Matashiya TV

Matashiya TV Matashiya! bahaushiyar tasha mai tsage gaskiya komai ɗacinta. Tasha mai zaman kanta, mu na yaɗa labarai ba tare da son zuciya ba
(1)

Gwamnatin tarayya da kungiyar malaman jami’o’i ta Kasa ASUU za su gudanar da wata sabuwar yarjejeniya da za ta inganta t...
12/01/2026

Gwamnatin tarayya da kungiyar malaman jami’o’i ta Kasa ASUU za su gudanar da wata sabuwar yarjejeniya da za ta inganta tsarin ilimin jami’o’in Kasar.

A wata sanarwa da ma’aikatar ilimi ta fitar a ranar Lahadi, ta ce za a gudanar da taron a ranar Laraba 14 ga watan Junairu a dakin taro na Asusun Tallafawa Manyan Makarantu TETFund da ke Maitama Abuja.

Ministan Ilimi Dakta Maruf Tunji Alausa, da Karamar Ministan Ilimi Farfesa Suwaiba Ahmad ne za su jagoranci taron.

Hakan dai na zuwa ne biyo bayan wa'adin kwanaki 14 na baya-bayan nan da kungiyar ta yi, na shirga yajin aiki.

Sai dai daga baya kungiyar ta dakatar da yajin aikin kafin ta tsunduma bayan kungiyar da gwamnatin tarayya sun gudanar da wata tattaunawa.

Daraktan yada labaran Ma’aikatar Folasade Boriowo ce ta bayyana ta cikin wata sanarwa da ta sanya wa hannu, ta ce an tsara yarjejeniyar ne bayan shafe shekaru da dama ana tattaunawa tsakanin gwamnatin da ASUU don magance matsalolin kungiyar.

A cewar ma’aikatar, yarjejeniyar ta yi daidai da shirin sabunta fatan na Shugaba Bola Tinubu, wanda ya amince da ilimi a matsayin dabarun ci gaban kasa, ci gaban al'umma, da tattalin arziki.

Haka kuma ana sanya ran yarjejeniyar za ta kara inganta zaman lafiya a makarantu, samar da ingantaccen yanayin ilimi, da kuma karfafa amincewa tsakanin dalibai, ma'aikatan jami'a, da sauran jama'a.

A cewar ma’aikatar kaddamar da yarjejeniyar za ta hada manyan jami’an gwamnati, wakilan kungiyar ASUU, shugabannin manyan makarantu, da ‘yan jarida.

12/01/2026

Labaran duniya 12/1/2026

An tsaurara matakan tsaro a ƙofar gidan gwamnatin Kano yayin da a ke sa ran gwamnan jihar Alhaji Abba Kabir Yusuf zai sa...
12/01/2026

An tsaurara matakan tsaro a ƙofar gidan gwamnatin Kano yayin da a ke sa ran gwamnan jihar Alhaji Abba Kabir Yusuf zai sauya sheƙa zuwa jam'iyyar APC yau Litinin.

Rundunar sojin Najeriya sun hallaka ƴan ta'adda takwas tare da k**a wasu a jihar Borno.Sannan wasu 11 sun miƙa wuya da m...
12/01/2026

Rundunar sojin Najeriya sun hallaka ƴan ta'adda takwas tare da k**a wasu a jihar Borno.

Sannan wasu 11 sun miƙa wuya da mak**ansu.

Jami'an sun samu nasarar ne a tsakanin ranakun 9 da 10 ga watan Janairun da mu ke ciki

An kuma lalata sansanin ƴan ta'addan a Dagumba, Bonne, Yaganari, Gosuri, Umchulr wanda ya shafi sansanin Abu Nazir da Abu Ahmed.

Jami'an sun kwato mak**ai da dama a Yale da Bula Gaida tare da lalata sansaninsu.

Sannan sun k**a mutane biyu da a ke zargi da addabar yankin arewa maso gabas da hare-hare.

TINUBU YA ISA ABU DHABI DON TARON ADSW 2026Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya isa birnin Abu Dhabi na ƙasar Haɗaɗɗiyar D...
12/01/2026

TINUBU YA ISA ABU DHABI DON TARON ADSW 2026

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya isa birnin Abu Dhabi na ƙasar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE) a daren Lahadi, domin halartar taron Abu Dhabi Sustainability Week (ADSW) na 2026, wanda zai fara a yau Litinin.

Jirgin Shugaban Ƙasan ya sauka a Sashen Shugaban Ƙasa na Filin Jirgin Sama na Zayed da misalin ƙarfe 11:30 na dare agogon Dubai. Ministan Harkokin Wajen UAE, Sheikh Shakhboot Nahyan Al Nahyan, tare da Jakadan UAE a Nijeriya, Salem Saeed Al-Shamsi, da Ministan Harkokin Wajen Nijeriya, Amb. Yusuf Maitama Tuggar, da kuma jami’an ofishin jakadancin Najeriya a Abu Dhabi ne s**a tarbe shi.

Haka kuma, wasu ministoci da s**a haɗa da Ministan Kasafi da Tsare-tsare, Atiku Bagudu, Ministan Masana’antu, Ciniki da Zuba Jari, Dr. Jumoke Oduwole, da Darakta-Janar na Hukumar Leken Asiri ta Ƙasa (NIA), Amb. Muhammed Muhammed, sun tarbe Shugaban Ƙasan a otal ɗinsa.

