Tsohuwar Ajiya

Tsohuwar Ajiya Domin nishaɗantar daku da tsofaffin bidiyo, labarai, da abubuwan da s**a faru a baya. Ku kasance tare damu a koda yaushe domin jin daɗinku.

We share old and new videos, precisely historical ones, where we see how things were before for entertainment, history, and your enjoyment.

GAYYATA ZUWA TARON ZIKIRIN JUMA’A A GAYAMai Martaba Sarkin Gaya, Alh. (Dr.) Aliyu Ibrahim Abdulkadir CNA, CPA, NIM (Kiri...
15/09/2026

GAYYATA ZUWA TARON ZIKIRIN JUMA’A A GAYA

Mai Martaba Sarkin Gaya, Alh. (Dr.) Aliyu Ibrahim Abdulkadir CNA, CPA, NIM (Kirimau Mai Gabas), na gayyatar al’umma zuwa babban Taron Zikirin Juma’a da za a gudanar a ranar 18 ga Satumba, 2026.

Taron zai ƙunshi Saukoki­n Al-Qur’ani Mai Girma, Dala’ilul Khairat, Wazifa tare da Zikiri da kuma addu’o’i, domin neman zaman lafiya, kwanciyar hankali, arziki da wadatar rayuwa.

Taron zai gudana ne ƙarƙashin jagorancin Malam Munzir Sheikh Dr. Yusuf Ali (Sarkin Malaman Gaya).

BABBAN BAƘO NA MUSAMMAN:
Mai Girma Gwamnan Jihar Kano,
Engr. Abba Kabir Yusuf.

URBAN TARO:
Mai Martaba Sarkin Gaya, Alh. (Dr.) Aliyu Ibrahim Abdulkadir CNA, CPA, NIM.
BABBAN BAƘO:

Mai Martaba Sarkin Dutse, Muhammad Hamim Sunusi.
BABBAN BAƘO MAI JAWABI:
Kwamishinan Addini na Jihar Kano, Hon. Ahmad Sani Auwal.

MASU MASAUKIN BAKI:
Shugabannin Kananan Hukumomin Gaya, Ajingi da Albasu.

MANYAN BAKI:
Hakiman Mai Martaba Sarkin Gaya

Rana: Juma'a 18/09/2026
Lokaci: 1:00 na rana zuwa 6:30 na yamma.
Jawabai daga malamai: Bayan Sallar Magriba zuwa Isha’i.

15/09/2026

Budurwa Ta Yiwa Ibro Tayin Auran Babarta

15/09/2026

Isowar Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, a wurin babban taron masu ruwa da tsaki kan cigaban yankin arewa ta tsakiya, wanda Hukumar Raya Yankin Arewa ta Tsakiya (NCDC) ta shirya, a yau Litinin a Abuja.

15/09/2026

Mu Shakata Da Marigayi Rabilu Musa Dan Ibro
🤣🤣🤣🤣
Kaje Abujan Ma Jiya E Yau!
Rigar Dai Ta Tayi Ko? To An Same Ki.

Najeriya Da Indiya Sun Sake Farfaɗo Da Alaƙar Cinikayyar Danyen Man Fetur Na Dalar Amurka Biliyan 15Najeriya da Indiya s...
15/09/2026

Najeriya Da Indiya Sun Sake Farfaɗo Da Alaƙar Cinikayyar Danyen Man Fetur Na Dalar Amurka Biliyan 15

Najeriya da Indiya sun amince da ƙarfafa dangantakar tattalin arzikinsu, yayin da Indiya ta nuna sha’awar sake ƙara sayen ɗanyen man fetur daga Najeriya.

An cimma matsayar ne a wata ganawar ƙasashen biyu tsakanin Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, da Firaministan Indiya, Narendra Modi, a gefen taron shugabannin ƙasashen BRICS da aka kammala a New Delhi.

Cinikin Najeriya da Indiya ya kai dala biliyan 14.95 a shekarar kuɗi ta 2021 zuwa 2022, kafin ya ragu sakamakon raguwar sayen ɗanyen man Najeriya da Indiya ke yi. Cinikin ya sauka zuwa dala biliyan 7.13 a 2024 zuwa 2025, kafin ya farfaɗo zuwa kusan dala biliyan 9 a 2025 zuwa 2026.

