Rahma TV

Rahma TV RAHMA TELEVISION FARIN CIKIN AL'UMMA. RADIO AND TV STATIONS

Domin aiko da abubuwan dake faruwa a inda kuke- 08100335970 , 07017233284
Domin samun sahihan labarai da shirye shirye kasance da Rahma TV da Rahma Radio 97.3FM dake Facebook da YouTube ko website a www.Rahma Tv.com

A wata sanarwa da Mai magana da yawun Rundunar ‘Yan sanda a Jahar Kaduna DSP Mansur Hassan ya fitar ya ce an gudanar da ...
31/08/2025

A wata sanarwa da Mai magana da yawun Rundunar ‘Yan sanda a Jahar Kaduna DSP Mansur Hassan ya fitar ya ce an gudanar da taronne ba tare da samunamincewar hukumomin tsaro ba wanda kuma ake zargin wasu ‘Yan bangar siyasa sun fara harba bindiga a wurin taron domin jefa firgici da tsoro a zukatan al'umma.

Rundunar ‘yan sandan ta ce sakamakon binciken farko-farko ya nuna cewa Tagin Kawancen Jam'iyyar ADC ne ya gudanar da taron, sai dai kuma Jagorancin Jam'iyyar ya musanta cewa ya na da masaniya akan taron.

Kwamishiniyar muhalli da ma'adanai Dr Margaret Elayo ta bayyana hakan jimkadan da kammala duba aikin tsaftar muhalli na ...
31/08/2025

Kwamishiniyar muhalli da ma'adanai Dr Margaret Elayo ta bayyana hakan jimkadan da kammala duba aikin tsaftar muhalli na karshen kowanne wata a birnin lafiya.

Kwamishiniyar wadda Babban Sakatare a ma'aikatar Muhallli Hussaini Babayi ya wakilta ta bayyana rashin jindadi da yadda ta taras da mayankar dabbobin ta zamani da ke a Lafiya, sai dai ta ce daga yanzu gwamnati ba za ta lamunci duk wani rashin tsabta a mayankar ba.

Wadannan kalamai dai shugaban ya furta su ne tun a Brazil ayayin ziyarar kwanaki biyu da ya kai kasar sai dai kuma tuni ...
31/08/2025

Wadannan kalamai dai shugaban ya furta su ne tun a Brazil ayayin ziyarar kwanaki biyu da ya kai kasar sai dai kuma tuni kalaman na shugaban kasa su ka haifar da bullar martani iri-iri a cikin kasar
nan inda shuwagabannin addinai su ka ce abin da ke faruwa a zahiri a cikin kasar nan ya sha Bambam da kalaman na shugaban kasa.

Ayayin ziyarar da ya kai Brazil, shugaban kasa Bola Tinubu ya shedawa Masu zuba Jari cewa sauye-sauyen da gwamnatinsa ta bijiro da su ya tsabtace tsarin gudanar da harkokin gwamnati
tare da sanyawa tsarin Musayar kudaden kasashen ketare ya dada zama a fayyace ba tare da kumbiya-kumbiya ba wanda hakanne ya sanya Nigeria ta Kulla Sabon kawance a bangaren fasaha da wadata kasa da abinci da kuma bangaren Sabunta makamashi.

Da ya ke jawabi ayayin taron gwamnonin shiyyar Arewa masogabas karo na 12 da ya gudana a Jahar Taraba, gwamna Babaganaum...
31/08/2025

Da ya ke jawabi ayayin taron gwamnonin shiyyar Arewa maso
gabas karo na 12 da ya gudana a Jahar Taraba, gwamna Babagana
umara Zulum na jahar Borno ya ce ilimi da kyautata fannin lafiyq da
kyautata tsaro da kuma samar da Ababan more rayuwa su ke a kan
gaba wajen samar da zaman lafiya da kuma cigaba.

Gwamna Babagana Umara Zulum ya kara da cewa talauci da rashin
aikin yi da kuma rashin kyauwun hanyoyi na kara haifar da rashin
tsaro a shiyyar.

A wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar kula da aikin‘Yansanda na kasa Ikechukwu Ani ya fitar ya karyata rahotanni...
31/08/2025

A wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar kula da aikin
‘Yansanda na kasa Ikechukwu Ani ya fitar ya karyata rahotannin da
ke yawo ta Kafaren sadarwa na Internet cewa an fara daukar
sabbin ‘Yan sanda na shekarar 2025.

Sanarwar ta ce hukumar kula da aikin ‘Yan sanda na kasa ta bukaci
matasa ‘Yan Nigeria da ke sha'awar shiga aikin Dan sanda da
su kara hakuri tare da sauraron tsarin da aka tanada a hukumance
wajen daukar sabbin ‘Yqn sanda a Nigeria.

31/08/2025

KANUN LABARAI

Hukumar kula da aikin ‘Yan sanda
ta kasa ta musanta cewa ta fara
daukar sabbin ‘Yan sanda na
shekarar 2025 a Nigeria.

Gwamnonin jahohin shiyyar Arewa
maso gabas sun ce daukar
matakin soji ba zai wadatar ba
wajen samar da tsaro har sai an
hada da wasu dabaru na daban.

Rundunar 'yansandan Najeriya
reshen jihar Kaduna ta zargi
tsohon Gwamna Nasir El-Rufai da
shirya taron siyasa ba bisa ƙa'ida
ba, inda ta ce an yi rikici har da
harba bindiga.

