Duk Kanwar Ja Ce

Duk Kanwar Ja Ce It's all about enlightenment, politics and pleasure, fun and entertainment.

26/07/2025

Ministan Ayyuka na Tarayya, Sanata Dave Umahi, ya bayyana cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu Yana da cikakken kuduri na ci gaba da gina dukkan sassan Najeriya ba tare da nuna bambanci ba, Yana mai jaddada cewa an kuduri aniyar tafiya da gaskiya da adalci wajen rabon ayyukan cigaba a fadin ƙasa.

Sanata Umahi ya bayyana hakan ne a martani ga kalaman tsohon Gwamnan Kano kuma dan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP a zaɓen 2023, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, wanda ya zargi gwamnatin Tinubu da fifita yankin Kudu fiye da Arewacin ƙasar.

“Shugaba Tinubu ya jajirce wajen ganin kowanne yanki ya ci gajiyar dimokuradiyya. Gwamnatinsa na aiki da kowane yanki bisa gaskiya da daidaito, ba tare da nuna bambancin siyasa, yare ko addini ba,” in ji Minista Umahi.

Ya ce ma’aikatarsa tana aiwatar da manyan ayyuka na tituna a sassa daban-daban na Arewa da Kudu, ciki har da sabunta manyan hanyoyi da ke haɗa jihohin Arewa maso Yamma da Arewa ta Tsakiya da sauran sassan ƙasar.

Ministan ya kara da cewa zargin nuna wariya a rabon ayyuka na iya haifar da rashin fahimta da rashin hadin kai, yana mai kira ga shugabannin siyasa da su rika duba abubuwa ta fuskar ƙasa baki ɗaya, ba yankin kansu kadai ba.

Aliko Dangote, ya sauka Daga mukaminsa na Shugaban Hukumar Gudanarwar Kamfanin Dangote Cement Plc.A Ranar Juma’a, Anthon...
26/07/2025

Aliko Dangote, ya sauka Daga mukaminsa na Shugaban Hukumar Gudanarwar Kamfanin Dangote Cement Plc.

A Ranar Juma’a, Anthony Chiejina, mai magana da yawun kamfanin, ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa ritayar ta fara aiki ne daga ranar 25 ga Yuli, 2025.

Daga bisani Hukumar Kamfanin ta bayyana cewa, Emmanuel Ikazoboh, wanda ke aiki a matsayin darekta mara zartarwa mai zaman kansa, an nada shi a matsayin sabon shugaban hukumar Gudanarwar.

Gwamnatin Jihar Anambra, ta rufe wani asibiti da ake ajiye mata suna haihuwa ana sayar da jiriran a jihar.Hukumomi, sun ...
26/07/2025

Gwamnatin Jihar Anambra, ta rufe wani asibiti da ake ajiye mata suna haihuwa ana sayar da jiriran a jihar.

Hukumomi, sun bayyana cewa sun bankaɗo asibitin ne, bayan rahoton sirri da s**a samu na cewa a asibitin ana amfani da mata wajen haihuwar jarirai ana sayarwa.

A yayin da s**a kai sumame asibitin mai suna "Mother and Child Hospital and Maternity," da ke Umunya a Ƙaramar Hukumar Oyi, ma'aikatan sun k**a wasu daga cikin ma'aikatan da wasu mata masu ciki guda biyar, da kuma ƙarin wasu matasa 10.

Gwamnatin Tarayya da Majalisar Ɗinkin Duniya na shirin kashe dala miliyan 159 don magance yunwa a jihohin Borno, Adamawa...
07/05/2025

Gwamnatin Tarayya da Majalisar Ɗinkin Duniya na shirin kashe dala miliyan 159 don magance yunwa a jihohin Borno, Adamawa da Yobe.

Gwamnatin Najeriya, tare da Majalisar Dinkin Duniya, ta ɓullo da wani shirin mayar da martani mai fuska daban-daban na dalar Amurka miliyan 159, don magance matsalar abinci mai gina jiki da ke kara tabarbarewa a yankunan arewa maso gabashin Najeriya, Borno, Adamawa, da Yobe.

An bayyana hakan ne a yayin kaddamar da wani shiri na bangarori da dama na magance kalubalen samar da abinci da abinci mai gina jiki a kakar bana ta 2025 a jihohin Borno, Adamawa da Yobe, wanda ya gudana a Abuja.

Farfesa Nentawe Yilwatda, Ministan Harkokin Agaji da Rage Talauci, ya bayyana cewa, “Tsarin yana neman dala miliyan 159 don samar da abinci na gaggawa, abinci, da harkokin kiwon lafiya da sauran taimakon ceton rai ga mutane miliyan 2 da ke cikin mawuyacin hali a jihohin BAY nan da watanni shida masu zuwa.

