Idon Mikiya

Idon Mikiya Jaridar Idon Mikiya, kafar sadarwa ce mai samar da gamsassun labarai, fayyace gaskiya shine jigon mu — 08060818081

Hukumomin NAIC Da BPP Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Don Ƙara Ƙarfafa Gaskiya A Harkar NomaHukumar kula da Inshorar Noma ta Nijer...
26/09/2025

Hukumomin NAIC Da BPP Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Don Ƙara Ƙarfafa Gaskiya A Harkar Noma

Hukumar kula da Inshorar Noma ta Nijeriya NAIC ta sake jaddada kudirinta na tabbatar da gaskiya, inganci da kuma karfafa hadin gwiwa da muhimman hukumomin gwamnati domin kare martabar fannin noma a kasar.

Shugaba NAIC, Rt. Hon. Yazeed Shehu Danfulani (Turakin Zamfara), a ranar Alhamis ya jagoranci tawagarsa a ziyarar ban girma zuwa ga Darakta-Janar na Hukumar Kula da Kadarorin Gwamnati BPP, Dr. Adebowale Adedokun, a Abuja babban birnin Nijeriya.

Ziyarar ta mayar da hankali kan yadda za a karfafa hadin gwiwar hukumomi, inganta gaskiya da bin ka’ida a tsarin saye-saye na gwamnati, tare da nufin bunkasa ingantaccen aiki a tsarin inshorar noma.

Danfulani, tare da rakiyar manyan daraktocin hukumar Rt. Hon. Abubakar Jarengol na ayyuka da fasaha da Mr Ayandayo Babaranti na kudi da gudanarwa ya jaddada kudirin hukumar NAIC na daidaita ayyukanta su zamo tsara a idon duniya.

Ya ce: “A hukumar NAIC mun yi imani cewa hadin gwiwar hukumomi shi ne ginshikin dorewar cigaba. Yin aiki tare da hukumar BPP zai tabbatar da bin ka’ida yadda ya k**ata tare da karfafa gaskiya da adalci, wadannan su ne ginshikan ci gaban inshorar noma a Nijeriya."

A nasa jawabin, Dr. Adedokun ya yaba da irin himmar hukumar NAIC karkashin jagorancin Dr Danfulani wajen tafiyar da ayyuka cikin gaggawa, tare da alkawarin cewa hukumar BPP za ta goyi bayan shirin da ke karfafa shugabanci nagari da tsaftace ayyukan gwamnati.

Ya jaddada cewa irin wadannan hadin gwiwa suna da matukar muhimmanci wajen tafiyar da ajandar gwamnatin Nijeriya ta fadada hanyoyin inganta tattalin arziki, musamman ta fannin noma.

Wannan sabon hadin gwiwar ya zama muhimmin mataki a kokarin NAIC na zurfafa hulda tsakanin hukumomi, karfafa tsarin aikinta da kuma goyon bayan hangen nesa na Gwamnatin Tarayya na tabbatar da shugabanci mai gaskiya kuma mai dorewa.

‎Kotun Majistare Ta Saki Sarkin Hausawan Maraba Bisa Belin Naira Miliyan 5‎‎A safiyar ranar Juma’a, 26 ga Satumba, 2025,...
26/09/2025

‎Kotun Majistare Ta Saki Sarkin Hausawan Maraba Bisa Belin Naira Miliyan 5

‎A safiyar ranar Juma’a, 26 ga Satumba, 2025, Kotun Majistare mai lamba ɗaya da ke karamar hukumar Karu, ta Jihar Nasarawa, ta bayar da belin Sarkin Hausawan Maraba, Alhaji Mani, kan kuɗi Naira miliyan biyar (₦5,000,000), bisa zargin batanci da ake yi masa.

‎Kotun, ƙarƙashin jagorancin Alkali Mai Riga, ta saurari karar da lauyan mai kara ya gabatar, inda aka karanta tuhume-tuhume kan Sarkin Hausawa da wasu mutum biyar da ake tuhuma tare da shi. Takardar ƙarar ta bayyana sunayan

‎1. Adamu Usman Mani
‎2. A. Rabbo
‎3. Murtala Baban Fati
‎4. Sarkin Fada - Murtala Muhammad
‎5.Ghali Mani
‎6. Dan Zago Yusuf

‎Sai dai sauran mutum biyar ba su bayyana a gaban kotu ba saboda ba a samu nasarar miƙa musu sammaci ba.

‎Alkali ya bayar da belin Sarkin a kan sharadin cewa zai bayar da tabbacin kuɗi har Naira miliyan biyar tare da masu tsaya masa.

