Kano Observer Hausa

Kano Observer Hausa Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Kano Observer Hausa, Media/News Company, Kano.

KANO UPDATE: Jamiyyar APC ta kasa ta goyi bayan Abdullahi Abbas a matsayin shugaban jam'iyyar na jihar Kano.Daraktan yad...
17/10/2021

KANO UPDATE: Jamiyyar APC ta kasa ta goyi bayan Abdullahi Abbas a matsayin shugaban jam'iyyar na jihar Kano.

Daraktan yada labaran jam'iyyar APC na kasa, Alhaji Salisu Na'inna Danbatta ne ya bayyana hakan ga Freedom Radio Kano.

Danbatta ya ce, tsarin jamiyyar shi ne duk inda ta ke da Gwamna to shi ne jagoran jam'iyya.

Saboda haka duk inda aka yi zabe sabanin wannan to ba halastacce bane, kuma ya saba da tsarin jam'iyyar APC.

Ya kara da cewa "Gwamna ko mai babban mukami idan bamu da Gwamna a jiha shi ne gaba a jam'iyya, a duba a gani wane zabe ne aka yi shi a inda hukumar zabe ta turo wakilai?".

"Wane zabe ne jami'an tsaro s**a je s**a tabbatar da tsaro a wajen? Wannan shi ne sahihin zaben da muka sani a jihar Kano."

Wannan na zuwa ne kwana guda bayan zaben shugabannin jam'iyyar APC na jihohi wanda ya bar baya da kura a wasu jihohin Najeriya.

An samu rabuwar kai a jihohin Neja, Kwara, Legas da kuma jihar Ogun da sauran su.

A nan Kano ma tsagin Gwamna Ganduje ya gudanar da zabensa tare da ayyana Alhaji Abdullahi Abbas a matsayin wanda ya yi nasarar zama shugaban jam'iyyar ta APC.

A daya bangaren shi ma tsohon Gwamnan Kano Malam Ibrahim Shekarau ya jagoranci nasa wanda ya ayyana Alhaji Ahmadu Haruna Danzago a matsayin sabon shugaban jamiyyar.

MUHAWARA : Ra'ayin Al'ummar Jahar Kano Ya rabu kashi Biyu. Inda Tsagin Gwamna Ganduje su zabi {Abdullahi Abbas} a Bangar...
17/10/2021

MUHAWARA : Ra'ayin Al'ummar Jahar Kano Ya rabu kashi Biyu. Inda Tsagin Gwamna Ganduje su zabi {Abdullahi Abbas} a Bangare guda kuma tawagar Al'ummar Kano bangaren Shekarau su Zabi ( Ɗanzago ) Shin cikinsu waye Zabinku ?

LABARI:- Mataimakin shugaban ƙasa, Furofesa Yemi Osibanjo SAN ya yi wa Sarauniyar Baton maraba ga wasan ƙasashe renon In...
17/10/2021

LABARI:- Mataimakin shugaban ƙasa, Furofesa Yemi Osibanjo SAN ya yi wa Sarauniyar Baton maraba ga wasan ƙasashe renon Ingila na 2022 da za a yi a Birmingham, a madadin shugaban ƙasa Buhari, jiya 16 ga Oktoba, 2021 a fadar shugaban ƙasa. Hoto: Tolani Alli.

DA ƊUMI-DUMI'Uwar Jam'iyyar APC ta Kasa ta barranta kanta daga Zaɓen da Ɓangaren Sanata Shekarau s**ayi a jiya.Hakan ya ...
17/10/2021

DA ƊUMI-DUMI

'Uwar Jam'iyyar APC ta Kasa ta barranta kanta daga Zaɓen da Ɓangaren Sanata Shekarau s**ayi a jiya.

Hakan ya biyo bayan jita-jitan da yake yawo a kafafen sadarwa ta zamani kan cewa jam'iyyar ta turo da wakili daga sakatariyar jam'iyar ta kasa domin kula da zaɓe da ɓangaren Shekarau suke ikirarin sunyi a wani kango.

~ Munkaila Isma'il

YANZU YANZUN NAN NAIRA MILIYAN BIYU.Daya daga cikin yan majalisar tarayyar Nigeria mai suna Hon. Abubakar kabir Bichi Da...
27/09/2021

YANZU YANZUN NAN NAIRA MILIYAN BIYU.

Daya daga cikin yan majalisar tarayyar Nigeria mai suna Hon. Abubakar kabir Bichi Dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar bichi a zauren majalisar tarayyar nigeria ya biyawa dalibai 85 kudin makaranta (Registration fees) akan kudin N 2, 000, 000:00. wanda suke karatu a jami'ar yusuf maitama university (Northwest) ta jihar Kano.

NFF zata karrama tsoffin 'yan wasan Super Falcons na1999A wannan Litinin 20 ga watan Satumba Hukumar Kwallon kafar Najer...
20/09/2021

NFF zata karrama tsoffin 'yan wasan Super Falcons na1999

A wannan Litinin 20 ga watan Satumba Hukumar Kwallon kafar Najeriya NFF zata karrama tsoffin tawagar ‘yan matan Super Falcons ajin shekarar 1999 wadanda s**a kai wasan daf da na kusa da na karshe na gasar cin kofin duniya na mata a Amurka.

