Alkalami

Alkalami Ku biyo mu domin ilimi da faɗakarwa da s**a danganci addinin Musulunci, sana’o’i, fasaha, kiwon lafiya da sauran su.

PANTAMI YA BADA UMARNIN RAGE FARASHIN DATA A NIGERIA:Gwamnatin Tarayya ta nemi hukumar Sadarwa ta Kasar NCC, da ta bullo...
06/11/2019

PANTAMI YA BADA UMARNIN RAGE FARASHIN DATA A NIGERIA:

Gwamnatin Tarayya ta nemi hukumar Sadarwa ta Kasar NCC, da ta bullo da hanyoyin rage kudin sayen data domin amfanar Yan Najeriya.

Ministan Sadarwa da bunkasa tattalin arziki ta hanyar sadarwa, Ali Pantami, ya bada umarnin a yau Talata. Yace ofishin sa na samun korafi da yawa daga wadanda abun ya shafa akan yawan cajin da kamfanonin sadarwa sukeyi akan datar.

Menene ra'ayinku a kan hakan?

Labari da dumi duminsa: Hukumar Kwastam ta yi mai 'dungurungum' , ta haramta shiga da fita da kowanne irin kaya Najeriya...
14/10/2019

Labari da dumi duminsa:

Hukumar Kwastam ta yi mai 'dungurungum' , ta haramta shiga da fita da kowanne irin kaya Najeriya

Hukumar hana fasa kwauri ta kasa da aka fi kira da 'Kwastam' (NCS) ta ce ba za a kara fitar da wani kaya ko shigo wa da shi cikin Najeriya ta kan iyakokin kasa ba.

Shugaban hukumar kwastam na kasa, Hameed Ali, ne ya bayyana hakan ranar Litinin yayin wani taro da manema labarai a Abuja.

Ali ya ce a halin da ake ciki yanzu, babu wasu kaya da za a iya shigo wa da su Najeriya sai ta iyakokin cikin ruwa, inda za a bincikarsu kafin su shigo cikin kasa jama'a su fara amfani da su.

Ya ce yin hakan zai bawa jami'an tsaro damar caje duk wani kaya da za a shigo da shi cikin Najeriya.

" Mu na fatan cewa a karshen wanna aiki da muke yi, za mu samu hadin kan makwabtan kasashe a kan irin kayan da za a shigo mana da su cikin kasa.

"Amma a haln yanzu, duk wasu kaya, masu illa ko akasin haka, ba zasu shigo ko su fita daga Najeriya ba.

"Ya k**ata na kore shakku a kan wanna batu, ba za a shigo da duk wasu kaya ba, saboda duk kayan da ake shigo wa da su ta iyakokin kasa za a iya shigo wa da su ta iyakokin ruwa.

"A saboda haka, mu na shawartar duk masu shigo da kaya da su yi amfani da iyakokin cikin ruwa domin shigo da kayansu. Akwai isashen tsaro a iyakokin mu na ruwa, hakan zai bamu damar caje duk wani kaya da aka shigo da shi, " a cewarsa.

ALHAMDULILLAH! NA ALLAH BASA KAREWA A DUNIYA.Wannan hoton da kuke gani wani bawan Allah ne mai suna Sulaiman Muhammad Da...
16/09/2019

ALHAMDULILLAH! NA ALLAH BASA KAREWA A DUNIYA.

Wannan hoton da kuke gani wani bawan Allah ne mai suna Sulaiman Muhammad Dabo wanda ya taimakwa wadannan yara. Ya gansu suna tallar mazar kwaila a wani t**i a garin zariya, inda ya sauka daga motarsa yaje ya tattauna dasu. A karshe dai ya samu damar tattaunawa da mahaifinsu, inda mahaifin nasu ya sanar dashi cewa ya ciresu daga makaranta ne sak**akon rashin kudin da zai biya musu.

Yanzu haka dai wadannan yara zasu fara karatu a wannan sabuwar Makaranta da aka bude, sune zasu zama daga cikin dalibanta na farko.

YANDA WANNAN BAWAN ALLAH YA TAIMAKI RAYUWAR WADANNAN YARA ALLAH YA TAIIMAKA MASA SHIMA.

YADDA MUKAYI DA WATA KARUWA!(ALLAH SARKI RAYUWA!)Wata Rana na sauka a wani Hotel, dake daya daga cikin jihohin da nake z...
15/09/2019

YADDA MUKAYI DA WATA KARUWA!

(ALLAH SARKI RAYUWA!)

