G2 Times Post

G2 Times Post A WANNAN SHAFI ZAKU SAMI SAHIHAN LABARAI DA SHIRIN BINCIKE (FACT-CHECKING) CIKIN HARSHEN HAUSA

Fiye da mutane 100 ne s**a rasu rayukansu, mafi yawansu ƴan kasuwa yayin wani harin kuskure da rundunar sojin Najeriya t...
13/04/2026

Fiye da mutane 100 ne s**a rasu rayukansu, mafi yawansu ƴan kasuwa yayin wani harin kuskure da rundunar sojin Najeriya ta ƙaddamar akan kasuwar Jilli da ke kan iyakar Borno da Yobe a arewacin Najeriya.

Shaidun gani da ido sun tabbatar da mutuwar fiye da mutane 100 a harin na kasuwar mako mako ta Jilli, yayin da wasu ke cewa adadin ya kai 200.

A tattaunawar RFI Hausa da wasu da s**a shaida faruwar lamarin, sun ce a halin yanzu mutanen yankin na cikin mawuyacin hali da kuma fargaba.

Haka zalika, wani da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce harin ya faru ne da tsakar ranar jiya Asabar ana tsaka da cin kasuwa, inda mutane s**a ji saukar bama-bamai kwatsam.

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Amnesty International ta tabbatar da mutuwar fiye da mutane 100, inda ta yi Allah wadai da wannan hari.

Daraktan Amnesty a Najeriya, Malam Isa Sunusi ya ce abun takaici ne yadda sojojin ƙasar ke kai hari da sunan kuskure, duk da cewa sun sha kai makamancinsa a baya amma basa gyara kuskurensu.

Rundunar sojin saman Najeriya dai ta ce ta yi nasarar halaka ƴan ta’adda a harin da ta kai yankin na Jilli, kodayake ba ta ce komai ma dangane da fararen hular da s**a mutu.

Ba wannan ne karon farko da sojojin Najeriya ke kai makamancin wannan hari ba da suke kira na kuskure, kan fararen hular da basu ji ba basu gani ba.

RFI Hausa

Wasu rahotanni daga jihar Borno sun bayyana cewa wasu jiragen yaki sun saki Boma-bomai kan jama'a, a wani kauye dake Kar...
12/04/2026

Wasu rahotanni daga jihar Borno sun bayyana cewa wasu jiragen yaki sun saki Boma-bomai kan jama'a, a wani kauye dake Karamar hukumar Gaidam.

Wannan mumunan labari da ke fitowa daga arewacin Najeriya, ya auku ne a wani yankin jihar Yobe da ke iyaka da jihar Borno, kuma har ya zuwa wannan lokaci ba a iya tantance adadin rayuka da s**a salwanta ba. Abu ne da ya faru lokacin da fararen hula ke cin kasuwa.

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Iran, Haji Babaei ya ce mashigar Hormuz ta kasance wurin da Tehran ba ta wasa da sh...
12/04/2026

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Iran, Haji Babaei ya ce mashigar Hormuz ta kasance wurin da Tehran ba ta wasa da shi, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Mehrs mai alaƙa da dakarun juyin juya halin ƙasar ta ruwaito.

Ya ƙara da cewa Iran ce ke da cikakken iko da mashigar, kuma dole jirage su biya haraji kafin wucewa.

A ɗaya gefen kuma Shugaba Trump ya dage cewa za a buɗe mashigar ''nan ba da jimawa ba'', kamar yadda ya wallafa a shafinsa na sada zumunta.

Mataimakin Shugaban Amurka, JD Vance bai ambaci mashigar ta Hormuz ba a jawabin da ya yi wa manema bayan tattaunawar da s**a ɗauki sa'o'i suna yi da wakilan Iran a Pakistan.

Muhimmiyar hanyar ruwan, wadda kashi 20 cikin 100 na man fetur da iskar gas na duniya ke bi ta wurin - na daga cikin sharuɗɗan tattaunawar.

Muhimmin sharaɗin da aka saka a tattaunawar shi ne wucewa ta mashigar lami lafiya.

Tun da farko rundunar sojin Amurka a Gabas ta Tsakiya ta ce jiragen sojinta biyu sun wuce ta mashigar a aranar Asabar, kodayake Iran ta musanta iƙirarin.

