16/06/2026
Kotun Ɗaukaka Ƙara ta soke hukuncin da Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ƙarƙashin Mai Shari’a Peter Lifu, ta yanke wanda ya umarci Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta cire rajistar wasu jam’iyyun siyasa da s**a haɗa da African Democratic Congress (ADC), Zenith Labour Party (ZLP) da wasu.
Siyasarmu TV ta rawaito, Kotun Ɗaukaka Ƙara ta amince da ƙarar daukaka ƙarar da jam’iyyun siyasar da abin ya shafa s**a shigar tare da goyon bayan INEC, inda ta bayyana cewa hukuncin Babbar Kotun Tarayya ba zai ci gaba da aiki ba.
Tun da farko, INEC ta bayyana mamakinta kan yadda Mai Shari’a Peter Lifu ya yanke hukuncin duk da cewa akwai matakan shari’a da ke gudana kan lamarin. Hukumar ta kuma nuna rashin gamsuwa da yadda ba a sanar da ita ranar yanke hukuncin ba, tana mai cewa ta samu labarin ne ta kafafen yaɗa labarai.
Da wannan sabon hukunci na Kotun Ɗaukaka Ƙara, jam’iyyun ADC, ZLP da sauran waɗanda lamarin ya shafa za su ci gaba da kasancewa cikin jerin halastattun jam’iyyun siyasa a Najeriya.
Me za ku ce?