Tsohuwar Ajiya

Tsohuwar Ajiya Domin nishaɗantar daku da tsofaffin bidiyo, labarai, da abubuwan da s**a faru a baya. Ku kasance tare damu a koda yaushe domin jin daɗinku.
(5)

We share old and new videos, precisely historical ones, where we see how things were before for entertainment, history, and your enjoyment.

"Dalilan da yasa ake ganin makiyaya a cikin birnin Abuja suna gararanba shi ne: kafin a kirkiri Abuja, a wancan lokaci k...
10/06/2026

"Dalilan da yasa ake ganin makiyaya a cikin birnin Abuja suna gararanba shi ne: kafin a kirkiri Abuja, a wancan lokaci kusan dazukan anan da dama wuraren kiyon dabbobi ne. To, bayan da aka kirkiri Abuja, an tanadi wurare da aka tsara jama'a za su zauna, tare da wuraren ofisoshi da wuraren gina kasuwanni da sauran wuraren more rayuwa, amma aka manta a keɓe tare da inganta inda dabbobi za su yi kiwo.

Akwai gandun daji guda huɗu da faɗin su ya kai hekta 33 a Abuja da aka ware tun da, sannan tun da aka ware waɗannan gandun dajin a wancan lokacin da aka kirkiri Abuja, ba a taɓa yin wani abu na inganta wurin ta yadda za a maida makiyaya wurin ba.

Tun bayan kafa ma’aikatar kula da bunƙasa kiyon dabbobi kusan shekara biyu da s**a wuce, ma’aikatar ta kulla alaƙa tare da Hukumar Gudanar da Babban Birnin Tarayya ta yadda za a inganta waɗannan wurare da ke yankunan ƙauyen Kau, Karshi da sauran wurare da ke Abuja.

Muna aiki tare da masu ruwa da tsaki wajen inganta waɗannan gandun dajin, sannan a duba yiwuwar maida makiyaya wurin sannu a hankali."

— Idi Muktar Maiha, Ministan Bunƙasa Kiyon Dabbobi, ya bayyana hakan ne a yayin taron manema labarai na Ranar Dimokuraɗiyya ta 2026 da aka gudanar a ranar Talata, 9 ga Yuni, 2026.

10/06/2026
TUNA BAYA.First Lady. Makarantace akai domin bawa matar Gwamna aikin yi mai makon shiga Gwammanti. Eng. Governor Rabiu M...
10/06/2026

TUNA BAYA.

First Lady. Makarantace akai domin bawa matar Gwamna aikin yi mai makon shiga Gwammanti. Eng. Governor Rabiu Musa Kwankwaso ne ya kirkiro wannan makarantar wacce yanzu take kofar Nassarawa ake alfahari da ita.

Abdulwahab Said Ahmad

Marigayi Sarkin Kano Ado Bayero da gwamnan jihar Kano Rabiu Kwankwaso, sun hallara kafin jana'izar mutanen da hadarin ji...
10/06/2026

Marigayi Sarkin Kano Ado Bayero da gwamnan jihar Kano Rabiu Kwankwaso, sun hallara kafin jana'izar mutanen da hadarin jirgin saman unguwar Gwammaja ya shafa a 6 ga watan Mayu, 2002, in da ya kashe mutane 149.

Ƴar wasan Hausa Meerah Shuaib
10/06/2026

Ƴar wasan Hausa Meerah Shuaib

Wacce ta fi iya gulma tsakanin Shukra da Bilkisu?Wanda ba su kalli Garwashi S5, E11 za su iya kalla yanzu haka a youtube...
10/06/2026

Wacce ta fi iya gulma tsakanin Shukra da Bilkisu?

Wanda ba su kalli Garwashi S5, E11 za su iya kalla yanzu haka a youtube channel din mu mai suna Fauziyya D. Sulaiman

Wannan Itace Marigayiya Hajiya Mai Riga Aliyu ta kasance cikin fitattun muryoyin da s**a yi tasiri sosai a gidan Rediyo ...
10/06/2026

Wannan Itace Marigayiya Hajiya Mai Riga Aliyu ta kasance cikin fitattun muryoyin da s**a yi tasiri sosai a gidan Rediyo Tarayya Kaduna a shekarun baya.

Murya da salonta wajen gabatar da shirye-shirye sun sa mutane da dama suke sauraro da sha’awa musamman a lokacin shirye-shiryen wasan kwaikwayo da karanta “Zabi Sonka”.

