INAYA Tv

INAYA Tv Newsweek Hausa

18/01/2026

😭😭😭

17/01/2026

Mutumin da yake a kan kuskure amma ya ɗauka yana kan gaskiya, abin tausayi ne ƙwarai.
Babbar masifa ita ce ka kasance a kan kuskuren, amma ka yi imani cewa kai ne a akan daidai.

17/01/2026

Qur,an: it’s only book that make the heart ❤️ (qalbi) to be comfort

16/01/2026

SAMUN KARIYA DAGA ALLAH (SWT)

Ku fara yininku da ambaton Allah سبحانه وتعالى da tuna Shi. Ku ambace Shi سبحانه وتعالى ambato mai yawa, ku yi tasbihi a gare Shi safe da yamma sai ku kara samun nutsuwa.

Duk wanda aka azurta shi da yawan ambaton Allah سبحانه وتعالى, to wannan ya samu babban rabo.

Tv

16/01/2026

😭😭 Allahumma ajjirna minan Narr

SHUGABAN MAJALISAR DATTAWAAn ruwaito cewa Shugaban Majalisar Dattawan Nigeria Senator Godswill Akpabio ya yanke jiki ya ...
16/12/2025

SHUGABAN MAJALISAR DATTAWA

An ruwaito cewa Shugaban Majalisar Dattawan Nigeria Senator Godswill Akpabio ya yanke jiki ya fadi, an garzaya da shi zuwa wani Asibiti a birnin London yana cikin t$aka mai wuy/¥a

Har zuwa yanzu dai Majalisar Dattawa da Gwamnatin Nigeria basu tabbatar ko karyata labarin ba

Idan ya tabbata bai da lafiya an kwantar dashi muna fatan Allah Ya bashi lafiya, Ya shiryar dashi hanya madaidaiciya

Dole A Gaggauta Binciken Ƙaramin Ministan Tsaro Kan Zargin Alaƙa Da Yan Bindiga, Cewar CNG..... Gamayyar Kungiyoyin Arew...
14/12/2025

Dole A Gaggauta Binciken Ƙaramin Ministan Tsaro Kan Zargin Alaƙa Da Yan Bindiga, Cewar CNG
..... Gamayyar Kungiyoyin Arewacin Najeriya Ta Buƙaci A Gaggauta Bincike Mai Zurfi Kan Zargin Da Ake Yiwa Matawalle Da Alaƙa Da Yan Bindiga

Ƙungiyar Coalition of Northern Groups (CNG) ta bayyana damuwa mai tsanani kan ikirarin da Musa Kamarawa, tsohon mataimaki na musamman ga tsohon Gwamnan Zamfara kuma Ministan Tsaron Ƙasa na yanzu, Bello Matawalle, ya yi a wani faifan bidiyon da yake nuna Matawallen na da alaƙa da tallafawa yan bindiga.

CNG ta ce zargin ya shafi tura kuɗi kai tsaye ga fitaccen shugaban ‘yan bindiga Bello Turji, sayen motocin Hilux da dama ga ƙungiyoyin ta’addanci, da kuma bayar da tallafin kayan aiki kamar gidaje, shanu da sauran dukiya, wanda ake zargin ‘yan siyasa daga Zamfara da maƙwabtanta s**a taimaka wajen aiwatarwa.

A cewar CNG, waɗannan ikirari suna nuna yiwuwar alaƙa mai zurfi tsakanin wasu manyan jami’an gwamnati da ‘yan bindiga, lamarin da ka iya rusa ƙoƙarin sojoji tare da ƙara jefa al’umma cikin haɗari.

Ƙungiyar ta ce irin waɗannan zarge-zarge ba za a iya watsi da su ta hanyar musantawa kawai ba, domin hakan na ƙara haifar da shakku cewa ana ɓoye gaskiya.

CNG ta kuma soki matakin Ministan na kai ƙara kan Sheikh Murtala Asada, tana mai cewa hakan na iya zama yunƙurin hana faɗin gaskiya, maimakon kare mutunci. Ta bukaci Sheikh Asada da ya fito da dukkan hujjojin da ke hannunsa ba tare da tsoro ba.

Ƙungiyar ta jaddada cewa babu wanda ya isa ya fi karfin doka, kuma ɓoye masu hannu a ta’addanci na raunana tsaro da amincewar jama’a.

Saboda haka, CNG ta nemi bincike mai zaman kansa, binciken da babu son zuciya, wanda Majalisar Ƙasa, hukumomin tsaro da Ofishin Babban Lauyan Ƙasa za su jagoranta, domin binciken kuɗaɗe, kayan aiki, sadarwa da duk wata shawara da ka iya taimaka wa ‘yan bindiga.

Ta ce dole a kare masu fallasa gaskiya, kuma duk jami’in gwamnati da aka samu da laifi ya fuskanci hukunci ba tare da la’akari da matsayinsa ko ƙarfin ikonsa ba.

CNG ta jaddada cewa Arewa ta sha wahala matuƙa sakamakon ‘yan bindiga, kuma wannan lokaci wata dama ce ta fuskantar tushen matsalar. Kare masu aikata laifi zai lalata makomar tsaro da amincewar jama’a. Lokacin ɓoyewa ya wuce, lokacin gaskiya da adalci ya yi.

Sa Hannun
Comr Jamilu Aliyu Charanchi
National Coordinator CNG

Rundunar ƴan sanda ta umarci ƴan sandan da ke gadin waɗannan manyan mutanen da su janye daga gadinsu su kuma koma office...
27/11/2025

Rundunar ƴan sanda ta umarci ƴan sandan da ke gadin waɗannan manyan mutanen da su janye daga gadinsu su kuma koma office a gobe Alhamis.

Manyan mutanen sun haɗa da Atiku Abubakar, Wike, Aisha Buhari, Namadi Sambo, Tanko Almakura da sauransu.

Din kuna ganin hakan zai kawo karshen matsalar tsaron da ake fama dai mu ita A wasu sassan arewacin Nigeria?

Da Dumi-Dumi:Gwamnatin Jihar Katsina Ta Umurci Makarantun Jeka-ka-Dawo Da Ba Na Kwana Ba Su Cigaba da Jarabawar Su
24/11/2025

Da Dumi-Dumi:

Gwamnatin Jihar Katsina Ta Umurci Makarantun Jeka-ka-Dawo Da Ba Na Kwana Ba Su Cigaba da Jarabawar Su

Innalillahi Wa'inna Illahiri Raju'un 😭 😭 💔 Wannan shine makwabcina shagona yana kallon shagonsa a unguwar Tashar Aibo Ji...
24/11/2025

Innalillahi Wa'inna Illahiri Raju'un 😭 😭 💔

Wannan shine makwabcina shagona yana kallon shagonsa a unguwar Tashar Aibo Jibia, Sunanshi DAN GASKE MAI MASARA yau kwana ukku kenan ranar alhims 18/11/2025 aka ɗaura wannan auren shida wannan yarinyar amma yau lahadi yakwanta yana bacci da rana tasa wuka tayi mashi yan kan rago. Allah yajikanshi da rahama 🤲..

Daga shafin
Gwagwaren Jibia ✍️

Address

Rijiyar Zaki Kano
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when INAYA Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share