Wata Rana na sauka a wani Hotel, dake daya daga cikin jihohin da nake zuwa, tarukan kungiya, da yammaci na sauka bayan na gama kintsawa acikin Dakina Sai na fito na zauna a harabar Hotel Din saboda wannan yana daya daga cikin Al,adata saboda Ina qaruwa da abubuwan mamaki ko Al,ajabi ko kuma nishadi, kowa yana yadda yaga dama saboda duk mai sauka a Hotel ya san da irin wannan tsarin.

Ina zaune can sai idanu na ya kai kan wata kyakkyawar matashiyar budurwa, mazajen bariki kowa Yana gabatar da kansa, gaskiya yarinyar nan tana da matukar kyau, aqallah na kwana a Hotel yafi sau dari biyu, tun da nake ban taba jin wata karuwa ta burgeni ba sai wannan kyakkyawar budurwa, gata fara gata doguwa, matashiyar budurwa, amman gata acikin tsakiyar karuwanci.

Na fi minti Goma ina son su tafi amman samarin sunqi tafiya.
Can k**ar misalin Sha biyu na fito Sai na hangeta zata fita, ban san lokacin da nace da ita, "kanwata har zaki fita?

Ga mamaki na Sai naga tayi murmushi tace yayana, ai bana kwana anan kullum"

Nace saboda me? tace saboda idan ban samu wanda ya biya kudin dakin da zamu kwana ba fita nake wani wurin ko za,a dace!!

Kawai Sai tausayin ta ya k**ani, nace mata muje in biya miki daki ki kwana Amman fa ke kadai, tace haba yaya na sai dai mu kwana tare, babu yadda banyi ba amman tace sai dai mu kwana tare, bansan san da nace mata na amince ba.

Muka je na biya kudin dakin kwana daya nata, na dawo dakinta, muna ta hira har karfe, biyu na dare, akallah munfi awanni muna hira, can wajen karfe biyu da rabi Sai na dafe cikina Ina nishin karya, nace mata, ciwona ne ya motsa, haka ta rakoni har dakina tare da tausaya min.

Ai kuwa ana kiran Sallar asubahi sai gata a dakina, anan tayi Sallar asubahi, Wallahi idan kaji nutsuwarta idan tana karatun Alkur, Ani sai ka tausaya wa rayuwarta.

Tare muka karya, sai kace wacce muka jima da haɗuwa, tausayin ta ya k**ani kwarai, na ce mata yanzu idan bata samu wanda zasu kwana ba yaya take yi?

Sai tace mun akwai wasu gayu da take zuwa unguwarsu kyauta suke kwana.

Na tausaya Mata kwarai da gaske, na tambayeta sunanta da garinsu, Bata ɓoye min komai ba.

Na gaya mata waye ni da kuma suna na, Sai dai gaskiya ban gaya mata sunan jihata da kuma sunana na asali ba saboda wasu dalilai...

Ta zayyana mun labarinta, ta gaya mun dalilin ta na zuwa wannan jiha da kuma sanadin shigarta karuwanci!

Tsautsayi da kaddara ce ta shigar dani karuwanci, sanadiyyar wata qawata, inada haddar Alqur'ani akai na, saboda na samu gatan iyayena.

Lokacin da zamu rubuta jarrabawar qualifying, ban ci ba, Ina zaton danne min akayi saboda inada kokarina daidai gwagwardo, mahaifina ya rasu da jimawa, mahaifiya ta bata da karfin da zata biya mun kudin jarrabawar, babban abin takaicin shine dukkan kawayena sun samu nasara, na rasa inda zan saka kaina.

Babu inda ban nemi mafuta ba amman na rasa samun mai biya mun, dukkan masu kuɗin unguwarmu babu wanda ban bi ba akan su taimaka min amman sai s**a gaza biya mun.

Akwai wata qawata ita ce ta hadani da wani saurayi, take ya biya mun kudin, gami da yi mun alheri iri iri.

Abin ka da kaddara, sai yayi Alkawarin aure na, amman da sharadin sai na saki jiki dashi, haka ko aka yi bansan kaddarar da tasa har yayi mun ciki ba, sannu sannu sai ga ciki ya bayyana, har aka fara surutai.

Aka tambaye ni wanda yayi mun na nuna shi, take ya amince da cewar cikinsa ne, yayi Alkawarin Aurena, iyayensa s**a ce atafau basu yarda ba, s**a ce sharri zan yi masa, ina ji Ina gani maganar Aure ta lalace, saboda bamu da gata, sannu sannu mutanen unguwa s**a tsane ni, s**a uzzurawa rayuwa ta.

