29/03/2026
El-Rufai ya butulcewa Atiku sai Uba Sani ya butulce masa, Tinubu ya butulce masa ta hanyar amfani da majalisa ya tafka masa rashin mutunci har a hana shi minista a gwamnatin da akwai masu dattin da s**a fishi k**ar Matawalle da Ganduje.
El-Rufai ya yi kokari da ya dauki darasi ya yi maza ya gyara barakarsa da Atiku dan koyawa Tinubu hankali, mutumin da ya hade kai da tsohon amininsa aka kulle shi har sai da bakin ciki ya kashe mahaifiyarsa, k**ar yadda shi ma ya kulle wasu.
Shi ma Kwankwaso ya butulcewa Atiku, sai Ganduje ya butulce masa, maimakon ya gyara barakar a 2023 sai ya ja daga, aka ci gwamnati sai Abba ya kara butulce masa bayan sun kwaci gwamnatin da kyar a hannun Tinubu.
An yi tsammanin Kwankwaso zai kara warewa a 2027 ya marawa makiya baya, amma sai ya zama muminin da ba zai yarda a kara cizonsa a rami daya ba. Yanzu da Atiku, El-Rufai da Kwankwaso sun hade waje daya daga Arewa, ga kuma Obi da Amaechi daga kudu.
Idan Atiku ya kafa gwamnati ba komai ne ya bashi wannan ba face hakuri da sanin mecece demokradiyya da muhimmancin hadin kai. Tinubu ya yi amfani da kudade masu nauyi wajen janye dukkan gwamnoni idan ban da Bala Mohammed (Kauran Bauchi).
Amma shi Atiku diplomasiyya yake amfani da ita, kenan Tinubu ya fi shi sharri wajen karfafa siyasar kudi da ke haddasa cin hanci da rashawa. A yau ba shi da kowa a Arewa da zai kara masa yakin da El-Rufai ya masa, duk yadda mu ke ganin laifukan El-Rufai ya yi kokari wajen yi wa tsarin APC na karbakarba adalci da ya ce dole mulki ya koma Kudu.
Tinubu ya fi Buhari illa ta wasu fuskoki, shi dan cin hanci da rashawa ne da karkatar da dukiyar al’umma zuwa yankinsa, shi kuma Buhari a kashin kansa ba barawo bane, amma ya yi zalunci ta hanyar yin galala da rayukan al’umma da nuna halin ko in kula kan matsalar talakawan da su ka kashe kansu a kansa.
Tinubu ke amfani da DSS ana k**a mutane. Yanzu ba magana ce ta dukkan wannan sabani ba, dukkansu suna da manyan laifuka da su ka yi mana na kashe kasa a baya. Kuma a yanzu haka mun rasa wadanda za su kwace goruba a hannun kuturu, kenan ta inda aka hau tanan za a sauka.
A taru a duba da hankali kar ayi fada ko a kara komawa baya. Idan aka yi kuskure a wannan karon ba za aji da dadi ba. Ina amfani da wannan shafin nawa dan na tabbatar ba a kara zabar Tinubu ba a 2027, ba shi da alheri, kuma ba zai taba yin adalci a mutanen Arewa ba.
Tun kafin a kafa wannan gwamnatin nake yakarta, kuma har yau ban daina ba saboda na yi imani ba ta da wani alheri sai sharri. Muslim-Muslim yaudara ce, kuma ADC ba za ta cire mu a matsala ba, amma za ta karfafi demokradiyya. A zabi yan majalisu masu kishi ta hayar dannawa kananan jam’iyyu ruwan kuri’u, hakan zai karfafa demokradiyya sosai ya bawa sabbin fuskoki da matasa dama.