Idon Mikiya

Idon Mikiya Jaridar Idon Mikiya, kafar sadarwa ce mai samar da gamsassun labarai, fayyace gaskiya shine jigon mu — 08060818081
(6)

Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Masu Riƙe Da Madafun IkoDaga Jaafar JaafarMasu riƙe da madafun iko ku bi duniya a sannu. In mu...
09/07/2026

Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Masu Riƙe Da Madafun Iko

Daga Jaafar Jaafar

Masu riƙe da madafun iko ku bi duniya a sannu. In mune yau, ba mune gobe ba. Kada ka ƙuntata wa wani don ka daɗaɗa wa gwamnati, domin gwamnati tamkar ‘zalunci’ take — ba ta dawwama. Duk gaskiyarka lokacin da kake rike da muƙamin gwamnati, in wata gwamnatin na so ta wulaƙanta ka za ta iya.

Ka duba shuhura da ƙarfin iko irin na Major Hamza Al-mustapha da Mohammed Abacha, amma da gwamnatin Obasanjo ta zo sai da s**a shafe shekaru a gidan yari.

Shin ba za ka hankalta da ƙasaita da ƙarfin iko irin na Sambo Dasuki da Bello-Adoke da Diezani Alison-Madueke da Stella Odua da Peter Godsday Orubebe da su Gordon Obua a lokacin mulkin Jonathan ba? Shin ba ka duba yadda s**a ƙarke a lokacin mulkin Buhari ba?

Shin ba za ka duba abin da ya faru da Godwin Emefiele ba ka hankalta? Mallam ka duba ƙasaita irin ta su Abubakar Malami da Hadi Sirika da Sale Mamman da Nasir El-Rufai a zamanin mulkin Buhari, yau ga shi su ne ke jewa daga kotu zuwa kurkuku.

Alƙalin tirabuna ta CCT Danladi Umar ya yi sharafinsa lokacin yana kan ganiyarsa. Ya sa an gurfar masa duk wani babba da ke takun saƙa da gwamnati, ko kuma wani mutum da gwamnati ke son ta ga bayansa. An gurfanar da shugaban majalisar dattawa Bukola Saraki da alƙalin alkalan Nigeria Justice Water Onnoghen a gabansa. Kai har Tinubu ya taɓa gurfana a gabansa.

Danladi Umar bai taɓa tunanin za a iya cire shi ba ba bisa ƙa’ida ba, amma da yake gwamnati, gwamnati ce, rana tsaka aka yi wa doka karan tsaye, aka cire shi yana ji, yana gani, kuma yau an aike shi kurkuku.

Masu rike muƙaman gwamnati, a bi duniya a hankali!

Matsalar Wutar Lantarki Ya Kusa Zama Tarihi a Najeriya Ƙarkashin Jagorancin Shugaba Tinubu Babban matsalar dake damun Ya...
09/07/2026

Matsalar Wutar Lantarki Ya Kusa Zama Tarihi a Najeriya Ƙarkashin Jagorancin Shugaba Tinubu

Babban matsalar dake damun Yan Najeriya a fagen wutar lantarki, ta kusa zama tarihi a Najeriya, domin kaso mafi yawa a ayyukan wutar lantarki na Gwagwalada Project Plant ya kusa kammaluwa.

Wakilan na musamman da Yan jaridu daga Kafafen yada labarai a Najeriya, sun ziyarci wajen don gudanar da Binciken kwakwaf akan gaskiyar aikin wutar.

Wanda tabi tawaga ta musamman Ƙarƙashin jagorancin hadimin Shugaban kasa, Abdulaziz-Abdulaziz. Don tabbatar da shirin “Gani ya kori ji” da Abdulaziz-Abdulaziz keyi.

Wannan aikin wuta me girman mega Watt 350 na cigaba da gudana yadda ya kamata, kuma zai wadatar da dukkan fadin Najeriya.

'Gani Ya Kori Ji': Aikin Sake Gina Titin Abuja–Kaduna Ya Kai Kashi 85 Cikin 100 Na KammaluwaA ci gaba da rangadin 'Gani ...
09/07/2026

'Gani Ya Kori Ji': Aikin Sake Gina Titin Abuja–Kaduna Ya Kai Kashi 85 Cikin 100 Na Kammaluwa

A ci gaba da rangadin 'Gani Ya Kori Ji' na manyan ayyukan gwamnatin tarayya a Arewacin Najeriya, tawagar yan jarida da ke rangadi tare da Babban Mai Taimakawa Shugaban Ƙasa kan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Malam Abdulaziz Abdulaziz, ta kai ziyara aikin sake gina babbar hanyar Abuja–Kaduna, bayan kammala duba ayyukan Kaduna Western Bypass da kuma tashar Green Ville CNG da ke jihar Kaduna.

