Rahma TV

Rahma TV RAHMA TELEVISION FARIN CIKIN AL'UMMA. RADIO AND TV STATIONS

Domin aiko da abubuwan dake faruwa a inda kuke- 08023724111; 08093552397; 08039738580; 08032799258
ku cigaba da kasancewa da Rahma TV da Rahma Radio 97.3FM dake Facebook da YouTube ko website a www.rahmatv.com

Ma’aikatan gwamnati su ne manyan ginshiƙan gudanar da ayyukan ƙasa, inda da dama daga cikinsu ke shafe shekaru masu yawa...
11/06/2026

Ma’aikatan gwamnati su ne manyan ginshiƙan gudanar da ayyukan ƙasa, inda da dama daga cikinsu ke shafe shekaru masu yawa suna hidimtawa al’umma da ƙasa har zuwa lokacin ritayarsu.

Bayan kammala aiki, wasu ma’aikata na fuskantar ƙalubale kamar tsadar rayuwa, rashin isasshiyar kulawar lafiya, da wahalar daidaita rayuwa ba tare da albashi na wata-wata ba, duk da irin gudunmawar da s**a bayar a tsawon shekarun aiki.

Wannan babban ƙalubale ne da ke tayar da muhawara, tare da kira ga gwamnati da ta fito da kyakkyawan tsari mai inganci wanda zai kare mutuncin waɗanda s**a kammala aikin gwamnati tare da tabbatar da jin daɗinsu bayan sun bar aiki.

Shin a ganinku Gwamnati na da wani shiri na musamman domin kula da ma’aikata bayan ritaya?

Muna maraba da saƙonnin ra'ayoyinku kan wannan batu domin karantawa a cikin Labaranmu.

10/06/2026

A ganin ku, me ya kamata ƙasashen Afrika suyi
sakamakon tozartar wa da akayi Omar Abdulkadir Artan?

10/06/2026

Jawabin Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ga Alhazan Kano a birnin Makka...

10/06/2026

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf yana ganawa da Alhazan Kano a Makkah

Shugaban hukumar Jin dadin Alhazan jihar Kano Alhaji Abubakar Ibrahim Matawalle ya shaida hakan ne a birnin Makka lokaci...
10/06/2026

Shugaban hukumar Jin dadin Alhazan jihar Kano Alhaji Abubakar Ibrahim Matawalle ya shaida hakan ne a birnin Makka lokacin taro da Jami'an Kula da Alhazan kananan hukumomin Kano 44.

Wakilinmu a birnin Makka Tukur S Tukur ya rawaito mana cewa Matawalle ya kuma ce da zarar an fara kwashe Alhazan za'a dauki kwana 3 zuwa 4 domin mayar da Alhazan gida Kano.

Yace da yardar Allah babu wani sake sauyin lokaci.

An gudanar da bikin kaddamarwar ne a jiya Talata a yankin OSEX–Wasa Road, inda aka bayyana aikin a matsayin wani muhimmi...
10/06/2026

An gudanar da bikin kaddamarwar ne a jiya Talata a yankin OSEX–Wasa Road, inda aka bayyana aikin a matsayin wani muhimmin ci gaba na bunkasa ababen more rayuwa a ƙasar nan.

Tinubu, wanda Shugaban Majalisar Dattijai Godswill Akpabio ya wakilta, ya ce gwamnatinsa na mai da hankali wajen aiwatar da ayyukan da ke kawo sauyi kai tsaye ga rayuwar ‘yan ƙasa.

Ya ce manufar gwamnatinsa ita ce samar da sakamako na zahiri maimakon alkawura kawai, musamman a fannin gine-gine da tattalin arziki.

Shugaba Tinubu ya ce aikin na nuna muhimmiyar rawar da ababen more rayuwa ke takawa wajen bunƙasa tattalin arziki da samar da ayyukan yi ga al'umma.

10/06/2026

Sakon ra'ayoyin ku tare da Usman I. Datti

Kudirin ya biyo bayan ƙudurin da Sanata Sunday Katung ya gabatar, tare da goyon bayan wasu sanatoci da s**a haɗa da many...
10/06/2026

Kudirin ya biyo bayan ƙudurin da Sanata Sunday Katung ya gabatar, tare da goyon bayan wasu sanatoci da s**a haɗa da manyan ‘yan majalisa daban-daban.

A yayin muhawara, Sanata Katung ya bayyana cewa masana’antar saƙa ta Najeriya ta durkushe matuƙa, duk da cewa a da tana ɗaya daga cikin manyan masu samar da ayyukan yi a ƙasar.

Ya ce an kafa masana’antar saƙa ta farko a Kaduna tun a shekarar 1957, sannan a shekarun 1960 zuwa 1970 gwamnati ta taimaka wajen bunƙasa ta har ta kai ga samun kamfanoni sama da 167 a ƙarshen shekarar 1980.

Sanatoci da s**a shiga muhawarar sun danganta rugujewar masana’antar da rashin kariya daga gwamnati, shigo da kaya ba bisa ka’ida ba, da kuma tabarbarewar tsarin masana’antu.

10/06/2026

Jam'iyyar APC ce ta lalata 'yayan Jama'a ta mayar da su 'yan daba -Cewar Abdulmajid Danbilki Kwamanda.

A cewar sanarwar fadar shugaban ƙasa, kuɗin zai taimaka wajen ƙarfafa cibiyoyin kula da lafiya da inganta tsarin gaggawa...
10/06/2026

A cewar sanarwar fadar shugaban ƙasa, kuɗin zai taimaka wajen ƙarfafa cibiyoyin kula da lafiya da inganta tsarin gaggawa na ƙasa domin dakile yaduwar cututtuka.

Haka kuma, an kafa Kwamitin Fadar Shugaban Ƙasa kan Shirye-shiryen Tunkarar Ebola da sauran barazanar cututtuka masu yaɗuwa.

Kwamitin zai kasance ƙarƙashin shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasa, Femi Gbajabiamila, tare da haɗin gwiwar hukumomin lafiya na tarayya da jihohi.

Wannan mataki ya biyo bayan damuwar da ta taso sakamakon rahotannin sake ɓullar cutar Ebola da aka samu a baya-bayan nan a Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo da kuma Uganda.

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Rahma TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Rahma TV:

Share