke da shi a Najeriya.

Shugaba Tinubu ya bayyana ilimi a matsayin tushen duk wani ci gaban ƙasa, abin da ya sa ma a cewarsa gwamnatinsa ke fifita ɓangaren tare da ganin ta kawar da duk wata matsala ta kuɗi da za ta hana ƴan ƙasar ci gaba da karatu ta hanysar tsarin tallafin karatu na NELFUND.

Shugaban ƙasar ya kuma ƙarfafa wa Nafisa da Rukayya da Hadiza gwiwar mayar da hankali a karatu tare da yi masu fatan samun ƙarin nasarori a rayuwarsu.

Source: bbc

Wannan dai na zuwa ne daidai lokacin da wa’adin aikin Bashir Adewale Adeniyi zai kare karshen watan mai k**awa wato 31 g...
31/07/2025

Wannan dai na zuwa ne daidai lokacin da wa’adin aikin Bashir Adewale Adeniyi zai kare karshen watan mai k**awa wato 31 ga watan Agustan 2025.

Ta cikin wata sanarwa da ta fito daga fadar shugaban kasar, mai dauke da sa hannun Bayo Onanuga mashawarci na musamman ga shugaban kasa a fanin yada labarai da dabaru, wadda ta ce Karin wa’adin zai taimakawa Adeniyi wajen tabbatar da kudirin gwamantin tarayya na inganta lamurran a kasar musamman abin da ya shafi hukumar.
BBC Hausa

28/07/2025

Wasu rahotannin na bayyana cewa Ƴanbindiga sun kashe wasu mutum 38 ta hanyar yi musu yankan rago, daga cikin mutum 56 da s**a yi garkuwa da su sak**akon gaza biyan kuɗin fansa da ƴanbindigar suke nema.

Mutanen da aka kashe ɗin sun kasance ƴan ƙauyen Banga da ke ƙarƙashin ƙaramar hukumar ƙauran Namoda da ke jihar Zamfara.

kafara BBC ta rawaito yadda Shugaban ƙaramar hukumar, Manniru Haidara Ƙaura wanda ya shaida mata yadda al'amarin ya faru, ya ce yawancin waɗanda aka yi wa yankan ragon matasa ne.

"Bayanin da muka samu shi ne sun yi musu yankan rago ne. Abin da ya faru shi ne ƴanbindigar sun nemi kuɗin fansa kuma aka harhaɗa aka ba su k**ar yadda s**a nema, inda kuma s**a saki mutum 18 da s**a haɗa da mata 17 da ƙaramin yaro guda ɗaya, a ranar Asabar,"in ji Haidara.

Kimanin watanni huɗu ne dai ƴan fashin daji s**a far wa ƙauyan na Banga da ke ƙaramar hukumar Ƙauran Namoda a jihar ta Zamfara inda s**a yi garkuwa da mutum 56.

"Bayanan da s**a zo mana shi ne ƴanbindigar sun nemi kuɗin fansa na naira miliyan 50 kuma an ba su amma duk da haka s**a zaɓi su kashe mutum 38. Su s**a san dalilin kashe su. Mutane ne da ba su da tunani da ba su da hankali. Sun manta ƴanuwansu ne suke kashewa kuma za mu haɗu a gaban Allah."

Shugaban ƙaramar hukumar ya kuma ƙara da cewa kawo yanzu mutum 16 da s**a dawo da su ranar Asabar na asibiti inda ake kula da lafiyarsu, inda gawar su kuma mutum 38 da aka kashe na wurin ƴanbindigar "k**ar yadda s**a saba ai ba sa bayar da ita."

Dangane kuma da abin da ya shafi jami'an tsaro a yankin, Manniru Haidara Ƙaura ya ce duk da a wasu wuraren yana jin labarin irin ƙoƙarin da jami'an tsaro ke yi amma a yankinsa labarin ya sha banban.

"Alal haƙiƙanin gaskiya jami'an tsaro ba sa ba mu irin tallafin da ya k**ata mu samu daga ɓagarensu ba ma samu....illa dai askarawa na jihar Zamfara su ne kawai suke taimakon mu."

Jami'an tsaron Najeriya dai musamman sojoji sun sha musanta zarge-zargen da ake yi musu na rashin ka ɗauki a wuraren hare-hare, inda suke cewa jama'a ne ba sa sanar da su da wuri sannan a mafi yawancin lokuta mutane ba su san irin koƙarin da suke yi ba.

Kwamitin zartarwa na Jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya, ya amince da naɗin Farfesa Nentawe Yilwatda  a matsayin sabon s...
24/07/2025

Kwamitin zartarwa na Jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya, ya amince da naɗin Farfesa Nentawe Yilwatda a matsayin sabon shugaban jam'iyyar na ƙasa.

An haifi Farfesa Yalwanta 8 ga watan Agustan 1968 dan siyasa ne da ya fito daga jihar Filato a Tsakiyar kasar, wanda masani ne a fannin Electrical engineering.

Wanda kafin wannan matsayi shine ministan jinƙai da kare aukuwa bala'oi a Nijeriya.

Wata kotun tarayya a jihar Kano dake arewa maso yammacin Nijeriya ta yanke wa Abubakar Ibrahim G. Fresh hukuncin daurin ...
24/07/2025

Wata kotun tarayya a jihar Kano dake arewa maso yammacin Nijeriya ta yanke wa Abubakar Ibrahim G. Fresh hukuncin daurin wata biyar a gidan gyaran hali ko kuma biyan tarar Naira 200,000, bayan samunsa da laifin wulakanta takardun kudi na Naira.

An gurfanar da shi a gaban Babbar Kotun Tarayya mai lamba 1 da ke Kano, bisa zargin watsa takardun kuɗi yayin wata huldar nishadi a shagon Rahama Sa’idu da ke unguwar Tarauni.

Bayan karanta masa tuhumar, G. Fresh ya amsa laifinsa, inda kotun ta yanke hukunci nan take.

22/07/2025

Ko me ya sa Shugaban Ƙasa waɗannan kalamai?

Hukumar dake lura da zirga-zirga ababan hawa ta jihar Kano KAROTA ta ci tarar wani direban motar kurkura da ya take sabb...
21/07/2025

Hukumar dake lura da zirga-zirga ababan hawa ta jihar Kano KAROTA ta ci tarar wani direban motar kurkura da ya take sabbin Shukokin ado da gwamnatin Kano ke yi a tsakiyar tituna domin kawata birnin.

Wannan na cikin wata sanarwa da ta fito daga hukumar wadda ta ce hukumar ta ci tarar direban ne bisa umarnin Kwamishinan Muhalli na jihar Kano, Dr. Dahiru M. Hashim, tare da tilasta masa ya maye gurbin bishiyun da ya lalata.

Mataimakin shugaban hukumar, Auwal Aranposu, ya yi gargaɗi ga direban da masu amfani da ababan hawa a jihar da su kiyaye dokokin muhalli domin kauce wa hukunci.

Address

NO. 80 ALI SHUGABA Street
Kano

Telephone

+2349027620636

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when G2 Times Media posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to G2 Times Media:

Share