Labarai24

Labarai24 Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Labarai24, Media/News Company, Kano.

Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un.Allah Ya yi wa Hajiya Maryam Nasiru Imam Rano rasuwa. Ta rasu a daren jiya Asabar. Z...
09/05/2026

Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un.

Allah Ya yi wa Hajiya Maryam Nasiru Imam Rano rasuwa. Ta rasu a daren jiya Asabar. Za a yi jana’izarta yau da misalin karfe 7:00 na safe a kofar gidan Liman Nasiru da ke Rano, unguwar Liman.

Marigayiyar ta rasu ta bar mijinta, Tsohon Liman Malam Nasiru Hassan, da kuma Liman Malam Mansur Liman Rano.

Allah Ya jikanta, Ya gafarta mata, Ya sanya Aljanna ce makomarta. Ameen.

Sanata Adolphus Wabara ya karɓi ragamar PDP bayan hukuncin Kotun ƘoliShugaban Kwamitin Amintattu (BoT) na jam’iyyar PDP ...
30/04/2026

Sanata Adolphus Wabara ya karɓi ragamar PDP bayan hukuncin Kotun Ƙoli

Shugaban Kwamitin Amintattu (BoT) na jam’iyyar PDP ya sanar da karɓar ragamar shugabancin jam’iyyar a matakin ƙasa, sak**akon hukuncin Kotun Ƙoli da ya soke shugabancin Tanimu Turaki da na Abdulrahman Muhammad.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da shugaban BoT na PDP, Sanata Adolphus Wabara, ya fitar ranar, inda ya ce matakin ya zama dole domin kauce wa gibin shugabanci a jam’iyyar.

Tinubu ya naɗa sabon ministan Lantarki na NajeriyaShugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya naɗa Mr Joseph Olasunkanmi Tegb...
30/04/2026

Tinubu ya naɗa sabon ministan Lantarki na Najeriya

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya naɗa Mr Joseph Olasunkanmi Tegbe a matsayin sabon ministan wutar lantarkin ƙasar.

A sanarwar da kakakin shugaban Bayo Onanuga ya fitar, ya ce an tura sunan Tegbe zuwa majalisar dattawa domin amincewa k**ar yadda dokokin ƙasar s**a tanada.

Wannan na zuwa ne bayan murabus ɗin da Adebayo Adelabu ya yi daga muƙamin domin shiga takara a zaɓen 2027.

Kotun Ƙoli ta tabbatar da shugabancin David Mark na ADCKotun Kolin Nijeriya ta tabbatar da shugabancin David Mark na Jam...
30/04/2026

Kotun Ƙoli ta tabbatar da shugabancin David Mark na ADC

Kotun Kolin Nijeriya ta tabbatar da shugabancin David Mark na Jam’iyyar ADC inda ta soke umarnin da Kotun Daukaka Ƙara da ke Abuja ta bayar a cikin rikicin shugabancin jam’iyyar adawar.

Wannan hukunci ya dawo da kwamitin zartarwa da David Mark ke jagoranta, wanda Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta taɓa cirewa daga rajista.

A cikin hukunci guda ɗaya da dukkan alkalan kwamitin biyar s**a amince da shi a ranar Alhamis, wanda Mai Shari’a Mohammed Lawal Garba ya jagoranta, Kotun Kolin ta bayyana cewa umarnin da Kotun Daukaka Ƙara ta bayar ba shi da amfani kuma ba a buƙatarsa.

Jam’iyyun adawa sun amince su goyi bayan ɗan takara ɗaya a 2027Jam’iyyun adawa a Nijeriya sun bayyana aniyarsu ta tsayar...
25/04/2026

Jam’iyyun adawa sun amince su goyi bayan ɗan takara ɗaya a 2027

Jam’iyyun adawa a Nijeriya sun bayyana aniyarsu ta tsayar da ɗan takarar shugaban ƙasa guda ɗaya a zaɓen 2027 domin ƙalubalantar jam’iyyar APC mai mulki.

Wannan na kunshe ne cikin sanarwar bayan taron ƙasa na jam’iyyun adawa da aka gudanar a Ibadan, Jihar Oyo, ranar Asabar 25 ga Afrilu 2026.

Sanarwar da aka wallafa a shafin PDP na Facebook ta ce jam’iyyun sun zargi APC da yunƙurin mayar da Nijeriya ƙasa mai jam’iyya ɗaya, tare da alƙawarin kare tsarin dimokuraɗiyya mai jam’iyyu da dama.

Oluremi Tinubu Ta Ƙaddamar Da Shirin ECoN A Kano, Ta Bukaci Mayar Da Hankali Kan Masana’antuUwargidan Shugaban Ƙasa, San...
23/04/2026

Oluremi Tinubu Ta Ƙaddamar Da Shirin ECoN A Kano, Ta Bukaci Mayar Da Hankali Kan Masana’antu

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta ƙaddamar da wani sabon shiri mai taken “Energise Commercialisation Now” (ECoN) a birnin Kano ranar Alhamis, inda ta yi kira ga ‘yan Nijeriya da su daina tsayawa ga tunanin ayyuka kawai, maimakon haka su duƙufa wajen gina masana’antu.

