17/01/2026
Rahoton da jaridar Politics Digest ta fitar ya nuna cewa, duk da doguwar tattaunawa da aka yi, shugabannin jam’iyyar APC a matakin Jihar Kano da na ƙasa baki ɗaya sun ƙi amincewa da buƙatar Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, na samun tikitin takarar gwamna kai-tsaye (automatic ticket) a zaɓen shekarar 2027.
Rahoton ya bayyana cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf ya gabatar da wasu sharuɗɗa kafin yanke shawarar sauya sheƙa zuwa APC, inda s**a haɗa da tabbacin tikitin takarar gwamna a 2027, damar zaɓar ministan da zai wakilci Jihar Kano a Majalisar Zartarwa ta Tarayya, da kuma ikon sauya wasu muƙamai a jihar da mutane masu biyayya gare shi.
Sai dai rahoton ya ce shugabannin APC sun nuna rashin amincewa da waɗannan sharuɗɗa, lamarin da ke ƙara jefa makomar tattaunawar cikin shakku, yayin da ake ci gaba da sa ido kan matakin da gwamnan zai ɗauka nan gaba.