Tawagar wanda kaftin Florence Omagbemi ke jagoranta, ta doke Koriya ta Arewa da ci 2-1 a filin Rose Bowl na Pasadena, Mercy Akide da Rita Nwadike, s**a zuru kwallayen a wancan lokaci, kafin ta sha kashi a hannun Amurka da ci 7-1.

A yayin wannan kasaitacen buki a Hotel Eko dake birnin Lagos za’a karrama mambobi tawagar mata ta shekarar 1999 su goma sha biyar da kuma koci Ismaila Mabo, inda Takwas daga cikinsu s**a taso daga kasar Amurka, sai dai abin takaici, daya daga cikin ‘yan wasan tsakiya na tawagar dake yawan kai hari, Ifeanyi Chiejine ta mutu a bara.

A bukin karrama ‘yan wasan Najeriya karo na farko da ya gudana a shekarar 2018 an samu bakwancin Shugaban FIFA Gianni Infantino sannan Shugaban CAF a lokacin Ahmad Ahmad.

YANZU-YANZU: Angarzaya Da Sheikh Dr, Abubakar Giro Argungu Asibiti Domin Duba Lafiyarsa.Muna neman addu'arku yan'uwa mus...
19/09/2021

YANZU-YANZU: Angarzaya Da Sheikh Dr, Abubakar Giro Argungu Asibiti Domin Duba Lafiyarsa.

Muna neman addu'arku yan'uwa musulmai daga bakunanku masu daraja, kusa Sheikh Dr Abubakar Giro Argungu cikin addu'oinku.

Muna rokon Allah yaba malan lafiya, alfarmar fiyayyen halitta ANNABI MUHAMMAD S.A.W

DAGA: Comrade Musa Garba Augie.

BABBAR MAGANA IGIYAR RUWA TA B***E...Barrister Inuwa Waya yayi Murabus daga kamfanin albarkatun Mai na kasa NNPC, a ciki...
19/09/2021

BABBAR MAGANA IGIYAR RUWA TA B***E...

Barrister Inuwa Waya yayi Murabus daga kamfanin albarkatun Mai na kasa NNPC, a cikin yunkurin dayake na shiga Takarar Gwamnan Jihar Kano a Jamiyyar APC a zaben 2023.

Inuwa waya dai ya kwana 2 ana Jin motsinsa na Tsayawa Takarar amma hakan be zamo tabbas se yanzu daya ajiye mukaminsa na NNPC.

Kubiyomu don jin yadda zata karke.

Observer Hausa.

Daga wace Karamar Hukumar kuke Kallonmu a Jihar Kano?
19/09/2021

Daga wace Karamar Hukumar kuke Kallonmu a Jihar Kano?

Cututtukan da Malamai ke fesawa jama'ar Kano sun fi HIV illa. -Baba Impossible.Kwamishinan harkokin addinai na jihar Kan...
18/09/2021

Cututtukan da Malamai ke fesawa jama'ar Kano sun fi HIV illa. -Baba Impossible.

Kwamishinan harkokin addinai na jihar Kano Dr Tahar Baba Impossible ya ce za a yi doka ta musamman da zata dinga duba ƙwaƙwalwar malamai kafin su fara gabatar da wa'azi.

Kwamishina ya bayyana haka ne ga sashen BBC Hausa cewa, zasu rubuta ƙuduri na musamman zuwa ga majalisar dokokin jihar kano ta bada damar duba ƙwaƙwalwar malamai kafin fara wa'azi a jihar Kano.

Baba Impossible ya Kara da cewa: Cututtukan da Malamai ke fesawa jama'ar Kano sun fi HIV illa".

Idan ba a manta ba, a makon da ya gabata ne majalisar malamai ta Kano ta mayar da martani kan cewa za a duba ƙwaƙwalwar malamai, inda s**a ce saidai a duba ƙwaƙwalwar yan siyasa.

Zuwa yanzu an cigaba da taƙaddama akan wannan ƙuduri na gwamnatin jihar Kano.

Ministan harkokin Sadarwa Sheikh Isa Pantami ya shiryawa sabon dan jam’iyyar APC Chief Femi Fani-Kayode liyafar cin abin...
18/09/2021

Ministan harkokin Sadarwa Sheikh Isa Pantami ya shiryawa sabon dan jam’iyyar APC Chief Femi Fani-Kayode liyafar cin abinci a gidansa.

A cewar Mista Fani-Kayode, ministan ya gayyace shi, shi da Gwamnan Zamfara Bello Matawalle.

“Ni da abokina kuma dan uwana Gwamna Bello Matawalle, mun ji dadin karamci and girmamawa da gayyatar liyafar cin abinci da abokina kuma dan uwana ministan Sadarwa Farfesa Isa Pantami ya gayyace mu a daren jiya, a gidansa na alfarma,” a cewar Mista Fani-Kayode a shafinsa na Facebook.

Ya ce sai da su ka raba dare su na hira kan al’amuran kasa da na waje.

YANZU YANZU... Dantakarar Shugabancin Jamiyyar APC a Jihar Kano Alh. Ahmadu Haruna Zago kenan yayin dayakai ziyara ga Ma...
18/09/2021

YANZU YANZU...

Dantakarar Shugabancin Jamiyyar APC a Jihar Kano Alh. Ahmadu Haruna Zago kenan yayin dayakai ziyara ga Mai Martaba Sarkin Rano, Alh. Kabiru Muhammad Inuwa a Fadarsa.

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kano Observer Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Kano Observer Hausa:

Share