Daga Ketare....
Shugaban rundunar sojin Rasha,

ya ce dakarun ƙasar na kai hare-
hare ba ƙaƙƙautawa a fagen

dagarsu da ke cikin Ukraine.

Masu Kallonmu Assalamu'alekum
Barkanmu da kasancewa a cikin
shirin labarai da rahotanni daga
nan Rahama Talabijin Farin cikin
al'umma.

Yau lahadi 7 ga watan Rabiul
Awwal shekara ta 1447AH wadda
ta yi daidai da 31 ga watan
Augustan shekarar 2025.

Babban malamin musulunci, Khalifan Sheikh Manzo Arzai, Khalifa Muktar (Alaramma) Sheikh Manzo Arzai, ya rasu a Kano.Imam...
31/08/2025

Babban malamin musulunci, Khalifan Sheikh Manzo Arzai, Khalifa Muktar (Alaramma) Sheikh Manzo Arzai, ya rasu a Kano.

Imam Muhammad Nur Muhammad Arzai, wanda ya sanar da cewa jana’izarsa za a gudanar da ita a ranar Lahadi da misalin ƙarfe 2:30 na rana, a Zawiyar Sheikh Manzo Arzai da ke Unguwar Arzai, Kano.

Marigayin ya shafe tsawon rayuwarsa cikin hidimomin addinin musulunci, yana koyarwa tare da jagorantar al’umma cikin shiriya da addu’a.

Al’ummar musulmi a Kano da sauran wurare na ci gaba da bayyana ta’aziyyarsu, tare da addu’ar Allah Ya jikansa, Ya gafarta masa, kuma Ya haɗa shi da Manzon Allah (SAW).

Tin da farkon wasan Mallorca ta zura ƙwallon ta hannun Vedat Muriqi a minti na 18, Sai dai mintuna kaɗan bayan haka, Rea...
30/08/2025

Tin da farkon wasan Mallorca ta zura ƙwallon ta hannun Vedat Muriqi a minti na 18, Sai dai mintuna kaɗan bayan haka, Real Madrid ta fake ta hannun Arda Güler a minti na 37, sannan daga nan Vinícius Júnior ya kara ta biyu bayan minti guda kacal (38’).

Da ya ke jawabi ayayin taron gwamnonin shiyyar Arewa maso gabas karo na 12 da ya gudana a Jahar Taraba, gwamna Babagana ...
30/08/2025

Da ya ke jawabi ayayin taron gwamnonin shiyyar Arewa maso gabas karo na 12 da ya gudana a Jahar Taraba, gwamna Babagana umara Zulum na jahar Borno ya ce ilimi da kyautata fannin lafiya da kyautata tsaro da kuma samar da Ababan more rayuwa su ke a kan gaba wajen samar da zaman lafiya da kuma cigaba.

Gwamna Babagana Umara Zulum ya kara da cewa talauci da rashin aikin yi da kuma rashin kyawun hanyoyi na kara haifar da rashin tsaro a shiyyar.

Shin ko daukar matakan rage radadin talauci da kuma samar da Ababan more rayuwa kadai sun wadatar wajen magance rashin tsaro kuwa dai da sauran lale?

30/08/2025

Shirin Lafiya Babbar Ni'ima.

Tare da Dr.Mahmoud Kawu Magashi Likita Mai Kula da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu daga Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano,(AKTH).

30/08/2025

KANUN LABARAI

Wasu Farfesoshi a Najeriya sun bukaci a daga albashinsu zuwa aƙalla
naira miliyan biyu da rabi a wata, inda s**a bayyana cewa duk abin da
ya gaza haka bai dace ba.

Kungiyar kwadago ta kasa NLC tace cire tallafin lantarki da gwamnatin
tarayya tayi ya jefa yan Najeriya cikin kuncin rayuwa.

An ceto mutane 9 daga haɗarin kwale-kwale da aka samu a jihar
Sokoto.

DAGA KASAHEN DUNIYA
Ma'aikatar harkokin wajan Amurka ta tabattar da soke bisa shugaban
Falasdinawa Mahmoud Abbas da wasu jami'ai Faalasdinawa 80.

ASABAR 6 GA WATAN RABIUL AUWAL 1447
30 GA WATAN AGUSTAN 2025.

An fara zura kwallo ta farko ne a minti na 27 lokacin da J. Cullen na Burnley ya ci wa yaci gida , wanda ya bai wa Manch...
30/08/2025

An fara zura kwallo ta farko ne a minti na 27 lokacin da J. Cullen na Burnley ya ci wa yaci gida , wanda ya bai wa Manchester United damar shiga gaba a wasan.

Sai dai a minti na 55,Lyle Foster ya zura kwallo ga Burnley, ya Inda ya maida Sakamakon wasan ɗaya da ɗaya sakamakon. Amma cikin minti biyu kacal, Bryan Mbeumo ya sake mayar da United gaba bayan ya zura kwallo ta biyu wato 2 da 1.

Burnley ba su yi kasa a gwiwa ba, inda J. Anthony ya dawo da kwallo a minti a 66, ya maida wasan 2 da 2.

Sai dai a ƙarshe, yayin da ake shirin rufe wasa, United ta samu bugun fanareti a minti na 90+7 wanda Bruno Fernandes ya zura raga, antshi wasa 3 da 2.

Address

Kano

Telephone

+2348023724111

Website

http://www.youtube.com/@rahmaTv1

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Rahma TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Rahma TV:

Share