Labarai24

Labarai24 Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Labarai24, Media/News Company, Kano.

In da na ci zaɓe nima sai na cire tallafin man fetur amma ba farar-ɗaya irin na Tinubu ba - Obi Peter Obi, dan takarar s...
10/06/2025

In da na ci zaɓe nima sai na cire tallafin man fetur amma ba farar-ɗaya irin na Tinubu ba - Obi

Peter Obi, dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar Labour Party (LP) a zaɓen 2023, ya ce da ya ci zaɓen da shi ma sai ya cire tallafin man fetur kuma ya kyale Naira ta neman wa kan ta daraja, k**ar sai yadda shugaba Bola Tinubu ya yi.

Da ya ke magana a wata hira da ya yi da gidan talabijin na Arise a jiya Litinin, Obi ya ce da zai aiwatar da manufofin a hankali a hankali ba farar-ɗaya ba gaba-gaɗi irin na Tinubu ba.

Tsohon gwamnan na Anambra ya ce kowa ya san cewa dole ne a kawo karshen "baƙala da cin hanci da rashawa" da ke tattare da tsarin tallafin man fetur.

Obi ya yi tambaya kan inda kudaden da ake tarawa cire daga tallafin man fetur suke tun lokacin da aka cire shi, ya kara da cewa kudaden ya k**ata a sanya su wajen yin aiyukan samar da "mahimman kayan more rayuwa".

Ya ce ba a samu wani gagarumin ci gaba ba tun bayan cire tallafin man fetur.

Ya kara da cewa da zai yi shawarwari da masu gudanar da aiki kan ingantaccen tsarin farashi na samfurin.

Fitaccen Jarumi a masana'antar Kannywood Adam A. Zango ya yi haɗari a hanyar Kaduna zuwa Kano.Mun samu labarin babu wand...
09/06/2025

Fitaccen Jarumi a masana'antar Kannywood Adam A. Zango ya yi haɗari a hanyar Kaduna zuwa Kano.

Mun samu labarin babu wanda ya rasa rai a haɗarin, sai dai an jikkata sosai, mota kuma ta yi ratsa-ratsa. Allah ya kyauta gaba, amin.

Mijina bai yi sata ba kuma duk kudin da ya tara wa Nijeriya sun yi ɓatan-dabo - Maryam Abacha Maryam Abacha, matar marig...
09/06/2025

Mijina bai yi sata ba kuma duk kudin da ya tara wa Nijeriya sun yi ɓatan-dabo - Maryam Abacha

Maryam Abacha, matar marigayi Janar Sani Abacha, tsohon shugaban soja na Najeriya, ta ce mijinta ya ajiye wa Najeriya kudi, amma aka wawashe su bayan rasuwarsa.

A wata hira da aka yi da ita a gidan talabijin na TVC, wacce jaridar TheCable ta rawaito, Maryam ta bukaci a kawo hujja da ke nuna cewa mijinta ya boye kudaden sata a kasashen waje.

Abacha ya mulki Najeriya a matsayin shugaban soja da kuma kwamandan rundunar sojin kasa daga 1993 zuwa 1998, kafin rasuwarsa a ranar 8 ga Yuni, 1998.

Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa ta kwato wasu kaso-kaso na kudaden da ake zargin Abacha ya boye a bankunan kasashen waje.

A cewar rahotanni, daga shekarar 2020, an kwato sama da dala biliyan 3.624 daga cikin kudaden da Abacha ya boye.

“Wa ne shaida na kudaden da ake cewa an boye?” in ji Maryam.

“Ka ga hannu ko shaida cewa kudin na waje ne? Kuma kudin da mijina ya adana wa Najeriya, cikin 'yan watanni sun bace. Babu wanda ke magana a kan hakan.”

Ta ce yadda ake ci gaba da zargin mijinta alamar wani mummunan hali ne da ke addabar al’umma.

“Me yasa kuke dora wa wani laifi? Ko kabilanci ne ko bambancin addini ne ko me ke damun 'yan Najeriya?” in ji ta.

Rundunar yan sandan jihar Kano ta tabbatar da rasuwar babban baturan yan sanda na karamar hukumar Rano sak**akon wata ha...
26/05/2025

Rundunar yan sandan jihar Kano ta tabbatar da rasuwar babban baturan yan sanda na karamar hukumar Rano sak**akon wata hatsaniyar da ta faru da safiyar wannan ranar ta litinin bayan da wasu fustattuan matasa s**a afkawa babban baturan yan sandan.

Hakan dai na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin rundunar yan sandan ya fitar SP Abdullahi Haruna ya ce babban baturan yan sandan na karamar hukumar ta Rano CSP Muhammad Baba Ali ya rasu ne a asibitin koyarwa na Malam Aminu Kano.

