Matashiya TV

Matashiya TV Matashiya! bahaushiyar tasha mai tsage gaskiya komai ɗacinta. Tasha mai zaman kanta, mu na yaɗa labarai ba tare da son zuciya ba
(1)

A yau ne marigayi sarkin Kano na 13, Alhaji Ado Bayero, ya ke cika shekaru 12 da rasuwa.An haife shi ranar 25 ga watan Y...
06/06/2026

A yau ne marigayi sarkin Kano na 13, Alhaji Ado Bayero, ya ke cika shekaru 12 da rasuwa.

An haife shi ranar 25 ga watan Yulin 1930, ya kuma rasu ranar 6 ga watan Yunin 2014, yana da shekaru 83 a duniya.

Ya zama sarkin Kano a ranar 23 ga watan Oktoban 1963 zuwa ranar 6 ga watan Yunin 2014 lokacin da Allah ya yi masa rasuwa. Inda ya shafe tsawon shekaru 51 a karagar mulki kuma sarki ma fi daɗewa a tarihin masarautar Kano.

Shin, da me kuke tunawa da shi?

06/06/2026

Taƙaitattun labarai 6/6/2026

05/06/2026

Kai tsaye labaran dare 5/6/2026

05/06/2026

Kai tsaye mu na yin aikin gwaji daga ɗakin labarai da kuma ɗakin shirye-shirye

Assalamu alaikum masu bibiyarmu idan Allah ya yarda za mu yi wani aikin gwani daga karfe 5-6pm na yamacin yau Juma'a a s...
05/06/2026

Assalamu alaikum masu bibiyarmu idan Allah ya yarda za mu yi wani aikin gwani daga karfe 5-6pm na yamacin yau Juma'a a shafinmu na Facebook.
Mun gode.

05/06/2026

Labaran duniya 5/6/2026

Gwamnatin Tarayya ta yi kira ga ƴan Najeriya da kafafen yaɗa labarai da ƙungiyoyin farar hula da hukumomin tsaro da su ƙ...
05/06/2026

Gwamnatin Tarayya ta yi kira ga ƴan Najeriya da kafafen yaɗa labarai da ƙungiyoyin farar hula da hukumomin tsaro da su ƙarfafa haɗin gwiwa a tsakanin su wajen yaƙi da ta’addanci da sauran nau’o’in tsauraran ra’ayoyi da ke barazana ga zaman lafiya da tsaron ƙasa.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis a Abuja a wajen wani babban taron manema labarai.

Ya ce yaƙi da ta’addanci ya na buƙatar haɗin kan ƙasa baki ɗaya ba tare da la’akari da bambance-bambancen siyasa da ƙabila da addini ko yanki ba.

Ministan ya ce: “Gwamnatin Tarayya tana kira ga ’yan ƙasa da kafafen yaɗa labarai da hukumomin tsaro da su haɗa kai wajen yaƙi da ta’addanci, domin duk wani hari da aka kai wa ɗan Nijeriya ɗaya tamkar an kai shi ne ga dukkan ’yan Nijeriya. Ta’addanci ba ya da ƙabila ko addini ko wata alaƙa da siyasa. Manufar sa ita ce haddasa ɓarna kawai.”

Ya bayyana cewa wannan ne ya haifar da ƙaddamar da gangamin , wanda ke kira ga dukkan ’yan Nijeriya da su haɗa kai wajen yaƙi da ta’addanci da sauran laifuffuka.

Idris ya kuma tabbatar wa da ’yan Nijeriya cewa gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu tana ci gaba da ƙoƙarin ganin an ceto dukkan ɗalibai da malamai da aka sace a hare-haren da s**a faru a jihohin Oyo da Borno.

Ya ce: “Ina so in tabbatar wa da dukkan ’yan Nijeriya cewa dawo da kowane yaro da kowane malami da ke hannun masu garkuwa cikin ƙoshin lafiya yana ci gaba da kasancewa babban fifikon gwamnati. Shugaban Ƙasa ya bayyana ƙarara cewa babu wani yaro da ya k**ata ya kasance a tsare, kuma gwamnati ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen tabbatar da cewa an gurfanar da masu hannu a waɗannan munanan laifuffuka a gaban shari’a.”

Ministan ya bayyana cewa hukumomin tsaro sun ƙara ƙaimi wajen tattara bayanan sirri da gudanar da sintiri da kuma ayyukan ceto domin kuɓutar da waɗanda aka sace tare da hukunta masu hannu a lamarin.

Ya ce dakarun rundunar "Operation Haɗin Kai" sun samu nasarori a Arewa-maso-gabas, inda s**a kashe 'yan ta’adda da dama tare da lalata sansanonin su da kuma ceto fararen hula.