Rundunar juyin juya halin Iran ta yi gargaɗin kai hari kan duk jirgin sojin da ya yi yunƙurin wucewa ta mashigar.

11/04/2026

Suwa Gwamnatin Najeriya ta lisafta cikin wadanda ke daukar Nauyin Ta'addanci a Kasar.

Dan Majalisa dake wakiltar Al’ummar kananan hukumomin Rano, Kibiya, da Bunkure, a zauren majalisar wakilai ta Najeriya H...
11/04/2026

Dan Majalisa dake wakiltar Al’ummar kananan hukumomin Rano, Kibiya, da Bunkure, a zauren majalisar wakilai ta Najeriya Hon.

Kabiru Alhassan Rurum, ya aikewa mai girma Gwamnan jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, sako bangajiya bisa ziyarar ta’aziyya da ya kai wa Mai Martaba Sarkin Rano, Alhaji Muhammad Isa Umar.

Wannan ziyara ta biyo bayan rasuwar mahaifiyar Sarkin, marigayi Hajiya Maimuna Isah Umar, da kuma rasuwar Mataimakin Sakataren Shirye-shirye na jam’iyyar APC na jiha, marigayi Abdussalam Umar Ginsau.

Wannan na cikin wata sanarwa da mai taimakawa Danmajalisar a faninn yada labarai Fatihu Yusuf Bichi ya fitar wadda ta ce “a madadin Masarautar Rano da daukacin al’ummar Rano, Kibiya, da Bunkure, Hon. Alhassan Rurum ya mika godiya ta musamman ga mai girma Gwamna Abba Kabir Yusuf, bisa wannan karamci na nuna juyayi da jajantawa Al’ummar Masarautar Rano masu daraja.

Hon. Rurum ya bayyana cewa irin wadannan ziyarce-ziyarce suna kara karfafa dankon zumunci tsakanin gwamnati da masu rike da sarautun gargajiya, sannan suna nuna irin shugabanci na kwarai da ke tsayawa tare da jama’a a lokutan rashi.

Daga karshe, ya yi addu’ar Allah ya jikan wadanda s**a rasu da rahama, sannan ya ba wa iyalansu da daukacin Masarautar Rano hakurin jure wannan rashi.

Hukumar leƙen asiri ta Amurka ta  bayyana cewa China na shirye-shiryen isar da sabbin makaman kariya daga hare-haren sam...
11/04/2026

Hukumar leƙen asiri ta Amurka ta bayyana cewa China na shirye-shiryen isar da sabbin makaman kariya daga hare-haren sama ga ƙasar Iran a ’yan makwanni masu zuwa, kamar yadda CNN ta ruwaito a ranar Juma’a, tana mai ambatar mutane uku da suke da masaniya kan lamarin.

CNN ta ce akwai alamu da ke nuna cewa China na ƙoƙarin tura kayayyakin ta wasu ƙasashe na daban domin ɓoye asalin inda makaman s**a fito.

Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka da Fadar White House da kuma ofishin jakadancin China da ke birnin Washington ba su mayar da martani ba dangane da buƙatar jin ta bakinsu da kamfanin dillancin labarai na Reuters ya nema.

CNN ta bayyana cewa China tana shirye-shiryen tura makaman kariya daga hare-haren jiragen sama da ake ɗora su a kafaɗa waɗanda aka sani da MANPADs, tana mai ambatar majiyoyin da ba ta bayyana sunansu ba.

Gwamnatocin Amurka da Iran na shirin gudanar da wata babbar tattaunawa a ranar Asabar a birnin Islamabad na ƙasar Pakistan, da nufin lalubo hanyoyin kawo ƙarshen yaƙin da s**a kwashe makwanni shida suna fafatawa.

Najeriya ta sako sunayen wasu mutane 48 da take zargin su ke daukar nauyin ta'addancin da ke addabar kasar. Duk da cewa ...
11/04/2026

Najeriya ta sako sunayen wasu mutane 48 da take zargin su ke daukar nauyin ta'addancin da ke addabar kasar.