Dan majalisar tarraya mai wakiltar Gaya, Ajingi da Albasu, Ghali Mustapha Tijjani ne ya gabatar da ƙudirin a zauren maja...
26/03/2025

Dan majalisar tarraya mai wakiltar Gaya, Ajingi da Albasu, Ghali Mustapha Tijjani ne ya gabatar da ƙudirin a zauren majalisar wakilai.

Wannan ƙudiri ya samu tsallake karatu na biyu, tare da kudirin kirkirar wasu jihohi, wanda s**a haɗa da jihohin Oke da Ijebu da Ife Ijesa daga jihar Ogun da kuma jihar Orlu daga yankin kudu maso gabas.

Wata Kotun Musulinci Ta Yankewa Barawon Agwagi Hukunci A Kano.Kotun shari’ar addinin muslinci dake unguwar Danbare Kano,...
25/03/2025

Wata Kotun Musulinci Ta Yankewa Barawon Agwagi Hukunci A Kano.

Kotun shari’ar addinin muslinci dake unguwar Danbare Kano, karkashin jagorancin mai shari’a Munzali Idris Gwadabe, ta yankewa wani mutum hukuncin daurin watanni uku a gidan a jiya da gyaran hali da tarbiya, ko zabin biyan tarar naira dubu talatin tare da tsalala masa bulala 20, bayan samun sa da laifin satar Agwagin guda biyu.

Al’ummar garin Gurungawa dake karamar hukumar Kumbotso, ne s**a yi nasarar k**a mutumin, mai suna Musa Garba, dan asalin jihar Bauchi, a lokacin da ya k**a wasu Agwagi guda 2 tare da sanya su a cikin buhu don kai su kasuwa ya siyar.
Bayan k**a shi ne jama’ar garin s**a mika shi ofishin yan sandan Kumbotso, su kuma s**a gurfanar dashi a gaban kotun dauke da takarar tuhumar laifin satar Agwagi.

Mai gabatar da kara na kotun ya karanto masa kunshin tuhumar da ake yi masa, inda nan take ya masa laifin da ake tuhumarsa da aikatawa.
Alkalin kotun Munzali Idris Gwadabe, ya yankewa masa hukuncin daurin watanni uku da kuma tsalala masa bulala 20, ko zabin biyan tarar naira dubu talatin.

Gidauniyar Dangote Ta Kaddamar Da Rabon Abinci Na Naira Biliyan 16 Ga Talakawan NijeriyaGidauniyar Aliko Dangote, a ciki...
17/03/2025

Gidauniyar Dangote Ta Kaddamar Da Rabon Abinci Na Naira Biliyan 16 Ga Talakawan Nijeriya

Gidauniyar Aliko Dangote, a cikin shirye-shiryenta na 2025, na bayar da tallafin abinci ga ‘yan Nijeriya, wanda aka kaddamar a ranar Alhamis, ta ware kudi kimanin Biliyan16 domin tallafa wa ralakawa ‘yan Najeriya masu nakasa da kuma marasa karfi.

Sama da mutum miliyan daya ne za su rabauta da tallafin buhunhunan shinkafa mai nauyin kilo gram 10 daga wannan tsarin na gidauniyar Aliko Dangote.

Da yake jawabi a wajen taron kaddamarwar, shugaban gidauniyar Aliko Dangote, Alhaji Aliko Dangote, ya ce an tsara yin rabon shinkafar buhu miliyan daya ne mai nauyin kilo gram 10, ga ‘yan Najeriya marasa karfi da raunana, a kananan hukumomi 774 na kasar, k**ar yadda yake a tsarin kamfani da kuma gidauniyarsa na nuna jinkai ga ‘yan kasar.

Dangote, wanda ya samu wakilcin diyarsa, Hajiya Mariya Aliko Dangote, ya ce: shirin na wannan shekara, an yi shi ne da nufin nuna tausayi da jinkai da nuna kulawa wajen taimakon jama’a bisa la’akari da halin da ake ciki na matsin rayuwa da durkushewar tattalin arziki.

Ya ce gidauniyar ta fara kaddamar da rabon tallafin ne a jihar Kano, bayan nan za a ci gaba da rabawa zuwa sauran jihohi, domin tabbatar da ganin cewa abincin ya isa hannun wadanda aka yi domin su a daukacin kananan hukumomin Nijeriya.

Alhaji Dangote, hamshakin attajirin nahiyar Afirka, ya ce sun hada kai da gwamnatin jihar ne wajen tabbatar da ganin an raba abincin ga mabukata a kowace jiha dake fadin Nijeriya.

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf wanda ya jagoranci kaddamar da rabon tallafin abincin a matakin kasa na wannan shekara, ya ce aiwatar da wannan shiri ya nuna tsantsar halin nuna jinkai da kulawar Alhaji Aliko Dangote wajen kawar da yunwa da fatara a Nijeriya.