Bayan watanni biyu shi wanda yayi mun cikin Allah yayi masa rasuwa, ni kuma bayan watanni hudu Sai na haifi yaro namiji amman bai zo da rai ba ya rasu!.

Bayan na haihu na nemi gafarar iyayena da dukkan Wanda na batawa, amman Wallahi duk da haka mutanen unguwarmu s**a tsangwameni, sau biyu ana samun ranar aure ana fasawa, saboda ko na samu mijin Aure, Sai mutanen unguwarmu suje suyi tsurku su rusa auren s**e wai na taɓa yin cikin shege!

Haka na rayu cikin kaskanci da wulakancin mutanen unguwar mu kuma da ace an taimaki rayuwata tunda fari da ba,azo wannan matakin ba yanzu.

Gaskiya ina da masifar son Aure, na sami damuwa kwarai da gaske.

Wannan tasa na yanke shawarar guduwa, wannan jihar, yau watana Tara a wannan jihar."

Lokacin da ta gama bani labarin fuskar ta cike da hawaye, na ce mata yanzu idan kika samu mijin Aure zakiyi auren, tace mun Wallahi zata yi amman da zan aure ta Wallahi ni za ta aura, ban san san da nace mata zan aure ki ba.

Washe gari muka sake Hotel saboda wasu dalilai, Hotel din da muka koma nace musu matata ce saboda gidan yana da tsari.
Kwanan mu biyu muka shirya batun Aure, nace zanje Inga mahaifanta, akwai wani Abokina a jiharsu, Wanda matarsa ta rasu, na kirawo shi na zayyana Masa komai, mutum ne mai fahimta da saukin kai tare da tausayawa Alumma,
Washe gari muka rankaya sai jiharsu amman sai da mukaje gidan su wannan abokin nawa acan ma muka kwana saboda dare.

Na Gaya Masa cewar nayi Alkawarin zan aure ta amman zancen gaskiya bani da halin auren Mata biyu, saboda baifi wata uku bikina ba a wannan lokacin.

Muka hada wani plan ni da shi.
Da safe muka gaisa na gabatar dashi agurin ta, nace mata duk duniya bani da amini sama dashi.

Misalin karfe Tara mukaje gidan su, Mahaifiyarta ta cika da murna, akayi maganar girma tare da cewar zan aureta.

Ban bar garinba Sai na bata karamar waya, sannan na samu sabon layi na bata, wannan abokin nawa yayi musu Alheri Mai yawan gaske.

Muka rabu cikin yanayi Mai cike da ban tausayi, lokaci zuwa, lokaci wannan abokin nawa dake jihar su yana zuwa wurin ta su gaisa, harma s**a shaqu s**a zamto k**ar Aminan juna.

Anyi sa'a ta mika dukkan lamuranta ga Allah, kullum bata da aiki sai ibada da kuma neman gafarar ubangiji.

Lokaci zuwa lokaci duk da ina da karamin karfi na kan tura musu da abinda ubangiji ya h**e min duk saboda in kwantar mata da hankali saboda munyi Alkawarin Aure,
duk abinda zan bata wannan abokin nawa shine yake kai mata.

Kusan kullum muna shafe awanni biyu ko uku muna waya domin wata rana har karfe biyun dare muna waya Ina qara kwantar Mata da hankalin ta akan ina nan Ina shirya mana bikin mu.

A gefe daya kuma Wallahi bazan iya aurenta ba, saboda biki na bai fi watanni uku ba.

Bayan sati biyu naje jiharsu mukayi wa iyayenta Goma ta Arziki, tare da Alkawarin zan turo da magabata na bayan sati biyu.

Kafin in tafi muka yi magana ta fuskarta juna da wannan aboki nawa, inda ya nuna min Wallahi yana son ta zai aure ta kuma zai rike ta cikin mutuntaka da Amana.

Muka shirya wani plan cewar bayan sati daya zai ce mata ALLAH yayi mini rasuwa.

Haka ko akayi bayan kwanaki aka ce mata bani da lafiya, idan muna waya har kukan tausaya min take yi ni kuma Sai na koma k**ar mara lafiyar Ina cewa ta yafe mun idan nayi mata laifi.

Bayan kwanaki kadan Sai wannan Aboki nawa ya sanar musu da rasuwata.

