BECHI TV

BECHI TV online media platform

Gwamnatin Najeriya ta yi gargaɗin cewa za a samu mamakon ruwan sama a jihohi 30 da babban birnin tarayya A buja, wanda a...
11/04/2025

Gwamnatin Najeriya ta yi gargaɗin cewa za a samu mamakon ruwan sama a jihohi 30 da babban birnin tarayya A buja, wanda ambaliya za ta iya biyo bayansa.

Jihohin da za su fi fuskantar barazana su ne: Abia da Adamawa da Akwa Ibom da Anambra da Bauchi da Bayelsa da Benue da Borno da Kuros Riba da Delta da Ebonyi da Edo da Gombe da Imo da Jigawa da Kebbi da Kogi da Kwara da Legas da Nasarawa da Neja da Ogun da Ondo da Osun da Oyo da Rivers da Sokoto da Taraba da Yobe da Zamfara da Abuja, k**ar yadda tashar Channels ta ruwaito.

Ministan albarkatun ruwa da tsaftace muhalli, Joseph Utsev ya bayyana a ranar Alhamis cewa za a fara ne da fuskantar mamakon ruwan sama a jihohin.
Ministan ya ce mamakon ruwan ne zai yi yawan gaske da zai jawo ambaliya a jihohin na Najeriya.

Ya bayyana cewa garuruwa 1,249 a ƙananan hukumomin 176 a jihohi 30 da babban birnin tarayya Abuja ne suke cikin barazanar.

Matatar man fetur ta Dangote ta sanar da rage farashin litar man fetur da take sayar wa ƴan kasuwa masu gidajen mai zuwa...
10/04/2025

Matatar man fetur ta Dangote ta sanar da rage farashin litar man fetur da take sayar wa ƴan kasuwa masu gidajen mai zuwa naira 865 daga naira 880.

Tashar Channels ce ta ruwaito hakan, inda ta ce wata majiya ce daga matatar ta tabbatar mata da rage farashin a ranar Alhamis.

Ragin farashin ya zo ne bayan wata tattaunawa da aka yi tsakanin matatar Dangote da ministan kuɗin Najeriya, Wale Edun a ranar Talata.

Bayan taron ne gwamnatin Najeriya ta ce yarjejeniyar sayar wa Dangote ɗanyen mai da naira na nan, kuma za a cigaba da amfani da ita bayan a baya kamfanin NNPCL ya sanar da kawo ƙarshen yarjejeniyar.

Da wannan matakin ne ake sa ran gidajen man fetur da suke da yarjejeniya da matatar Dangote irin su MRS da Ardova da Heyden da sauransu za su rage farashin litar man fetur ɗinsu.

Sufeto Janar na ‘Yansandan Kasa ya janye gayyatar Sarki Muhammadu Sunusi zuwa Abuja, ya umarci rundunar yan sanda ta Kan...
06/04/2025

Sufeto Janar na ‘Yansandan Kasa ya janye gayyatar Sarki Muhammadu Sunusi zuwa Abuja, ya umarci rundunar yan sanda ta Kano ta karbi bayanan sarki a rubuce kan abin da ya faru.

Babban sufeton 'yan sanda Kayode Egbetokun ya bada umarnin gayyatar Sarkin Kano Muhammadu Sunusi zuwa Abuja don gudanar ...
05/04/2025

Babban sufeton 'yan sanda Kayode Egbetokun ya bada umarnin gayyatar Sarkin Kano Muhammadu Sunusi zuwa Abuja don gudanar da bincike kan rikicin da aka samu a cikin tagawar Sarkin a ranar Sallah, lamarin da ya janyo rasuwar wani matashi.

Wasikar gayyatar wanda hannun Kwamishinan ‘yan sanda mai lura da ayyuka na musamman Olajide Rufus Ibitoye ya sanyawa hannu ta bukaci Sarkin ya bayyana a hedikwatar hukumar da ke Abuja a ranar Talata, 8 ga Afrilu, 2025, da karfe 10:00 na safe.

