Tsohuwar Ajiya

Tsohuwar Ajiya Domin nishaɗantar daku da tsofaffin bidiyo, labarai, da abubuwan da s**a faru a baya. Ku kasance tare damu a koda yaushe domin jin daɗinku.
(1)

We share old and new videos, precisely historical ones, where we see how things were before for entertainment, history, and your enjoyment.

Sponsored Shugaba Tinubu ya taya Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf murnar zagayowar ranar haihuwarsaShugaban ƙasa Bola Ahmed...
04/01/2026

Sponsored

Shugaba Tinubu ya taya Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf murnar zagayowar ranar haihuwarsa

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, murnar cika shekaru 63 a duniya, wanda ya cika ranar 5 ga watan Janairu, 2026.

A cikin saƙon taya murnar da ya fitar, Shugaba Tinubu ya yaba da halayen nagarta da rikon amana da tawali’u da kuma jajircewar Gwamna Yusuf wajen hidimar al’umma, yana mai cewa waɗannan halaye sun bayyana karara a yadda yake tafiyar da harkokin mulkin Jihar Kano.

Tinubu ya bayyana cewa an zaɓi Abba Kabir Yusuf a matsayin gwamnan Kano a shekarar 2023 a ƙarƙashin jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP), inda kafin hakan ya taɓa riƙe muƙamin Kwamishinan Ayyuka, Gidaje da Sufuri daga shekarar 2011 zuwa 2015 a lokacin mulkin tsohon gwamnan jihar, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso.

Shugaban ƙasar ya bayyana Kano a matsayin cibiyar siyasar ci gaba a Arewa, yana mai cewa salon mulkin Gwamna Yusuf ya sake jaddada ƙudurorin ci gaban ƙasa da ƙasa (grassroots development) da kuma rage wa talakawa raɗaɗin rayuwa, k**ar yadda marigayi Malam Aminu Kano ya assasa tun da dadewa.

A cewar Tinubu:
“Ƙwarewar Gwamna Yusuf a harkokin shugabanci, musamman shekarun da ya yi yana jagorantar manyan ma’aikatun jiha a matsayinsa na kwamishina, sun taimaka masa wajen aiwatar da sauye-sauyen ababen more rayuwa da ake gani a Kano a yau.

“Ya kaddamar da shirye-shiryen sabunta birane, gina gadaje da hanyoyi, ciki har da aikin gina tituna masu tsawon kilomita biyar a kowace ƙaramar hukuma ta jihar.

“Haka kuma na samu labarin cewa ayyana dokar ta-baci a fannin ilimi da ya yi ta haifar da gagarumin ci gaba a sak**akon ɗaliban Kano a jarrabawar NECO.”

Shugaba Tinubu ya yi wa Gwamnan Kano fatan tsawon rai da ƙarin shekarun jagoranci mai cike da sauye-sauye da alheri ga al’ummar jihar.

KAZA DA MUZURUKaza ce dai ta ce ba ta son kowa a cikin duk 'yan uwanta zakaru masu nemanta. Ta dage ita sai muzuru kawai...
04/01/2026