Gwamnan wanda mataimakinsa, Comrade Aminu Abdulsalam Gwarzo ya wakilta, ya ce za a raba buhun shinkafar guda dubu 120, mai nauyin kilogram 10 a daukacin kananan hukumomi 44 dake fadin jihar Kano.

A jawabinta ga manema labarai, Babbar Darakta kuma Babbar jami’ar gudanarwar gidauniyar Aliko Dangote, Zouera Youssoufou ta ce an tsara shirin ne a matsayin wata hanya ta tallafa wa gwamnatoci wajen yaki da talauci da yunwa a Nijeriya.

Mukaddashin Babban Kwamandan Hisbah na jihar Kano, Dr. Mujahid Aminudden ya gode wa gidauniyar ta Dangote kan bijiro da wannan shiri, inda ya roki sauran ‘yan Nijeriya da suyi koyi da halin Dangote.

Ya ce Hukumar Hisbah za ta tsaya tsayin daka wajen ganin tallafin yaje hannun wadanda s**a cancanta.

Wani da ya yi magana a madadin wadanda s**a ci gajiyar tallafin mai suna Ibrahim Ahmed ya yaba wa Aliko Dangote, inda ya yi addu’ar Allah ya ci gaba da taimakonsa a harkokinsa na kasuwanci.

Gidauniyar Dangote Ta Kaddamar Da Rabon Abinci Na Naira Biliyan 16 Ga Talakawan Nijeriya
17/03/2025

Gidauniyar Dangote Ta Kaddamar Da Rabon Abinci Na Naira Biliyan 16 Ga Talakawan Nijeriya

Gidauniyar Aliko Dangote, a cikin shirye-shiryenta na 2025, na bayar da tallafin abinci ga ‘yan Nijeriya, wanda aka kaddamar a ranar Alhamis, ta ware kudi kimanin Biliyan16 domin tallafa wa ralakaw…

Innalillahi wa inna ilaihi raji’un.Allah yayiwa Sakataren masarautar Rano dake jihar Kano Alhaji Sani Haruna Rano, rasuw...
17/03/2025

Innalillahi wa inna ilaihi raji’un.

Allah yayiwa Sakataren masarautar Rano dake jihar Kano Alhaji Sani Haruna Rano, rasuwa.

Kafin rasuwarsa shi ne tsohon shugaban makarantar kowayar da kiwon lafiya ta (School of Health Technology, Kano).

Inda za'ayi jana'izarsa a safiyar yau da misalin ƙarfe 10 na safe a gidansa dake Unguwar Na'ibawa Layin Ɗan hassan.

Muna addu'ar Allah ya jiƙansa.

Hukumar EFCC a Kano ta cafke fitacciyar ƴar TikTok ɗin nan Murja Ibrahim Kunya bisa zargin yin liƙi da kuɗin Najeriya.Wa...
16/03/2025

Hukumar EFCC a Kano ta cafke fitacciyar ƴar TikTok ɗin nan Murja Ibrahim Kunya bisa zargin yin liƙi da kuɗin Najeriya.

Wata majiya a hukumar ta tabbatarwa da Freedom Radio k**a Murjan.

Ko a kwanakin baya ma EFCCn ta k**a wasu ƴan TikTok da s**a haɗar Al'amin G-Fresh da Ashir Idris kan irin wannan zargin.

Za a binciki hanyar da Sanata Natasha ta bi ta samu damar halartar majalisar mata ta Majalisar Dinkin Duniya IPUJaridar ...
16/03/2025

Za a binciki hanyar da Sanata Natasha ta bi ta samu damar halartar majalisar mata ta Majalisar Dinkin Duniya IPU

Jaridar Premium Times da ake wallafawa a Nijeriya ta gano cewa hukumomin tsaron ciki na DSS da NIA zansu binciki hanyar da Sanatar Kogi ta tsakiya Natasha Akpoti ta bi har ta samu damar halartar majalisar mata ta Majalisar Dinkin Duniya IPU ba tare da samun sahalewa a hukumace ba.

Hukumomin dai za su binciki wanda ya yi musabbabin zuwanta IPU, da wanda ya tantance ta da kuma gano ko wasu gungun mutane ne s**a dauki nauyin wannan ziyara tata don cin fuskar Nijeriya, gwamnati da al'ummar kasar.

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Kano ya ziyarci mataimakin shugaban majalisar Dattawa Barau I Jibril, a gidan sa dake b...
14/03/2025

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Kano ya ziyarci mataimakin shugaban majalisar Dattawa Barau I Jibril, a gidan sa dake birnin tarayya Abuja.

Address

Kano
700104

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Labarai24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share