Rahotanni na nuni da cewa, fitaccen Malamin addinin musulunci a Nigeria, Sheikh Idris Abdulaziz Dutsen Tanshi, Allah ya ...
03/04/2025

Rahotanni na nuni da cewa, fitaccen Malamin addinin musulunci a Nigeria, Sheikh Idris Abdulaziz Dutsen Tanshi, Allah ya karbi rayuwar sa, a wannan daren.

Gwamnan jihar Edo, Monday Okpebholo ya kawo ziyarar jaje ga gwamnatin jihar Kano da iyalan mafarauta 16 da ɓatagari su k...
31/03/2025

Gwamnan jihar Edo, Monday Okpebholo ya kawo ziyarar jaje ga gwamnatin jihar Kano da iyalan mafarauta 16 da ɓatagari su ka kone su har lahira a garin Uromi na jihar.

Da ya ke jawabi a gidan gwamnati, Okpebholo ya nuna kaɗuwa bisa lamarin, inda ya tabbatar da cewa 14 eaga waɗanda su ka aikata kisan sun shiga hannu kuma za a tabbatar an yi wa iyalan wadanda aka kashe adalci.

Gwamna Yusuf ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta baiyana fuskoki da sunayen mutane da aka k**a kan kisan gillar, inda ya bukaci gwamnan Edo din da ya tabbatar an biya diyya ga iyalan mamatan.

Barka da Sallah, Allah ya sa wannan Eid ta zama mafi albarka a rayuwar mu, Allah ya sa muyi bikin Sallah cikin aminci, f...
30/03/2025

Barka da Sallah, Allah ya sa wannan Eid ta zama mafi albarka a rayuwar mu, Allah ya sa muyi bikin Sallah cikin aminci, farin ciki, da soyayya. Barka da Sallah!

Cikin hotuna: Yadda Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya gudanar da Sallar idi karama a birnin tarayya Abuja.📸 Facebook/Bo...
30/03/2025

Cikin hotuna: Yadda Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya gudanar da Sallar idi karama a birnin tarayya Abuja.

📸 Facebook/Bola Ahmed Tinubu

Rundunar Ƴan sandan Kano sun haramta yin Hawan Sallah a bikin Karamar Sallah.
28/03/2025

Rundunar Ƴan sandan Kano sun haramta yin Hawan Sallah a bikin Karamar Sallah.

Ana zargin cewa wasu jami’an Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi (NDLEA) sun kashe wani ɗalibin sakandire a Ung...
08/11/2024

Ana zargin cewa wasu jami’an Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi (NDLEA) sun kashe wani ɗalibin sakandire a Unguwar Dangi ta Ƙaramar Hukumar Kanam da ke Jihar Filato.

Mazauna unguwar sun bayyana cewa jami’an sun kashe matashin mai suna Faisal Yakubu Hussaini yayin wani samame da s**a kai yankin.

A cewar mazauna waɗanda s**a nemi bahasin ko an kai samame yankin ne saboda aikata wani laifi, jami’an sun gaza bayar da wani gamsasshen bayani.

Shugaba da kuma Sakataren Ƙungiyar Ci gaban Kanam, Barista G Abdullahi da ND Shehu Kanam, sun tabbatar da faruwar lamarin yayin da suke Allah wadai.

Shugabannin sun bayyana damuwa kan lamarin da s**a alaƙanta da ƙetare iyakar ’yancin matashin da abin ya shafa.

A yayin da suke tabbatar da cewa jami’an na NDLEA suna da damar aiwatar da ayyukansu bisa duk wani tanadi da doka ta yi, sun kuma yi tir da faruwar lamarin da cewa sai an bi wa matashin haƙƙinsa.

Cikin sanarwar da s**a fitar, sun buƙaci mahukunta da su gaggauta k**a jami’an da ake zargi da wannan aika-aikar domin su gurfana a gaban shari’a.