KAZA DA MUZURU
Kaza ce dai ta ce ba ta son kowa a cikin duk 'yan uwanta zakaru masu nemanta. Ta dage ita sai muzuru kawai ta ke so da aure.
Iyayenta ma s**a ce ba za su ba ta
shi ba. Ita kuma ta ce shi. ta ke so.
Da s**a ga ta dage, sai s**a ce,
"To, mu dai babu ruwammu. Kada ki
je ki jawo mana abin da zai hallaka mu baki đaya.
Kaza kuwa ta ce ita dai shi ta ke so,
ba za ta sake ba..
Sai aka kirawo ƙawayenta s**a
rarraba goron biki.
Shi ke nan, aka yi biki. Sai 'yam matan amarya s**a je sUna waka suna cewa:
'Ke kaza kar ki jawo mana
tserereniya da muzuru,'
Sai kaza ta ce:
"Shi ba ya cín kaji, mhn.
Shi ba zal ci kaji ba, mhn.
In ji dai ni na kai kaina, mhn,
Shỉ ke nan, sal s**a ce da makaɗin
ya sauya musu kida.
Shi kuwa makadin zakara ne, saboda
a dangin amarya ya ke. Sannan ga
kuma angwaye muzurai sun jeru,
Suna jin waka.
Shi ke nan, sai 'yar ƙaramar kaza ta
shiga fage ta ce:
'Ni auta, autar kaza,
In waiwaya haka,
In muskuta haka,
Sai na kan ji kidan da dadi.'
Sai ta fita wata kumå ta shiga
ta ce:
'Ni wake-waken kaza,
Kazar da ba a duka,
Kazar da ba a zagl.
In waiwaya haka,
In muskuta haka,
Sai na kan ji kidan da dadi.
Shi kuma makadin zakara, yana
cewa:
'Daga baya-baya naka tsaya.
In na ji kaya-kaya in noƙe."
Sai kuma kaza ta uku ta shiga
ta ce:
'Ni ja-ja ja-jar kaza,
Kazar da ba a duka.
Kazar da ba a zagi,
In waiwaya haka,
In muskuta haka,
Sai na kan ga idon muzuru!"
Daga nan fa sai angwaye muzurai
s**a yiwo kan 'yan biki kaji
radadada.
Muzurai s**a fara cirah su kai, su
ƙafa, su fukafiki na kaji. Ita kuwa
amarya sai cewa ta ke yi, kar ka
cire mini fukafiki. Kar ka cire mini
kai.' S**a isa gida da ƙyar, suna
cewa: "Ga shi ta jawo mana tsiya.
Wanda bai ji bari ba, zai ji hoho. An
ce ta bari ta ƙi.'
Kurunkus kan ɗan ƙusu.

Kuma har yanzu ana damawa da ita. Muna gaishe da Yaya Yakubu Musa. Taskira, Satumba 2013
04/01/2026

Kuma har yanzu ana damawa da ita. Muna gaishe da Yaya Yakubu Musa.
Taskira, Satumba 2013

Yaya sunan wannan wurin na farko, kuma wanne suna ya koma daga baya? Ko har yanzu akwai wurin? A wanne gari yake?
04/01/2026

Yaya sunan wannan wurin na farko, kuma wanne suna ya koma daga baya? Ko har yanzu akwai wurin? A wanne gari yake?

The Lion and the tortoise
03/01/2026

The Lion and the tortoise

ƊAN-ƘASHIN-GWIWAWata rana an yi wata mace mai yawan roƙon haihuwa. Ran nan sai wani đan kurji ya fito mata a kan gwiwart...
03/01/2026

