22/09/2019
ZURIYAR SARKIN KANO DABO: INA MUKA DOSA?
(Revised Edition).
Gudunmawa Daga:
ARC. AHMAD ABBA YUSUF.
Domin Murnar Cika Shekaru Dari Biyu (200) Na Zuriyar Sarkin Kano Ibrahim Dabo A Mulkin Kano.
(Ibrahim Dabo Dynasty Bicentenary: 1819 - 2019).
GABATARWA:
Sullubawan Dabo (Zuriyar Sarkin Kano Ibrahim Dabo) na daga cikin manyan gidaje wadanda s**a shahara kuma suke da kima a idon Jama'a, ba a nan Kano kadai ba, har da sauran sassa na kasar nan da ma sauran kasashe na duniya. Allah SWT Ya albarkaci Zuriyar da yawan mutane da ya haura sama da Dubu Hamsin (over 50,000); wadanda s**a yadu a Arewacin Nigeria da sauran sassa na duniya. Haka kuma, Allah SWT Ya damka ragamar Sarautar Kano a hannun 'yan wannan gida yau tsawon shekaru 200 kenan; tun bayan da Mai Alfarma Ameerul Mu'mineen Muhammad Bello dan Shehu Usman Danfodiyo ya tabbatar da nadin Mallam Ibrahim Dabo Bin Mahmud a matsayin Sarkin Kano; ranar Ashirin da Daya ga watan Satumba na shekarar 1819 Miladiyya (21/09/1819). Zuwa yanzu, wannan gida ya samar da Sarakunan Kano guda Goma Sha Uku (13), daga cikin Sarakuna Goma Sha Hudu (14) na Daular Shehu Usman Danfodiyo a nan Kano. Bugu da kari, wannan gida na Dabo ya samar da manyan mutane wadanda s**a shahara a fannoni daban-daban na rayuwa a fadin duniya. Mutum bai yi kuskure ba idan ya ce Zuriyar Sarkin Kano Dabo su ne kashin bayan cigaban Kano, duba da muhimmiyar rawar da suke takawa wajen inganta al'amuran Addini da Sarauta da Tattalin Arziki da ilimi da kiwon lafiya da Hadin-Kai da zaman lafiya da siyasa da sauran fannoni na cigaba. Masana tarihi sun yi ittifaki cewa, Zuriyar Sarkin Kano Dabo mutane ne masu tsantsar ilimi da kiyaye dokokin Allah SWT da kunya da kawaici da jarumta da "Tawadhi'u" da gaskiya da rikon amana da KARFAFA ZUMUNCI da jajircewa wajen yin sana'oi domin dogaro-da-kai da kwarewa wajen shugabancin Jama'a; bisa tausayi da adalci, da dai sauran "Makaarimul-Akhlaaq."
ME MUKE SO MU ZAMA?:
Yayin da 'Yan-uwa suke murnar cika shekaru Dari Biyu (200) da mulkin Kano a hannun wannan zuriya tamu, ni kuma babban abinda ya ja hankali nah shi ne, yanda a hankali a hankali muka fara sauka daga kan kyakkyawan tsari da magabata s**a dora mu. Idan muka tsaya muka yi duba a tsanaki za mu ga cewa, kyawawan dabi'u da aka san 'yan wannan gida da su tun iyaye da kakanni, yanzu sun fara zama tarihi. Mun dakko dabi'u marasa kyau mun yafa wa kanmu. Abin takaici, sai ka ga mutum cikakken Basullube, amma babu karatun boko babu na Addini babu sana'a, sannan dabi'unsa ma ba masu kyau ba ne, amma yana tinkaho shi jikan Dabo ne, bayan Allah Ya sani, Mallam Dabo ba haka ya gudanar da rayuwar sa ba!
Zumunci kuwa yanzu dama ba a maganarsa. Yanzu Idan ba ka da mulki ko kudi, toh ba za a yi zumunci da kai ba. Karfi da yaji an kirkiro rabe-rabe kamar su "Dan Sarki" (wai Basullube wanda babansa ya yi Sarki), "Dan Hakimi" (Basullube wanda babansa Hakimci kawai ya yi) da kuma "Dan Mallam" (Basullube wanda babansa bai yi Hakimci ba kuma bai yi Sarki ba). Haka kuma, wai akwai wadanda ake kira 'YAN FULANIN DAA (Zuriyar Dabo wadanda kakannin su s**a yi Sarki amma yanzu sarautar ba a gidansu take ba), da kuma DIDDIGAR QAYA (zuriyar Dabo wadanda iyayensu da kakannin su ba su taba yin sarauta ba.
