Best Media

Best Media Best Media zai kasance shafin da zai dinga kawo labarai akan lamuran da s**a shafi rayuwar yau da kullum, cikin harshen Hausa da Turanci

28/10/2022

MARIGAYI MALAM ALBANI ZARIA YACE DANGANE DA ATIKU.

A cikin wannan bidiyon bayani ne Malam Albani Zaria yakeyi akan Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP Alhaji Atiku Abubakar, an dawo da bidiyon ne saboda al'umma su fadaka akan maganganun da akeyi na danganta Atiku da mai kishin Arewa.

KAMAR HAKA DAI......Daga Usman Rabiu Kwankwaso Lokacin da Wazirin Adamawa Alhaji Atiku Abubakar Ya samu daman zama matai...
23/09/2022

KAMAR HAKA DAI......

Daga Usman Rabiu Kwankwaso

Lokacin da Wazirin Adamawa Alhaji Atiku Abubakar Ya samu daman zama mataimakin shugaban kasa daga 1999 zuwa 2007, lokacin ne Alhaji Bola Ahmad Tinubu Ya samu damar zama gwamnan jihar Lagos.

Sai mu duba abubuwan da s**a ma alumma gwargwadon damar da kowa ya samu, sai muyi musu hisabi.

Dan haka masu kokarin nuna kishin arewa akan Alhaji Atiku Abubakar ba nuga sun nuna a mulkin shugaba buhari ba, lokacin da ake ta kokarin gyara mama hanyoyin mu, railway, wutan nepa din mu da PDP ta kashe, s**a kasa gyara wa....

Na Tabbata Zan Dawo Da Najeriya Cikin Hayya Cinta, Idan Na Zama Shugaban Ƙasa ~ Bola Ahmad TinubuƊan takarar shugaban ƙa...
23/09/2022

Na Tabbata Zan Dawo Da Najeriya Cikin Hayya Cinta, Idan Na Zama Shugaban Ƙasa ~ Bola Ahmad Tinubu

Ɗan takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin Inuwar Jamiyyar All Progressives Congress (APC) Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya ce yana da dukkan abin da ya k**ata domin ganin Najeriya ta samu cigaba na rayuwa idan aka Zaɓe shi a matsayin shugaban Najeriya.

Tinubu ya ce yana da hanyar da za ta sake ɗaukaka Najeriya da kuma kawo ci gaba ga kowa da kowa, ya ƙara da cewa “Zan iya tafiyar da hanya zuwa wadata, na san hanyar ilimi domin na yi imani da shi, na san hanyar da za a magance matsalar rashin tsaro. ƙasar."

Sai dai ya yi kira ga ƴan Najeriya da su ba shi damar yin aiki ta hanyar ba shi kuri’unsu.

Ya ce, “Za mu yi aiki tare ne domin ba za mu koma lokacin da ake tari ba, ba za mu bari a yi mulkin k**a karya ba.”

KANA DA ZABI UKU....Ko dai Kaci AMALA, ko kasha Ruwan FARO ko kuma ka cika cikin ka da kayan MARMARI....Wanda ya dace da...
08/06/2022

KANA DA ZABI UKU....

Ko dai Kaci AMALA, ko kasha Ruwan FARO ko kuma ka cika cikin ka da kayan MARMARI....

Wanda ya dace dakai, shi zaka dauka...

Kwankwaso ya shige a kirashi da Local Champion, mutumin da ya kawo sabuwar jam'iyyar da a kasa da wata biyar ta samu San...
06/06/2022

Kwankwaso ya shige a kirashi da Local Champion, mutumin da ya kawo sabuwar jam'iyyar da a kasa da wata biyar ta samu Sanatoci, yan Majalisar tarayya da jihohi, kuma jam'iyyar take da yan takarar gwamna a jihohi masu yawa.

Kwankwaso Ikon Allah

TAMBAYA GAREMUA yanzu da ake tsaka da hada hadar siyasa a Nigeria, jam'iyyu suke ta fitar da Mutanen da zasuyi musu taka...
06/06/2022

TAMBAYA GAREMU

A yanzu da ake tsaka da hada hadar siyasa a Nigeria, jam'iyyu suke ta fitar da Mutanen da zasuyi musu takara a kowanne bangare, su kuma al'ummar gari masu jefa kuri'a suke da shirin zabar wanda suke kauna ko suke ganin k**ar zaiyi musu abun da suke so.

A Nigeria babu wadataccen Tsaro, kayan masarufi suke kara hauhawa, ganin likita yake kara zama lamari na kudi, yan makarantar gaba da Secondary suke zaune a gida, karatu yayi tsada, abunci yake neman gagarar da yawa cikin al'umma.

GA TAMBAYAR......