A yayin ziyarar, jami'an da ke kula da aikin sun yi wa tawagar cikakken bayani kan yadda aikin ke gudana, inda s**a bayyana cewa an kammala kusan kashi 85 cikin 100 na aikin sake gina t**in. Tawagar ta nuna gamsuwa da irin saurin aiwatar da aikin da kuma ingancin aikin da ake yi a ɗaya daga cikin manyan hanyoyin da ke da muhimmanci ga tattalin arziki da zirga-zirgar Najeriya.

An bayyana cewa t**in Abuja–Kaduna na daga cikin manyan hanyoyin da ke haɗa Babban Birnin Tarayya da jihohin Arewa, tare da sauƙaƙa zirga-zirgar matafiya, jigilar kayayyaki da gudanar da harkokin kasuwanci. Da zarar an kammala aikin, ana sa ran zai rage lokacin tafiya, sauƙaƙa cunkoson ababen hawa, inganta tsaron masu amfani da hanya da kuma ƙara bunƙasa harkokin tattalin arziki a yankunan da t**in ya ratsa.

Jami'an aikin sun kuma bayyana cewa ana sake gina t**in ne da kankare mai ƙarfi (reinforced concrete pavement) maimakon kwalta, domin tabbatar da ɗorewa, rage yawan lalacewa da kuma tsawaita rayuwar t**in. Sun ce aikin na daga cikin manyan ayyukan da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke aiwatarwa a ƙarƙashin Ajandar Sabunta Fata (Renewed Hope Agenda) domin inganta ababen more rayuwa da ƙarfafa haɗin kai tsakanin sassan ƙasar.

Da yake jawabi bayan rangadin, Malam Abdulaziz Abdulaziz ya bayyana t**in Abuja–Kaduna a matsayin ɗaya daga cikin muhimman hanyoyin sufuri a Najeriya, yana mai cewa gwamnatin tarayya ta ba aikin fifiko saboda irin gudummawar da yake bayarwa wajen haɗa yankuna da bunƙasa tattalin arziki. Ya ƙara da cewa shirin 'Gani Ya Kori Ji' na bai wa masu aikin jarida damar ganin ci gaban ayyukan gwamnati da idonsu, domin isar da sahihan bayanai ga al'umma. Tawagar ta yabawa gwamnatin tarayya da Ma'aikatar Ayyuka bisa irin ci gaban da aka samu, tare da bayyana fatan cewa kammala aikin zai ƙara sauƙaƙa zirga-zirga, inganta tsaro da kuma amfani ga miliyoyin 'yan Najeriya da ke amfani da hanyar Abuja–Kaduna.

Jajirtattun 'Yan Siyasa Ne Kaɗai Ke Iya Shiga ADC – TambuwalTsohon gwamnan Sokoto, Sanata Aminu Waziri Tambuwal, ya ce j...
09/07/2026

Jajirtattun 'Yan Siyasa Ne Kaɗai Ke Iya Shiga ADC – Tambuwal

Tsohon gwamnan Sokoto, Sanata Aminu Waziri Tambuwal, ya ce jajirtattun 'yan siyasa masu son yi wa al'umma hidima ne kaɗai za su iya shiga jam'iyyar ADC.

Tambuwal ya bayyan haka ne yayin da yake karɓar tsohon shugaban ƙaramar hukumar Tangaza, Isa Salihu Kalenjeni, zuwa jam'iyyar bayan ya fice daga APC.
TĀLLĀ: Dama ce ta musamman ga masu sha'awar fara kasuwancin data, ko sanya wa kan su, ku Sauke Application na KSBDATA daga ‘Playstore’ zuwa kan wayoyin ku yanzu ku mori Data da kati ‘Airtime’ mafi arha. 👇👇

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.ksbdata.app

Ku tuntuɓe mu ta WhatsApp 👇👇

https://wa.me/2349018986971

Ka Tabbatar Da Tsaron Peter Obi Tare Da Gaggauta Sakin Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna Nasir El-Rufai – Atiku Abubakar Ga Gw...
09/07/2026

