Rahma TV

Rahma TV RAHMA TELEVISION FARIN CIKIN AL'UMMA. RADIO AND TV STATIONS

Domin aiko da abubuwan dake faruwa a inda kuke- 08023724111; 08093552397; 08039738580; 08032799258
ku cigaba da kasancewa da Rahma TV da Rahma Radio 97.3FM dake Facebook da YouTube ko website a www.rahmatv.com

12/08/2026

MURNAR CIKA SHEKARU 15

NA GUDANAR DA RAHMA RADIO 97.3 FM

RAHMA RADIO 97.3 FM
FARIN CIKIN AL’UMMA.

Muna godiya ga dukkan masu sauraronmu da masu tallafa mana bisa irin goyon bayan da suke ba mu tsawon shekaru.

A ranar 19 ga watan nan na ogusta hukumar zabe ta kasa inec zata sakarwa masu neman kujerar shugabancin kasarnan da masu...
12/08/2026

A ranar 19 ga watan nan na ogusta hukumar zabe ta kasa inec zata sakarwa masu neman kujerar shugabancin kasarnan da masu neman kujerun Majalisun dokoki na kasa mara domin fara yakin neman zabe, a duk lokaci irin wannan ana samun fargaba kan yiwuwar samun rikice rikicen siyasa.

Wace hanya kuke ganin za a bi wajan kaucewa rikice rikice yayin gangamin zaban na 2027.
Sai munji daga gareku.

Katsina United ta karyata rahotannin da ke yawo cewa ɗan wasa Chinedu Ozor ya farfaɗo.Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Katsina U...
12/08/2026

Katsina United ta karyata rahotannin da ke yawo cewa ɗan wasa Chinedu Ozor ya farfaɗo.

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Katsina United ta tabbatar da rasuwar ɗan wasanta, Chinedu Ozor, wanda ya faɗi yayin wasan sada zumunta da Niger Tornadoes a filin wasa na Muhammad Dikko da ke Katsina.

Ƙungiyar ta ce rahotannin da ke cewa Chinedu ya farfaɗo bayan lamarin ba gaskiya ba ne, inda ta tabbatar da cewa bai sake farfaɗowa ba.

Katsina United ta kuma roƙi jama’a da su daina yaɗa jita-jita da bayanan da ba a tabbatar da su ba, tare da bai wa iyalansa da abokan wasansa damar yin jimamin rasuwarsa cikin mutunci.

Mai Martaba Sarkin Bauchi, Rilwanu Adamu, ne ya naɗa Jonathan sarautar a wani biki da aka gudanar a Fadar Sarkin da ke c...
12/08/2026

Mai Martaba Sarkin Bauchi, Rilwanu Adamu, ne ya naɗa Jonathan sarautar a wani biki da aka gudanar a Fadar Sarkin da ke cikin birnin Bauchi a ranar Talata.

An karrama tsohon shugaban ƙasar ne bisa gudummawar da ya bayar wajen ƙarfafa dimokuraɗiyya, zaman lafiya da haɗin kan ƙasa a lokacin da yake jagorantar Nijeriya.

A wajen bikin, Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, wanda ya jagoranci tawagar jami’an gwamnati da sauran manyan baki zuwa fadar Sarkin, ya gode wa Masarautar Bauchi bisa karrama tsohon shugaban ƙasar.

Ya ce irin gudummawar da Jonathan ya bayar wajen tafiyar da ƙasar da kuma inganta zaman lafiya sun cancanci yabo da karramawa.

A nasa jawabin, tsohon Shugaban Ƙasa Goodluck Jonathan ya nuna godiya ga Mai Martaba Sarkin Bauchi da al’ummar jihar bisa wannan karramawa, tare da bayyana farin cikinsa da girmamawar da Masarautar ta yi masa.

Bisa zargin gazawar Gwamnatin Tarayya da gwamnatocin jihohi wajen aiwatar da yarjejeniyar 2025 tsakanin gwamnati da ASUU...
12/08/2026

Bisa zargin gazawar Gwamnatin Tarayya da gwamnatocin jihohi wajen aiwatar da yarjejeniyar 2025 tsakanin gwamnati da ASUU.

Matakin ya biyo bayan taron majalisar zartarwa ta ƙasa na ƙungiyar da aka gudanar a Jami’ar Abuja.

ASUU ta umurci rassan jami’o’in da abin ya shafa su fara da bai wa gwamnati wa’adin kwanaki 14, kafin ɗaukar matakin yajin aiki.

Shugaban ASUU, Farfesa Christopher Piwuna, ya ce za a gudanar da wani taron gaggawa a ƙarshen watan Agusta ko farkon Satumba domin yanke wasu muhimman matakai.

Tsohuwar matar jarumin Kannywood Adam A. Zango, Maimuna Musa, ta ce matsin lamba daga ‘yan uwa da kuma wasu masu sharri ...
12/08/2026

Tsohuwar matar jarumin Kannywood Adam A. Zango, Maimuna Musa, ta ce matsin lamba daga ‘yan uwa da kuma wasu masu sharri ne ainihin dalilin da ya haddasa mutuwar aurensu da Adam Zango.

Maimuna tace, tunda farko an rufe batun ne kawai da zancen matsalar genotype.

"Matsin lambar dangi da katsalandan na wasu ne ainihin dalilin da ya sa aurena da Adamu ya mutu, sai dai muka rufe batun da batun rashin dacewar Genotype."

Me za ku ce?

