Matashiya TV

Matashiya TV Matashiya! bahaushiyar tasha mai tsage gaskiya komai ɗacinta. Tasha mai zaman kanta, mu na yaɗa labarai ba tare da son zuciya ba
(1)

Kun yarda zogale ya fi kaza?
08/08/2026

Kun yarda zogale ya fi kaza?

Bayan jihar Kano, jihohi shiga daga arewacin Najeriya ne su ka shiga gasar sana'o'i da Matashiya TV ta shirya.An shirya ...
08/08/2026

Bayan jihar Kano, jihohi shiga daga arewacin Najeriya ne su ka shiga gasar sana'o'i da Matashiya TV ta shirya.

An shirya gasar ne da nufin ƙarfafawa matasa a kan sana'o'insu tare da basu dama don baje basirar da su ke da ita da kuma ƙarewa a sana'o'i na hannu da kasuwanci.

Matasa daga jihohin Kaduna, Jigawa, Katsina, Bauchi, Zamfara da Sokoto ne su ka shiga gasar.

Zuwa yanzu ɗaiɗaikun matasa kusan 200 ne su ka shiga bayan ƙungiyoyi masu dubban mambobi a ciki.

08/08/2026

Taƙaitattun labarai 8/8/2026

Me ku ke marmarin yayin da a ke ruwan sama?
07/08/2026

Me ku ke marmarin yayin da a ke ruwan sama?

07/08/2026

Labaran duniya 7/8/2026

A ƙoƙarinsa na ganin kawunsa ya zarce a karo na biyu a zaɓen gwamnan jihar Osun, fitaccen mawaƙin nan Davido ya yi baraz...
07/08/2026

A ƙoƙarinsa na ganin kawunsa ya zarce a karo na biyu a zaɓen gwamnan jihar Osun, fitaccen mawaƙin nan Davido ya yi barazanar kai ƙara wajen shugaban Amurka, Donald Trump, muddin aka yi maguɗi a zaɓen gwamnan jihar ta Osun da za a gudanar ranar 15 ga watan Agusta.

Davido ya bayyana hakan ne yayin da ake wata tattaunawa da shi ta kai tsaye, inda ya ke goyon bayan kawun na sa, GwamnaAdemola Adeleke na jihar Osun, wanda ya ke neman tazarce a zaɓen da ke tafe ƙarƙashin jam'iyyar Accord.

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barcelona ta miƙa tayin yuro miliyan 45 ga Manchester City domin ɗaukar Rodri, sai dai tuni Cit...
07/08/2026

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barcelona ta miƙa tayin yuro miliyan 45 ga Manchester City domin ɗaukar Rodri, sai dai tuni City ɗin ta yi watsi da wannan tayin.

Jaridar The Athletic ta ruwaito cewa Manchester City ɗin ta na buƙatar aƙalla yuro miliyan 75 zuwa 80 kafin ta bari ɗan wasan ya tsallaka zuwa kowacce ƙungiya.

An zaɓi tsohon shugaban ƙasar Benin, Patrice Talon, a matsayin shugaban majalisar dattijai na farko watanni kaɗan bayan ...
07/08/2026

An zaɓi tsohon shugaban ƙasar Benin, Patrice Talon, a matsayin shugaban majalisar dattijai na farko watanni kaɗan bayan saukarsa daga kujerar shugabancin ƙasar.

An zaɓe shi ne domin ya shafe tsawon shekaru biyar a matsayin shugaban sabuwar majalisar dattijan ƙasar da aka kafa, bayan ya samu ƙuri'u 24 cikin guda 25 da aka kaɗa cikin wani zaɓen sirri da aka gudanar ranar Alhamis.

An yi tsammanin dawowar tsohon shugaban ƙasar cikin sha'anin mulki tun shekarar da ta gabata, bayan ya amince da gyaran kundin tsarin mulkin ƙasar domin ƙirƙiro sabuwar majalisar.

A watan Afrilun da ya gabata ne dai aka gudanar da babban zaɓen ƙasar, inda tsohon ministan kuɗi, Romuald Wadagni, ya samu nasara da gagarumin rinjaye bayan ya lashe kashi 94 cikin 100 na ƙuri'un da aka kaɗa.

Sai dai shi ma tsohon shugaban ƙasar kuma jagoran jam'iyyar hamayya, Thomas Boni Yayi, ya nuna sha'awarsa na ƙalubalantar Talon a zaɓen shugaban majalisar dattijan da aka gudanar.

Amman kuma ya rasa goyon bayan wasu daga cikin ƴan sabuwar majalisar da aka ƙirƙira, waɗanda naɗa su aka yi ba zaɓarsu ba.

Da ya ke nasa jawabin, sabon shugaban majalisar dattijan, Patrice Talon, ya bayyana majalisar a matsayin ta musamman, saboda haka zai kasance babban kuskure idan ya ce ba zai yi aiki a cikinta ba.

07/08/2026

Labaran Duniya 7/8/2026

Shugaban Matashiya TV Abubakar Murtala Ibrahim ne ya sanar da haka a wata wasiƙar yabawa da godiya da ya bai wa shugaban...
07/08/2026

Shugaban Matashiya TV Abubakar Murtala Ibrahim ne ya sanar da haka a wata wasiƙar yabawa da godiya da ya bai wa shugaban kamfanin Ammasco Alhaji Mustapha Ado Muhammad ranar Alhamis.

Wasiƙar mai ɗauke da kwanan watan 6/8/2026, ta yabawa shugaban kamfanin Ammasco bisa yadda ya ke ƙoƙari wajen ganin matasa sun samu cigaba a al'amuransu da kuma kulawa da ma'aikatan da ke ƙarƙashinsa.

Shugaban Matashiya TV ya ce shigowar kamfanin Ammasco a gasar sana'o'i da Matashiya TV ta shirya ya sake tabbatar da kishin matasan da shugaban Ammasco ke da shi wajen ganin matasa sun tsaya da ƙafarsu.

Ya ce ra'ayi da kishin matasa ya zo a daidai lokacin da matasan ke buƙatar kulawa ta musamman tare da bijiro da hanyoyin da za su ƙarfafa musu gwiwa don ganin an kawar da tunaninsu daga aikata laifuka.

A sakamakon haka Matashiya TV ta bayar da dama domin horas da ma'aikatan gidan rediyon yadda za su samu ƙwarewa a ɗaukar hoto da bidiyo kuma kyauta.

Wannan dai na a matsayin tukwici da a ka ce yabawar kyauta ne.

Shugaban Ammasco Alhaji Mustapha Ado Muhammad ya ce za su ci gada da bayar da gudunmawa a harkokin matasa ta kowacce fuska kuma a kowanne lokaci.

Za a bayar da horon ne a watan Satumba mai kamawa.

Address

Northwest Street Kabuga Road
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Matashiya TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Matashiya TV:

Shortcuts

Share