13/05/2026
Yau Shekaru 75 Da Gobarar Sinimar El-duniya A Birnin Kano
A ranar 13 ga watan Mayu 1951. Gobara ta kone gidan sinimar El-Duniya, in da ta kashe mutane 331 cikin mutane 600 da su ka shiga sinimar. Wannan dai shi ne adadi mafi yawa da aka samu asarar rayuka a wani bala’i na kwana daya a tarihin Kano, kuma gobara mafi muni a tarihin Najeriya.
Wani bincike da gwamnatin mulkin mallaka ta Birtaniya ta gudanar ya gano cewa gobarar ta tashi ne a dakin haska Fim ta kuma bazu a saman silin din gidan sinimar dake gefen kasuwannin Kantin Kwari da Sabon Gari. Kusan dukkan wadanda abin ya shafa dai samari ne masu shekaru 18-34 tare da wasu yara ciki har da wani yaro dan shekara 9 da s**a yi cincirindo a gidan sinimar.
Sai dai mafi yawan ‘yan jihar Kano sun fassara wannan bala’in a matsayin ladabtarwa daga Allah. Nan da nan aka fara yada jita-jitar cewa fim din da ake nunawa a wannan rana a El-Duniya yana nuna siffar Annabi Muhammad (SAW).
Wasu kuma sun yi imanin cewa yayin da ake gina sinimar, mutanen da ke wucewa ta hanyar yau da kullum suna la'antar ginin Cinimar, saboda yawan tsinuwar ne yasa gidan sinimar ya kone. Wadannan jita-jitar sun yi karfi sosai har ta tilastawa gwamnatin mulkin mallaka ta dauki sanarwar wayar da kan jama'a ta hanyar gidan rediyo.
- Muhammad Cisse