ƊAN-ƘASHIN-GWIWA
Wata rana an yi wata mace mai yawan roƙon haihuwa. Ran nan sai wani đan kurji ya fito mata a kan gwiwarta. Sai ta ce, "Allah ka ba ni da ko da na ƙashin gwiwa ne ma mana?"
Shi ke nan, take sai ta ɓincine ƙurjin nan na kan gwiwarta. Sai kuwa ta ga ɗa ya fito subul. Sai ta yi murna.
Bayan ta gama murna, sai ta ce, "To, yau kuma ina zan sami itacen wanka?"
Sai Ɗan-Ƙashin-Gwiwa ya ce, "ya ba ga ni ba?"
Sai kuwa ya je ya yiwo mata itace mai yawa, ya kawo mata.
Ta kuma cewa, "Ko ina zan sami abincin da zan ci?"
Sai ya ce, "Iya ba ga ni ba?"
Sai ya je gidan namun dawa ya ɗebo mata alk**a da shinkafa da dai hatsi iri iri ya kawo mata.
Kullun sai ya je ya debo mata hatsi himi, har daKullu nan namun dawa s**a gane cewa ana yi musu satar hatsinsu.
Sai s**a yi shawara s**a bar kura jiran Barawon don in ya zo yin sata ta k**a shi, ta đaure, kafin su dawo.
Shi ke nan. S**a bar kura jiran. Tana zaune sai Ɗan-Ƙashin-Gwiwa ya zo.
Sai ta ce, "To, da ma ashe kai ne ka ke zuwa kana yi mana sata?"
Sai ya ce, "Au, ke aka bari jira yau?"
Sai kuwa ya ɗauki kura ya ɗaga ta sama ya raɗa ta da ƙasa tim. Ya ciro gashin kansa guda daya ya đaure ta ya jefa sama. Ya debi kayan abinci ya yi tafiyarsa
abinsa.
Can sai ga namun dawa sun dawo. S**a samu kura a sama a ɗaure. S**a sauko đa ita s**a tambaye ta yadda aka yi.
Kura ta ce, "Ai wannan ɓarawon ya fi ƙarfina."
Sai s**a ce, To wannan sai zaki ne zai iya ke nan,"
Aka bar zaki jira. Zaki yana zaune yana jira sai ga Ɗan-Ƙashin-Gwiwa ya zo.
Sai zaki ya ce, "To, ashe da ma kai ne ka ke zuwa kana yi mana sata? To yau Allah ya sa na k**a ka."
Sai Dan-Kashin-Gwiwa ya ce, "Au, yau kuma kai aka bari jira?"
Sai ya ɗauki zaki ya fyada da ƙasa. Ya ciro gashin kansa guda daya ya ɗaure zaki da shi. Ya debi kayan abinci yadda ya ke so ya tafi abinsa.
Da namun dawa s**a dawo s**a samu zaki a wannan hali, sai s**a ce, "Yaya aka yi haka kuma zaki?"
Sai ya ce, "Ai wannan ɓarawon ya fi karfina.'"
Sai s**a ce, "Ai wannan sai dai giwa ce kawai za ta iyar masa."
Sai s**a tafi s**a bar giwa jiran ɓarawo. Tana cikin jira sai ga Ɗan-Ƙashin-Gwiwa ya zo. Sai ta ce da shi, wato da ma kai ne ka ke zuwa kana kwashe mana kaya ko? To na ritsa ka yau."
Sai ya ce, "Af, yau kuma ke aka bari iira
Sai ya dauke ta ya damfara da kasa. Ya ciro gashin kansa daya ya daure ta da shi. Ya yi tafiyarsa abinsa.
Can sai sauran namun dawa s**a zo. Da s**a ga giwa a wannan hali, sai s**a ce, *Me kuma ya faru giwa?"
Sai ta ce da su, "Ai wannan ɓarawon ya fi ƙarfina."
Sai s**a ce, "To tun da ya ke abin ya fi ƙarfin giwa ma ai sai mu gudu.'"
Sai s**a shiga haɗa, kaya. Suna ta shirin gudu. Kafin su gama sai Ɗan-Ƙashin-Gwiwa ya ji labari ya rugo da
gudu ya shiga tandun mai. Namun dawan ba su gan shi ba.
Da s**a gama shiri, sai kura ta ce ita ce Za ta dauki tandun man. Sai aka yarda ta dauka.
Sai s**a dauki kaya s**a k**a hanya. Suna cikin tafiya sai kura ta ce, "Ni zan ba da waƙa, ku kuma kuna amsawa,"
Sai s**a ce, "To, bisimilla."
Sai kura ta fara sa waka:
Mun rarrabo da Ɗan-Ƙashin-Gwiwa;
Ɗan shegiya.
Ana cikin wannan hali, sai kura sarkin kwaɗayi ta ce za ta fitsari. Su kuwa sai s**a ce da ita ta ba su tandun màn. Sai ta ce, "Au, zan sha muku ne?"
Sai ta tafi yin fitsari da tandun man. Ta je ta bude tandu za ta saci mai sai ta ga Ɗan-Ƙashin-Gwiwa a ciki yana yi mata daƙuwa yana cewa, '"Uwaki. ldan kuwa
kika faɗa, to kisanki zan yi."
Ta ce, To. Ba zan fada ba.'"
Ta dauki tandu ta tafi wurin abokan tafiyarta jikinta rawa saboda tana jin tsoron Dan-Kashin-Gwiwa.
Sai ta ce, "Oho. Ba kome."
Sai s**a ce, "To ai sai ki ci gaba da sa mana waka. Kura ta ƙi."
S**a ce, "Ai ke ce kika fara, kuma ke za ki ci gaba da yi."
Sai kura ta ce, "To "
Sai ta fara sabuwar waka:
Mun rarrabo, mun rarrabo,
Da Ɗan-Ƙashin-Gwiwa,
Mai ɗan zanko, ɗan arziki.
Sai s**a ce, "A'a, ai da ba haka ki ke fada a cikin waƙar ba."
Da ta ga sun gane ta, sai ta yi wuf ta jefar da kuttun man ta ce, shi ne a cikI."
Sai kowa ya k**a gabansa.
S**a yi watsi da kayan, s**a ruga da gudu gaba daya.
Dan-Kashin-Gwiwa kuwa sai ya yi ta jidon kaya yana kai wa babarsa. Ya jide tsaf. S**a sami abin da za su daɗe suna ci.
Shi ke nan..
Kurunkus kan kusu. Ba don Gizo ba da na yi karya. Dama karyar na shirga.