Ni a jihar Kano nake amman sai nace mata a jihar Kaduna nake.

Tayi kuka k**ar ranta zai futa, tayi kuka iya kuka, domin har kusan shidewa take yi idan tana kuka, idanun ta s**a kumbura ta koma wani yanayi.

Dukkan wanda ya sanni da wani layin Glo,. Mai lambar 080557811** tun da aka ce na rasu na dena amfani da layin saboda ita ma dashi take kira na.

Sannu sannu wannan Aboki nawa yana kwantar mata da hankali tare da yi mata nasihohi,
cikin Ikon Allah, har yace zai aureta zai maye gurbi na.

Haka ko akayi, tazarar Aurena da nasu sati uku ne kawai, aka kaita gidansa ya riketa rikon Aminci da nasara.

Ya kyautatawa rayuwarta, da yake gidan da yake akwai baranda, babba da kuma gareji, sai ta bude makarantar karatun Alkur,Ani Mai girma, inda "yammata da yara suke zuwa, kafin kace menene wannan ubangiji ya albarkaci wannan makaranta.

Zancen nan da nake muku haihuwarta biyu duk tagwaye maza, suna nan cikin kwanciyar hankali da kosasshiyar lafiya.

Har yanzu bata san Ina raye ba, har yanzu bata san plan muka hadaba da mijinta, ina nan zan shammaceta wata rana muje har jihar ni da iyalina da "yayana domin ganawa da junanmu.

DARASIN DA ZAMU DUBA

(1) Mafi yawancin wadanda ke yawon karuwanci da zamu yi bincike da mun nemo musu mafuta.

(2) Shin me yasa mutanen unguwa wasu basa taimakon, makwabtansu, shin da ace an tallafawa wannan budurwa zata shigo karuwanci har wani ya yaudareta yayi Mata ciki?

(3)yanzu da bamu haduba ba shikenan a haka zata rayu cikin kazamin karuwanci?

(4) Shin da bata tuba ba shikenan anyi asarar hafizar Alkur,Ani kenan?

(5) Shin menene yasa Al,ummarmu ke tozarta wanda yayi laifi yace ya tuba? Shin mu bama aikata laifin kenan mu tuba?
(6) shin me yasa mutanen unguwar su s**a tozarta ta, saboda tayi cikin shege, me yasa ba,a zargi wanda ya yaudare ta yayi Mata cikin?

Ya k**ata mu kula da hakkin makwabtaka, mu dinga agazawa Wanda ya Gaza, mu dai na manta Alherin mutum mu bijiro da sharrinsa.

Idan akace ga lalatacce a unguwarmu kada mu tozarta shi mu fara saurarar uzirinsa kafin mu yanke hukunci.

Ubangiji ka ganar damu.

Koda yaushe so nake na taimakawa wanda ya bar hanya madaidaciya na bashi shawara da gudun mawa wajan gyara goban sa.

SHEKARU UKU A GIDAN YARI BISA SHIGO DA BUHU DAYA NA SHINKAFA NAJERIYAHukumar Kwatam Dake Najeriya Tace Duk Wanda Aka K**...
14/09/2019

SHEKARU UKU A GIDAN YARI BISA SHIGO DA BUHU DAYA NA SHINKAFA NAJERIYA

Hukumar Kwatam Dake Najeriya Tace Duk Wanda Aka K**a Da Fasa Kaurin Shigo Da Shinkafa Najeriya, To Hukuncin Zaman Gidan Kurkuku Ne Akansa Na Tsawon Shekaru Uku.

Babban Kwanturolan Hukumar Kwatam Na Kasa Col. Hameed Ali Ne Ya Bayyana Haka, Yayin Da Yake Bayani a Iyakar Nigeria Da Niger A Karamar Hukumar Maigatari Dake Jihar Jigawa A ranar Alhamis. Yace Shigo Da Kayan Abinci Najeriya Ta Barauniyar Hanya Yana Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Karya Tattalin Arzikin Najeriya.

