Duk Kanwar Ja Ce

Duk Kanwar Ja Ce It's all about enlightenment, politics and pleasure, fun and entertainment.

‘Yan takarar sanata Kano ta tsakiya a jam’iyyar APC sun janyewa Mallam Ibrahim Shekarau bayan gwamna Abba Kabir Yusuf ya...
10/05/2026

‘Yan takarar sanata Kano ta tsakiya a jam’iyyar APC sun janyewa Mallam Ibrahim Shekarau bayan gwamna Abba Kabir Yusuf ya jagoranci zaman sulhu.

‘Yan takarar sun hada da Usman Bala, Sha’aban Sharada, Danyaro Yakasai, Abbas Sani Abbas, Abdulfatah Zango da kuma Shehu Isah Direba.

20/01/2026

DA DUMI-DUMI: Kwankwaso zai gana da Tinubu

Tsohon Gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso zai gana da shugaban ƙasa Tinubu a yammacin yau Talata.

A jiya ne kuma, shugaba Tinubu ya gana da gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf a yayin da jita-jita ta yi karfi kan cewa gwamnan zai koma jam'iyyar APC.

Jaridar Politics Digest ta rawaito cewa, Gwamnan na Kano ne ya hada ganawar tsakanin Tinubu da Kwankwaso.

Karin bayani na nan tafe.....

Rahoton da jaridar Politics Digest ta fitar ya nuna cewa, duk da doguwar tattaunawa da aka yi, shugabannin jam’iyyar APC...
17/01/2026

Rahoton da jaridar Politics Digest ta fitar ya nuna cewa, duk da doguwar tattaunawa da aka yi, shugabannin jam’iyyar APC a matakin Jihar Kano da na ƙasa baki ɗaya sun ƙi amincewa da buƙatar Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, na samun tikitin takarar gwamna kai-tsaye (automatic ticket) a zaɓen shekarar 2027.

Rahoton ya bayyana cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf ya gabatar da wasu sharuɗɗa kafin yanke shawarar sauya sheƙa zuwa APC, inda s**a haɗa da tabbacin tikitin takarar gwamna a 2027, damar zaɓar ministan da zai wakilci Jihar Kano a Majalisar Zartarwa ta Tarayya, da kuma ikon sauya wasu muƙamai a jihar da mutane masu biyayya gare shi.

Sai dai rahoton ya ce shugabannin APC sun nuna rashin amincewa da waɗannan sharuɗɗa, lamarin da ke ƙara jefa makomar tattaunawar cikin shakku, yayin da ake ci gaba da sa ido kan matakin da gwamnan zai ɗauka nan gaba.

22/11/2025

Gwamnatin Najeriya ta tura babban ministan tsaron ƙasar, Muhammad Badaru Abubakar, zuwa jihar Neja inda aka sace ɗalibai 'fiye da 200'.

Ƙaramin ministan tsaron ƙasar, Muhammed Bello Matawalle ne ya bayyana haka ranar Juma'a da maraice a cikin shirin Ra'ayi Riga na BBC Hausa.

''Shi ma Badaru zai je Neja k**ar yadda aka turoni Kebbi, domin ƙoƙarin gwamnati na kuɓutar da ɗaliban da aka sace'', in ji shi

Tuni dai Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya tura ƙaramin ministan tsaron zuwa jihar Kebbi - inda ƴanbindiga s**a sace ɗalibai ƴanmata 25 - domin sanya idanu kan ƙoƙarin kuɓutar da ɗaliban.

26/07/2025

Ministan Ayyuka na Tarayya, Sanata Dave Umahi, ya bayyana cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu Yana da cikakken kuduri na ci gaba da gina dukkan sassan Najeriya ba tare da nuna bambanci ba, Yana mai jaddada cewa an kuduri aniyar tafiya da gaskiya da adalci wajen rabon ayyukan cigaba a fadin ƙasa.

Sanata Umahi ya bayyana hakan ne a martani ga kalaman tsohon Gwamnan Kano kuma dan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP a zaɓen 2023, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, wanda ya zargi gwamnatin Tinubu da fifita yankin Kudu fiye da Arewacin ƙasar.

“Shugaba Tinubu ya jajirce wajen ganin kowanne yanki ya ci gajiyar dimokuradiyya. Gwamnatinsa na aiki da kowane yanki bisa gaskiya da daidaito, ba tare da nuna bambancin siyasa, yare ko addini ba,” in ji Minista Umahi.