Tsakaninka Da Allah, zaka yi zabe ne da cikekken tunanin wanda zaka zaba zaiyi maka aikin gyara kasarka, ko kuwa dai zakayi zabe ne saboda dan takarar yana jam'iyyarka ne, ko zakayi zabe ne saboda kana kaunar wanda zaka zaba..

Shin a zuciyarka kana da amincin yan siyasa suna neman mulki ne saboda jin dadinka, ko kuwa saboda kansu suke nema.

05/06/2022

MARTANIN SHUGABAN APC GA TINUBU.

A hirarsa da gidan Rediyon BBC Hausa, shugaban jam'iyyar APC Abdullahi Adamu yayi martani mai zafi akan Bola Ahmed Tinubu

AZABAR ALLAH NA JIRANKU....Cikin fushi shugaba Muhammadu Buhari yake sanar da wadanda s**a kai hari Choci a jihar Ondo h...
05/06/2022

AZABAR ALLAH NA JIRANKU....

Cikin fushi shugaba Muhammadu Buhari yake sanar da wadanda s**a kai hari Choci a jihar Ondo har s**a Ka*she masu ibadah, shugaban ya cigaba da cewa aikin assha ne wanda Allah ba zai kyale ba, sannan yasha alwashin hukunci mai radadi akan makasan.

A yau lahadi ne wasu da baa san ko su waye ba, s**a kai mummanan hari a lokacin da masu ibada s**a hadu don gudanar da ayyukan Ibadah a chocin dake jihar Ondo.

KANA MAGANA KAMAR BUGAGGE..... martanin Shugaban Jam'iyya Ga Bola Tinubu Shugaban Jam'iyyar APC na kasa Abdullahi Adamu ...
05/06/2022

KANA MAGANA KAMAR BUGAGGE.....

martanin Shugaban Jam'iyya Ga Bola Tinubu

Shugaban Jam'iyyar APC na kasa Abdullahi Adamu yayi martani mai zafi ga Dan Takarar kujerar shugabancin Nigeria Bola Ahmed Tinubu, martanin ya biyo bayan kalaman dashi Tinubu ya furta a wajen taron ganawa da Delegates a Abekuta, inda Tinubu yake cewa badon shi ba da Muhammadu Buhari bai zama shugaban Nigeria ba, har ya kara da cewa Buhari yana kuka kashirban amma yaje ya bashi hakuri tare da mayar dashi shugaban kasa...

Abdullahi Adamu yace ko kadan kalaman na Tinubu basu k**ata ba, domin dai ko a buge yake bai k**ata a jiyoshi yana furta kalaman rashin da'a ga shugaban Nigeria, kuma tabbas ba zasu kyale ba.

Lamura dai suna kara daukan zafi a lokacin da ake saura kwana daya da zaben fitar da gwani dake faruwa yanzu haka....

BOLA AHMED TINUBU NE KAWAI YA CANCANTA DA SAMUN TIKITIN TAKARA.Idan ba Bola Tinubu ba, waye ya cancanta da zama dan taka...
04/06/2022

BOLA AHMED TINUBU NE KAWAI YA CANCANTA DA SAMUN TIKITIN TAKARA.

Idan ba Bola Tinubu ba, waye ya cancanta da zama dan takarar kujerar shugaban kasa a jam'iyyar APC, shi kadai ne wanda yafi kowa dacewa da mulkar Nigeria a shekarar 2023, ku duba dukkan yan takarar dake APC zaku ga ba wanda bai amfana da aikin Tinubu ba.

Babban kuskure ne ace ba Tinubu bane dan Takara, hakan zai iya zama babban abun kunya ga jam'iyyar APC.

NIMA MATASHI NE.A wani bidiyo dake yawo a shafukan sadarwar zamani, wanda ake kyautata zaton sabon bidiyo ne, an hango D...
03/06/2022

NIMA MATASHI NE.

A wani bidiyo dake yawo a shafukan sadarwar zamani, wanda ake kyautata zaton sabon bidiyo ne, an hango Dan Takarar kujerar shugabancin Nigeria karkashin Jam'iyyar APC Bola Ahmed Tinubu yana bayyana cewa shima fa Matashi ne, domin zuciyarsa cike take da kwazo da kuma kuzari, don haka dole ne a saka shi a layin matasan Nigeria.

Amma wasu na ganin Tinubu yayi wannan sanarwar ne, bayan da Shugaban kwamitin tantance yan takara na jam'iyyar APC ya fitar da sanarwar dake cewa sun kori yan takara goma daga cikin sha ukun da s**a nemi tsayawa takara, sannan ragowar ukun da s**a dauka dukkansu Matasan dattijai ne masu kuzari.

Tuni dai lamura s**a fara daukar zafi a jam'iyyar APC.

Address

Kano

Telephone

+2348087673220

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Best Media posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Best Media:

Share