Shettima ya ce Najeriya za ta duba buƙatar Indiya ta sake ƙara sayen ɗanyen man fetur, a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na jawo ƙarin zuba jari da ƙulla dangantakar tattalin arziki da za ta taimaka wajen faɗaɗa ƙarfin samar da kayayyaki a ƙasar.

Ƙasashen biyu sun kuma tattauna faɗaɗa haɗin gwiwa a fannonin makamashi mai tsafta, wutar lantarki, kiwon lafiya, bunƙasa ƙwarewar ma’aikata, fasahar hada-hadar kuɗi da sauran sabbin fannoni. Firaminista Modi ya kuma nuna godiya ga Najeriya bisa kyakkyawar tarbar da take bai wa ɗimbin ’yan ƙasar Indiya da ke zaune da gudanar da harkokin kasuwanci a Najeriya.

14/09/2026
14/09/2026

🎥 Yadda aikin sashin da aka kammala na babbar hanyar Abuja–Kaduna, mai tsawon kusan kilomita 118 yake a yau 13 ga Satumba, 2026, bayan gudanar da aikin gyara da sake gina hanyar.

Aikin na daga cikin manyan ayyukan samar da ingantattun hanyoyin sufuri a Najeriya da Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke yi, wanda zai taimaka wajen sauƙaƙa zirga-zirga da rage wahalhalun matafiya tsakanin Abuja da Kaduna.


KANO VENDORS VIBES 10 IS COMING! Kana da sana’a? Kana da kaya da kake son tallatawa? Ko kana neman sabbin kwastomomi?Wan...
13/09/2026

KANO VENDORS VIBES 10 IS COMING!

Kana da sana’a? Kana da kaya da kake son tallatawa? Ko kana neman sabbin kwastomomi?

Wannan damar taka ce!

KANO VENDORS VIBES 10 – TRADE FAIR na zuwa da babbar dama ga ‘yan kasuwa da masu sana’o’i domin baje kolin sana’o’insu, tallata kayayyaki, samun sababbin kwastomomi da haɗuwa da sauran ‘yan kasuwa.

📅 1st & 2nd OCTOBER

💰 STALL FEE: ₦30,000

🍔 FOOD
🥤 DRINKS
🛍️ PRODUCTS
🎮 GAMES

Kada ka bari a baka labari. Ka yi rijista yanzu domin ka samu gurinka a wannan gagarumin taro.

📞 SPONSOR/ENQUIRIES:
07033023352

📧 [email protected]

👉 REGISTER NOW!





13/09/2026

Marigayi Sarkin kano Alh Ado Bayero

Tun bayan hawansa mulki a ranar 29 ga Mayu 2023, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya fuskanci basuss**a da nauyin da aka gada d...
13/09/2026

Tun bayan hawansa mulki a ranar 29 ga Mayu 2023, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya fuskanci basuss**a da nauyin da aka gada daga baya, tare da ɗaukar matakai domin warware su.

Daga basuss**an kuɗin musayar waje, kuɗaɗen kamfanonin jiragen sama da s**a makale, bashin IMF, zuwa hakkokin ’yan fansho da ’yan kwangila, gwamnatin Shugaba Tinubu ta ɗauki matakai da dama wajen biyan waɗannan basuss**a da hakkoki.

Ga jadawalin wadannan basuss**a da Gwamnatin ta biya dan ɗaukewa Najeriya nauyin su, ana kuma cigaba da biyan wasu.

Address

F8 Zaria Road
Kano
700233

Opening Hours

Monday 09:00 - 17:00
Tuesday 09:00 - 17:00
Wednesday 09:00 - 17:00
Thursday 09:00 - 17:00
Friday 09:00 - 17:00
Saturday 09:00 - 17:00
Sunday 09:00 - 17:00

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Tsohuwar Ajiya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Tsohuwar Ajiya:

Shortcuts

Share

Category