PEN PRESS TV

PEN PRESS TV PEN PRESS TV HAUSA Kamfanin jarida ce mai zaman kanta, dake watsa ingantattun labaran ƙasa da ma Duniya bakiɗaya.

Gwamnatin Tarayya ta musanta rahotannin da ke yawo a yanar gizo cewa Hukumar Shirya Jarabawar Shiga Manyan Makarantu (JA...
16/10/2025

Gwamnatin Tarayya ta musanta rahotannin da ke yawo a yanar gizo cewa Hukumar Shirya Jarabawar Shiga Manyan Makarantu (JAMB) ba za ta sake zama dole wajen shiga makarantun gaba da sakandare a ƙasar ba.

Wasu rubuce-rubuce da s**a yadu a yanar gizo sun yi iƙirarin cewa Gwamnatin Tarayya ta daina amfani da JAMB wajen shiga jami’o’i, polytechnics, da kwalejojin ilimi, kuma kowace cibiyar za ta gudanar da jarabawar shiga ta kanta.

A cikin wata sanarwa da Daraktan Hulda da Jama’a na Ma’aikatar Ilimi, Boriowo Folasade, ya fitar ranar Alhamis, Ministan Ilimi, Tunji Alausa, ya bayyana wannan ikirarin a matsayin “ƙarya, ba shi da tushe.”

Ministan ya ƙara da cewa wannan rubutu da ya yadu ba shi ne na ma’aikatar ba.

“A kowane lokaci ma’aikatar ba ta taɓa bayar da wata sanarwa ko izni da ke nuni da cewa JAMB ba ta da muhimmanci a shiga makarantun gaba da sakandare ba,” in ji Alausa.

Ya tabbatar da cewa JAMB na nan a matsayin hukumar doka da ta samu izini wajen shirya jarabawar shigarwa da kuma tsara yadda ake karbar dalibai zuwa dukkan makarantun gaba da sakandare a ƙasa baki ɗaya.

Tsarin shigarwa ta hanyar JAMB dai na ci gaba da aiki yadda ya k**ata, kuma duk wani bayani daban ya k**ata a yi watsi da shi kwata-kwata,” in ji ministan.

Alausa ya yi kira ga jama’a musamman matasa masu neman shiga makarantu, iyayensu, da makarantun gaba da sakandare da su dogara kacokan ga hanyoyin sadarwa na hukuma na Ma’aikatar Ilimi da JAMB don samun sahihan bayanai game da manufofin shigarwa.

Ya kuma jaddada ci gaba da haɗin kai tsakanin ma’aikatar da JAMB tare da sauran hukumomi da s**a dace domin tabbatar da gaskiya, adalci, da amincewa a tsarin shigar da dalibai cikin makarantun gaba da sakandare na Najeriya.

“Muna nan muna bin diddigi wajen kare gaskiyar tsarin shigarwa da tabbatar da cewa cancanta da bin ka’ida su ne su ke jagorantar dukkan karbuwar dalibai a manyan makarantun gaba,” in ji shi.

Yana mai gargadin kafofin watsa labarai, masu rubutu a yanar gizo, da dandamalin sada zumunta da su guji wallafa bayanai marasa tabbaci.

“Ya k**ata a guji yada bayanai marasa gaskiya da za su jawo ruɗani marar amfani a fannin ilimi,” in ji shi.

Ministan ya sake jaddada cewa babu wani sauyi a matsayin JAMB, wanda ya ci gaba da kasancewa cibiyar da ba za a iya musanta rawar da take takawa ba a tsarin ilimin gaba da sakandare na Najeriya. Duk wata wallafa ko rubutu a yanar gizo da ke da wata sabuwar ikirari dabam “ƙarya ce gaba ɗaya kuma ya k**ata a ɗauke ta haka."

Fitowar jam'iyya mai suna Action Peoples Party (APP) da Dr. Chima Amadi, mai fafutukar ci gaba da wanda ya kafa The Mazi...
16/10/2025

Fitowar jam'iyya mai suna Action Peoples Party (APP) da Dr. Chima Amadi, mai fafutukar ci gaba da wanda ya kafa The Mazi Organization (TMO), a matsayin dandamalin sa na zaben gwamna na 2027.

Jiga-jigan jam’iyyun APC, PDP da ADC sun amince wannan sanarwa ta haifar da tsoro na yuwuwar sauya sheka mai yawa.