Duk da cewa akwai wasu da sunayensu s**a fito cikin jerin wadanda ake zargin, ya zuwa yanzu dai gwamnatin ba ta kai ga bayar da cikakkun bayanai a kan mutanen ba.

ba dai wannan ne karon farko da kasar ke furta cewa wasu a kasar ne ke daukar nauyin rashin zaman lafiyar dake addabar al'umma ba, sai dai a wannan lokacin ana tsoron yin amfani da gabatowar siyasa wajen ayyana sunayen wadanda zasu iya bawa gwamnatin ruwa a kakar zabe mai gabatowa.

ko a lokacin shugaba buhari an bayyana cewa su daga cikin jami'an gwamnati ne ke daukar nauyin ta'addanci a kasar ko da yake har zuwa karshen Gwamnatin ba'a kai ga bayyana ko su waye ke daukar nauyin ba.

Da Alama dai Tinubu na kokarin yin abinda gwamnatocin baya s**a gagara yi akan matsalar rashin tsaron kasar.

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya bukaci ‘yan kasar su sake kasancewa masu karfin hali, saboda har yanzu kasar na cikin y...
11/04/2026

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya bukaci ‘yan kasar su sake kasancewa masu karfin hali, saboda har yanzu kasar na cikin yanayi mai kyau idan ka kwatanta da wasu kasashen.

Tinubu ya bayyana ne yayin da yake jawabi a wata ziyarar aiki da ya kai jihar Bayelsa, da kuma kaddamar da wasu ayyuka a jihar, yana Magana ne kan yadda man Fetur yayi tsada a kasar gami da Karin wahalhalu da al’umma ke fuskanta sakamakon hakan.

Ya kara da cewa yana jin koke-koken da al’umma key i ta fannoni daban- daban na tattalin arziki.

“Farashin man fetur ya yi tsada sosai, amma ku duba wasu ƙasashe, kawai mu gode wa Allah tare cewa halin da kuke ciki ya fi na wasu kyawu.”

Tinubu ya kwatanta halin da Nijeriya ke ciki da na sauran ƙasashen Afirka, inda ya bayyana cewa wannan ƙalubalen ba a nan kaɗai ya tsaya ba.

“Ku duba abin da ke faruwa a Kenya, da ma sauran ƙasashen Afirka, ku ji irin abubuwan da suke fuskanta. Ba za mu koma baya ba. Za mu ci gaba da nemo hanyoyin rage raɗaɗin wahala ga marasa ƙarfi. Wannan gwamnati ce mai nuna kulawa,” in ji shi.

Shugaban ya ce gwamnati na ƙoƙarin sauƙaƙa wa ’yan ƙasa matsalolin da suke fuskanta, sannan ya ɗora alhakin matsin tattalin arzikin kan wasu abubuwa da s**a shafi duniya baki ɗaya.

Majalisar dokokin Iran ta samar da wani daftarin dokoki kan yadda ƙasar za ta riƙa iko da mashigar Hormuz, kuma ana sa r...
10/04/2026

Majalisar dokokin Iran ta samar da wani daftarin dokoki kan yadda ƙasar za ta riƙa iko da mashigar Hormuz, kuma ana sa ran kaɗa ƙuri'a kan daftarin a cikin mako mai zuwa.

Shugaban hukumar kula da ayyuka na majalisar, Mohammed Reza Rezaei Kochi ya ce daftarin ya ƙunshi sauye-sauye kan yadda jiragen ruwa ke ratsawa ta mashigar Hormuz sannan kuma akwai tsarin karɓar kuɗaɗe daga jiragen.

Mista Kochi ya bayyana wa kafar dillancin labarai ta Fars cewa "ɗaukacin ƴan majalisar za su amince da daftarin sannan daga baya a sanar da fara amfani da shi".

Bayanai sun nuna cewa daftarin ya ƙunshi wasu matakai guda biyar:

- Haramcin ratsawar jiragen abokan gaba: Za a haramta wa duk wani jirgin dakon man fetur mai alaƙa da Amurka da Isra'ila ratsawa ta mashigar Hormuz har abada.

-Karɓar haraji: Za a karɓi kuɗi a matsayin jangali kan aikin yin jagora da tabbatar cewa jiragen ruwa sun ratsa ta wannan mashiga cikin aminci.

