Tsohuwar Ajiya

  • Home
  • Tsohuwar Ajiya

Tsohuwar Ajiya Domin nishaɗantar daku da tsofaffin bidiyo, labarai, da abubuwan da s**a faru a baya. Ku kasance tare damu a koda yaushe domin jin daɗinku.
(7)

We share old and new videos, precisely historical ones, where we see how things were before for entertainment, history, and your enjoyment.

19/07/2025

Hi everyone! 🌟 You can support me by sending Stars - they help me earn money to keep making content you love.

Whenever you see the Stars icon, you can send me Stars!

Allah swt ya jiƙan Bature Gagare. Domin karanta wanene shi, maza ku garzaya shafin Farfesa Abdalla Uba Adamu da Ibrahim ...
19/07/2025

Allah swt ya jiƙan Bature Gagare. Domin karanta wanene shi, maza ku garzaya shafin Farfesa Abdalla Uba Adamu da Ibrahim Sheme don samun ilmi.

Bankin Arewa. Ka taɓa buɗe akawun a ciki ko kuwa?
18/07/2025

Bankin Arewa. Ka taɓa buɗe akawun a ciki ko kuwa?

Wato a 1955, har ranar Isra'i, Nisfi Sha'aban, da Lailatul Ƙadri ake yi. Ai kun san lokacin ko?
18/07/2025

Wato a 1955, har ranar Isra'i, Nisfi Sha'aban, da Lailatul Ƙadri ake yi. Ai kun san lokacin ko?

17/07/2025

Majalisin Yabon Annabi tare Malam Jamilu Ƙofar Waika a Tudun Maliki Kano.

Buɗe Masallacin Gidan Ƙadiriyya, 1974 Kwanan baya ne aka yi shagalin bude Masallacin Ƙadiriyya da aka gina a Unguwar Kab...
16/07/2025

Buɗe Masallacin Gidan Ƙadiriyya, 1974 Kwanan baya ne aka yi shagalin bude Masallacin Ƙadiriyya da aka gina a Unguwar Kabara, cikin Bìrnin Kano wanda ke hade da Makarantar Islamiyya da Laburare wadanda dukansu aka kashe jimlar kudi sama da Naira 60,000 wajen kammalawa.

A cikin jawabinsa ga taron dubban Musulmi da s**a hallara wajen, kafin ya yanke kirtanin tabbatar da budewar, Sarkin Kano Alhaji Ado Bayero, ya yi kira ga dukan ƙungiyoyin Musulmi na Kasan nan tare kuma da dukan Musulmin da suke da hali dasu riƙa giggina Masallatai da Makarantun Islamiyya yadda za su ba da tasu gudunmawar a cikin tsanaki wajen ginin Musulunci. Alhaji Ado Bayero, kuma ya tabbatar, cewa ta irin wadannan kyawawan ayyuka ne Musulmi na kwarai zai gina addìninsa, daga baya ya ci moriyar abin a duniya da lahira.

A nasa jawabin, Kwamishinan Watsa Labarai da Al'adun gargajiya na Jihar Kano, Alhaji Yusufu Mitama Sule, Danmasanin Kano, ya ba da tarihin gidan Ƙadiriyya na Kano ne, inda aka yi Masallacin a Kabara da kuma irin ƙwazon zuriyar gidan wajen ganin gidan tare da đarikar sun rayu.

Daga nan ne kuma sai ya gode wa kwamitin ginin saboda kokarin đa s**a yi, sa'an nan kuma ya gode wa dukan wađanda s**a taimaka da kuđi ko da gaba wajen ginin Masallacin tare da Makarantar don amfanin dukan Musulmi.

A cikin nasa jawabin, Shugaban Kwamitin ginin Masallacin, kuma Shugaban Ɗarikar Ƙadiriyya a Nijeriya da Yammacin Afirka, Alhaji Muhammadu Nasiru Kabara, Sarkin Yakin Shehu Usman Dan Fodiyo ya bayyana asalin kafuwar dukan wadanda s**a jaddada Musulunci a Nijeriya tun
shekaru aru-aru da s**a wuce sun jaddada tare da Kadiriyya ne.

Alhaji Muhammadu Nasiru Kabara ya bayyana sunayen Waliyyan farko da s**a gabata, k**ar su Wali Danmarina, da Wali Dan Masani, har zuwa kan Shehu Usman Dan Fodiyo wadanda dukansu babu irin gwagwarmayar da ba su sha ba wajen tabbatad da Darikar Kadiriyya a zamanin rayuwarsu.

Ya kuma ce Darikar Kadiriyya kashi biyu ce da wadda ake yi a boye, ba a bayyane ba, da kuma wadda ake bayaynawa a cikin jama'a wadda Nijeriya ke bi da sauran kasashen da ke makwabtaka da ita.
Alhaji Muhammadu Nasiru Kabara kuma ya yi kira ga dukan Musulmi da su tashi haikan wajen fuskantar kowace irin takala da ta taso wa addinsu. Tun da farko kuwa, kafin a kai ga fara jawaban, Sheik Abdul Basidi Abdulsamadu, Shugaban makarantan Alkur'ani a Jumhuriyar Masar, wanda ya zo Nijeriya mussamman don bikin bude Masallacin bisa gayyata, sai da ya karanta wadansu Surori daga cikin Alkur'ani Mai Girma.

