08/09/2026
Gwamnan Jihar Benue, Hyacinth Iormem Alia, ya kira taron gaggawa da ƙungiyoyin matasa da magoya bayansa daga faɗin jihar domin halartar wani taro a safiyar Talata.
Siyasarmu TV ta rawaito cewa Kwamishinan Yaɗa Labaran Jihar Benue, Solomon Iorpev, ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da ya fitar a daren Litinin, 7 ga Satumba, 2026.
Sanarwar ta ce taron zai gudana ne a IBB Square da ke Makurdi yau Talata, 8 ga Satumba, da ƙarfe 9:00 na safe, inda aka bukaci matasa da magoya baya daga ƙananan hukumomi 23 na jihar su halarta.
Gwamnatin jihar ta kuma umarci shugabannin ƙananan hukumomi da sauran shugabannin siyasa su tabbatar da tattara matasa da magoya bayan gwamnati domin halartar taron a kan lokaci.
Sai dai sanarwar ba ta bayyana sunan jam’iyyar da taron yake da alaƙa da ita ko kuma takamaiman batutuwan da za a tattauna ba.