Abba Kabir Yusif Reporters

Abba Kabir Yusif Reporters Kwankwasiyya

Mai Girma Jagora, Sanata Dr. Rabiu Musa Kwankwaso, ya kaddamar da sabuwar makaranta mai suna Nafisatu Medical University...
21/10/2025

Mai Girma Jagora, Sanata Dr. Rabiu Musa Kwankwaso, ya kaddamar da sabuwar makaranta mai suna Nafisatu Medical University a garin Kwankwaso, dake cikin Karamar Hukumar Madobi.

Wannan gagarumin aiki yana daga cikin ayyukan alkhairi da Jagora ya assasa domin murnar zagayowar ranar haihuwarsa.

Allah ya kara wa Jagora lafiya, hikima da tsawon rai.

21/10/2025

Kwankwaso dan kishin kasa ne irinsu marigayi Malam Aminu Kano da Abubakar Rimi, in ji Shugaba Tinubu

A sakon taya murnar Kwankwaso ya cika shekaru 69 a duniya, Shugaba Tinubu ya ce tasirin siyasar Kwankwaso ya karade Arewacin Nijeriya, musamman Kano.

A madadin Mai Girma Managing Director na KASCO, Dr. Kabiru Sani Yakubu , muna mika sakon taya murna na zagayowar ranar h...
21/10/2025

A madadin Mai Girma Managing Director na KASCO, Dr. Kabiru Sani Yakubu , muna mika sakon taya murna na zagayowar ranar haihuwa ga Mai Girma Jagora na NNPP a kasa, Engr. Dr. Rabiu Musa Kwankwaso, FNSE.

Allah Ya kara maka lafiya, hikima da tsawon rai mai albarka. Jagorancinka na gaskiya, kishinka ga talaka, da jajircewarka wajen gina al’umma, sun zamo abin koyi ga dukkan masu neman ci gaban kasa.

Muna fatan Allah Ya ci gaba da kareka, Ya karfafa maka gwiwa wajen ci gaba da jagoranci cikin nasara da kwanciyar hankali.

Idris Ibrahim Adam
SR kasco

JAGORA @69 ❤️❤️❤️Amadadin Al'ummar Karamar Hukumar Ajingi Masu Albarka, Karkashin Jagorancin Me Girma Shugaban Karamar H...
21/10/2025

JAGORA @69 ❤️❤️❤️

Amadadin Al'ummar Karamar Hukumar Ajingi Masu Albarka, Karkashin Jagorancin Me Girma Shugaban Karamar Hukumar Ajingi Dr Abdulhadi Zubairu Chula Muna Taya Jagoran Darikar Kwankwasiyya Na Duniya Ash-Shaik Akaramakallahu Maulana Sanata Rabi'u Kwankwaso Murnar Cika Shekaru 69 Masu Albarka A Duniya.

Muna Rokon Allah Yasanya Albarka Da Shekaru Masu Albarka 🤲
Allah Ya baka Shugabancin Najeriya Oga ❤️

Sako Daga Shugaban Karamar Hukumar Ajingi Dr Abdulhadi Yakubu PhD. CON.
CHEIF SECURITY OFFICER AJG LG.

✍️
ENGR KHALID AJINGI
MEDIA AIDE TO DR CHULA
EXECUTIVE CHAIRMAN AJINGI LOCAL GOVERNMENT.
Tue, 21/10/2025

Ga cikakken Tarihin Gwagwarmayar Rabiu Musa Kwankwaso — ɗaya daga cikin fitattun jagororin siyasa da masu tasiri a tarih...
21/10/2025

Ga cikakken Tarihin Gwagwarmayar Rabiu Musa Kwankwaso — ɗaya daga cikin fitattun jagororin siyasa da masu tasiri a tarihin Najeriya, musamman a Arewacin ƙasar:



🟥 Cikakken Sunansa:

Injiniya (Sen.) Rabiu Musa Kwankwaso, FNSE, FNIQS, PhD

🟩 Haihuwa da Farko:
• An haife shi a ranar 21 ga Oktoba, 1956 a Kwankwaso Town, ƙaramar hukumar Madobi, Jihar Kano.
• Ya fito daga gida mai daraja, kuma iyayensa sun kasance masu tsantseni da bin addini.