Yawanmu shi ma ya zama na "taron tsintsiya ba shara," domin kuwa kowanne "kare da doki" zai iya zuwa ya ci mutuncin wannan gida namu kuma babu abinda za mu iya yi a kai, hasali ma sai dai ya samu hadin-kai daga wasu daga cikinmu. Babban abin takaicin shi ne, wadanda s**a fi kowa cin moriyar sarautar, su ne ake hada kai da su wajen rushe ginin da iyaye da kakanni s**a sadaukar da lokacinsu da dukiyoyin su da ma rayukansu wajen ginawa!
DA DAN GARI AKAN CI GARI:
Dabarun yaki suna da yawa, daga cikinsu akwai yin amfani da dan gari a ci garinsu da yaki. Duk mai biye da tarihin Kano ya san yanda kakannin mu Fulani s**a yi amfani da wannan dabara ta yaki a kan Chiroman Kano Danmama (dan Sarkin Kano Alwali) wanda ya taimaka musu lokacin Jihadi s**a hambare mahaifin sa daga Sarautar Kano. Burinsa a wancan lokacin shi ne, idan an samu nasarar kawar da mahaifin nasa, shi sai a nada shi a matsayin Sarkin Kano. Amma daga karshe mai ya faru da shi? A duba tarihi! Haka Mallam Usman Bahaushe (wanda shi ma dan-uwan Sarkin Kano Alwali ne) shi ma ya taimaka wa Fulanin wajen rushe mulkin da kabilarsa (Habe) s**a shafe sama da shekara dari Takwas (800) suna yi a wancan lokacin. Shi ma wacce irin riba ya samu? Haka kuma tarihi ya nuna yanda Turawan Mulkin mallaka s**a yi amfani da wannan dabara a kan Chiroman Kano Abdu Lele (dan Sarkin Kano Tukur). Shi s**a sako a gaba cikin rundunar su, tare da yi masa alkawarin idan ya rako su Kano s**a ci ta da yaki, za su nada shi Sarkin Kano. Haka kuwa aka yi, domin Chiroma Abdu Lele ya cika wannan alkawari nasa ga Turawan Mulki, inda ya rako su Kano; garin iyayen sa da kakannin sa, su ka ci ta da yaki. Haka kuma ya raka su Gidan Sarki s**a shiga s**a kori iyalin dan-uwan sa, Sarkin Kano Alu. Shi ma Chiroma Abdu Lele, da me Turawa s**a saka masa bayan sun yi amfani da shi sun cimma burinsu? Mu duba tarihi! Tabbas "gani ga wane ishi wane tsoron Allah," saboda haka duk rintsi kada ka yarda ka hada kai da magauta a ci mutuncin dan-uwanka, idan bukatar su ta biya, kai ma jefar da kai za su yi!
SHAWARA/RUFEWA:
Ina kira ga dukkan Zuriyar Dabo cewa, kada cika shekaru Dari Biyu (200) a mulki ya rude mu har mu yi zaton cewa shikenan "MU ZA MU YI TA YI HAR MAHADI." Muna fatan hakan dai, amma tabbas idan muka cigaba da sauka daga kan tsari wanda magabata s**a dora mu; wato kiyaye dokokin Allah da sauran kyawawan dabi'u, toh Allah Zai iya kawar da mu, Ya kawo wadanda s**a fi mu kyautatawa! Haka kuma, ina kira a gare mu da mu hade kanmu mu, mu cigaba da zama a matsayin mu na TSINTSIYA MADAURINKI DAYA domin mu ci moriyar yawan da Allah Ya namu. Mu daina nuna banbanci a tsakanin mu, mu koma kan tsari na gaskiya kamar yanda magabata s**a rayu, cewa DUK WANDA YA FITO DAGA TSATSON MALLAM IBRAHIM DABO, DAN SARKI NE. Yanzu muna cikin wani zamani mai cike da rudani da kuma sauye-sauye, wanda ka raina a yau ko kake ganin bai isa ba, gobe zai iya zama a samanka. Saboda haka mu yi zumunci da juna saboda Allah ba sabo da abin duniya ba, mu tsarkake zukatanmu daga kyashi da hassada da son-rai. Mu yi kokari wajen koyi da kyawawan halaye na magabata, ba kawai mu rika alfaharin nasabtuwa da su ba.
Daga karshe, Hausawa sun ce: "GYARA KAYANKA, BA YA ZAMA SAUKE MU RABA," ina kira gare mu da babbar murya cewa, mu dawo cikin hayyacin mu kuma mu fuskanci kalu-bale da yake gabanmu, mu yi karatun ta-nutsu; kafin lokaci ya kure mana, mu gyara abubuwan da muke yi, wadanda ka iya zama barazana ga martabar da muke takama da ita ta wannan gida. Idan kuma muna ganin a hakan dai za mu cigaba da tafiya toh, amma tambayar da ya kamata mu yi wa kanmu ita ce INA MUKA DOSA?
©AHMAD ABBA YUSUF,
Muharram, 1440 A.H
September, 2019 C.E.