‎An dage sauraron shari’ar zuwa wani lokaci domin ci gaba da shari’a, yayin da ake jiran gurfanar da sauran wadanda ake tuhuma tare da Sarkin.

INEC Ta Yi Watsi Da Buƙatar Yiwa Tafiyar Matasa Rijista A Matsayin Jam'iyyar Siyasa Da Sunan Access PartyINEC ta bayyana...
26/09/2025

INEC Ta Yi Watsi Da Buƙatar Yiwa Tafiyar Matasa Rijista A Matsayin Jam'iyyar Siyasa Da Sunan Access Party

INEC ta bayyana dalilin ta da cewa sunan jam'iyyar na "AP" ya yi k**a da "DLP".

Jigo a tafiyar matasa Barsita Audu Bulama Bukarti, ya bayyana rashin amincewarsa kan dalilin da hukumar ta bayar.

TALLA: Domin fara sána'ár DATA ko kuma ku dinga saka wa kanku, ku sáuké Mánhájar KSBDATA a PláyStore.
👇👇👇
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.ksbdata.app

Website
👇👇👇
https://app.ksbdata.com

WhatsApp
👇👇👇
https://wa.me/2349018986971

Matatar Mai Ta Dangote Ta Sallami Dukkan Ma'aikatanta 'Yan Nijeriya Saboda Zargin SataA takardar da shugaban gudanarwa n...
26/09/2025

Matatar Mai Ta Dangote Ta Sallami Dukkan Ma'aikatanta 'Yan Nijeriya Saboda Zargin Sata

A takardar da shugaban gudanarwa na "Human Asset Management" Femi Adekunle, ya sakawa hannu ranar Alhamis 25 ga watan Satumba, 2025, ta bayyana cewa;

Sak**akon yawaitar rahotanni na ɓarna da aka samu a wasu sassan matatar mai, wanda ya janyo matsala ta tsaro sosai, ya sanya hukumar gudanarwa ta tilasta yin cikakken shiri na wannan ma’aikata.

TALLA: Domin fara sána'ár DATA ko kuma ku dinga saka wa kanku, ku sáuké Mánhájar KSBDATA a PláyStore.
👇👇👇
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.ksbdata.app

Website
👇👇👇
https://app.ksbdata.com

WhatsApp
👇👇👇
https://wa.me/2349018986971

TÁLLAH: Idan Ku Ká Fará Amfäní Da Kamfanín Käsuwancín Datá Da Katín Wayá Na KSBDATA Ba Za Ku Sáke Amfäní Da Wani Kamfaní...
26/09/2025

TÁLLAH: Idan Ku Ká Fará Amfäní Da Kamfanín Käsuwancín Datá Da Katín Wayá Na KSBDATA Ba Za Ku Sáke Amfäní Da Wani Kamfanín Ba

Duba línk a comment section👇👇👇

Ina masu sána'ar dáta da katín wáya ga dama ta samu, KSBDATA mun shírya ba ku ríbá mai yawa, za ku iya síyan dáta ku saka wa kánku da wannan ápplícatíon ɗin námu na KSBDATA, muddin ku ka fára amfani da KSBDATA ba za ku iya daínawa ba saboda íngancín dátar mu.

Dámúwárku game da mátsálár dáta ko sáyán katín wáya ta zo ƙarshe idan har ku ka fará aíki da mánhájármu ta Ksbdata wato ‘Applícátíon na Kamfanín ‘KSBDATA. Dátar mu tana da ingancí sosai za ku jima kuna amfani da íta ba ta ƙare ba.

Ku sáuke “Applícátíon” ɗin mu na Ksbdata a “Pláystore” zuwa kán wáyoyínku:

Duba línk a comment section👇👇👇

UNGA80: Nijeriya Ta Nemi A Yafe Bashi Ga Ƙasashen Da Ake Bi Da Ba Da Damar Yin Kasuwanci Domin Samun Cigaba Mai ƊorewaSh...
25/09/2025

UNGA80: Nijeriya Ta Nemi A Yafe Bashi Ga Ƙasashen Da Ake Bi Da Ba Da Damar Yin Kasuwanci Domin Samun Cigaba Mai Ɗorewa

Shugaban Bola Ahmed Tinubu, ya yi kira ga ƙasashen duniya da su yafe bashi ga ƙasashe masu tasowa, yana mai cewa hakan hanya ce madaidaiciya ta wanzar da zaman lafiya da ci gaba.