Da take jawabi a wajen taron, Sanata Oluremi ta bayyana cewa Nijeriya ƙasa ce mai cike da fasaha da hazaka, inda kullum ake samun sabbin ra’ayoyi daga jami’oi da cibiyoyin fasaha, amma abin takaicin shi ne yawancin waɗannan ra’ayoyin ba sa komawa ayyukan da za su amfani al’umma a aikace.

Manufar shirin ECoN

Uwargidan Shugaban Ƙasar ta ce: “Wannan shiri na ECoN wani gagarumin mataki ne na dinke barakar da ke tsakanin tunanin ayyuka da aiwatar da su. Muna son samar da yanayi inda za a tallafa wa ra’ayoyin matasa da masu bincike domin su zama manyan masana’antu.”

Ta ƙara da cewa shirin zai taimaka kwarai wajen samar da ayyukan yi, bunƙasa tattalin arziki, da kuma sanya Nijeriya takara da sauran ƙasashen duniya a fagen kasuwanci da fasaha. Ta kuma nanata cewa mata da matasa ne za su kasance a gaba-gaba a dukkan shirye-shiryen gwamnati.

A nasa jawabin, Ministan Fasaha da Kimiyya, Dr. Kingsley Udeh, ya ce an samar da ECoN ne domin magance tsohuwar matsalar nan ta Nijeriya, inda ake bincike mai kyau amma ba a kai shi kasuwa domin ya zama kuɗi.

A cewarsa, bincike da dama na nan sun maƙale a dakunan gwaje-gwaje (laboratories) saboda rashin kuɗi ko kuma rashin hanyar kai su ga masu saye.

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya nuna jin daɗinsa kan yadda aka zaɓi Kano domin ƙaddamar da wannan shiri na ƙasa da kuma na shiyyar Arewa maso Yamma. Ya bayyana cewa Kano ta riga ta fara shiri ta hanyar inganta ilimin kimiyya da fasaha da kuma faɗaɗa hanyoyin sadarwa na zamani (ICT).

Shi ma Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, wanda ya yi magana a madadin Gwamnonin Arewa maso Yamma, ya lashi takobin cewa gwamnonin shiyyar za su ba da cikakken haɗin kai. Ya bayyana cewa Jihar Jigawa ma na shirin kafa "Garuruwan Fasaha" (Technology Village) domin bunkasa harkar bincike da jan hankalin masu zuba jari.

Kotu Ta Sa An Dawo Da Sheikh Abduljabbar Kano Daga Gidan Yarin KujeA yau Laraba ne aka tabbatar da isowar Sheikh Abdulja...
22/04/2026

Kotu Ta Sa An Dawo Da Sheikh Abduljabbar Kano Daga Gidan Yarin Kuje

A yau Laraba ne aka tabbatar da isowar Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara, zuwa birnin na Dabo, biyo bayan umarnin Kotun Daukaka Kara.

An dauko malamin ne daga gidan gyaran hali na Kuje da ke Abuja, inda yake tsare, domin ya samu damar bayyana a gaban kotu a ranar Alhamis (gobe) don ci gaba da shari’ar da ake yi da shi.

Idan ba a manta ba, a zaman kotun da ya gabata a makon nan, Sheikh Abduljabbar ta bakin wakilan sa ya nemi kotun da ta ba shi damar kare kansa da kansa tare da bayyana a gaban alkalai don gabatar da hujjojinsa, k**ar yadda dokar kasa ta tanada.

Bayan duba bukatar tasa, Kotun Daukaka Kara da ke zamanta a Kano ta ba da umarnin a kawo shi kusa, domin ba shi damar gudanar da kare kansa yadda ya k**ata ba tare da wani tsaiko ba.

Ana sa ran cewa zaman na gobe Alhamis zai dauki hankalin jama'a da dama, ganin cewa wannan ne karon farko da Sheikh Abduljabbar zai sake bayyana a gaban kotu a Kano tun bayan yanke masa hukunci da wata kotu tayi a 2022.

Shugaba Tinubu ya yi sabbin nade-nade a hukumomin ilimi ta NijeriyaShugaban Nijeriya Bola Tinubu ya amince da sabbin naɗ...
22/04/2026

Shugaba Tinubu ya yi sabbin nade-nade a hukumomin ilimi ta Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya amince da sabbin naɗe-naɗe a wasu manyan hukumomin ilimi, ciki har da Hukumar Shirya Jarabawar NECO da Hukumar Ilimin Fasaha ta Ƙasa.

