
07/05/2025
Gwamnatin Tarayya da Majalisar Ɗinkin Duniya na shirin kashe dala miliyan 159 don magance yunwa a jihohin Borno, Adamawa da Yobe.
Gwamnatin Najeriya, tare da Majalisar Dinkin Duniya, ta ɓullo da wani shirin mayar da martani mai fuska daban-daban na dalar Amurka miliyan 159, don magance matsalar abinci mai gina jiki da ke kara tabarbarewa a yankunan arewa maso gabashin Najeriya, Borno, Adamawa, da Yobe.
An bayyana hakan ne a yayin kaddamar da wani shiri na bangarori da dama na magance kalubalen samar da abinci da abinci mai gina jiki a kakar bana ta 2025 a jihohin Borno, Adamawa da Yobe, wanda ya gudana a Abuja.
Farfesa Nentawe Yilwatda, Ministan Harkokin Agaji da Rage Talauci, ya bayyana cewa, “Tsarin yana neman dala miliyan 159 don samar da abinci na gaggawa, abinci, da harkokin kiwon lafiya da sauran taimakon ceton rai ga mutane miliyan 2 da ke cikin mawuyacin hali a jihohin BAY nan da watanni shida masu zuwa.
“Wannan Tsari ba wai tsari da dabaru ba ne kawai, a’a, alkawari ne cewa babu wani yaro a Borno, Adamawa, ko Yobe da ya kamata ya kwana da yunwa a lokacin da duniya ke da isasshen abinci, kada wata uwa ta rasa ’ya ta yanayin da muka san yadda za mu bi da ita, kuma mutuncin ba zai taba zama sanadin rikici ko talauci ba.
Duk Kanwar Ja Ce