The HausaTimes

The HausaTimes Your go-to source for authentic news
& Uncovering fascinating and unbelievable facts from astronomy and cosmology, alongside history and geopolitics.
(1)

ʼYan'uwa Hausawa,ku tashi ku kare kan ku da dukiyoyin ku; kowane addinin da dokar Kashashe sun sahale Haka, Allah ya bam...
17/08/2026

ʼYan'uwa Hausawa,ku tashi ku kare kan ku da dukiyoyin ku; kowane addinin da dokar Kashashe sun sahale Haka, Allah ya bamu sa’a, akan ‘yan ta’adda".

Suna cewa ba 'yan ta'adda da ke kashe wasu kabilu ke son raba kawunan 'yan Arewa ba mu da muke kukan ana kashe namu ne k...
17/08/2026

Suna cewa ba 'yan ta'adda da ke kashe wasu kabilu ke son raba kawunan 'yan Arewa ba mu da muke kukan ana kashe namu ne ke son raba kawunan al'umma. Akwai hankali a nan?"

Fuullannii_Bandits sun kashe mutum biyu tare da jagorantar Sallar Juma’a a Babban Masallacin Izalah da ke ƙauyen "Kaya",...
17/08/2026

Fuullannii_Bandits sun kashe mutum biyu tare da jagorantar Sallar Juma’a a Babban Masallacin Izalah da ke ƙauyen "Kaya", a Ƙaramar Hukumar Tambuwal ta Jihar Sokoto.

Wani mazaunin ƙauyen, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya shaida wa Daily Trust cewa maharan sun shiga ƙauyen ne da misalin ƙarfe 11:00 na safiyar Juma’ar da ta gabata, inda s**a shafe kusan sa’o’i bakwai suna gudanar da ayyukansu ba tare da wata turjiya ba.

A cewarsa, ’yan bindigar sun tilasta wa mazauna ƙauyen zama a cikin gidajensu, yayin da suke shiga gida-gida suna satar shanu.

Ya ce lokacin da lokacin Sallar Juma’a ya yi, maharan sun nufi Masallacin Izalah, inda s**a yi kiran sallah sannan s**a jagoranci Sallar Juma’ar.

Bayan kammala sallar, sai ’yan bindigar s**a shiga shaguna tare da satar kayayyaki, sannan s**a kai hari ga masu sana’ar POS, inda s**a kwashe kuɗaɗe da darajarsu ta kai miliyoyin naira.

Majiyar ta ƙara da cewa maharan sun bar ƙauyen da misalin ƙarfe 5:00 na yamma, amma s**a sake dawowa da safiyar Asabar, inda s**a sake kwashe wasu shanu.

Lamarin ya jefa mazauna ƙauyen cikin fargaba da rashin tabbas, yayin da suke ci gaba da nuna damuwa kan tsaron rayukansu da dukiyoyinsu.

"Shugaban ƙungiyar Hausawa ya bayyana cewa a ranar Litinin 17 ga watan Agusta, 2026, ƙungiyar ta kai ziyara gidan gyaran...
17/08/2026

"Shugaban ƙungiyar Hausawa ya bayyana cewa a ranar Litinin 17 ga watan Agusta, 2026, ƙungiyar ta kai ziyara gidan gyaran hali (prison) na Gwauron Dutse a Kano.

A cikin bayaninsa, shugaban ya ce an kai tallafin kayan abinci ga daurarru. A gaban su ne aka raba kayan, inda sama da mutane 400 – mata da maza – s**a amfana da tallafin.

Ya kuma bayyana cewa ya zagaya wani ɓangare na gidan yari don ganin yanayin da yake ciki. A cewarsa, gaskiya akwai bukatar sababbin gine-gine a cikin gidan.

Ƙungiyar ta yi nasarar aiwatar da biyan tarar mutane biyar da ke da ƙananan laifi.
Shugaban ya yi fatan Allah ya saka da alkhairi ga duk waɗanda s**a ba su gudummawa ta hanyar shawarwari da kuɗi. Ya kuma yi addu’ar Allah ya ba daurarru mafita, kuma ya tsare su da shiga irin wannan gida.

"An shigo kasar Hausa da rigar musulunci, an samu karbuwa saboda rigar musuluncin da aka shiga. Ashe, da wata manufa aka...
17/08/2026

"An shigo kasar Hausa da rigar musulunci, an samu karbuwa saboda rigar musuluncin da aka shiga. Ashe, da wata manufa aka shigo. Aka yi wa Kakan nin mu yankan rago, aka kwace masarautan mu da dukiyoyin mu da sunan jihadi" Barr. Ahmed Musa

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya yi kira ga al’ummar Fulani da su gargadi ‘ya’yansu da ke cikin dazuka su dawo...
13/08/2026

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya yi kira ga al’ummar Fulani da su gargadi ‘ya’yansu da ke cikin dazuka su dawo gida su daina aikata laifuka, yana mai cewa satar mutane domin neman kuɗin fansa ta jefa al’ummar cikin zargi da fushin jama’a.

Ya ce:

“’Yan uwana, ba zan ji tsoron faɗa muku gaskiya ba. Duk wanda aka sace a daji, daga baya aka sake shi, zai ce Fulani ne s**a sace shi.

“Saboda haka, ku faɗa wa ‘ya’yanku da ke cikin daji su dawo gida domin mu zauna lafiya. Ba zai yiwu ana sace mutane, ana karɓar kuɗin fansa daga gare su, sannan a ce ba za su yi fushi da ku ba.

“Mutane sun fusata da Fulani. Babu wanda yake hana ku kiwo, ko zuwa makaranta, ko zama cikin lumana. Amma kun san cewa wasu daga cikin ‘ya’yanku suna aikata munanan laifuka ga jama’a. Ko da ba a k**a su ba a yau, wata rana za su fuskanci sak**akon abin da suke yi.”

"Wasu Hotunan yan Ƙungiyar Hausawan Nigeria reshen jihar Legas a bakin aiki. 10/8/2026"Wane fata kuke masu?
10/08/2026

"Wasu Hotunan yan Ƙungiyar Hausawan Nigeria reshen jihar Legas a bakin aiki. 10/8/2026"

Wane fata kuke masu?

"Kada ku bari su yaudare ku da kishin Arewa. Karya suke suna amfani da Arewa ne domin su danne Hausawa" cewar shugaban k...
10/08/2026

"Kada ku bari su yaudare ku da kishin Arewa. Karya suke suna amfani da Arewa ne domin su danne Hausawa" cewar shugaban kungiyar Hausawa me za ku ce?

Daga:Ibrahim Gamji✍️

Me za ku ce??
07/08/2026

Me za ku ce??

"Idan dai yanzu babu Hausawa sai harshen Hausa, to kuwa tabbas yanzu babu Turawa sai harshen Turanci"~ prof  cisse
06/08/2026

"Idan dai yanzu babu Hausawa sai harshen Hausa, to kuwa tabbas yanzu babu Turawa sai harshen Turanci"~ prof cisse

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when The HausaTimes posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share

Category