kanawa Post news

kanawa Post news Domin samun labarai masu inganci ka ziyarci tashar kanawa Post news

Ana fargabar mutane da dama sun rasu yayin da dan kunar bakin wake ya tada bom a Masallaci a MaiduguriAn rawaito cewa da...
24/12/2025

Ana fargabar mutane da dama sun rasu yayin da dan kunar bakin wake ya tada bom a Masallaci a Maiduguri

An rawaito cewa daruruwan masu ibada sun rasa rayukansu bayan wani ɗan kunar bakin wake ya tayar da bam a masallacin Juma’a na Gambarou da ke Maiduguri, babban birnin jihar Borno.

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa wasu daga cikin masu ibadar da s**a tsira daga harin sun ce maharan sun shiga masallacin a ɓoye, sannan s**a tayar da bam ɗin ne a lokacin sallar Magariba tare da jama’a.

“Ɗan kunar bakin waken ya tayar da bam ɗin ne a raka’a ta farko ta sallar Magariba. Mutane da dama sun mutu, wasu kuma sun jikkata da raunuka iri-iri,” in ji wani da ya tsira.

Sai dai ba a samu wanda ya ɗauki alhakin harin nan take ba, amma ana zargin ƙungiyar Boko Haram da aikatawa, kasancewar ta ƙaddamar da hare-haren kunar bakin wake da dama a yankin cikin ‘yan watannin da s**a gabata.

YANZU-YANZU: Lauya Ya Maka Gwamnan Gombe da CP a Kotu Bisa Zargin Tauye Haƙƙin Jama’aBarrister Nuhu Dantani, lauya mai r...
31/08/2025

YANZU-YANZU: Lauya Ya Maka Gwamnan Gombe da CP a Kotu Bisa Zargin Tauye Haƙƙin Jama’a

Barrister Nuhu Dantani, lauya mai rajin kare haƙƙin bil’adama, ya shigar da ƙara a Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, yana zargin Gwamnan Jihar Gombe da Kwamishinan ’Yan Sanda na jihar da tauye ’yancin zirga-zirgar jama’a da cin zarafi.

A cewarsa, matakin na gwamnatin jihar na hana motsi da sanya matsin lamba kan mutane ya saba da kundin tsarin mulki. Ya ce:
"Duk wanda yake take haƙƙin dan Adam, ba za mu bar shi ba har sai inda ƙarfinmu ya kare!"

Barrister Dantani ya bayyana Gwamnan a matsayin mai taurin kai, yana mai jaddada cewa lokaci ya yi da za a kare ’yancin jama’a ta hanyar shari’a. Ana sa ran kotun za ta fara sauraren ƙarar nan bada jimawa ba.

Gwamna Fubara da mabiyansa sun ƙauracewa zaɓen ƙananan hukumomi na jihar Rivers Dakataccen gwamnan jihar Rivers, Siminal...
31/08/2025

Gwamna Fubara da mabiyansa sun ƙauracewa zaɓen ƙananan hukumomi na jihar Rivers

Dakataccen gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara ya ƙauracewa zaɓen ƙananan hukumomi da aka gudanar a juya Asabar a jihar.

Jaridar VANGUARD ta gano cewa na-jikin gwamnan kamar su Edison Ehie, shugaban ma'aikatan fadar gidan gwamnati, Tammy Danagogo, sakataren gwamnatin da kuma shugabannin kananan hukumomi 23 da aka sauke da sauran magoya bayan Fubara duk ba a gan su a wajen zaɓen ba.

VANGUARD ta biyo cewa tun lokacin fara zabe har zuwa lokacin kammala shi babu wanda ya je rumfar zaben daga cikin yan tawogar Fubara din.

Jaridar ta biyo cewa Fubara ya na London kuma tun gabanin zaben bai dawo Nijeriya ba ballantana yanke gidan sa na Opoho ba ballantana ma ya je rumfar zaben.

Sai dai har yanzu VANGUARD ta ce ba ta samu bayani kan dalilan da ya hana Fubara da mukarraban sa zuwa zaben ba.

Ba a yi wa Musulman Nijeriya adalci ba da Juma'a ta kasance ranar aiki a mako - Reno Omokri Tsohon mai ba wa shugaban ƙa...
30/08/2025

Ba a yi wa Musulman Nijeriya adalci ba da Juma'a ta kasance ranar aiki a mako - Reno Omokri

Tsohon mai ba wa shugaban ƙasa shawara, Reno Omokri, ya bukaci a yi gyara tsarin ranakun aiki a Najeriya domin bai wa Musulmai damar gudanar da sallar Juma’a ba tare da cikas ba, yana mai bayyana tsarin da ake amfani da shi yanzu a matsayin rashin adalci.