Ka Tabbatar Da Tsaron Peter Obi Tare Da Gaggauta Sakin Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna Nasir El-Rufai – Atiku Abubakar Ga Gwamnatin Tarayya
TĀLLĀ: Dama ce ta musamman ga masu sha'awar fara kasuwancin data, ko sanya wa kan su, ku Sauke Application na KSBDATA daga ‘Playstore’ zuwa kan wayoyin ku yanzu ku mori Data da kati ‘Airtime’ mafi arha. 👇👇

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.ksbdata.app

Ku tuntuɓe mu ta WhatsApp 👇👇

https://wa.me/2349018986971

TĀLLĀ: Ku Sāyā Data Mafi Inganci Da Arha A Wurin MuIdan kuka fara amfani da kamfanin  kasuwancin DATA da katin waya na K...
09/07/2026

TĀLLĀ: Ku Sāyā Data Mafi Inganci Da Arha A Wurin Mu

Idan kuka fara amfani da kamfanin kasuwancin DATA da katin waya na KSBDATA ba za ku sake amfani da wani kamfanin ba.

Ina masu sana'ar data da katin waya? ga dama ta samu, KSBDATA mun shirya ba ku rìbà mai yawa, zaku iya siyan DATA ku sakawa kanku da wannan Application ɗin namu na KSBDATA, muddin kuka fara amfani da KSBDATA ba za ku iya dainawa ba saboda ingancin datarmu.

Ku sauke “Application” ɗinmu na KSBDATA a “Playstore” zuwa kan wayoyinku.👇
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.ksbdata.app

Ku tuntuɓe mu ta WhatsApp👇
https://wa.me/2349018986971

‘Gani Ya Kori Ji’: Aikin Kaduna Western Bypass Da Zai Rage Cunkoson Ababen Hawa a Kaduna Ya Zarce Kashi 50% Na Kammaluwa...
09/07/2026

‘Gani Ya Kori Ji’: Aikin Kaduna Western Bypass Da Zai Rage Cunkoson Ababen Hawa a Kaduna Ya Zarce Kashi 50% Na Kammaluwa

A ci gaba da rangadin ‘Gani Ya Kori Ji’ na manyan ayyukan gwamnatin tarayya a Arewacin Najeriya, tawagar manema labarai dake rangadi tare da Babban Mai Taimakawa Shugaban Ƙasa kan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Malam Abdulaziz Abdulaziz, ta kai ziyara zuwa aikin t**in Kaduna Western Bypass, domin duba yadda aikin ke gudana tare da samun bayanai kai tsaye daga jami’an da ke kula da shi.

A yayin ziyarar, jami’an kamfanin Sanford Industry Limited, masu aiwatar da aikin, sun bayyana cewa aikin ya kai sama da kashi 50 cikin 100 na kammaluwa, inda ake ci gaba da gudanar da aiki a sassa daban-daban na t**in. Sun kuma tabbatar wa tawagar cewa gwamnati ta samar da isasshen kuɗaɗen gudanar da aikin, lamarin da ya ba da damar ci gaba da aikin ba tare da tsaiko ba.

An bayyana cewa aikin, wanda aka bayar da kwangilarsa a shekarar 2021 kuma aka fara aiwatar da shi a 2023, ya ƙunshi gina t**in mai layuka biyu mai tsawon kilomita 21.5, wanda jimillar shimfiɗar kankarensa ta kai kusan kilomita 43. Haka kuma aikin ya haɗa da gina gadojin tsallaka t**i guda takwas, domin kare rayuka da inganta tsaron masu amfani da hanyar.

Jami’an aikin sun ƙara da cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta sake duba kuɗin kwangilar domin ya dace da sauye-sauyen tattalin arziki, matakin da ya taimaka wajen ƙara saurin gudanar da aikin. Sun bayyana kwarin gwiwar cewa idan aka ci gaba da aiki a wannan mataki, za a kammala aikin cikin wa’adin da aka tsara.

Manema labaran da ke cikin shirin ‘Gani Ya Kori Ji’ sun bayyana cewa da zarar an kammala Kaduna Western Bypass, zai rage cunkoson ababen hawa a cikin birnin Kaduna, ya sauƙaƙa jigilar kayayyaki da zirga-zirgar matafiya, tare da bunƙasa harkokin kasuwanci da tattalin arzikin jihar da ma yankin Arewa baki ɗaya. Sun ce aikin wata shaida ce ta ƙudirin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na ci gaba da aiwatar da manyan ayyukan more rayuwa a ƙarƙashin Ajandar Sabunta Fata (Renewed Hope Agenda) domin inganta rayuwar al’ummar Najeriya.