-Tallafa wa takardar kuɗin Iran: A ƙoƙarin bunƙasa darajar takardar kuɗi ta riyal, duk wani jirgi mai ratsawa zai biya jangali ne ta amfani da takardar kuɗin Iran ta Riyal.

-Amfani da sunan Mashigar Gulf: Za a buƙaci duk wani jirgin da zai ratsa ya yi amfani da asalin sunan da aka san mashigar da shi, wato mashigar Persia a duk takardun da za a cike da kuma bayanan da suke bayarwa na tafiya.

-Yadda za a kasafta kuɗi: Za a kasafta kuɗaɗen jangali da aka samu kamar haka: Za a kashe kashi 30% wajen ƙarfafa soji da tabbatar da tsaron yanki, sai kuma kashi 70% don inganta rayuwar al'umma.

10/04/2026

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya gargadi "yan Kwankwasiyya, kan Abin da ya kira cin mutuncin da suke masa.

Rabiu Musa Kwankwaso Dino Melaye Kashim Shettima Dino Melaye Rabi'u Sani Hassan

Ofishin jakadancin Amurka da ke Abuja babban birnin tarayyar Najeriya, ya sanar da soke duk wasu buƙatun neman biza da a...
10/04/2026

Ofishin jakadancin Amurka da ke Abuja babban birnin tarayyar Najeriya, ya sanar da soke duk wasu buƙatun neman biza da aka shigar.

Ta buƙaci masu neman shiga ƙasarta su duba saƙonninsu na imel don samun cikakkun bayanai kan mataki na gaba.

A wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis, ofishin Jakadancin Amurkar ya ce za a ci gaba da gudanar da tantance neman bizar a ofishin jakadancinta da ke Legas.

Sanarwar ta ce jami'anta za su ci gaba da duba bayanan ƴan Amurka ne kawai a yanzu musamman ga masu buƙatar gaggawa.

Wannan matakin na zuwa ne bayan da gwamnatin Amurka ta buƙaci jami'anta da ke aiki a Najeriya su yi gaggawar barin ƙasar, saboda dalilai na tsaro.

Amurkar ta ce duk waɗanda ayyukansu ba su zama wajibi ba, da ke a ofishin jakadancinta a birnin tarayya Abuja, su tattara kayansu da iyalai domin barin ƙasar.

A wani saƙo da ta wallafa a shafinta a ranar Laraba, Amurkar ta kuma lissafa wasu jihohin Najeriyar 23 daga kudu da arewacin ƙasar, inda ta ce suna da haɗari, kuma ta gargaɗi ƴan ƙasarta su guji tafiya zuwa waɗannan jihohin da ta ɗora su a mataki na huɗu na gargaɗi.

Rahotanni daga jihar Borno na cewa mayaƙan Boko Haram sun hallaka babban kwamandan rundunar haɗin gwiwa da ke aiki a yan...
09/04/2026

Rahotanni daga jihar Borno na cewa mayaƙan Boko Haram sun hallaka babban kwamandan rundunar haɗin gwiwa da ke aiki a yankin Benisheikh na ƙaramar hukumar Kaga da ke jihar Borno.

Birgediya Janar O.O Braimah ya rasa ransa ne tare da mayaƙan sa kai na Civilian JTF bayan da s**a yi wani ɗauki ba daɗi tsakaninsu da ƴan Boko Haram ɗin da s**a ƙaddamar da harin kan sansaninsu.

Maharan sun farwa ƙauyen Benisheikh da Pulka duk ƙarkashin ƙaramar hukumar Gwoza, inda nan take sojoji da dakarun Civilian JFT s**a mayar da martani, kuma a nan ne mutanen s**a gamu da ajalinsu.

Da take bayani rundunar sojin Najeriya ta ce mayaƙan sun afkawa ƙauyen ne da misalin ƙarfe 1 na daren Alhamis, inda s**a riƙa harbin kan mai uwa da wabi, tare da kona motocin da ke ajiye a bakin hanya.

Birgediya Janar Braimah shine Kwamanda na 4 da mayaƙan Boko Haram s**a kashe cikin watanni uku, bayan da hare-harensu s**a tsanata a baya-bayan nan.

Address

NO. 80 ALI SHUGABA Street
Kano

Telephone

+2349027620636

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when G2 Times Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to G2 Times Post:

Share