Ya ce ma’aikatarsa tana aiwatar da manyan ayyuka na tituna a sassa daban-daban na Arewa da Kudu, ciki har da sabunta manyan hanyoyi da ke haɗa jihohin Arewa maso Yamma da Arewa ta Tsakiya da sauran sassan ƙasar.

Ministan ya kara da cewa zargin nuna wariya a rabon ayyuka na iya haifar da rashin fahimta da rashin hadin kai, yana mai kira ga shugabannin siyasa da su rika duba abubuwa ta fuskar ƙasa baki ɗaya, ba yankin kansu kadai ba.

Aliko Dangote, ya sauka Daga mukaminsa na Shugaban Hukumar Gudanarwar Kamfanin Dangote Cement Plc.A Ranar Juma’a, Anthon...
26/07/2025

Aliko Dangote, ya sauka Daga mukaminsa na Shugaban Hukumar Gudanarwar Kamfanin Dangote Cement Plc.

A Ranar Juma’a, Anthony Chiejina, mai magana da yawun kamfanin, ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa ritayar ta fara aiki ne daga ranar 25 ga Yuli, 2025.

Daga bisani Hukumar Kamfanin ta bayyana cewa, Emmanuel Ikazoboh, wanda ke aiki a matsayin darekta mara zartarwa mai zaman kansa, an nada shi a matsayin sabon shugaban hukumar Gudanarwar.

Gwamnatin Jihar Anambra, ta rufe wani asibiti da ake ajiye mata suna haihuwa ana sayar da jiriran a jihar.Hukumomi, sun ...
26/07/2025

Gwamnatin Jihar Anambra, ta rufe wani asibiti da ake ajiye mata suna haihuwa ana sayar da jiriran a jihar.

Hukumomi, sun bayyana cewa sun bankaɗo asibitin ne, bayan rahoton sirri da s**a samu na cewa a asibitin ana amfani da mata wajen haihuwar jarirai ana sayarwa.

A yayin da s**a kai sumame asibitin mai suna "Mother and Child Hospital and Maternity," da ke Umunya a Ƙaramar Hukumar Oyi, ma'aikatan sun k**a wasu daga cikin ma'aikatan da wasu mata masu ciki guda biyar, da kuma ƙarin wasu matasa 10.

Gwamnatin Tarayya da Majalisar Ɗinkin Duniya na shirin kashe dala miliyan 159 don magance yunwa a jihohin Borno, Adamawa...
07/05/2025

Gwamnatin Tarayya da Majalisar Ɗinkin Duniya na shirin kashe dala miliyan 159 don magance yunwa a jihohin Borno, Adamawa da Yobe.

Gwamnatin Najeriya, tare da Majalisar Dinkin Duniya, ta ɓullo da wani shirin mayar da martani mai fuska daban-daban na dalar Amurka miliyan 159, don magance matsalar abinci mai gina jiki da ke kara tabarbarewa a yankunan arewa maso gabashin Najeriya, Borno, Adamawa, da Yobe.

An bayyana hakan ne a yayin kaddamar da wani shiri na bangarori da dama na magance kalubalen samar da abinci da abinci mai gina jiki a kakar bana ta 2025 a jihohin Borno, Adamawa da Yobe, wanda ya gudana a Abuja.

Farfesa Nentawe Yilwatda, Ministan Harkokin Agaji da Rage Talauci, ya bayyana cewa, “Tsarin yana neman dala miliyan 159 don samar da abinci na gaggawa, abinci, da harkokin kiwon lafiya da sauran taimakon ceton rai ga mutane miliyan 2 da ke cikin mawuyacin hali a jihohin BAY nan da watanni shida masu zuwa.

“Wannan Tsari ba wai tsari da dabaru ba ne kawai, a’a, alkawari ne cewa babu wani yaro a Borno, Adamawa, ko Yobe da ya k**ata ya kwana da yunwa a lokacin da duniya ke da isasshen abinci, kada wata uwa ta rasa ’ya ta yanayin da muka san yadda za mu bi da ita, kuma mutuncin ba zai taba zama sanadin rikici ko talauci ba.

Duk Kanwar Ja Ce

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Duk Kanwar Ja Ce posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category