18/08/2026
Ƙungiyar Obi-Kwankwaso ta naɗa Muawiya Mairoba a matsayin Mataimakin Mai Gudanarwa na Ƙasa
Ƙungiyar Obi-Kwankwaso ta naɗa Malam Muawiya Gambo Mairoba a matsayin sabon Mataimakin Mai Gudanar da Ƙungiya na Ƙasa (Deputy National Coordinator), inda ya maye gurbin Malam Samir Hanga, wanda kwanan nan ya bar ƙungiyar bayan ya sauya sheka daga Nigeria Democratic Congress (NDC) zuwa All Progressives Congress (APC).
Mai Gudanar da Ƙungiyar na Ƙasa, Malam Chibuisi Mba, ne ya sanar da naɗin a ƙarshen mako. Ya ce matakin na daga cikin ƙoƙarin ƙarfafa haɗin kan siyasa da kuma inganta ayyukan ƙungiyar.
Mairoba, wanda ɗan Jihar Kano ne, ƙungiyar ta bayyana shi a matsayin ƙwararren mai tara magoya baya daga matakin ƙasa, kuma babban mai goyon bayan manufofin siyasar tsohon Gwamnan Jihar Anambra, Peter Obi, da tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso.
Da yake magana a ranar Lahadi, Mairoba ya tabbatar da naɗinsa. Ya bayyana cewa shugabannin ƙungiyar ne s**a yanke shawarar cike gurbin bayan tafiyar Hanga.
Ya ce shugabannin Obi-Kwankwaso New Nigeria Movement sun gabatar da sunansa ga babbar kwamitin yanke shawara na ƙungiyar a ranar Lahadi, inda aka amince da naɗinsa a matsayin Mataimakin Mai Gudanar da Ƙungiya na yankin Arewa maso Yamma (North-West).
Mairoba ya ce shugabannin sun ga ya dace a cike gurbin da ya samu saboda sauya shekar siyasa da tsohon mai riƙe da mukamin, Samir Hanga, ya yi.
Ya ce:
“Bayan sauya shekar siyasa da mutumin da ke riƙe da wannan matsayi a baya, Samir Hanga, ya yi daga NDC zuwa APC, shugabannin Obi-Kwankwaso New Nigeria Movement sun gabatar da batun ga babban kwamitin ranar Lahadi. Daga nan ne aka tabbatar da ni a matsayin Mataimakin Mai Gudanar da Ƙungiya na Arewa maso Yamma, bayan an cire tsohon mai riƙe da mukamin wanda ya bar jam’iyyar.”
Mairoba ya nuna godiyarsa ga shugabannin ƙungiyar ƙarƙashin jagorancin Chibuisi Mba, saboda amincewar da s**a yi da shi. Ya kuma yi alƙawarin amfani da ƙwarewarsa da kwarewarsa wajen tara magoya baya daga tushe domin ƙarfafa ƙungiyar a faɗin Arewa maso Yamma da Najeriya baki ɗaya.
A cikin sanarwar naɗin, ƙungiyar ta buƙaci mambobinta da shugabanninta su marabci Mairoba tare da ba shi cikakken goyon baya a sabon matsayinsa.
Shugabancin ƙungiyar ya bayyana kwarin gwiwar cewa kuzarin Mairoba, jajircewarsa da ƙwarewarsa za su taimaka wajen ƙarfafa tsarin ƙungiyar da kuma inganta harkokin tattara magoya baya a faɗin ƙasar.