15/09/2026
GAYYATA ZUWA TARON ZIKIRIN JUMA’A A GAYA
Mai Martaba Sarkin Gaya, Alh. (Dr.) Aliyu Ibrahim Abdulkadir CNA, CPA, NIM (Kirimau Mai Gabas), na gayyatar al’umma zuwa babban Taron Zikirin Juma’a da za a gudanar a ranar 18 ga Satumba, 2026.
Taron zai ƙunshi Saukokin Al-Qur’ani Mai Girma, Dala’ilul Khairat, Wazifa tare da Zikiri da kuma addu’o’i, domin neman zaman lafiya, kwanciyar hankali, arziki da wadatar rayuwa.
Taron zai gudana ne ƙarƙashin jagorancin Malam Munzir Sheikh Dr. Yusuf Ali (Sarkin Malaman Gaya).
BABBAN BAƘO NA MUSAMMAN:
Mai Girma Gwamnan Jihar Kano,
Engr. Abba Kabir Yusuf.
URBAN TARO:
Mai Martaba Sarkin Gaya, Alh. (Dr.) Aliyu Ibrahim Abdulkadir CNA, CPA, NIM.
BABBAN BAƘO:
Mai Martaba Sarkin Dutse, Muhammad Hamim Sunusi.
BABBAN BAƘO MAI JAWABI:
Kwamishinan Addini na Jihar Kano, Hon. Ahmad Sani Auwal.
MASU MASAUKIN BAKI:
Shugabannin Kananan Hukumomin Gaya, Ajingi da Albasu.
MANYAN BAKI:
Hakiman Mai Martaba Sarkin Gaya
Rana: Juma'a 18/09/2026
Lokaci: 1:00 na rana zuwa 6:30 na yamma.
Jawabai daga malamai: Bayan Sallar Magriba zuwa Isha’i.