05/06/2026
Gwamnatin Tarayya ta yi kira ga ƴan Najeriya da kafafen yaɗa labarai da ƙungiyoyin farar hula da hukumomin tsaro da su ƙarfafa haɗin gwiwa a tsakanin su wajen yaƙi da ta’addanci da sauran nau’o’in tsauraran ra’ayoyi da ke barazana ga zaman lafiya da tsaron ƙasa.
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis a Abuja a wajen wani babban taron manema labarai.
Ya ce yaƙi da ta’addanci ya na buƙatar haɗin kan ƙasa baki ɗaya ba tare da la’akari da bambance-bambancen siyasa da ƙabila da addini ko yanki ba.
Ministan ya ce: “Gwamnatin Tarayya tana kira ga ’yan ƙasa da kafafen yaɗa labarai da hukumomin tsaro da su haɗa kai wajen yaƙi da ta’addanci, domin duk wani hari da aka kai wa ɗan Nijeriya ɗaya tamkar an kai shi ne ga dukkan ’yan Nijeriya. Ta’addanci ba ya da ƙabila ko addini ko wata alaƙa da siyasa. Manufar sa ita ce haddasa ɓarna kawai.”
Ya bayyana cewa wannan ne ya haifar da ƙaddamar da gangamin , wanda ke kira ga dukkan ’yan Nijeriya da su haɗa kai wajen yaƙi da ta’addanci da sauran laifuffuka.
Idris ya kuma tabbatar wa da ’yan Nijeriya cewa gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu tana ci gaba da ƙoƙarin ganin an ceto dukkan ɗalibai da malamai da aka sace a hare-haren da s**a faru a jihohin Oyo da Borno.
Ya ce: “Ina so in tabbatar wa da dukkan ’yan Nijeriya cewa dawo da kowane yaro da kowane malami da ke hannun masu garkuwa cikin ƙoshin lafiya yana ci gaba da kasancewa babban fifikon gwamnati. Shugaban Ƙasa ya bayyana ƙarara cewa babu wani yaro da ya k**ata ya kasance a tsare, kuma gwamnati ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen tabbatar da cewa an gurfanar da masu hannu a waɗannan munanan laifuffuka a gaban shari’a.”
Ministan ya bayyana cewa hukumomin tsaro sun ƙara ƙaimi wajen tattara bayanan sirri da gudanar da sintiri da kuma ayyukan ceto domin kuɓutar da waɗanda aka sace tare da hukunta masu hannu a lamarin.
Ya ce dakarun rundunar "Operation Haɗin Kai" sun samu nasarori a Arewa-maso-gabas, inda s**a kashe 'yan ta’adda da dama tare da lalata sansanonin su da kuma ceto fararen hula.
A cewar sa, ayyukan tsaro a yankunan Arewa-maso-yamma da Arewa-ta-tsakiya da Kudu-maso-gabas da Kudu-maso-kudu sun taimaka wajen rusa sansanonin masu aikata laifi da tarwatsa ƙungiyoyin masu garkuwa da mutane da kuma ƙara kare muhimman kadarorin ƙasa.
Idris ya ce nasarorin da ake samu a yaƙi da ta’addanci suna da alaƙa da ingantaccen haɗin gwiwa tsakanin hukumomin tsaro da musayar bayanan sirri da amfani da fasahar zamani da kuma haɗin gwiwa da ƙasashen waje.
Ya ce: “Abin da ya bambanta wannan tsarin da muke amfani da shi a yanzu shi ne haɗa matakan soji da ayyukan da s**a dogara da bayanan sirri da amfani da fasahar zamani da haɗin gwiwa tsakanin yankuna da kuma sa hannun al’umma. Wannan cikakken tsari yana ci gaba da raunana ƙarfin ƙungiyoyin ’yan ta’adda da masu aikata laifuffuka.”
Ministan ya kuma yi nuni da nasarorin da aka samu a ɓangaren shari’a, ciki har da hukuncin da aka yanke wa waɗanda aka samu da hannu a harin ta’addancin da aka kai Cocin St. Francis da ke Owo a Jihar Ondo a watan Yuni 2022.
Ya ce Gwamnatin Tarayya ta kuma fara ɗaya daga cikin manyan shari’un masu laifin ta’addanci a tarihin ƙasar nan, inda ɗaruruwan waɗanda ake zargi suke fuskantar shari’a.
Ya ce: "Adalci yana daga cikin muhimman ginshiƙan tsaron ƙasa. Bayan matakan soji, gwamnati tana tabbatar da cewa duk masu hannu a ayyukan ta’addanci sun fuskanci hukuncin doka. Shari’un da ake yi wa waɗanda ake zargi da ta’addanci da kuma hukuncin da a ka yanke wa wasu daga cikin su na aika saƙo ƙarara cewa ba za a ƙyale masu laifi su tsira daga hukunci ba.”
Ministan ya yi kira ga kafafen yaɗa labarai da su ci gaba da bin ƙa’idojin aikin jarida wajen rahoto kan al’amuran ta’addanci.
Ya ce: “Yayin da ya k**ata kafafen yaɗa labarai su ci gaba da bayar da rahotanni cikin sahihanci da nuna ƙwarewa, dole ne mu yi taka-tsantsan kada mu taimaka wa ƴan ta’adda wajen cimma manufofin su ba tare da sani ba. Aikin jarida mai ɗa’a na iya hana su samun irin shaharar da suke nema, tare da tabbatar da cewa jama’a sun samu sahihan bayanai.”
Ya buƙaci ƴan Najeriya da su kasance masu sa ido tare da bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai, sannan su guji yaɗa duk wani saƙo da ke ƙoƙarin haddasa rarrabuwar kai ta fuskar ƙabila ko addini ko siyasa.
Ministan ya sake jaddada cewa Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin jama’a har sai an kawo ƙarshen ta’addanci da sauran munanan laifuffuka.
“Nijeriya ta sha fuskantar lokuta masu wuya a baya kuma ta fito daga cikin su da ƙarfin ta. Haka nan za mu shawo kan wannan ƙalubale. Idan muka haɗa kai tare da tsayawa tsayin daka kan manufar mu, za mu tabbatar da cewa ta’addanci ba shi da makoma a Nijeriya."
Taron ya samu halartar Babbar Sakatariyar Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Dakta Binyerem Ukaire; Sufeto-Janar na ’Yan Sanda wanda jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, DCP Anthony Okon Placid, ya wakilta; Daraktan Yaɗa Labarai na Rundunar Soji, Janar Sama'ila Uba, da wasu manyan jami’an gwamnati da masu ruwa da tsaki a lamarin.