Lumana Radio International

Lumana Radio International A Broadcast Media Channel page that shares the content of Lumana Radio International, owned by Yakubu Musa Fagge
(6)

A wata sanarwa da fadar shugaban ƙasa Tinubu ta fitar, ta nuna Shugaban Najeriyar ya amince da naɗin shugabannin Kwalejo...
01/08/2026

A wata sanarwa da fadar shugaban ƙasa Tinubu ta fitar, ta nuna Shugaban Najeriyar ya amince da naɗin shugabannin Kwalejojin Horar da Aikin Noma na Tarayya guda Uku da s**a haɗa da ta Akure dake Ondo, da ta Kano da kuma ta Daɗin kowa dake Gombe.

Dr. Salisu Salisu shi shugaba Tinubun ya naɗa shugaban kwalejin koyon aikin Noman ta tarayya dake Kano, wanda mutane irinsu Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo mamallakin rukunin Jami'o'in MAAUN ke yabawa naɗin.

A wata sanarwa da hukumar jami'o'in MAAUN ɗin ta fitar, Farfesa Gwarzo ya bayyana Dr. Salisu Salisu a matsayin gogaggen masanin lamuran bincike akan harkokin noma da gwaje-gwaje, wanda yace ƙwarewarshi zata taimaka gaya wajen ƙara bunƙasa kwalejin ta fuskar bincike da sabbin fasahar noma.

Mamallakin jami'o'in MAAUN ɗin, ya godewa Tinubu bisa fifita cancanta wajen wannan naɗi, tare da bawa shugaban ƙasar tabbacin cewar ba zai yi dana sani ba.

Farfesa Gwarzo, ya kuma taya sabon shugaban kwalejin Horar da aikin Noman Salisu Salisu murna, tare da buƙatar shi da ya dage wajen bujuro da manufofi da tsare-tsare managarta da zasu taimakawa ɗaliban kwalejin da ma al'uma.

Sabon shugaban kwalejin koyon aikin Noman dai ɗan asalin Kano ne, kuma babban malami a ɓangaren gwaje-gwajen sinadarai da binciken sabbin dabarun noma, wanda ya riƙe shugabancin kwalejin na riƙon ƙwarya.

31/07/2026

Ɓoyayyun Lamuran da aka fara Ganowa Tsakanin El-Rufa'i da ICPC...!

31/07/2026

Abubuwan da aka Gano akan Tsare El-Rufa'i da ICPC ta yi...!

30/07/2026

Ƙissar yadda Baba Impossible ya kai Khalifa Isyaka Rabi’u Ƙara Kotu da Abinda Sarki Ado ya yi mai...!"

30/07/2026

"Yadda Na kai Khalifa Isyaka Rabi’u Kotu da Abinda Sarki Ado ya yi...!"

Jami'an tsaron Najeriya sun kashe wasu mutum uku da ake zargin 'yan bindiga ne, tare da ceto mutum tara da aka yi garkuw...
30/07/2026

Jami'an tsaron Najeriya sun kashe wasu mutum uku da ake zargin 'yan bindiga ne, tare da ceto mutum tara da aka yi garkuwa da su a wani samame da s**a kai a jihar Kwara, kamar yadda shafin Channels Television mai zaman kansa ya ruwaito a ranar 30 ga Yuli.

An gudanar da samamen ne tare da haɗin gwiwar jami'an Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS), dakarun tsaron gandun daji da mafarauta da kuma 'yan sa-kai a yankunan Obbo-Aiyegunle, Ejiu-Ora da Osi da ke ƙaramar hukumar Ekiti a jihar Kwara, kusa da iyakar jihar Neja.

An yi garkuwa da mutanen ne daga al'ummar Eju, kuma ana cikin tafiya da su ta cikin daji zuwa jihar Neja lokacin da jami'an tsaron s**a kai dauki.

Jihar Kwara ta fuskanci ƙaruwa a hare-haren da ake kai wa fararen hula da jami'an tsaro cikin watannin baya-bayan nan.

A ranar 22 ga Yuli, Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya amince da kafa sabon bataliyar sojoji a jihar domin yaƙar masu aikata laifuka, ciki har da 'yan bindiga da kuma ƙungiyar Mahmuda, wadda gwamnati ta bayyana a matsayin wani reshe na Boko Haram.

28/07/2026

Wani Aminin Abacha ya Faɗi Haƙiƙanin Abinda ya Kashe shi...!

28/07/2026

Haƙiƙanin Abinda Ya Kashe Abacha...!

27/07/2026

Tsakanin Kwankwaso da Rufa'i Hanga: Baba Impossible Again...!

27/07/2026

To fah! Yau kuma kamar Kwankwaso Baba ya hau...!

Address

Kano

Telephone

+2348022828280

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Lumana Radio International posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share

Category