A cewar sa, ayyukan tsaro a yankunan Arewa-maso-yamma da Arewa-ta-tsakiya da Kudu-maso-gabas da Kudu-maso-kudu sun taimaka wajen rusa sansanonin masu aikata laifi da tarwatsa ƙungiyoyin masu garkuwa da mutane da kuma ƙara kare muhimman kadarorin ƙasa.

Idris ya ce nasarorin da ake samu a yaƙi da ta’addanci suna da alaƙa da ingantaccen haɗin gwiwa tsakanin hukumomin tsaro da musayar bayanan sirri da amfani da fasahar zamani da kuma haɗin gwiwa da ƙasashen waje.

Ya ce: “Abin da ya bambanta wannan tsarin da muke amfani da shi a yanzu shi ne haɗa matakan soji da ayyukan da s**a dogara da bayanan sirri da amfani da fasahar zamani da haɗin gwiwa tsakanin yankuna da kuma sa hannun al’umma. Wannan cikakken tsari yana ci gaba da raunana ƙarfin ƙungiyoyin ’yan ta’adda da masu aikata laifuffuka.”

Ministan ya kuma yi nuni da nasarorin da aka samu a ɓangaren shari’a, ciki har da hukuncin da aka yanke wa waɗanda aka samu da hannu a harin ta’addancin da aka kai Cocin St. Francis da ke Owo a Jihar Ondo a watan Yuni 2022.

Ya ce Gwamnatin Tarayya ta kuma fara ɗaya daga cikin manyan shari’un masu laifin ta’addanci a tarihin ƙasar nan, inda ɗaruruwan waɗanda ake zargi suke fuskantar shari’a.

Ya ce: "Adalci yana daga cikin muhimman ginshiƙan tsaron ƙasa. Bayan matakan soji, gwamnati tana tabbatar da cewa duk masu hannu a ayyukan ta’addanci sun fuskanci hukuncin doka. Shari’un da ake yi wa waɗanda ake zargi da ta’addanci da kuma hukuncin da a ka yanke wa wasu daga cikin su na aika saƙo ƙarara cewa ba za a ƙyale masu laifi su tsira daga hukunci ba.”

Ministan ya yi kira ga kafafen yaɗa labarai da su ci gaba da bin ƙa’idojin aikin jarida wajen rahoto kan al’amuran ta’addanci.

Ya ce: “Yayin da ya k**ata kafafen yaɗa labarai su ci gaba da bayar da rahotanni cikin sahihanci da nuna ƙwarewa, dole ne mu yi taka-tsantsan kada mu taimaka wa ƴan ta’adda wajen cimma manufofin su ba tare da sani ba. Aikin jarida mai ɗa’a na iya hana su samun irin shaharar da suke nema, tare da tabbatar da cewa jama’a sun samu sahihan bayanai.”

Ya buƙaci ƴan Najeriya da su kasance masu sa ido tare da bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai, sannan su guji yaɗa duk wani saƙo da ke ƙoƙarin haddasa rarrabuwar kai ta fuskar ƙabila ko addini ko siyasa.

Ministan ya sake jaddada cewa Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin jama’a har sai an kawo ƙarshen ta’addanci da sauran munanan laifuffuka.

“Nijeriya ta sha fuskantar lokuta masu wuya a baya kuma ta fito daga cikin su da ƙarfin ta. Haka nan za mu shawo kan wannan ƙalubale. Idan muka haɗa kai tare da tsayawa tsayin daka kan manufar mu, za mu tabbatar da cewa ta’addanci ba shi da makoma a Nijeriya."

Taron ya samu halartar Babbar Sakatariyar Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Dakta Binyerem Ukaire; Sufeto-Janar na ’Yan Sanda wanda jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, DCP Anthony Okon Placid, ya wakilta; Daraktan Yaɗa Labarai na Rundunar Soji, Janar Sama'ila Uba, da wasu manyan jami’an gwamnati da masu ruwa da tsaki a lamarin.

Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa an samu gagarumin ci gaba a tattaunawar kafa rundunar ’yan sandan jihohi, inda ake s...
05/06/2026

Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa an samu gagarumin ci gaba a tattaunawar kafa rundunar ’yan sandan jihohi, inda ake sa ran gabatar da gyaran kundin tsarin mulki nan ba da jimawa ba domin ba da damar aiwatar da shirin.

Shugaban ma'aikatan fadar shugaban ƙasa, Femi Gbajabiamila, ne ya bayyana hakan bayan wata ganawa da aka yi a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja ranar Alhamis, wadda ta haɗa manyan jami’an gwamnati da shugabannin majalisun dokoki kan batun kafa ’yan sandan jihohi.