Kafin isowarsa Abu Dhabi, Shugaba Tinubu ya shafe wani ɓangare na hutun ƙarshen shekara a Turai, inda ya yi muhimman tattaunawa da Shugaban Rwanda, Paul Kagame, da Shugaban Faransa, Emmanuel Macron.

Taron ADSW 2026, mai taken “The Nexus of Next, All Systems Go”, dandali ne na duniya da ke haɗa shugabanni, masu tsara manufofi, masu zuba jari da ƙwararru domin tattaunawa da ɗaukar matakai kan ci gaba mai dorewa, yaƙi da sauyin yanayi, sauya tsarin mak**ashi da bunƙasa tattalin arziki da ya haɗa kowa da kowa.

Ziyarar ta ƙara jaddada kyakkyawar alaƙar diflomasiyya da tattalin arziki tsakanin Najeriya da UAE, tare da nuna matsayar Najeriya a matsayin ƙasa mai taka rawa a tattaunawar duniya kan ci gaba mai dorewa.

12/01/2026

Taƙaitattun labarai 12/1/2026

11/01/2026

Labaran duniya 11/1/2026

Gwamnatin Jihar Edo ta jaddada kudurinta na tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin mazauna jihar, inda ta bayyana cewa t...
11/01/2026

Gwamnatin Jihar Edo ta jaddada kudurinta na tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin mazauna jihar, inda ta bayyana cewa tuni matakan da s**a dauka na samar da sak**ako mai kyau wajen yaki da garkuwa da mutane, kungiyoyin asiri, da sauran ayyukan miyagun laifuka.

A cewar wata sanarwa a ranar Asabar mai dauke da sa hannun Dr Patrick Ebojele babban sakataren yada labaran gwamnan jihar Sanata Monday Okpebolo ne ya bayyana hakan a lokacin da yake jawabi kan karuwar matsalar rashin tsaro.

Gwamnan ya bayyana cewa gwamnatinsa ta sanya jari mai yawa a fannin tsaro na zamani, tattara bayanan sirri, da hadin gwiwar hukumomi don tunkarar masu aikata laifukaa.

Gwamnan ya ce za su tabbatar da magance matsalar sace-sacen mutane ta hanyoyin dabarun zamani, inda ya ce a halin yanzu ana ci gaba da gudanar da ayyukan tsaro a fadin jihar.

Acewarsa gwamnatin Jihar ba za ta kyale masu aikata laifi ba ko masu daukar nauyinsu, inda ya ce dukkan wanda ke da hannu a cikin yin garkuwa da mutane da matsalar tsaro, da kuma kungiyoyin asiri, da sauran wasu laifuka za a gurfanar da su a gaban kotu, yana mia cewa Jihar Edo ba mafakar masu aikata laifuka bace.

Gwamnan ya bukaci al’ummar Jihar da su kwantar da hankulansu, su kuma kiyaye da bin doka da oda, kuma su ci gaba da gudanar da harkokinsu na yau da kullum, yana mai tabbatar musu da cewa gwamnatinsa na da karfin gaske wajen shawo kan matsalar tsaro.

Sun janye daga fara yajin aikin da su ka shirya yi daga gobe Litinin bayan shiga tsakani da mataimakin shugaban ƙasa San...
11/01/2026

Sun janye daga fara yajin aikin da su ka shirya yi daga gobe Litinin bayan shiga tsakani da mataimakin shugaban ƙasa Sanata Kashim Shettima ya yi.

Tsohon gwamnan jihar Sokoto Aminu Waziri Tambuwal, ya koka da halin da Najeriya ke ciki, yana mai gargadin cewa Kasar na...
11/01/2026

Tsohon gwamnan jihar Sokoto Aminu Waziri Tambuwal, ya koka da halin da Najeriya ke ciki, yana mai gargadin cewa Kasar na cikin hadari.

Tambuwal ya bayyana hakan ne a lokacin da ya ke jawabi a wajen bikin cikarsa shekaru 60 a duniya a ranar Asabar, ya ce al’ummar kasar na bukatar ceto cikin gaggawa ta hanyar shugabanci na gaskiya da hadin kan kasa..

Tambuwal ya ce ya zama dole su kuduri aniyar yin aiki tare da ceto kasar, da ke cikin hadari wanda hakan zai yuwune ta hanyar tsarin gamayya.

Taron ya samu halartar manyan ‘yan siyasa da dama, ciki har da shugaban majalisar dattawa Sanata Godswill Akpabio, wanda shugaban marasa rinjaye na majalisar dattawa Abba Moro ya wakilta, da babban malami mabiya addinin kirista na cocin Katolika ta Jihar Sokoto Matthew Hassan Kukah.

Sauran sun hada da Tsohuwar Kakakin Majalisa Patricia Etteh Yakubu Dogara, Ministan Gidaje Ahmed Musa Dangiwa; da kuma tsoffin gwamnoni da s**a hada da Rotimi Amaechi, Aminu Masari, Udom Emmanuel, Ibikunle Amosun, Gbenga Daniel, da kuma sakataren jam’iyyar ADC Rauf Aregbesola.

Sauran su ne tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan, da tsohon mataimakin shugaban Ƙasa Atiku Abubakar, tsohon shugaban majalisar David Mark, tsohon gwamnan jihar Edo Adams Oshiomhole da dai sauransu.

11/01/2026

Labaran duniya 11/1/2025

Address

France Road
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Matashiya TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Matashiya TV:

Share