
31/08/2025
A wata sanarwa da Mai magana da yawun Rundunar ‘Yan sanda a Jahar Kaduna DSP Mansur Hassan ya fitar ya ce an gudanar da taronne ba tare da samunamincewar hukumomin tsaro ba wanda kuma ake zargin wasu ‘Yan bangar siyasa sun fara harba bindiga a wurin taron domin jefa firgici da tsoro a zukatan al'umma.
Rundunar ‘yan sandan ta ce sakamakon binciken farko-farko ya nuna cewa Tagin Kawancen Jam'iyyar ADC ne ya gudanar da taron, sai dai kuma Jagorancin Jam'iyyar ya musanta cewa ya na da masaniya akan taron.