“Wannan Tsari ba wai tsari da dabaru ba ne kawai, a’a, alkawari ne cewa babu wani yaro a Borno, Adamawa, ko Yobe da ya k**ata ya kwana da yunwa a lokacin da duniya ke da isasshen abinci, kada wata uwa ta rasa ’ya ta yanayin da muka san yadda za mu bi da ita, kuma mutuncin ba zai taba zama sanadin rikici ko talauci ba.

Duk Kanwar Ja Ce

Sanata Kawu Sumaila (Kano ta Kudu) ya sauya sheka daga jam’iyyar NNPP zuwa APC a hukumance a zaman majalisar na yau. Shu...
07/05/2025

Sanata Kawu Sumaila (Kano ta Kudu) ya sauya sheka daga jam’iyyar NNPP zuwa APC a hukumance a zaman majalisar na yau. Shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio ne ya karanta wasikar sauya shekar tasa.

Duk Kanwar Ja Ce

Shugabancin Dattawan Karamar Hukumar Kumbotso  na Jam'iyyar NNPP sun dakatar da Jagoran jam'iyyar a Ƙaramar Hukumar Dany...
05/03/2025

Shugabancin Dattawan Karamar Hukumar Kumbotso na Jam'iyyar NNPP sun dakatar da Jagoran jam'iyyar a Ƙaramar Hukumar Danyaro Yakasai tare da maye gurbinsa da Hon. Abdullahi Dauda (A.A karansi).

Anyi wanan dakatarwa ne karkashin shugaban Dattawan jam'iyyar na Kumbotso Hon. Alh. Idi Mariri da kuma masu ruwa da tsaki na yankin a cikin wata takarda da sakataren kwamitin Dattawan Dr Nazifi Umar ya sanya wa hannu.

Haka kuma jam'iyyar NNPP ta kori Hon. Ali Musa Danmaliki da shugaban jam'iyyar na Mazabar Ɗanmaliki Malam Dan Ali da sakatarensa, biyo bayan sak**akon binciken kwamitin da aka kafa musu a baya.

Da yake bayyana korar mai rikon shugabancin jam'iyyar NNPP na Karamar Hukumar ta Kumbotso ya gargaɗi duk masu ƙokarin kawo musu rigingimu a Jam'iyyar.

"An samu goyon bayan 'yan majalisa da gwamnan Kaduna."Mazauna Kudancin Kaduna na ci gaba da fafutukar ganin majalisa ta ...
05/03/2025

"An samu goyon bayan 'yan majalisa da gwamnan Kaduna."

Mazauna Kudancin Kaduna na ci gaba da fafutukar ganin majalisa ta kirkiri jihar Gurara.

Kungiyar SOKAPU ta ce Gurara tana da kananan hukumomi 12, kuma tafi wasu jihohi girma.

Hukuncin kotu a kan zaben kananan hukumomin Ribas ya jawo zaman ɗar-ɗar a Kano.Kotun Koli ta soke zaben kananan hukumomi...
05/03/2025

Hukuncin kotu a kan zaben kananan hukumomin Ribas ya jawo zaman ɗar-ɗar a Kano.

Kotun Koli ta soke zaben kananan hukumomin Ribas.

Irin wannan shari'a a kan zaben jihar Kano na gaban babbar kotun tarayya.

"Manyan jiga-jigan ‘yan siyasar Kano da Kaduna da wasu da dama daga arewacin kasar nan na shirin komawa jam'iyyar SDP do...
17/02/2025

"Manyan jiga-jigan ‘yan siyasar Kano da Kaduna da wasu da dama daga arewacin kasar nan na shirin komawa jam'iyyar SDP domin kada shugaban kasa Tinubu a zaben 2027

Sauran jam’iyyun siyasar kasar na fama rikicin cikin gida hakan tasa s**a yanke shawarar shiga jam'iyyar SDP, kuma a yanzu ba wata jam'iyyar da zata iya kada APC inba jam'iyyar SDP ba a cewar shugaban jam'iyyar SDP Shattima

Yace Jam'iyyar PDP na fama da rigimar Shugabanci da rashin hadin kai, itama NNPP mai mulkin kano ta fada rikicin cikin gida wanda ya kai ga raba jam'iyyar biyu Mai Kayan Marmari da Mai Littafi, don haka wadannan manyan yan siyasa tuni tattaunawa tayi nisa domin shiga jam'iyyar SDP

~Hon. Aliyu Shatgima
Shugaban jam'iyyar SDP na Jihar Kano

Kotu a Kano ta soma sauraron shari’ar zargin Abdullahi Abbas da Fa'izu Alfindiki da yiwa Abba Gida-gida ɓantanci.
17/02/2025

Kotu a Kano ta soma sauraron shari’ar zargin Abdullahi Abbas da Fa'izu Alfindiki da yiwa Abba Gida-gida ɓantanci.

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Duk Kanwar Ja Ce posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category