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙara Ƙaimi Wajen Yi Wa Kowane Ɗan Najeriya Rajistar Shaidar Ɗan Ƙasa Ta DijitalGwamnatin Tarayya ta...
08/07/2026

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙara Ƙaimi Wajen Yi Wa Kowane Ɗan Najeriya Rajistar Shaidar Ɗan Ƙasa Ta Dijital

Gwamnatin Tarayya ta ƙara ƙaimi wajen tabbatar da cewa an yi wa kowane ɗan Nijeriya rajistar shaidar ɗan ƙasa ta dijital a faɗin ƙasar, ta hanyar ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin Ma'aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai da Hukumar Kula da Shaidar Ɗan Ƙasa (NIMC).

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana hakan a ranar Laraba a Abuja yayin da ya karɓi baƙuncin Babbar Darakta kuma Babbar Jami'ar Gudanarwa ta NIMC, Dakta Abisoye Coker-Odusote, da tawagar ta, waɗanda s**a kai masa ziyarar girmamawa domin gabatar da muhimman tanade-tanaden sabuwar Dokar NIMC ta 2026.

Ministan ya ce ingantaccen tsarin tantance shaidar 'yan ƙasa yana da matuƙar muhimmanci wajen kyautata shugabanci, tsara cigaban ƙasa, bunƙasa harkokin kuɗi, haɓaka sauyin fasahar zamani da kuma aiwatar da Ajandar Sabunta Fata ta Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu.

Ya ce: “Tsarin tantance shaidar 'yan ƙasa shi ne ginshiƙin ajandar sauye-sauyen Shugaban Ƙasa. Domin idan za a aiwatar da gyare-gyare, dole ne a san waɗanda ake yi wa. Idan ba a san adadin jama'a ba, da tsarin yawan su da yadda s**a kasu, ta yaya za a tsara musu ingantattun tsare-tsare?”

Idris ya yaba wa shugabancin Dakta Coker-Odusote, yana mai cewa yi wa sama da mutum miliyan 136 rajista babban cigaba ne, amma har yanzu akwai kusan mutum miliyan 100 da ba a yi wa rajista ba.

Ya ce: “Mutum miliyan 136 da aka riga aka yi wa rajista babban cigaba ne, amma har yanzu akwai kusan 'yan Nijeriya miliyan 100 da s**a rage, kuma su ma ya kamata a yi musu rajista. Kowane ɗan Nijeriya ya cancanci a saka shi cikin tsare-tsaren cigaban ƙasa.”

Ministan ya ce cimma burin yi wa kowa rajista yana buƙatar ci gaba da wayar da kan jama'a, musamman a matakin ƙananan hukumomi da al'ummomi. Don haka ya buƙaci NIMC da ta ƙara haɗin gwiwa da Hukumar Wayar da Kai ta Ƙasa (NOA), wadda ke da ofisoshi a dukkan ƙananan hukumomi 774 na ƙasar nan.

Ya ce: “Hukumar Wayar da Kai ta Ƙasa ita ce mafi dacewa wajen isa ga al'ummomin karkara. Ina roƙon ku da ku ƙara ƙarfafa haɗin gwiwar ku da NOA domin mu duka mu tabbatar da cewa kowane ɗan Nijeriya ya fahimci muhimmancin tsarin shaidar 'yan ƙasa.”

Haka kuma ya yaba wa NIMC bisa yadda ta kiyaye bayanan jama'a, yana mai cewa babu wani rahoton kutsen da ya yi sanadin fallasa bayanan masu rajista.

Ya ƙara da cewa: “Na yi farin cikin jin cewa ba ku taɓa fuskantar matsalar kutsen bayanai ko da sau ɗaya ba. Kare sirrin bayanai, gudanar da aiki cikin gaskiya da kuma amincewar jama'a su ne ginshiƙan nasarar tsarin shaidar dijital, kuma za mu ci gaba da amfani da dukkan kafafen yaɗa labarai na Ma'aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai wajen tallafa wa shirye-shiryen wayar da kan jama'a.”

