Mikiya Hausa Times

Mikiya Hausa Times Burinmu shine kawo muku ingantattun labarai

Rundunar hadin Guiwa ta sojojin Nigeria ta gano wani sansanin mayakan iswap a tafkin chadi Wanda anan ne mayakan suke ha...
11/04/2022

Rundunar hadin Guiwa ta sojojin Nigeria ta gano wani sansanin mayakan iswap a tafkin chadi Wanda anan ne mayakan suke hada wasu mak**ai da suke amfani dashi wajen kai hari.

Cikin wata sanarwa da shelkwatar tsaro ta kasa ta wallafa a shafinta ta bayyana Hakan amatsayin wata Babbar nasara wadda ta samu.

Ta kara da cewa tana cigaba da kakkabe sansanonin mayakan bisa jajircewar dakarun sojojin Nigeria

Mataimakin alkalin wasa kenan yake cigaba da aikinsa duk da Faduwa da yayi
11/04/2022

Mataimakin alkalin wasa kenan yake cigaba da aikinsa duk da Faduwa da yayi

Da wane Birni yake k**a acikin Biranen Nigeria?
11/04/2022

Da wane Birni yake k**a acikin Biranen Nigeria?

Adamu yunusa dan gwani kenan tsohon na Hadimin kwankwaso yayinda ya sayi form na tsayawa takarar Gwamnan kano karkashin ...
11/04/2022

Adamu yunusa dan gwani kenan tsohon na Hadimin kwankwaso yayinda ya sayi form na tsayawa takarar Gwamnan kano karkashin jam'iyyar PDP.

Sanata abdullahi adamu sabon shugaban jam'iyyar apc na kasa kenan yake jagorantar sallah.Abdullahi adamu ya tare da jiga...
11/04/2022

Sanata abdullahi adamu sabon shugaban jam'iyyar apc na kasa kenan yake jagorantar sallah.

Abdullahi adamu ya tare da jiga jigan jam'iyyar na kasa ciki harda sanata Ahmad lawan shugaban majalisar dattawa na kasa.

Jim kadan Da Bayyana aniyarsa ta Neman kujerar Shugaban kasa Farfesa yemi osinbanjo kuma mataimakin shugaban kasa a hali...
11/04/2022

Jim kadan Da Bayyana aniyarsa ta Neman kujerar Shugaban kasa Farfesa yemi osinbanjo kuma mataimakin shugaban kasa a halin yanzu.

Tuni dai mutane s**a fara rungumar tafiyar tsarin yemi osinbanjo awasu jihohin Nigeria

Haka kuma Rahotanni daga Kano na Cewa matasa da mutane daban daban ne s**a rungumi tsarin tafiyar ta osinbanjo domin cigaba Da Jagorancin Nigeria.

Acewar osinbanjo yayinda yake Bayani game da aniyarsa ta Neman kujerar shugaban kasa yace tsawon shekaru bakwai amatsayinsa na mataimakin shugaban kasa tare da muhammadu Buhari suna aiki badare babu rana wajen Fito da tsare tsare da zasu ciyar da kasarnan Gaba.

Ya kuma yi alkawarin Dora ayyukan raya kasa da shugaba Buhari ya faro tare da kawo wasu managarta.

11/04/2022

Jami'an sojoji a Kaduna sunyi nasarar k**a wasu Tulin masu Garkuwa Da Mutane

Iyalan tsohon shugaban Kasar jamhuriyar Niger marigayi Ba'are mainasara na cigaba da kira Ga Hukumomin kasar akan su Bin...
10/04/2022

Iyalan tsohon shugaban Kasar jamhuriyar Niger marigayi Ba'are mainasara na cigaba da kira Ga Hukumomin kasar akan su Binciko wadanda s**a yiwa maigidan nasu kisan Gilla.

Iyalan marigayin wadanda s**a Gudanar da Taron tunawa dashi shekaru 22 da yimasa kisan Gilla wadanda masu tsaron lafiyasa s**a aiwatar awancan lokaci.