Masu goyon baya daga kowane bangare na siyasa na tunkarar wannan sabon motsi da ake ganin yana karfi sosai a karkashin al’umma.

Wani babban jami’i a jam’iyyar adawa da bai so a ambaci sunansa ya ce: “Wannan ba karar siyasa ce ta kowace rana ba. Abin da Dr. Amadi da TMO s**a kafa cikin shekaru uku da s**a wuce shafi ne na al’umma wanda ya shiga kowanne karamar hukuma guda 27. Wannan ne ke sa mana barci bai zo ba.”

Masanin siyasa Nze Joe Ogbe ya ce: “APP ba jam’iyya ce kawai ba; tsarin ne na motsi da ya riga ya wanzu. Wannan ne yasa tsofaffin shugabanni ke firgita—ba matsalar dan siyasa ne na yau da kullum suke fuskanta ba, sai cibiyar tsari mai inganci.

“Fitowar Amadi da APP shi ne alamar sauyi a shekaru,” in ji Ogbe. “Shaidar cewa siyasa a Imo na komawa daga mutum zuwa manufa.”

A taron kaddamarwa a Owerri, Dr. Amadi ya bayyana APP a matsayin “sabuwar kwangila tsakanin shugabanci da al’umma,” inda ya ce, “lokacin shugabanci mai tafiya da al’umma a Imo ya zo.”

Ya jaddada cewa APP tana wakiltar karfin siyasa na motsi mai zurfi da TMO ta gina ta hanyar ci gaban al’umma, karfafa matasa, da shirye-shiryen manufofi a duk kananan hukumomi 27 cikin shekaru uku da s**a wuce.

“Ba muna gina wata dabam dabam ba ce mai wucewa ba," in ji Amadi. "Wannan motsi ne na dogon lokaci da aka haifar daga gajiya da siyasar manyan mutane da bukatar shugabanci mai gaskiya.”

Masu lura da siyasa suna ganin wannan kaddamarwa ta APP da Amadi jagoranta na daga cikin muhimman sauye-sauye kafin zaben 2027, suna cewa jam’iyyar na iya zama inda masu rashin gamsuwa da tsofaffin jama’iyyun za su taru don samun sahihan shugabanni.

Sun ce ta hanyar The Mazi Organization, Amadi ya yi tarurrukan zama cikin gari, horar da matasa, da ayyukan al’umma wanda masana ke cewa ya tabbatar da sahihancin sa a jama’a kafin ya fito fili a siyasa.

Jami’ar Northwest da ke Kano ta naɗa Farfesa Aisha Garba Habib a matsayin mukaddashiyar shugabar jami’a, bayan kammala w...
16/10/2025

Jami’ar Northwest da ke Kano ta naɗa Farfesa Aisha Garba Habib a matsayin mukaddashiyar shugabar jami’a, bayan kammala wa’adin Farfesa Mukhtar Atiku Kurawa na shekaru biyar a kan wannan muƙami.

Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Abubakar Ibrahim, shugaban sashen hulɗa da jama’a na jami’ar, ya fitar a madadin magatakardar jami’ar.

Sanarwar ta bayyana sauyin shugabanci a matsayin “mai cike da lumana da tarihi,” kasancewar wannan shi ne karo na farko da mace za ta shugabanci jami’ar tun kafuwarta.

A cewar sanarwar: “Bisa tsarin gadon shugabanci na jami’ar, Farfesa Aisha Garba Habib, wadda take mataimakiyar shugabar jami’a ta ɓangaren ilimi, ta karɓi jagoranci a matsayin mukaddashiya.”

An gudanar da bikin mika ragamar aiki tsakanin Farfesa Kurawa da manyan jami’an jami’ar, inda ya kammala wa’adinsa tare da sanya hannu a kan takardun mika aiki.

Sanarwar ta ce, jami’ar ta cika da farin ciki da motsin rai yayin da ma’aikata, ɗalibai da tsoffin ɗalibai s**a nuna godiya da yabo ga jagoranci, hangen nesa da nasarorin da Farfesa Kurawa ya samu a lokacin mulkinsa.

Daga cikin ayyukan karshe da ya kaddamar akwai Hajiya Rabi Aminu Dantata Female Students’ Common Room, wacce marigayi Alhaji Aminu Alhassan Dantata ya gina domin walwalar ɗalibai mata, ginin da aka bayyana a matsayin muhimmiyar gudunmawa ga jin daɗin ɗalibai da ci gaban ilimi.

