Tsohuwar Ajiya

Tsohuwar Ajiya Domin nishaɗantar daku da tsofaffin bidiyo, labarai, da abubuwan da s**a faru a baya. Ku kasance tare damu a koda yaushe domin jin daɗinku.

We share old and new videos, precisely historical ones, where we see how things were before for entertainment, history, and your enjoyment.

Ai ka taɓa amfani da wannan ka wanke kayan ka ko?
16/11/2025

Ai ka taɓa amfani da wannan ka wanke kayan ka ko?

Multilinks kenan a shekarar 1996 lokacin sai 'salula'. Ai kana da irinta lokacin ko?
15/11/2025

Multilinks kenan a shekarar 1996 lokacin sai 'salula'. Ai kana da irinta lokacin ko?

12/11/2025

I Waye??? I Marwan 2 I

Gwamnatin Tarayya ta rage kuɗin aikin Hajjin bana na shekarar 2026. Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON) ta sanar da rage ku...
10/11/2025

Gwamnatin Tarayya ta rage kuɗin aikin Hajjin bana na shekarar 2026.

Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON) ta sanar da rage kuɗin aikin Hajji na shekarar 2026 ga mahajjata daga sassa daban-daban na ƙasar, inda aka samu sauƙin kuɗi idan aka kwatanta da na bara.

A cikin sanarwar da hukumar ta fitar, an bayyana cewa mahajjata daga yankin Borno da Adamawa za su biya Naira miliyan 7,579,020.96, maimakon Naira miliyan 8,327,125.59 da s**a biya a 2025, ragun da ya kai Naira 748,104.63.

Haka kuma, masu niyyar tafiya daga yankin Arewa za su biya Naira miliyan 7,696,769.76, wanda ke nuna ragin Naira 760,915.83 daga kuɗin bara da ya kai Naira miliyan 8,457,685.59.

A ɓangaren masu tafiya daga Kudancin ƙasar kuwa, farashin da aka sabunta na 2026 shi ne Naira miliyan 7,991,141.76, raguwar Naira 792,943.83 daga kuɗin 2025 da ya kai Naira miliyan 8,784,085.59.

Hukumar ta ce wannan ragin kuɗi na zuwa ne sakamakon ƙoƙarin da gwamnati da hukumomin da abin ya shafa suke yi domin sauƙaƙa wa alhazai, tare da tabbatar da cewa farashin bai zama cikas ga masu niyyar gudanar da ibadar Hajji ba.

NAHCON ta kuma tabbatar da cewa za ta ci gaba da aiki tare da hukumomin Saudiyya da sauran masu ruwa da tsaki domin tabbatar da shirin Hajji na 2026 ya gudana cikin nasara da tsari.

Sponsored..Comrade Labbasi Ya Zama Garkuwa Ga Marayu 20!”An karrama Comr. Labbasi Abdullahi Ja'oji daga Makarantar Usman...
10/11/2025

Sponsored..

Comrade Labbasi Ya Zama Garkuwa Ga Marayu 20!”

An karrama Comr. Labbasi Abdullahi Ja'oji daga Makarantar Usmaniyya Littahfizil Qur’an, Sheka Sabuwar Abuja, bisa daukar nauyin marayu 20 har zuwa kammala karatun Al-Qur’ani.

An gudanar da bikin a African Anchor Event Hall, Shoprite Kano, inda aka bayyana su a matsayin ginshikai wajen ci gaban ilimi da kula da marayu.

Idan aka gyara tsarin mulki aka ƙara Jihohi, a ina zaka samu kanka? Hoto: Newswatch Afrilu 8, 1996.
09/11/2025

Idan aka gyara tsarin mulki aka ƙara Jihohi, a ina zaka samu kanka?
Hoto: Newswatch Afrilu 8, 1996.

09/11/2025

KARRAMAWA TA MUSAMMAN!

An karrama Comr. Labbasi Abdullahi Ja'oji daga Makarantar Usmaniyya Littahfizil Qur’an, Sheka Sabuwar Abuja, a girmamawa bisa gudummawar da ya bayar wajen daukar nauyin marayu 20 har zuwa kammala karatun su na Al-Qur’ani.

Wannan gagarumin yabo ya gudana a dakin taro na African Anchor Event Hall, Shoprite Kano, inda aka bayyana Comr. Labbasi a matsayin ginshikin ci gaban makaranta da kula da marayu.

05/11/2025

🎥 Yaudarar Shugaban Kasar Amurka Donald Trump wajen amfani da Najeriya don ceto makomar siyasar sa a Amurka.

Ofishin Mai Baiwa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Tsaron Ƙasa (NSA) tare da shugabannin hukumomin tsaro za su yi jawabi ga man...
03/11/2025

Ofishin Mai Baiwa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Tsaron Ƙasa (NSA) tare da shugabannin hukumomin tsaro za su yi jawabi ga manema labarai a yammacin wannan rana ta Litinin, kamar yadda jaridar The Nation ta rawaito

Wannan taron manema labaran na zuwa ne a matsayin martani ga barazanar da Shugaban Ƙasar Amurka Donald Trump ya yi, cewa zai tura sojoji domin su fuskanci ’yan ta’adda a Najeriya.

Daraktan Janar na Hukumar Wayar da Kai ta Ƙasa (NOA), Mallam Lanre Issa-Onilu, ne ya bayyana haka a yayin taron manema labarai na wata-wata na haɗin gwiwar hukumomin tsaro na ƙasa, wanda ake gudanarwa domin sabunta bayanai ga kafafen yada labarai kan matakan da gwamnati ke ɗauka wajen magance matsalar tsaro da sauran munanan dabi’u.

01/11/2025

Address

F8 Zaria Road
Kano
700233

Opening Hours

Monday 09:00 - 17:00
Tuesday 09:00 - 17:00
Wednesday 09:00 - 17:00
Thursday 09:00 - 17:00
Friday 09:00 - 17:00
Saturday 09:00 - 17:00
Sunday 09:00 - 17:00

Website

https://www.tsohuwarajiya.com.ng/, https://www.tsohuwarajiya.ng/

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Tsohuwar Ajiya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Tsohuwar Ajiya:

Share

Category