16/10/2025
                                            Gwamnatin Tarayya ta musanta rahotannin da ke yawo a yanar gizo cewa Hukumar Shirya Jarabawar Shiga Manyan Makarantu (JAMB) ba za ta sake zama dole wajen shiga makarantun gaba da sakandare a ƙasar ba.
Wasu rubuce-rubuce da s**a yadu a yanar gizo sun yi iƙirarin cewa Gwamnatin Tarayya ta daina amfani da JAMB wajen shiga jami’o’i, polytechnics, da kwalejojin ilimi, kuma kowace cibiyar za ta gudanar da jarabawar shiga ta kanta.
A cikin wata sanarwa da Daraktan Hulda da Jama’a na Ma’aikatar Ilimi, Boriowo Folasade, ya fitar ranar Alhamis, Ministan Ilimi, Tunji Alausa, ya bayyana wannan ikirarin a matsayin “ƙarya, ba shi da tushe.”
Ministan ya ƙara da cewa wannan rubutu da ya yadu ba shi ne na ma’aikatar ba.
“A kowane lokaci ma’aikatar ba ta taɓa bayar da wata sanarwa ko izni da ke nuni da cewa JAMB ba ta da muhimmanci a shiga makarantun gaba da sakandare ba,” in ji Alausa.
Ya tabbatar da cewa JAMB na nan a matsayin hukumar doka da ta samu izini wajen shirya jarabawar shigarwa da kuma tsara yadda ake karbar dalibai zuwa dukkan makarantun gaba da sakandare a ƙasa baki ɗaya.
Tsarin shigarwa ta hanyar JAMB dai na ci gaba da aiki yadda ya k**ata, kuma duk wani bayani daban ya k**ata a yi watsi da shi kwata-kwata,” in ji ministan.
Alausa ya yi kira ga jama’a musamman matasa masu neman shiga makarantu, iyayensu, da makarantun gaba da sakandare da su dogara kacokan ga hanyoyin sadarwa na hukuma na Ma’aikatar Ilimi da JAMB don samun sahihan bayanai game da manufofin shigarwa.
Ya kuma jaddada ci gaba da haɗin kai tsakanin ma’aikatar da JAMB tare da sauran hukumomi da s**a dace domin tabbatar da gaskiya, adalci, da amincewa a tsarin shigar da dalibai cikin makarantun gaba da sakandare na Najeriya.
“Muna nan muna bin diddigi wajen kare gaskiyar tsarin shigarwa da tabbatar da cewa cancanta da bin ka’ida su ne su ke jagorantar dukkan karbuwar dalibai a manyan makarantun gaba,” in ji shi.
Yana mai gargadin kafofin watsa labarai, masu rubutu a yanar gizo, da dandamalin sada zumunta da su guji wallafa bayanai marasa tabbaci.
“Ya k**ata a guji yada bayanai marasa gaskiya da za su jawo ruɗani marar amfani a fannin ilimi,” in ji shi.
Ministan ya sake jaddada cewa babu wani sauyi a matsayin JAMB, wanda ya ci gaba da kasancewa cibiyar da ba za a iya musanta rawar da take takawa ba a tsarin ilimin gaba da sakandare na Najeriya. Duk wata wallafa ko rubutu a yanar gizo da ke da wata sabuwar ikirari dabam “ƙarya ce gaba ɗaya kuma ya k**ata a ɗauke ta haka."