The Breaking

The Breaking This is the Official Page that will be bringing you the activities of the Nassarawa LG Kano

27/05/2025

Flag off of Reconstruction of Zungeru Road Sabon Gari Kano.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya mika diyyar naira miliyan 600 ga mazauna Bulbula da Gayawa. Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba K...
08/05/2025

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya mika diyyar naira miliyan 600 ga mazauna Bulbula da Gayawa.

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci babban taron mika chakin diyya na sama da Naira miliyan 600 ga mazauna unguwannin Bulbula da Gayawa, da ke cikin Kananan Hukumomin Nassarawa da Ungogo.

Wannan diyya na da nasaba da gidaje da filaye da aka karɓa daga mazauna yankunan da zaizayar ƙasa ke addaba, domin bai wa gwamnati damar gyara wannan muhimmin yanki.

A nasa jawabin, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta gudanar da manyan ayyuka domin magance matsalar zaizayar ƙasa a yankin.

Ya ce za a shimfiɗa manyan bututun magudanan ruwa domin hana ambaliya, musamman a lokacin damina, tare da gina sabbin hanyoyi a saman kwatocin da za a gyara, kamar yadda aka yi a titin Wuju-Wuju na unguwar Goron Dutse, karamar hukumar Gwale.

Shugabannin kafafan yada labarai a Kano na Radio da Talabijin sun dauki matakin dakatar da yin shirye-shiryen siyasa kai...
08/05/2025

Shugabannin kafafan yada labarai a Kano na Radio da Talabijin sun dauki matakin dakatar da yin shirye-shiryen siyasa kai tsaye domin dakile kalaman batanci da kuma tarzoma a jihar.

Matakin ya biyo bayan wani taro da s**a gudanar a ofishin kwamishinan yada labarai da niyyar kawo gyara kan yadda ake yada labarai musamman na siyasa.

An bayyana wannan mataki ne a wani taron tattaunawa da ake yi duk bayan lokaci wanda ya gudana a Ma’aikatar Yada Labarai...
08/05/2025

An bayyana wannan mataki ne a wani taron tattaunawa da ake yi duk bayan lokaci wanda ya gudana a Ma’aikatar Yada Labarai da Harkokin Cikin Gida, tsakanin jami’an gwamnati da shugabannin kafafen yada labarai. Kwamishinan Yada Labarai, Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya ne ya jagoranci taron.

A cewar wata sanarwa da Sani Abba Yola, Daraktan al'amura na musamman na ma’aikatar ya sanya wa hannu, an dauki wannan mataki ne “domin hana yaduwar kalaman da ka iya tayar da rigima” da kuma kare hadin kan addini da al’adun mutanen jihar.

“Ba ma kokarin takura ‘yan adawa ba,” in ji Kwamared Waiya a yayin jawabi ga shugabannin kafafen yada labarai. “Burinmu shi ne kare al’adu da dabi’u da addini na Kano.”

An cimma wasu matsayai na daban a yayin zaman. “Duk wanda zai bayyana a kafafen yada labarai domin tattaunawa dole ne ya rattaba hannu a wata takarda da ke nuna alkawarin kin amfani da kalaman batanci, cin mutunci, ko na cin zarafin,” in ji sanarwar.

An kuma umurci masu gabatar da shirye-shirye da su kauce wa tambayoyi masu tayar da hankali ko “nuna alamu da ka iya janyo amsoshin da za su bata suna ko kuma su kaskantar da martabar Jihar Kano.”

Kwamared Waiya ya ce an rage yawan amfani da kalaman batanci a shirye-shiryen rediyo da talabijin, yana mai danganta hakan da ci gaba da tuntuba da fahimtar juna da ke gudana tsakanin ma’aikatar da kafafen yada labarai.

Ya kara da cewa gwamnati ta kaddamar da shirye-shiryen wayar da kai ga masu gabatar da shirye-shiryen siyasa, masu sharhi a kafafen yada labarai, da mambobin Majalisar Limaman Juma’a.

“Muna son ganin sakonni suna zuwa cikin natsuwa da gaskiya, ba tare da cin zarafi ko wani abu da zai tauye mutuncin jiharmu ba,” in ji Waiya.

Address

Nasarawa Local Government Sectariat
Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when The Breaking posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share