Tinubu, wanda Mataimakin Shugaban ƙasa, Kashim Shettima, ya wakilta, ya yi wannan kira ne a lokacin da yake gabatar da jawabin ƙasa a babban taron Majalisar Dinkin Duniya karo na 80 a birnin New York.

“Muna buƙatar wani sabon tsarin doka mai ɗaurewa, mak**ancin kotun duniya ta kuɗi, da zai ba ƙasashe masu tasowa damar kubuta daga ɗaurewar tattalin arziki na dogaro da fitar da albarkatun kasa ba tare da sarrafawa ba,” in ji Tinubu.

Ya bayyana Lagos Action Plan da aka tsara shekaru da dama da s**a gabata, wadda ta bayyana hanyar kaucewa bashi da dogaro da shi, tare da baiwa ƙasashe damar ƙirƙira daga cikin gida a fannoni k**ar noma, ma’adinai da kuma sarrafa man fetur.

Shugaban ya yaba da ƙirƙirar African Continental Free Trade Area (AfCFTA), yana mai cewa hakan babban abin alfahari ne da zai ƙara haɗa kan ƙasashen nahiyar.

Ya kuma ce Najeriya ta tsaya tsayin daka wajen cimma Manufofin Cigaba masu Dorewa (SDGs), wanda a cewarsa, za a iya cimma hakan ne ta hanyar mai da hankali kan manyan manufofi na haɓakar tattalin arziki da bunƙasa arziki.

Dangane da harkokin Afirka, Tinubu ya ce Najeriya tana maraba da yunƙurin zaman lafiya a Jamhuriyar Demokraɗiyyar Congo, tare da jaddada cewa zuba jari na ƙasa da ƙasa zai iya kawo ƙarshen rikice-rikicen da s**a shafi ma’adinai.

Ya ce saka hannun jari a bincike, haɓakawa da kuma sarrafa waɗannan ma’adinai a nahiyar Afirka zai taimaka wajen sauya tsarin samar da kayayyaki ga kasuwar duniya, tare da rage rikice-rikice tsakanin manyan ƙasashe.

Shugaban ya ƙara da cewa Najeriya da sauran ƙasashen Afirka sun yi nasarori a cikin shekarun baya-bayan nan wajen gyara harkokinsu na cikin gida.

“Idan aka samu sauye-sauye da za su ƙarfafa tsarin kuɗaɗen duniya, za mu iya kai wannan ci gaba mataki na gaba, inda kasuwanci, zuba jari da riba za su buɗe sabbin damammaki ga nahiyarmu.”

Haɗakar Malaman Izala Na Jihar Kano Sun Shigar Da Takardar Koke Ga Ofishin Sakataren Gwamnatin JiharBiyo bayan shigar da...
25/09/2025

Haɗakar Malaman Izala Na Jihar Kano Sun Shigar Da Takardar Koke Ga Ofishin Sakataren Gwamnatin Jihar

Biyo bayan shigar da ƙorafi da wasu mazauna jihar Kano s**a yi kan Malam Lawal Triumph, haɗakar Malaman Izala na jihar sun shigar da takardar koke ga ofishin Sakataren gwamnatin Jihar a ranar Alhamis.

Tawagar ƙarƙashin jagorancin Dokta Abdallah Usman Gadon Ƙaya sun shaidawa manema labarai cewa sun kawo ƙorafinsu ne a rubuce dangane da zargin da ake yiwa ɗaya daga cikin Malaminsu da sakin baki akan Annabi Muhammad Sallalahu Alaihi Wasallam.

Malamin ya ƙara da cewa su ba sa yin zanga-zanga, kuma suna fata za a gayyacesu a kowane lokaci domin tattaunawa.

25/09/2025

Ni yanzu sunana (Dr.) kawai nake amsawa, dan ko Asibiti naje ni ne (Dr.), Inji Rarara

Muna Neman A Bawa Jami'an Mu Iznin Riƙe Mak**ai A Bakin Aiki — Hukumar Kiyaye Haɗura Ta Nijeriya FRSCMe za ku ce?
25/09/2025

Muna Neman A Bawa Jami'an Mu Iznin Riƙe Mak**ai A Bakin Aiki — Hukumar Kiyaye Haɗura Ta Nijeriya FRSC

Me za ku ce?

A Yiwa Guy Din Nan (Rarara) Bayani Fa, Tun Kafin Ya Fara Yawo Da Akwatun Allura, Inji Sadiya Adam Sulaiman
25/09/2025

A Yiwa Guy Din Nan (Rarara) Bayani Fa, Tun Kafin Ya Fara Yawo Da Akwatun Allura, Inji Sadiya Adam Sulaiman

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Idon Mikiya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share