
27/08/2025
Murtala Zhang Kenan, Ɗan Jaridar Kasar Sin da ya ƙware a magana da Harshen Hausa.
Zhang Weiwei, wanda aka fi sani da Murtala, ɗan jaridar kasar Sin da ya yi karatun Hausa a Jami’ar Beijing Foreign Studies, ya shahara a Najeriya saboda kwarewarsa wajen iya harshen Hausa. A matsayinsa na wakilin China Radio International, ya shafe kusan shekaru kimanin 6 a Najeriya inda ya gudanar da hira da fitattun mutane ciki har da Sarkin Kano, tare da nuna kishin al’adu da harshen Hausa.
Haka kuma, Murtala Zhang daga birnin Sin ya burge jama’a da iyawar Hausa k**ar jakin Kano cikin shigar gargajiya, inda ya taya Hausawa murnar Ranar Hausa ta Duniya, lamarin da ya kara jawo sha’awa da yabon muhimmancin harshen Hausa a idon duniya.