Farfesa Kurawa ya kuma ziyarci wurin aikin YUMSUK Microfinance Bank Limited, wani banki da Babban Bankin Najeriya (CBN) ya amince da shi ƙarƙashin tsarin “Non-Interest (Islamic) Microfinance Bank”, wanda aka kafa a lokacin shugabancinsa domin ƙarfafa shigar al’umma cikin harkokin kuɗi a jami’ar.

A lokacin sallamarsa, ma’aikata da ɗalibai sun raka shi daga ofishinsa zuwa gidansa a cikin wata gagarumar faretin ban kwana abin da sanarwar ta bayyana a matsayin “shaida ta girmamawa da soyayyar da al’ummar jami’ar ke masa saboda jagoranci nagari da gaskiya.”

“Ficewar Farfesa Kurawa ta nuna ƙarshen wani muhimmin lokaci a tarihin jami’ar,” in ji sanarwar. “Gaskiya, kirkira da jajircewar da ya nuna wajen inganta ilimi za su ci gaba da zama abin koyi ga al’ummar jami’ar da ma ƙasar baki ɗaya.”

Jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) ta Jihar Legas ta ce Najeriya ba za ta zama kasa mai jam’iyya guda ɗaya ba, ko ...
16/10/2025

Jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) ta Jihar Legas ta ce Najeriya ba za ta zama kasa mai jam’iyya guda ɗaya ba, ko da yake akwai yawaitar barin jam’iyyun adawa zuwa jam’iyya mai mulki, All Progressives Congress (APC).

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa gwamnonin jihohi da ’yan majalisar dattijai, ’yan majalisar wakilai da na majalisun dokoki na jihohi da aka zaba a jam’iyyar PDP da wasu jam’iyyun sun yi watsi da jam’iyyunsu s**a koma APC.

NAN ta tunatar da cewa gwamnan PDP, Peter Mbah na Jihar Enugu da Douye Diri na Bayelsa kwanan nan sun shiga cikin yawan ’yan majalissar tarayya da na jihohi a jihokinsu.

Gwamnan Akwa Ibom, Umo Eno ya bar PDP ya shiga APC a farkon watan Yuni, yayin da gwamnan Delta, Sheriff Oborevwori da wanda ya gabace shi, Dr Ifeanyi Okowa, tare da ’yan PDP da dama a Delta s**a koma APC.

A martaninsa, Mataimakin Shugaban PDP na Jihar (Legas Tsakiya), Mista Hakeem Olalemi, ya shaida wa NAN cewa ba za a ruguza jam’iyyar saboda yawan barin jam’iyya ba, ya ce PDP tana cikin zukatan ’yan Najeriya.

Ya ce masu barin PDP suna yin hakan ne don dalilai na son kai, kuma wannan gagarumin matsalar ba za ta tantance sak**akon zaben 2027 ba.

“Ina iya sanar da duk wanda ke sha’awar jin cewa PDP za ta tsaya tsayin daka bayan taron jam’iyyarmu na watan Nuwamba.

“Ina da tabbacin cewa ’yan Najeriya ba su shirya zama kasar jam’iyya guda ba saboda hakan zai kawo mulkin k**a karya da danniya. ’Yan Najeriya na son tsarin dimokiradiyyar jam’iyyun da yawa.

“Mutanen Najeriya nagari ba za su amince da hakan (jam’iyya guda ba). Gwamnatin APC ba ta burge mutane a kasar. ’Yan Najeriya za su nuna hakan a zaben,” in ji Olalemi.

Sai dai babban jagoran PDP ya ce sauyin jam’iyya ba sabon abu bane.

Ya kara da cewa, “Mutane na canja jam’iyya, amma mene ne dalilin su na barin PDP su shiga APC?

“Shin rikici ne a PDP? Idan haka ne, hakan na nuna ba su da ƙarfin hali su tsaya su gyara rikicin don jin dadin ’yan Najeriya da ke sa ran samun ceton daga jam’iyyar adawa.

“Idan akwai rikici a gida ko a iyali inda aka haife mu, shin ya k**ata mu bar gidan mu mu tafi gidan wani?

“Abinda ake so shine a jira a warware rikicin. Idan gudun PDP ne zai sa su zama mutane, to mu gani a 2027.”