Sakataren Kungiyar Jama'at Nasril Islam, Alhaji Tbrahim Dasuki, Baraden Sakkwato, ya halarci wurin, inda ya bayad da gudunmawar Naira 1,000 a madadin Jama'atul Nasril Islam. Alhaji Muhammadu Nasiru Kabara ya bayar da gudunmawar littattafai guda 20,000 ga sabon Laburaren, da aka bude a gefen Masallacin.

Muhimman Mutane daga Kasashen makwabta da kuma gida Nijeriya sun halarci shagalin bude Masallacin wanda ya ƙayatar ainun.
Gaskiya Ta Fi Kwabo, 16 Satumba, 1974

Sponsored SAƘON TAYA MURNAIna miƙa sakon taya murna na musamman ga Shugaban Hukumar Kula da Nagartar Ayyuka ta Kasa (NPC...
16/07/2025

Sponsored

SAƘON TAYA MURNA

Ina miƙa sakon taya murna na musamman ga Shugaban Hukumar Kula da Nagartar Ayyuka ta Kasa (NPC) Hon Dr. Baffa Babba Danagundi bisa cika shekara ɗaya a wannan matsayi mai muhimmanci.

Shekara ɗaya kenan da Allah ya h**e maka jagorancin wannan hukuma, wanda cikin ɗan ƙanƙanin lokaci aka fara ganin sauyi da gyara a tsarin gudanarwa, da kuma jajircewa wajen tabbatar da gaskiya da adalci a wannan hukuma.

Muna fatan Allah ya ƙara maka basira, lafiya da kwarin gwiwa wajen ci gaba da jagorantar wannan hukuma cikin ƙwarewa da amana.

Allah ya sanya wannan shekara daya ta kasance tubalin nasarori da alfanu masu dorewa, ya kuma kara maka nisan kwana cikin cigaba da hidimar kasa. Muna alfahari da kai.

Abdul Saye Ungogo
S.A Social Media To DG NPC
Laraba 16/07/2025

Muhammadu Buhari a lokutan baya. Leadership News 14-07-2025.
14/07/2025

Muhammadu Buhari a lokutan baya.
Leadership News 14-07-2025.

Allah yasa can tafi nan, Amin.
13/07/2025

Allah yasa can tafi nan, Amin.

Sponsored KWAMANDAN ISWAP IBN ALI YA MIKA WUYA BAYAN DA SOJOJIN NAJERIYA S**A HALLAKA YAN TA’ADDA DA DAMA A BORNOSojojin...
13/07/2025

Sponsored

KWAMANDAN ISWAP IBN ALI YA MIKA WUYA BAYAN DA SOJOJIN NAJERIYA S**A HALLAKA YAN TA’ADDA DA DAMA A BORNO

Sojojin Najeriya sun sake samun nasara a fagen yaki da ta’addanci, yayin da babban kwamandan ‘yan ta’addan ISWAP, Ibn Ali, ya mika wuya tare da ajiye dukkan mak**ai da alburusai dake hannunsa. Wannan nasarar ta faru ne a Bama, Jihar Borno, yayin da dakarun Operation Hadin Kai ke ci gaba da matsa wa ‘yan ta’adda lamba a yankin Arewa maso Gabas.

A cewar kakakin rundunar tsaro ta kasa, Manjo Janar Markus Kangye, dakarun sun gudanar da jerin hare-hare daga ranar 4 zuwa 10 ga watan Yuli, a wurare da dama k**ar su Platari, Dajin Sambisa, da Timbuktu Triangle, inda s**a hallaka daruruwan ‘yan ta’adda. A cikin wannan lokaci, mata da maza da yara daga cikin ’yan ta’addan da s**a karaya sun mika wuya ga dakarun Najeriya, suna neman gafara da aminci.

Bayan haka, an samu nasarar ceto mutane hudu da aka sace, da k**a wasu masu taimaka wa ‘yan ta’adda guda biyar. Haka kuma, an kwato mak**ai da alburusai masu yawa, tare da tarwatsa wasu bama-bamai da kuma kwato kuɗaɗe daga hannun ‘yan ta’addan.

Wannan lamari na nuni da yadda hadin gwiwar dakarun Najeriya da sauran hukumomin tsaro ke haifar da gagarumar nasara a yankunan da ake fama da rikici.

Bayan ya faɗi zaɓen Gwamna a 1983, Muhammadu Abubakar Rimi yace ba zai je kotu ba, saboda ɓata lokacin, kuma Gwamnatin N...
12/07/2025

Bayan ya faɗi zaɓen Gwamna a 1983, Muhammadu Abubakar Rimi yace ba zai je kotu ba, saboda ɓata lokacin, kuma Gwamnatin NPN ta azzalumai ba zasu yi masa adalci ba!
Bayan yabar jamiyyar PRP ya koma NPP ne, wacce anan yai takara. Ya samu kuri'a #511, 811, yayin da ɗan takarar PRP Sabo Bakin Zuwo ya samu #715, 523.
Daily Times, Agusta 22, 1983

Address


Opening Hours

Monday 09:00 - 17:00
Tuesday 09:00 - 17:00
Wednesday 09:00 - 17:00
Thursday 09:00 - 17:00
Friday 09:00 - 17:00
Saturday 09:00 - 17:00
Sunday 09:00 - 17:00

Website

https://www.tsohuwarajiya.com.ng/, https://www.tsohuwarajiya.ng/

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Tsohuwar Ajiya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Tsohuwar Ajiya:

Shortcuts

  • Address
  • Opening Hours
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share