Littafi: Ibrahim Yaro Yahaya, Tatsuniyoyi da wasanni na 4.

Kun gane wacce ƙofa ce wannan a Kano? Ko har yanzu akwai ta?
03/01/2026

Kun gane wacce ƙofa ce wannan a Kano? Ko har yanzu akwai ta?

Ali and the Angel 1. Kun tuna wannan!
02/01/2026

Ali and the Angel 1. Kun tuna wannan!

Ai kun tuna Mr. Giwa ko? Aji 3 na Firamare.
02/01/2026

Ai kun tuna Mr. Giwa ko? Aji 3 na Firamare.

The Green Buttons
1. Mr Giwa is a shopkeeper. He has a shop in Lawal's village.
His shop is full of things to sell. He sells knives, nails, buttons and books. He also sells cloth, tea, sugar, salt and soap.
One day Lawal's sister, Rabat, went to Mr Giwa's shop.
2. RABAT: Good evening, Mr Giwa. Mother wants some green buttons for my new school uniform. Have you got any, please!
MR GIWA: Yes, there are some in that box. How many does she want?
RABAT: She wants twelve, please.
MR GIWA: Here they are.

3.RABAT: My mother also wants some tea, some salt and some soap.
MR GIWA: How much does she want?
RABAT: She told me to get a packet, of tea, half a kilo of salt
MR GIWA: Here's a packet of tea. Here's a piece of soap. And here's half a kilo of salt.
RABAT: Thank you very much. Mother says she'Il pay you tomorrow.
MR GIWA: That's all right, Rabat.

4. MR GIWA:Imet your father last night. He said he wanted some wood and some nails to make a chair. Please telI him I've
got a lot of new nails today and some good pieces of wood.
RABAT: Ill tell him when he comes home. Thank you very much, Mr Giwa. Goodbye.
MR GIWA: Goodbye, Rabat.

Do you remember primary 3 in 1970s to 1990s?

02/01/2026

I Dala'ilul Karatu I ❤️

02/01/2026

I Dala'ilul Karatu I

02/01/2026

I Karatun Diwani I

Address

F8 Zaria Road
Kano
700233

Opening Hours

Monday 09:00 - 17:00
Tuesday 09:00 - 17:00
Wednesday 09:00 - 17:00
Thursday 09:00 - 17:00
Friday 09:00 - 17:00
Saturday 09:00 - 17:00
Sunday 09:00 - 17:00

Website

https://www.tsohuwarajiya.com.ng/, https://www.tsohuwarajiya.ng/

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Tsohuwar Ajiya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Tsohuwar Ajiya:

Share

Category