Hukumar NSCDC reshen jihar Jigawa ta fara gudanar da  binciken kisan wata yarinya mai shekaru uku a ƙaramar hukumar Kiya...
16/10/2025

Hukumar NSCDC reshen jihar Jigawa ta fara gudanar da binciken kisan wata yarinya mai shekaru uku a ƙaramar hukumar Kiyawa.

Wannan na cikin wata sanarwa da kakakin hukumar, ASC Badaruddeen Tijjani, ya fitar a Dutse.

An fara neman yarinyar daga ranar Talata, 14 ga Oktoba, 2025, amma an samu gawarta a jeji dake kusa da unguwarsu ranar Laraba, 15 ga Oktoba, tare da raunuka da dama.

Binciken asibiti ya tabbatar an yi mata fyade, azabtarwa, sannan aka kashe ta.

Hukumar ta yi Allah wadai da wannan mummunan abu, kuma kwamandan NSCDC, Muhammad Kabiru, ya umurci sashen leken asiri da bincike su yi haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro wajen kamo masu laifin.

An mika gawar ga iyalanta domin jana'iza.

Ana kira ga jama’a su taimaka ta hanyar bai wa hukumomi rahoton duk wani shakka ko wani abu na musamman.

Ministan Yaɗa Labarai, Mohammed Idris, ya bayyana cewa yana sa ran jam’iyyar APC za ta ƙara samun rinjaye a ƙasar nan ta...
16/10/2025

Ministan Yaɗa Labarai, Mohammed Idris, ya bayyana cewa yana sa ran jam’iyyar APC za ta ƙara samun rinjaye a ƙasar nan ta hanyar mamaye akalla jihohi 30 daga cikin 36 kafin shekarar 2026.

Idris ya bayyana hakan ne a yayin taron dabarun aiki na watanni uku-uku na shekarar 2025 da ƙungiyar gwamnonin APC ta shirya a Maiduguri, babban birnin jihar Borno.

Ya ce taron ya mayar da hankali ne kan yadda za a ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin gwamnatin tarayya da jihohin da jam’iyyar ke mulki, domin tabbatar da daidaitaccen ci gaban ƙasa.

Ya ce yawaitar sauya sheka daga ‘yan adawa zuwa APC na ƙara tabbatar da cewa jam’iyyar na samun karɓuwa a tsakanin al’umma saboda kyawawan manufofi da shirye-shiryen Shugaba Bola Ahmed Tinubu, musamman a fannin tattalin arziki da ci gaban al’umma.

“Yanzu haka, jama’a na ganin sak**akon gyare-gyaren da ake yi daga daidaituwar darajar Naira zuwa tsare-tsaren da ke ƙara inganta rayuwar ‘yan ƙasa. Wannan ne ke jawo mutane da dama su rungumi jam’iyyar APC,” in ji Idris.

Ministan ya ƙara da cewa gwamnatin Tinubu za ta ci gaba da aiwatar da manufofi masu ma’ana da nufin tabbatar da ingantaccen mulki, bunƙasar tattalin arziki.

Yayin da yake magana, Shugaban Riko na Hukumar, Injiniya Isyaku Umar Kwa, ya ce wannan mataki na biyu zai inganta tsarin...
16/10/2025

Yayin da yake magana, Shugaban Riko na Hukumar, Injiniya Isyaku Umar Kwa, ya ce wannan mataki na biyu zai inganta tsarin lamuran shara, tattarawa da raba sharar gida a Duk Kwankwasiyya City, don tabbatar da tsaftar tituna da wuraren jama’a. Haka kuma za a ci gaba da kyawun wuraren jama’a, ciki har da wuraren shakatawa da gungun jama’a, domin ƙara ƙarfin al’umma da ƙyawun gani.

Kwa ya ce wannan mataki zai ƙara ƙarfafa mazauna Kwankwasiyya City, Bandirawo, da Amana su shiga harkar kiyaye tsafta da lafiya a unguwannensu. Ya ce wannan yunƙurin tsafta na taimakawa wajen rage cututtuka masu alaƙa da sharar gida ta hanyar inganta tsarin tafiyar da sharar gida da kiyaye tsafta.

Shugaban ya ƙara da cewa, “Tsafta alhakin kowa ne. Muna kira ga duk mazauna da ma’aikatan Kamfanin su yi haɗin kai wajen kiyaye biranenmu su kasance masu tsafta da aminci,”.

