01/08/2026
A wata sanarwa da fadar shugaban ƙasa Tinubu ta fitar, ta nuna Shugaban Najeriyar ya amince da naɗin shugabannin Kwalejojin Horar da Aikin Noma na Tarayya guda Uku da s**a haɗa da ta Akure dake Ondo, da ta Kano da kuma ta Daɗin kowa dake Gombe.
Dr. Salisu Salisu shi shugaba Tinubun ya naɗa shugaban kwalejin koyon aikin Noman ta tarayya dake Kano, wanda mutane irinsu Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo mamallakin rukunin Jami'o'in MAAUN ke yabawa naɗin.
A wata sanarwa da hukumar jami'o'in MAAUN ɗin ta fitar, Farfesa Gwarzo ya bayyana Dr. Salisu Salisu a matsayin gogaggen masanin lamuran bincike akan harkokin noma da gwaje-gwaje, wanda yace ƙwarewarshi zata taimaka gaya wajen ƙara bunƙasa kwalejin ta fuskar bincike da sabbin fasahar noma.
Mamallakin jami'o'in MAAUN ɗin, ya godewa Tinubu bisa fifita cancanta wajen wannan naɗi, tare da bawa shugaban ƙasar tabbacin cewar ba zai yi dana sani ba.
Farfesa Gwarzo, ya kuma taya sabon shugaban kwalejin Horar da aikin Noman Salisu Salisu murna, tare da buƙatar shi da ya dage wajen bujuro da manufofi da tsare-tsare managarta da zasu taimakawa ɗaliban kwalejin da ma al'uma.
Sabon shugaban kwalejin koyon aikin Noman dai ɗan asalin Kano ne, kuma babban malami a ɓangaren gwaje-gwajen sinadarai da binciken sabbin dabarun noma, wanda ya riƙe shugabancin kwalejin na riƙon ƙwarya.