Mutane da yawa suna tuna da ita ta hanyar shirye-shirye irin su:

“Duniya Budurwar Wawa”

" Shafa Labari Shuni "

“Shehu Umar”

“Magana Jari Ce”

Shirye-shiryen karanta “Zabi Sonka”

Da Wasu shirye-shiryen nishadi da fadakarwa da ake gabatarwa a Rediyon Kaduna a lokacin.

Hakika tsofaffin ma’aikatan gidan rediyo sun taka rawa wajen ilmantarwa da nishadantar da al’umma musamman kafin zuwan kafafen sada zumunta na yanzu.

Dawanne acikin shirye shiryenta zaku iya tinawa da'ita a shekarun baya ?

Allah ya jikanta da rahama amin' Allah ya albarkaci zuri'arta amin

Allah yajikan wadanda s**a rasu daga cikin ma’aikatan gidan rediyo da rahama da gafara, ya kara lafiya da nisan kwana ga masu rai. Amin.

✍️ Yau Ibrahim Dankama

09 Yuni 2026

10/06/2026

Sha'iri Malam Auwal Iguda

1993

An Bayyana Babban Sauyin da aka samu a Abuja, Inda aka Sanar da Kammala Ayyuka Wanda  Za'a  Fara Kaddamarwa Daga Sati Ma...
10/06/2026

An Bayyana Babban Sauyin da aka samu a Abuja, Inda aka Sanar da Kammala Ayyuka Wanda Za'a Fara Kaddamarwa Daga Sati Mai Zuwa Don Bikin Cika Shekaru 3 da Tinubu Yayi Akan Mulki

Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya bayyana cewa manyan ayyukan gine-gine da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta aiwatar a Abuja sun kammala kuma sun shirya domin kaddamarwa, yayin da ake shirin bikin cika shekaru uku na mulkinsa.

Wike ya bayyana hakan ne yayin duba wasu muhimman ayyuka a Abuja, inda ya ce gwamnatin Tinubu ta nuna ƙudirin gaske wajen sauya fasalin babban birnin ƙasa ta hanyar inganta hanyoyi, gadoji da sauran ababen more rayuwa.

A cewarsa, dukkanin ayyukan da aka duba sun kai matakin kammalawa da ya kai kashi 100 cikin 100, yana mai cewa hakan hujja ce ta cewa an kawo ci gaba mai ma’ana ga al’umma.

Daga cikin ayyukan da aka duba akwai gadar Jahi–Gwarimpa, hanyar filin jirgin sama zuwa Kuje, hanyar Kuje zuwa Gwagwalada, titunan Outer Southern Expressway, da kuma gyaran ƙofar shiga birnin Abuja (Abuja City Gate).

Wike ya bayyana jin daɗinsa kan ingancin aikin da kamfanonin kwangila s**a yi, inda ya ce ayyukan za su inganta zirga-zirga tare da rage cunkoso da wahalar tafiya a birnin Abuja da kewayenta.

Ya ce musamman hanyoyin Airport zuwa Kuje da Kuje zuwa Gwagwalada sun rage tsawon lokacin tafiya tsakanin birni da yankunan da ke kewayen Abuja, abin da ya ce ya inganta rayuwar mazauna sosai.

Ministan ya kuma yaba da gyaran da aka yi wa Abuja City Gate, yana mai cewa hakan zai ƙara wa birnin Abuja martaba a idon duniya a matsayin babban birni na zamani.

Ya ƙara da cewa ana shirin fara kaddamar da ayyukan a mako mai zuwa, inda ya ce shugabannin gwamnati daban-daban za su wakilci Shugaba Tinubu wajen buɗe wasu daga cikin ayyukan.

Wike ya kuma yi kira ga kafafen yaɗa labarai da su taimaka wajen bayyana irin ci gaban da ake samu a FCT, yana mai cewa abin da ake yi a Abuja yana nuna yadda gwamnati ke kawo sauyi ga rayuwar al’umma.

A cewarsa, an kuma shirya fara wasu sabbin ayyukan hanyoyi a nan gaba domin ci gaba da bunƙasa ababen more rayuwa a babban birnin tarayya.

Address

F8 Zaria Road
Kano
700233

Opening Hours

Monday 09:00 - 17:00
Tuesday 09:00 - 17:00
Wednesday 09:00 - 17:00
Thursday 09:00 - 17:00
Friday 09:00 - 17:00
Saturday 09:00 - 17:00
Sunday 09:00 - 17:00

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Tsohuwar Ajiya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Tsohuwar Ajiya:

Share

Category