🟥 Ilimi:
• Primary School: Kwankwaso Primary School (1962–1967)
• Secondary School: Gwarzo Boarding School (1968–1972)
• Technical College: Wudil Craft School, da kuma Kano Technical College.
• Tertiary: Kaduna Polytechnic – inda ya karɓi National Diploma (ND) da Higher National Diploma (HND) a fannin Injiniya.
• Ya kuma yi karatu a Middlesex Polytechnic da Loughborough University a Ingila, inda ya sami Master’s Degree in Water Engineering.
• A 2022, ya kammala PhD in Water Engineering daga Sharda University, India.



🟩 Farkon Aikin Gwamnati:
• Ya fara aiki a WRECA (Water Resources and Engineering Construction Agency) na Kano, inda ya rike mukamai daban-daban daga injiniya zuwa babban darakta.
• Gwaninta da kwarewarsa a fannin injiniya ne s**a ja hankalin gwamnati zuwa gare shi.



🟥 Shigarsa Siyasa:
• Kwankwaso ya shiga siyasa a farkon shekarun 1990, lokacin Jam’iyyar SDP (Social Democratic Party).
• Ya zama ɗaya daga cikin masu tasiri a Kano State House of Assembly, kuma daga baya aka zaɓe shi Memba a Majalisar Tarayya a 1992.
• A nan ne ya zama Deputy Speaker na House of Representatives – wanda ya nuna hazakarsa da iya jagoranci.



🟩 Zamansa Gwamna na Kano (1999–2003, 2011–2015):

🕘 Zamansa na Farko (1999–2003):
• Ya zama Gwamnan Kano a karkashin Jam’iyyar PDP bayan nasarar 1999.
• Ya kafa Tsarin Kwankwasiyya Movement – wanda ya mayar da hankali kan ilimi, ci gaban matasa, da aikin gwamnati cikin gaskiya.
• Ya kafa makarantu, hanyoyi, da asibitoci; ya samar da Civil Service Reform da tsarin free education ga talakawa.
• Duk da nasarorin da ya samu, siyasar Kano ta rikice a 2003, kuma ya sha kaye wajen neman wa’adin biyu.

🕘 Ministan Tsaro (2003–2007):
• Bayan ya bar mulki, Shugaba Olusegun Obasanjo ya nada shi Minister of Defence.
• A wannan lokacin, ya taka muhimmiyar rawa wajen gyaran tsarin tsaro da ci gaban rundunar sojijin kasa, Sam Dana ruwa

🕘 Zamansa na Biyu (2011–2015):
• Ya dawo mulki bayan shekaru 8, inda ya sake lashe zaɓen Kano a karkashin PDP, kafin daga baya ya koma APC.
• Wannan karo ya fi tasiri saboda ya mai da hankali sosai kan ilimi da ci gaban matasa:
• Ya gina sabbin jami’o’i biyu (KUST da North-West University).
• Ya tura dubban ɗalibai karatu zuwa ƙasashen waje (India, Malaysia, China, UK, da sauransu).
• Ya gina sabbin tituna, asibitoci, kasuwanni, da gidaje.
• Ya kafa Kwankwasiyya Scholarship Scheme, wanda ya taimaka wa matasa masu hazaka.

Bayan gama gwamna ya tsayar da dan Takarar Gwamna Wato tsohon gwamnan kano Ganduje kuma ya ci zabe Sannan shi kuma ya Tsaya takarar Sanata kuma yaci yayi Sanata mai wakiltar kano ta tsakiya 2025 zuwa 2019



🟥 Jagorancin Kwankwasiyya Movement:
• Kwankwasiyya – wata manhaja ce ta siyasa da ke gina adalci, ilimi, aiki tukuru, da taimakon jama’a.
• Alamarta ja ce, alamar juriya da sadaukarwa.
• Masu bin wannan tafarki suna sanye da hula ja, wadda ta zama tambari ta tunani da tsabta a siyasa.