Jaridar PUNCH ta rawaito cewa a wani bidiyo da ya wallafa a shafinsa na Facebook a jiya Juma’a, Omokri ya bayyana cewa kafin zuwan mulkin mallaka, Juma’a ta kasance ranar hutu a mako ga Musulmi.

Ya ce bai dace ba a bar Lahadi a matsayin ranar hutu ga Kiristoci yayin da ake tilasta wa Musulmai yin aiki a ranar Juma’a duk da muhimmancin ranar ga addininsu.

“Ina ganin ba a yi wa al’ummar Musulmi adalci ba mu kasance da Juma’a a matsayin ranar aiki a Najeriya. A asali, kafin mulkin mallaka, ba haka abin yake ba,” in ji Omokri.

Ya bayar da shawarar a daidaita lokutan aiki a Najeriya ta yadda ofisoshi za su rufe da wuri a ranar Juma’a.

A cewarsa, ana iya fara aiki da wuri daga Litinin zuwa Alhamis, sannan a kammala aikin ranar Juma’a tun kafin rana tsaka.

Dan Allah Nawa Ake Saida irin wannan Keken Mai Kwando a Gaba a, Kasuwa ?Masana Lafiya Sunce Tukin Keke Yafi Kara Lafiya ...
30/08/2025

Dan Allah Nawa Ake Saida irin wannan Keken Mai Kwando a Gaba a, Kasuwa ?

Masana Lafiya Sunce Tukin Keke Yafi Kara Lafiya Akan Mota Ko Babur 🏃🏽‍➡️🏋🏻‍♀️

Ma'aikatar Muhalli ta Kano ta fara biyan bashin albashin ma’aikatan wucin-gadi 512 Ma’aikatar Muhalli da Sauyin Yanayi t...
29/08/2025

Ma'aikatar Muhalli ta Kano ta fara biyan bashin albashin ma’aikatan wucin-gadi 512

Ma’aikatar Muhalli da Sauyin Yanayi ta Jihar Kano ta fara biyan bashin alawus-alawus na ma’aikatan wucin-gadi su 512.

Kwamishinan Muhalli da Sauyin Yanayi, Dakta Dahir M. Hashim ne ya jagoranci kaddamar da biyan kuɗin tare da Daraktan Hukumar REMASAB.

A wata sanarwa da ya sanyawa hannu a Kano yau Juma’a, Dakta Hashim ya bayyana cewa daga cikin ma’aikatan 512 na wucin-gadi, 412 ma'aikatan duba-gari ne.

Dakta Hashim ya ce wannan shi ne kashi na ƙarshe na biyan albashi da ma'aikatan fanni daban-daban na ma'aikatar ke bin ma’aikatar.

“Da muka zo mun tarar da tarin bashin albashi da aka kasa biya yawancin ma’aikatan wucin gadi.

"A watan farko mun biya ragowar hakkokin ma’aikatan shara su 2,869. Ba da jimawa ba muka biya hakkokin masu tsaron jeji su 229.

“Yau kuma, da cikakken goyon bayan Mai Girma Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, mun fara biyan bashin alawus na ma’aikatan wucin-gadi 512, cikin har da duba-gari su 412,” in ji kwamishinan.

Ya bayyana cewa daga yanzu , ma’aikatar za ta mayar da hankali wajen sake horaswa, gina ƙwarewa, da kuma ƙarfafa ƙwararru a cikin ma’aikata.

“Haka kuma za mu gano guraben ƙwarewa da ake bukata, mu ɗauki sabbin ƙwararru inda ya zama dole, sannan mu fara mai da waɗanda s**a cancanta daga wucin gadi zuwa na dindindin. Ba za mu cimma burinmu ba sai da mutanen da s**a dace da aikin,” inji shi.

Takara ta da Makinde za ta yi armashi idan PDP ta amince a zaben 2027 - Bala Muhammad_DCL Hausa
29/08/2025

Takara ta da Makinde za ta yi armashi idan PDP ta amince a zaben 2027 - Bala Muhammad

_DCL Hausa

29/08/2025

Muna nazarin fayil ɗin ɗaya dijin…
Jaafar Jaafar

Annabi Muhammad s a w
29/08/2025

Annabi Muhammad s a w

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when kanawa Post news posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share