Tun da farko, Darakta Janar na Hukumar Wayar da Kan Jama'a ta Ƙasa (NOA), Mallam Lanre Issa-Onilu, ya tabbatar da cewa hukumar za ta ci gaba da tallafa wa NIMC wajen wayar da kan jama'a ta hanyar cibiyoyin ta da ke faɗin ƙasar nan.

Ya ce: “Mun san muna aiki tare, amma ina fatan za ku ci gaba da tuntuɓar mu domin mu ga yadda za mu ƙara ba da gudunmawa. Muna da wakilci a wuraren da kuke son zuwa domin wayar da kan jama'a da faɗakar da su.”

A nata jawabin, Babbar Darakta ta NIMC, Dakta Abisoye Coker-Odusote, ta ce sabuwar Dokar NIMC ta 2026 ta sabunta tsarin kula da shaidar ɗan ƙasa a Nijeriya, inda ta ƙunshi tanade-tanade kan kare bayanai, tsaron intanet, inganta tsarin bayanan gwamnati na zamani da kuma ƙarfafa amincewar jama'a da tsarin dijital.

Ta ce: “Shugaban Ƙasa ya umurce mu da mu fara rajistar jama'a daga unguwa zuwa unguwa, domin yana son tabbatar da cewa mutanen karkara da na matakin al'umma ba a hana su cin gajiyar duk wani shirin tallafin gwamnati ba.”

Ta bayyana cewa hukumar ta fara gangamin rajista a dukkan unguwanni 8,809 na Nijeriya domin tabbatar da cewa an yi wa kowane ɗan ƙasa rajista, ciki har da mata, yara, masu naƙasa, mazauna karkara, 'yan gudun hijira, baƙin da ke zaune bisa doka da kuma 'yan Nijeriya mazauna ƙasashen waje.

A nasa jawabin, Shugaban Sashen Hulɗa da Jama'a na NIMC, Dakta Kayode Adegoke, ya ce sabuwar dokar ta sauya tsarin kula da shaidar ɗan ƙasa a Nijeriya baki ɗaya.

Ya ce: “NIMC ta wuce matsayin mai adana bayanai kawai, ta zama babbar hukuma ta ƙasa da ke da alhakin kula da tsarin shaidar dijital. A yanzu, NIMC ita ce kaɗai hukumar da aka ba ikon kula da tsarin shaidar dijital a Nijeriya.”

Ya ƙara da cewa dokar ta samar da tsarin doka na Digital Public Infrastructure (DPI) da Public Key Infrastructure (PKI), tare da ƙarfafa kariyar bayanan jama'a da faɗaɗa amfani da Lambar Shaidar Ɗan Ƙasa (NIN) a ayyukan gwamnati da kamfanoni masu zaman kan su.

A cewar sa, NIMC ta haɗa tsarin ayyukan ta da fiye da ma'aikatu, hukumomi da cibiyoyin gwamnati 250, tare da ƙaddamar da sababbin fasahohi da s**a inganta ayyukan rajista tare da rage lokacin da ake ɗauka wajen yi wa jama'a rajista.

Ziyarar ta samu halartar Darakta Janar na NOA, Mallam Lanre Issa-Onilu; Babbar Darakta kuma Babbar Jami'ar Gudanarwa ta NIMC, Dakta Abisoye Coker-Odusote; Daraktan Sashen Samarwa, Wallafe-wallafe da Adana Takardu, Mista Ibidapo Okunnu; Mataimakiyar Darakta mai kula da Hulɗa da Jama'a da Ladabi, Misis Fatoke Folasade, da sauran manyan jami'an Ma'aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai da na Hukumar NIMC.

Kalaman Matar El-Rufa'i Sun Taɓa Zuciyata – Peter ObiPeter Obi ya ce kalaman Hajiya Asiya El-Rufa'i, wadda ta roƙi Shuga...
08/07/2026

Kalaman Matar El-Rufa'i Sun Taɓa Zuciyata – Peter Obi

Peter Obi ya ce kalaman Hajiya Asiya El-Rufa'i, wadda ta roƙi Shugaba Bola Ahmed Tinubu kan halin da mijinta ke ciki, sun taɓa zuciyarsa.

Obi ya ce lamarin ya nuna muhimmancin tabbatar da adalci ga kowa ba tare da nuna bambanci ba, yana mai kira da a mutunta doka tare da kare haƙƙin 'yan ƙasa.

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Idon Mikiya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share