🟩 Rayuwa Bayan Gwamnati:
• Ya tsaya takarar shugaban ƙasa a 2019 da 2023 karkashin NNPP (New Nigeria People’s Party).
• Duk da bai ci zabe ba, ya zama mai karfin tasiri a Arewa da Najeriya baki ɗaya.
• Kwankwaso yana da daraja ta kasa da kasa saboda gudunmawarsa ga ilimi, tsarin ruwa, da jagoranci mai gaskiya.



🟥 Gwagwarmaya da Gaskiya:
• Duk da tsanantawa daga abokan siyasa, bai taba daina tsayawa kan adalci da gaskiya ba.
• Ya kasance mai kare talaka, mai tsoron Allah, kuma mai kishin Arewa da Najeriya gaba ɗaya.
• Gwagwarmayarsa ta mayar da hankali kan ilimi, aikin yi, cigaban matasa, da dimokuraɗiyya mai inganci.



🟩 Gajeriyar Kammalawa:

Rabiu Musa Kwankwaso ba kawai dan siyasa ba ne — malami ne, injiniya ne, mai hangen nesa, kuma gogaggen jagora wanda ya kafa al’ada ta siyasa mai ma’ana a Kano da Najeriya baki ɗaya

21/10/2025

Madugu@69. Happy birthday to you sir Engr. Sen Rabiu Musa Kwankwaso

Isowar Mai Girma Gwamna Gidan Jagora Kwankwaso Cikin Daren Nan A Shirye Shiryen Cikar Kwankwaso Shekara 69
20/10/2025

Isowar Mai Girma Gwamna Gidan Jagora Kwankwaso Cikin Daren Nan A Shirye Shiryen Cikar Kwankwaso Shekara 69

Bayan sabbin Babura da MD KASCO, Dr Kabiru Sani YakubuK da DMD KASCO, Hon Hon Aminu Aminu Maifamfo s**a bawa SSR KASCO, ...
20/10/2025

Bayan sabbin Babura da MD KASCO, Dr Kabiru Sani YakubuK da DMD KASCO, Hon Hon Aminu Aminu Maifamfo s**a bawa SSR KASCO, Aminu Shehu Yusuf da SR KASCO Idris Ibrahim Adam Gaya, sun kuma gwangwaje su da ofisoshi domin cigaba da inganta ayyukansu na dakkowa Gwamnan Kano, Alhaji Abba K Yusuf, rahoto na musamman daga wannan Kamfani na samar da Taki na Gwamnati.

An Kammala Masallacin Sheikh Jaafar Mahmud Adam, Da Ke Ƙaramar Hukumar Rogo. Wanda Maigirma Gwamna Alhaji Abba Kabir Yus...
19/10/2025

An Kammala Masallacin Sheikh Jaafar Mahmud Adam, Da Ke Ƙaramar Hukumar Rogo.

Wanda Maigirma Gwamna Alhaji Abba Kabir Yusuf, Ya bada aikin kammalashi.

Allah Ya Saka Masa Da Mafificin Alkhairinsa.

Barka da Sauka Maigirma Gwamna Alhaji Abba K Yusuf 🙏
19/10/2025

Barka da Sauka Maigirma Gwamna Alhaji Abba K Yusuf 🙏

YANZU YANZUMai Girma Jagoran Kwankwasiyya Sen. Rabiu Musa Kwankwaso ya sauka a jahar Kano a shirye-shiryen bikin murnar ...
19/10/2025

YANZU YANZU

Mai Girma Jagoran Kwankwasiyya Sen. Rabiu Musa Kwankwaso ya sauka a jahar Kano a shirye-shiryen bikin murnar zagayowar ranar haihuwarsa da za ayi a ranar Talata 21st October 2025.

Address

Kano

Telephone

+2347065534425

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Abba Kabir Yusif Reporters posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Abba Kabir Yusif Reporters:

Share

Category