Rundunar ’yan sandan Kano ta k**a wasu mutane uku da ake zargi da satar ababen hawa, a wani samame da aka gudanar bisa s...
12/08/2026

Rundunar ’yan sandan Kano ta k**a wasu mutane uku da ake zargi da satar ababen hawa, a wani samame da aka gudanar bisa sahihan bayanan sirri.

Rundunar ta kuma kwato babur mai kafa uku guda huɗu da kuma wata motar kirar Pontiac Vibe.

Sabon tsarin zai maye gurbin tsarin da ake amfani da shi a baya, wanda ke tilasta wa kamfanoni yin yarjejeniya daban-dab...
12/08/2026

Sabon tsarin zai maye gurbin tsarin da ake amfani da shi a baya, wanda ke tilasta wa kamfanoni yin yarjejeniya daban-daban da Gwamnatin Tarayya kafin su fara gudanar da manyan ayyukan hako man fetur da iskar gas.

Ana sa ran sabon tsarin zai taimaka wajen jawo sabbin jarin kuɗi har dala biliyan 50 zuwa fannin mai da iskar gas na Najeriya, tare da farfaɗo da wasu manyan ayyukan hako mai a teku da aka dakatar tsawon shekaru. Daga cikin ayyukan da ake sa ran za su amfana da wannan mataki akwai aikin Bonga South West na kamfanin Shell, wanda darajarsa ta kai kusan dala biliyan 10.

Mai ba Shugaban Ƙasa shawara kan yaɗa labarai da dabarun sadarwa, Bayo Onanuga, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata. Ya ce sabon tsarin zai samar da ƙa’idoji da sharuddan da za su kasance iri ɗaya ga kamfanonin da s**a cancanci zuba jari, maimakon a bar kowane kamfani ya sake yin shawarwari da gwamnati kan nasa yarjejeniyar.

A cewar Onanuga, tsarin da ake amfani da shi a baya ya sanya harkokin zuba jari a ayyukan hako mai da iskar gas daga zurfin teku yin tafiya a hankali, tare da haifar da rashin tabbas, wanda hakan ya sa wasu manyan ayyuka s**a tsaya na tsawon shekaru.

Ya ce matakin na yanzu ya biyo bayan ganawar da Shugaba Tinubu ya yi da Babban Daraktan Kamfanin Shell, Wael Sawan, inda shugaban ya bayar da umarnin samar da hanyoyin da za su buɗe sabon shafin zuba jari a wannan fanni.

Gwamnatin ta ce babu wani tsohon ma’aikacin da ya cancanci biyan kuɗi da za a bari ba tare da an biya shi ba.Darakta-Jan...
12/08/2026

Gwamnatin ta ce babu wani tsohon ma’aikacin da ya cancanci biyan kuɗi da za a bari ba tare da an biya shi ba.

Darakta-Janar na Ofishin Gyaran Ayyukan Gwamnati, Dasuki Arabi, ne ya bayyana hakan a Jihar Gombe a ranar Talata, yayin da ake gudanar da aikin tantance tsofaffin ma’aikata da waɗanda s**a cancanci karɓar haƙƙoƙinsu a jihohin Arewa maso Gabas.

Arabi ya ce manufar aikin tantancewar ita ce gano dukkan sahihan buƙatun biyan kuɗi, domin tabbatar da cewa duk wanda yake da haƙƙin karɓar kuɗi ya samu cikakken abin da ya dace da shi. Ya ce Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince da gudanar da wannan tantancewa ta ƙarshe domin warware sauran buƙatu da korafe-korafen da ake da su.

Ya bayyana cewa Ofishin Gyaran Ayyukan Gwamnati na aiki tare da Ofishin Akanta-Janar na Tarayya, da hukumomin yaƙi da cin hanci, domin tantance bayanan tsofaffin ma’aikatan da ke neman biyansu haƙƙoƙinsu.

Ya ƙara da cewa an riga an warware sama da kashi 99 cikin ɗari na ƙorafe-ƙorafen da aka gabatar wa gwamnati kan rashin biyan haƙƙoƙin ma’aikata. Inda ya ce aikin tantancewar da ake yi yanzu za ta taimaka wajen kammala warware sauran sahihan buƙatun biyan kuɗaɗen.

Ministan Raya Harkar Dabbobi, Alhaji Idi Maiha, ne ya bayyana hakan bayan ya yi wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu bayan...
12/08/2026

Ministan Raya Harkar Dabbobi, Alhaji Idi Maiha, ne ya bayyana hakan bayan ya yi wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu bayani kan ayyukan ma'aikatar tasa a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja.

Ya ce za a fara shirin gwajin ne a Wase da ke Jihar Filato, domin gwada sabon tsarin kiwo kafin a faɗaɗa shi zuwa sauran wuraren da aka zaɓa.

Ministan ya bayyana jihohin da aka zaɓa da s**a haɗa da Benue, Filato, Nasarawa, Kaduna da Adamawa, tare da Babban Birnin Tarayya Abuja. Ya ce an zaɓi waɗannan wurare ne saboda sun kasance daga cikin yankunan da s**a fi fuskantar rikice-rikicen manoma da makiyaya a shekarun baya-bayan nan.

Gwamnatin Tarayya ta ce fara shirin a waɗannan yankuna na daga cikin matakan da ake ɗauka domin samar da ingantaccen tsarin kiwo, rage rikice-rikicen da ke tsakanin manoma da makiyaya, da kuma bunƙasa harkar kiwo a matsayin wani muhimmin ɓangare na tattalin arzikin ƙasa.

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Rahma TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Rahma TV:

Shortcuts

Share