Kazalika, sun gargaɗi matasan yankin da su yayyafa wa zukata ruwan sanyi domin kiyaye doka da oda a yayin da s**a cewa ba za su yi ƙasa a gwiwa ba don ganin an shari’a ta ɗauki matakin da ya dace.

Manema labarai sun tuntubi mai magana da yawun rundunar NDLEA, Abba Muhammad Sani, inda ya ce zai gudanar da bincike gabanin mayar da martani kan lamarin.

Rundunar Sojin Nijeriya ta tabbatar da ɓullar wata sabuwar ƙungiyar ta’adda mai suna Lakurawa a jihohin Sakkwato da Kebb...
08/11/2024

Rundunar Sojin Nijeriya ta tabbatar da ɓullar wata sabuwar ƙungiyar ta’adda mai suna Lakurawa a jihohin Sakkwato da Kebbi, da ke zama babban ƙalubalen ga sha’anin tsaro a Arewa maso Yammacin ƙasar.

Rundunar ta kuma ayyana wasu ƙasurguman ’yan ta’adda guda tara da take nema ruwa a jallo, tana mai cewa za ta yi duk mai yiwuwa domin ganin ta yi maganin su cikin ƙanƙanin lokaci.

Daraktan Sadarwa na Hedikwatar Tsaro ta Najeriya, Manjo-Janar Edward Buba ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai an Abuja.

Jaridar Aminiya ta ruwaito cewa, a bayan nan ne Gwamnatin Sakkwato ta yi ƙorafin cewa wata sabuwar ƙungiyar ta’adda ta bulla a jihar.

Kazalika, mazauna ƙauyukan Jihar Borno sun soma bayyana fargabar kwararowar ’yan ta’adda a yayin da dakarun sojin ƙasar Chadi ke ci gaba da tsananta ayyukan kakkaɓe mayaƙan Boko Haram a gaɓar Tafkin Chadi.

Da yake bayani, Manjo-Janar Edward Buba, ya ce mayaƙan sabuwar ƙungiyar suna kwararowa ne jihohin Sakkwato da Kebbi daga wasu sassa na ƙasar Nijar da kuma Mali tun bayan juyin mulkin da sojoji s**a yi, lamarin da ya gurgunta alaƙar soji tsakanin ƙasashen.

Sai dai ya bayyana cewa, gabanin juyin mulkin da sojoji s**a yi, akwai kyakkyawar alaƙata tsananta tsaro tsakanin jami’an tsaro a iyakokin ƙasashen Najeriya da maƙwabciyarta Nijar.

Gwamnatin Najeriya ta sanar da cewa daga yanzu kyauta za a riƙa yi wa mata tiyatar haihuwa, wato Cesarean Sections (C.S)...
08/11/2024

Gwamnatin Najeriya ta sanar da cewa daga yanzu kyauta za a riƙa yi wa mata tiyatar haihuwa, wato Cesarean Sections (C.S) a duk faɗin ƙasar.

Ministan Lafiya, Farfesa Muhammad Pate ne ya sanar da hakan a yayin wani taron kwanaki biyu na bitar harkokin kiwon lafiya da aka gudanar an Abuja.

Pate ya ce wannan na ɗaya daga cikin matakan da Gwamnatin Tarayya ta ɗauka domin rage mace-macen mata da ake samu a lokacin haihuwa a faɗin ƙasar.

Haka kuma, Ministan ya ce wannan na ɗaya daga cikin manufofin Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu na ganin an bai wa mata kulawa ta musamman.

Ministan ya ƙara da cewa, bai dace ba a ce wata mace ta mutu a Najeriya saboda ba ta da halin biyan kuɗin tiyatar haihuwa.

Bayanai na cewa wannan matakin zai taimaka wajen magance wahalhalu, da kashe maƙudan kuɗaɗen da ake fama da su yayin da sauran ababen buƙatar yi wa mace tiyatar ta haihuwa.

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when BECHI TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share