Gwamnatin jihar Kano na ƙoƙarin dawo da waɗannan manyan biranen cikin kyakkyawar hali, musamman Kwankwasiyya, wanda aka kafa a zamanin Buhari, domin magance matsalolin gidaje, yawaitar birane da ƙalubale na dorewa.

Hanyoyin tsaftacewa suna da matuƙar muhimmanci wajen cimma waɗannan burin cigaban birane, in ji shi.

Gwamnatin Jihar Kano karkashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf na taya Malam Abubakar Balarabe Kofar Naisa murnar nad...
16/10/2025

Gwamnatin Jihar Kano karkashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf na taya Malam Abubakar Balarabe Kofar Naisa murnar nadinsa a matsayin Janar Manaja na Guarantee Radio 94.7 FM Kano.

Naɗinsa a matsayin GM na Guarantee Radio na daraja ce ga shekaru na sadaukarwa, kwarewa, da rawar gani wajen bunƙasa harkar yada labarai a jihar da kasa baki daya.

Kofar Naisa ya shahara a matsayin kwararren mai aikin jarida mai gaskiya da jajircewa wajen inganta ilimantarwa da hidimar al’umma.

Gwamnatin jihar na da tabbacin cewa Manajan Janar na zamani zai kawo sabbin dabaru, jagoranci mai kyau da kuzari wajen tafiyar da Guarantee Radio bisa manufar tashar ta yada labarai nagari da amintattu a Kano.

Ana roƙon Malam Kofar Naisa, a madadin Gwamnatin Jihar, ya ci gaba da kiyaye ƙa’idar ƙwararru da ingantaccen hidima, yayin da Ma’aikatar Bayani da Harkokin Cikin Gida ke tabbatar da goyon bayan ci gaban bangaren yada labarai a matsayin muhimmiyar abokiyar hulɗa wajen inganta gaskiya, nagartar shugabanci da shiga harkokin jama’a.

Ministan Harkokin Ma’adanai, Dr Dele Alake, ya ce a rufe makarantu a Najeriya da suke karbar kuɗin makaranta a kuɗin kas...
16/10/2025

Ministan Harkokin Ma’adanai, Dr Dele Alake, ya ce a rufe makarantu a Najeriya da suke karbar kuɗin makaranta a kuɗin kasashen waje.

Alake ya bayyana haka a bikin Ranar Zinariya ta Najeriya a Abuja, yayin makon ma’adanai na kasa na 10, inda ya kalubalanci wannan dabi’a a matsayin rashin gaskiya cikin tattalin arzikin kasa.

Ya ce zai kai bukatar a rufe irin wadannan makarantu ga Majalisar Zartarwa ta Tarayya saboda yadda suke jan kudin kasashen waje cikin tattalin arzikin Najeriya.

Ministan ya kara da cewa gwamnati na shirin daukar matakai ta zamani don dakile duk wani zamba a harkar zinariya, da bunkasa darajar naira.

Tsarin sayen zinariya kai tsaye daga ma’adanai na gida a naira zai taimaka wajen kara ajiyar kudin waje da karfafa naira.

A jawabinta, Fatima Shinkafi, Darakta na SMDF, ta ce binciken zinariya a Najeriya na karuwa kuma ta yi kira ga masu halarta su kara amfani da damammakin zinariya.

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Katsina ta cafke wata ƙungiya ta mutane 11 da ake zargin masu fashi da makami ne da ke tayar...
16/10/2025

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Katsina ta cafke wata ƙungiya ta mutane 11 da ake zargin masu fashi da makami ne da ke tayar da jijiyoyin ƙwaƙwalwa a hanyoyin Sha’iskawa-Charanchi da Katsina-Kankia-Kano.

DSP Abubakar Aliyu, mai magana da yawun hukumar, ya shaida wa manema labarai a Katsina ranar Laraba cewa waɗanda ake zargin suna toshe hanyoyin ne sannan su sace mota-motar da ba su sani ba.

Sunayen masu zargin sun haɗa da: Dikko Maaru, Dardau Kabir, Muntari Musa, Labaran Amadu, Usman Maaru, Lawal Zubairu, Nasiru Sanusi, Adamu Kabir, Abdullahi Zubairu, Muhammad Usman da Sale Shehu, duk suna tsakanin shekaru 21 zuwa 35.