Gbajabiamila ya ce an fara nazari da tattaunawa kan yadda za a kafa rundunar tun watanni uku zuwa huɗu da s**a gabata bisa umarnin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, kuma an samu ci gaba mai yawa a aikin.

Ya bayyana cewa kafa ’yan sandan jihohi ba abu ne da za a yi cikin gaggawa ba, domin akwai batutuwan kundin tsarin mulki da dokoki da dole ne a tantance su sosai kafin aiwatarwa.

A cewarsa, yanzu hankalin masu ruwa da tsaki ya karkata ne kan yadda za a yi gyaran kundin tsarin mulki, sannan daga baya a samar da dokokin da za su ba da cikakken iko da tsarin gudanar da rundunar.

Ya ƙara da cewa mafi yawan ’yan Najeriya da masu ruwa da tsaki sun amince da bukatar kafa ’yan sandan jihohi, inda muhawarar yanzu ba ta kan ko a kafa su ko a’a ba, sai dai yadda za a samar da ingantaccen tsarin doka da gudanarwa domin su yi aiki yadda ya k**ata.

Gbajabiamila ya ce za a gabatar wa Shugaba Tinubu cikakken rahoto kan sak**akon ganawar domin ci gaba da matakan da s**a dace.

A cewarsa, manufar kafa ’yan sandan jihohi ita ce ƙarfafa tsaron cikin gida, inganta tattara bayanan sirri daga matakin ƙasa da kuma bai wa gwamnatocin jihohi damar magance matsalolin tsaro cikin sauri da inganci.

Shugaba Tinubu ya sha bayyana cewa tsarin ’yan sandan jihohi na daga cikin hanyoyin da za su taimaka wajen fuskantar ƙalubalen tsaro da ke addabar ƙasar nan, tare da ƙara kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Ganawar ta samu halartar Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau I. Jibrin; Mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai, Benjamin Kalu; Ministan Shari’a kuma Babban Lauyan Tarayya, Lateef Fagbemi; da Sufeto Janar na ’Yan Sanda, Tunji Disu, tare da sauran manyan jami’an gwamnati.

05/06/2026

Taƙaitattun labarai 5/6/2026

Rundunar ‘yan sanda a jihar Ribas ta bayyana cewa jami’anta sun k**a wasu mutane uku da ake zargi da hannu a kisan wani ...
04/06/2026

Rundunar ‘yan sanda a jihar Ribas ta bayyana cewa jami’anta sun k**a wasu mutane uku da ake zargi da hannu a kisan wani direban motar bas mai shekaru 55 mai suna Christopher Akpabio a unguwar Asarama da ke karamar hukumar Andoni ta jihar.

Rundunar ta ce k**a wadanda ake zargin ya biyo bayan rahoton da ta samu na sace direban a ranar 22 ga watan Mayu, 2026, lamarin da ya sa rundunar ta fara gudanar da bincike kan bacewar direban.

Kakakin Rundunar ’Yan sanda a Jihar, Blessing Agabe ita ce ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ta fitar a Fatakwal a yammacin yau Alhamis tare da aika wa manema labarai.

Kakakin ta ce wadanda ake zargin sun hayar direban ne daga Garrison, wata babbar mahadar a Fatakwal, da sunan zai kai su wani ƙauye a jihar Rivers domin halartar taron auren.

A cewar sanarwar, ya yin da suke kan hanyarsu ta zuwa unguwar Asarama, barayin su ka tare direban, inda su ka kashe shi, su ka binne gawarsa a wani rami mara zurfi a yankin, sannan su ka tafi da motar ta sa.

Sanarwar ta kara da cewa bisa dabarun yaki da miyagun laifuka na Kwamishinan ‘yan sanda a Jihar Olugbenga Adepoju, bisa ga umarnin babban sufeton ‘yan sanda Olatunji Rilwan Disu, rundunar ta samu gagarumar nasara da gudanar da bincike kan zargin kisan da kuma k**a mutane uku da ake zargi da aikata laifin fashi da makami.

Wadanda ake zargin sun hada da David Mark mai shekaru 30, ɗan asalin Ƙaramar Hukumar Andoni, Nkajit Williams mai shekaru 45, shi ma ɗan asalin Ƙaramar Hukumar Andoni,Godgift John mai shekaru 33, ɗan asalin Ƙaramar Hukumar Okrika.

Rundunar ta ce ta kuma kwato motar mamacin, ya yin da a ka kai gawar mamacin babban asibitin koyarwa na Jami'ar Port Harcourt domin ƙarin bincike.
A halin yanzu bincike yana ci gaba da gudana, kuma an tsananta bincike domin k**a mutum cikin na huɗu da ya tsere.

Address

Northwest Street Kabuga Road
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Matashiya TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Matashiya TV:

Share