Sanarwar da mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin yaɗa labarai, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Laraba ta ce matakin na daga cikin ƙoƙarin ƙarfafa hukumomin ilimi a ƙarƙashin Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya.

Shugaba Tinubu Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Ibrahim GaladimaShugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya nuna alhininsa kan rasuwar fi...
19/04/2026

Shugaba Tinubu Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Ibrahim Galadima

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya nuna alhininsa kan rasuwar fitaccen mai kula da harkar wasanni kuma jagoran al’umma a Jihar Kano, Alhaji Ibrahim Galadima.

Marigayi Galadima ya riga mu gidan gaskiya ne a ranar Asabar yana da shekaru 78 a duniya.

Kafin rasuwarsa, Ibrahim Galadima ya rike muk**ai daban-daban a matakin jiha da na tarayya. Ya taba zama Shugaban Hukumar Wasanni ta Jihar Kano, sannan ya yi kwamishina har sau biyu a jihar.

Haka kuma, ya taba rike mukamin Shugaban Hukumar Kwallon Kafa ta Kasa (NFA), wacce yanzu aka sani da NFF, tsakanin shekarar 2002 zuwa 2006.
Bayan ya bar aikin gwamnati, an nada shi sarautar Galadiman Fagge, inda ya jagoranci al'ummarsa ta Fagge da ke birnin Kano.

A cikin wata sanarwa da Mai Magana da Yawun Shugaban Kasa, Bayo Onanuga ya fitar ranar Lahadi, Shugaba Tinubu ya bayyana rasuwar Galadima a matsayin babban rashi ga harkar wasanni da ma Najeriya baki daya.

Shugaban ya jaddada cewa ba za a taba mancewa da irin gagarumar gudunmawar da marigayin ya bayar wajen bunkasa kwallon kafa ba, tun daga matakin karkara har zuwa matakin koli.

"Ibrahim Galadima ya sadaukar da rayuwarsa wajen ciyar da wasanni gaba. Najeriya za ta dade tana tunawa da ayyukansa," in ji Tinubu.

Daga karshe, Shugaban Kasa ya mika sakon ta'aziyyarsa ga iyalan mamacin, da Gwamnatin Jihar Kano, da kuma daukacin masoya wasanni na gida da waje, tare da addu'ar Allah ya jikan sa da rahama.

NELFUND Ta Biya Wa Daliba 6,385 na Jami’ar Lafiya Kudin Makaranta Miliyan 795Hukumar bayar da lamuni ga dalibai ta kasa ...
19/04/2026

NELFUND Ta Biya Wa Daliba 6,385 na Jami’ar Lafiya Kudin Makaranta Miliyan 795

Hukumar bayar da lamuni ga dalibai ta kasa (NELFUND), ta fitar da kudi har naira miliyan dari bakwai da casa’in da biyar da dubu dari bakwai da ashirin da tara da dari biyar (₦795,729,500) domin biyan kudin karatun dalibai dubu shida da dari uku da tamanin da biyar (6,385) na Jami’ar Gwamnatin Tarayya da ke Lafiya (FULafia), Jihar Nasarawa.

Hakan na ƙunshe cikin wata wasikar godiya da jami’ar ta aika wa hukumar ta NELFUND mai dauke da sa hannun Shugaban Jami’ar (Vice Chancellor), Farfesa Mohammed Isa Kida.

A cikin wasikar, jami’ar ta nuna cewa an turo kudaden ne kashi uku tsakanin watan Fabrairu da Maris na wannan shekara k**ar haka:

A ranar 16 ga Fabrairu, 2026, ta biya wa dalibai 4,563 Naira 565,249,500; sai ranar 24 ga Fabrairu, 2026 da aka biya wa ɗalibai 636 Naira 82,189,000; sai kuma 3 ga Maris, 2026 da aka biyawa ɗalibai 1,186 Naira 148,291,000. Jimillar adadin ɗaliban ya k**a 6,385 wanda aka biya musu Naira 795,729,500.

Farfesa Isa Kida ya bayyana jin dadinsa da kuma yabawa hukumar kan yadda take gudanar da ayyukanta cikin gaskiya da rikon amana. Ya ce wannan tallafi babban abin farin ciki ne ga daliban jami'ar, domin zai share musu hawaye tare da basu damar ci gaba da karatunsu ba tare da fargabar kudin makaranta ba.

"Tasirin da NELFUND ke yi a rayuwar dalibanmu ba abin da za a iya kwatantawa ba ne. Mun gode kwarai da gaske kan sadaukarwarku wajen bunkasa ilimi a Najeriya," in ji shi.

Wannan tallafi na zuwa ne a karkashin shirin "Renewed Hope" na gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, da nufin tabbatar da cewa babu dalibin da ya rasa damar yin karatu saboda rashin hali.

Address

Kano
700104

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Labarai24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share