DSP Aliyu ya ce, “An samu nasarar cafke ɗaya daga cikin ƙungiyar ranar Lahadi zuwa ƙarfe 10 na safe, bayan an samu bayanin sirri mai inganci.

“Nan take jami’anmu s**a bi sawun wanda ake zargin har s**a k**a shi, abin da ya kai ga k**a sauran mambobin ƙungiyar.”

A yayin bincike, an samo agogon hannu 80, wayoyin salula 9, da wuka daga hannun masu zargin.

Kwamishinan ‘Yan Sanda, Bello Shehu, ya yaba wa jami’an da rawar da s**a taka kuma ya gode wa jama’a bisa goyon bayansu.

Aliyu ya rawaito cewa CP ya nemi jama’a su ci gaba da bayar da muhimman bayanai don taimakawa yaki da laifi a jihar.

Ya kuma ce za a gurfanar da masu zargin a kotu bayan kammala bincike.

Majalisar Zartaswa ta Jihar Kebbi ta amince da gyaran asibitoci guda bakwai a fadin jihar da kuɗin Naira biliyan 4.05.Al...
16/10/2025

Majalisar Zartaswa ta Jihar Kebbi ta amince da gyaran asibitoci guda bakwai a fadin jihar da kuɗin Naira biliyan 4.05.

Alhaji Junaidu Marshall, Babban Lauyan Gwamnatin Jihar kuma Kwamishinan Shari’a, ya bayyana haka bayan taron majalisar a Birnin Kebbi. Asibitocin da za a gyara sun hada da na Kambaza, Suru, Kamba, Dirin-Daji, Kangiwa, Koko da Yauri.

Asibitin Argungu kuma an riga an gyara shi tare da samar da kayan aiki na zamani, yayin da wasu asibitoci a Zaga, Zuru, Bunza, Gulma, Bena, Jega, Shanga da Sir Yahaya a Birnin Kebbi suna cikin gyara ko kammalawa.

An gyara asibitoci 16 cikin jihar, yayin da aka samu sabon amincewa kan asibitoci bakwai. Gwamna Nasir Idris ya yi alkawarin gyara asibitoci 30 gaba daya kafin ya kammala mulki.

Majalisar ta amince da sakin Naira miliyan 570 ga Hukumar Kula da Kiwon Lafiya ta Jihar (KECHEMA) domin yi wa mutane 45,000 rajista, ciki har da kowane karamar hukuma da mutane 200 masu rauni.

Hakanan an amince da gyaran cibiyoyin kiwon lafiya na asali guda 42 yayin da aka riga an gyara 73 a karkashin shirin tallafi na Bankin Duniya.

An ba da tallafin Naira miliyan 407.5 ga Hukumar Kula da Magunguna da Kayan Likita ta Jihar domin samar da magunguna masu rahusa.

An kafa Hukumar Kididdiga ta Jihar Kebbi, inda aka ware Naira miliyan 900 a matsayin kudin fara aiki, tare da naɗa Prof. Umar Usman a matsayin Babban Mai Kididdiga.

Majalisar ta kuma amince da sayen injinan noman kasa 2,000 a farashin Naira biliyan 3 a karkashin shirin Kaura Development Agenda (KADAGE) domin bunkasa noma.

Haka zalika an ware Naira biliyan 1.4 domin sayan kayan makaranta don inganta yanayin koyarwa a dukkan makarantun jihar.

Gwamnan Jihar Kebbi ya ɗauki wata babbar ƙungiyar tsaro ta ƙasa da ƙasa don magance ayyukan 'yan bindiga da Lakurawa. Ah...
16/10/2025

Gwamnan Jihar Kebbi ya ɗauki wata babbar ƙungiyar tsaro ta ƙasa da ƙasa don magance ayyukan 'yan bindiga da Lakurawa. Ahmed Sale Jnr, shugaban Gsafety mai hedkwata a China, ya ce ƙungiyar tana aiki a ƙasashe 36 tana amfani da fasahar zamani wajen tattara bayanai don yakar ‘yan ta’adda.

Sale ya bayyana cewa za su hada kai da tsaro na jiha da na tarayya don kawo karshen wannan matsala ta amfani da fasaha mai zurfi. Ya kara da cewa gwamnati na iyakance wajen amfani da fasahar zamani, lamarin da ke hana samun nasara sosai a yaki da ta’addanci.

Address

Sani Kabara Along Zoo Road Kano
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when PEN PRESS TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share