Marigayi ba'are mainasara dai yayi suna ciki da wajen Niger kuma tun Bayan yimasa kisan gilla ake ta kiraye kiraye da a hukunta wadanda s**a yi wancan Mummunan aiki

Wata kungiyar matasa a karamar Hukumar tarauni sunyi kira ga Hajiya Rukayya da Ta Fito ta kuma nemi kujerar majalisar ji...
10/04/2022

Wata kungiyar matasa a karamar Hukumar tarauni sunyi kira ga Hajiya Rukayya da Ta Fito ta kuma nemi kujerar majalisar jiha a karamar Hukumar Tarauni

Kungiyar matasan wadanda s**a ziyarci hajiya Rukayya s**a kuma mika mata Takardar dake nuna Goyon Baya Ga mata su nemi shugabanci sun Bayyana Gamsuwa Da Kuma Jajircewa Ga Hajiya Rukayya.

Acewarsu ana Bukatar matasa a sha'anin Shugabanci a wasu Bangarori, Hakan Yasa s**a yi kira Gareta Da Ta nemi Kujerar wadda s**a Bayyana Goyon Bayansu gareta.

Ana ta Bangaren Hajiya Rukayya ta Bayyana Jin Dadinta da Kuma Bayyana Kudirinta na Neman wannan Kujera Kasancwar akwai Bukatar mata a sha:anin Jagoranci

Tace lokaci yayi da Mata fa kuma matasa zasu tashi tsaye wajen Neman Kujerun da zasu taimaki al'ummarsu a wannan Lokaci.

Hajiya Rukayya dai yar jarida ce dake aiki a daya Daga Cikin Kafafan yada labarai a kano kuma yar kasuwa mai zaman kanta.

Hajiya Rukayya tana taimakon mara sa Karfi dake tsakanin Al'umma.

Tana kuma samun lambar yabo daga Kungiyoyi da daidaikun mutane wadanda s**a gamsu da Yadda take tafiyar da harkokinta

Babbar kotun jiha mai lamba 15 karkashin mai shari’a Nasiru Saminu ta yi watsi da bukatar hukumar KAROTA na ta dakatar d...
10/04/2022

Babbar kotun jiha mai lamba 15 karkashin mai shari’a Nasiru Saminu ta yi watsi da bukatar hukumar KAROTA na ta dakatar da aiwatar da hukuncin hana goyon babur mai kafa biyu.

A zaman kotun na yau, mai shari’a Nasiru Saminu ya ki amincewa da bukatar ta su, inda kuma ya yankewa hukumar ta KAROTA tarar naira dubu goma bisa bata mata lokaci.

Tun da farko dai kotun ta bukaci hukumar KAROTA da ta biya tarar naira miliyan daya da dubu dari shida ga wasu mutum biyu da s**a yi zargin cewa jami’an hukumar sun k**a su a kan laifin yin goyo.

Daya daga cikin masu shigar da kara Kwamared Bello Basi ya shaidawa manema labarai cewa kotun ta saurari bukatar hukumar ta KAROTA, sai dai bayan nazari ta yi watsi da bukatarsu, ta kuma ci tarar su naira dubu goma.

Masu sana'ar talla a kura a kasuwannin kano da kuma masu kasa kaya suna Neman abinda zasu ci da iyalansu sun shiga tasku...
10/04/2022

Masu sana'ar talla a kura a kasuwannin kano da kuma masu kasa kaya suna Neman abinda zasu ci da iyalansu sun shiga tasku a kano

Gwamntin Nigeria ta nemi gafarar yan kasar sak**akon katsewar Hasken wutar lantarki da yafaru Ranar juma'a da da gabata....
10/04/2022

Gwamntin Nigeria ta nemi gafarar yan kasar sak**akon katsewar Hasken wutar lantarki da yafaru Ranar juma'a da da gabata.

Hakan ya faru ne sak**akon yadda batagri s**a lalata turakun dake kawo wutar mai karfin 330 kilovolt wanda ya shafi kasar gabadaya.

Cikin wata sanarwa da mataimaki na musamman ga ministan wutar lantarkin Mr isa sunusi ya fitar yace Gwamnati na yin iya kokarunta wajen gyara matsalar da ta haifar da rashin wutar a Nigeria.

Tun daga shekarar 1999 har kawo wannan lokaci an Gaza samin shugaban da zai yiwa wutar Nigeria diban karan mahaukaciya duk da makudan kudin da ake narkawa akasar.

Address

No 856kofarmazugal
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Mikiya Hausa Times posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Mikiya Hausa Times:

Share