"Gwamantin Tarayya Tana Kokari Wajen Bunkasa Harkokin Noma, Musamman Noman Shinkafa, Amma Shinkafar Kasar Waje Ana Shigo Da Ita Kasa Ta Haramtacciyar Hanya Yana Barnatar Da Manufofin Gwamanti. Mafi Yawan Wannan Shinkafar Ana Shigo Muku Da Ita A Babura Ta Barauniyar Hanya Ne." ~ Inji Shi

"Babu Wata Matsaya, Duk Wanda Muka K**a Saimun Gurfanar Dashi Gaban Shari'a, Kuma Mafi Karancin Hukuncin Akan Fasakaurin Shigo Da Shinkafa Buhu Guda, Shine Hukuncin Zaman Gidan Kurkuku Na Shekaru Uku." ~ Inji Hamid Ali

Daga Karshe Hamid Ali Ya Roki Mutane Mazauna Kusa Da Bakin Boda Akan Su Bawa Gwamanti Hadin Kai Wajen Sanar Da Wasu Shigowa Da Kayan Abinci Ta Barauniyar Hanya Cikin Kasar Nan, Su Sanar Da Hukumomin Tsaro Wani Bayani Mai Amfani.

WIKE SHAIDANI NE A DALILIN RUSHE MASALLACIN MU"Ni mamba ne a masallacin Trans-Amadi Central Mosque. Wannan masallaci a n...
31/08/2019

WIKE SHAIDANI NE A DALILIN RUSHE MASALLACIN MU

"Ni mamba ne a masallacin Trans-Amadi Central Mosque. Wannan masallaci a nan nake sallah kai harma da Iyali na...Wike kana ikirarin babu wani Masallaci wai karya ake maka. Kaine ka ke karya, haka zaliki kai ka sani karya kakeyi... Mun mallaki kasar wajen ta hanyar bin tsayi da amfani wajen bin dako lokacin mallakar wannan filin masallacin, kuma mun mallaki filin ne domin gina wannan masallaci"

~Alhaji Tajudden Sari Dokubo

Sake Dawowar Masu Garkuwa Kan Hanyar Abuja - Kaduna.Yanzu haka DCP Abba Kyari da tawagar sa sun fara sintiri da jirage m...
29/08/2019

Sake Dawowar Masu Garkuwa Kan Hanyar Abuja - Kaduna.

Yanzu haka DCP Abba Kyari da tawagar sa sun fara sintiri da jirage madu saukar Ungulu akan Hanyar da kuma dajukan dake kewayen hamyar.

HADIZA GABON NA SAKE GINAWA TSOHON DA RUWA YA CINYEWA GIDA A YOBE GIDAN NASH*Tauraruwar fina-finan Hausa, Hadiza Gabon w...
28/08/2019

HADIZA GABON NA SAKE GINAWA TSOHON DA RUWA YA CINYEWA GIDA A YOBE GIDAN NASHI

Tauraruwar fina-finan Hausa, Hadiza Gabon wadda kuma ta shahara wajan bayar da taimako ga marasa galihu ta taimaki tsohonnan da hotunanshi s**a watsu sosai a shafukan sada zumunta bayan da ruwa ya rabashi da muhallinshi.

Taimakon da Hadiza Gabon ta wa Abba Babuga dake Fataskum jihar Yobe shine sake gina mai gidanshi da ruwa ya cinye.

Shafin gidauniyar Hadiza Gabon din na Instagram ya wallafa hotunan yanda tuni aka fara aikin sake ginawa Abba Babuga gidanshi da ruwa ya cinye.

Muna fatan Allah ya saka mata da Alheri

KARYA NE BA MU RUSA MASALLACI A RIBAS BA- GWAMNA WIKEGwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike ya karyata batun da ke cewa, gwamn...
27/08/2019

KARYA NE BA MU RUSA MASALLACI A RIBAS BA- GWAMNA WIKE

Gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike ya karyata batun da ke cewa, gwamnatin jihar ta rusa Masallaci a birnin Fatakwal, inda ya ce; wadansu bata-gari ne kawai s**a kirkiri rahotannin domin haifar da kiyayya da hatsaniya. A lokacin da yake yi wa manema labarai jawabi a wurin da aka ce an rusa Masallacin na Trans Amadi, Gwamnan ya ce, babu wani ginannen Masallaci a wurin, a don haka babu wani gini da aka rusa.

Gwamnan ya kara da cewa; ya samu kira ta wayar tarho daga dimbin fitattun mutane a Nijeriya game da labarin, inda ya ce tabbas wannan labarin kanzon kurege ne wanda kuma aka yi ta yadawa a shafukan sada zumunta.

Gwamnan ya yi karin bayani, inda yake cewa, wasu mutane sun fara dai sanya tubalin haramtaccen gini a wurin duk da cewa ba su samu izinin gudanar da aikin ginin ba a hukumance. Maginan sun maka gwamnatin jihar a kotu amma ba su yi nasara ba k**ar yadda Wike ya shaida wa manema labarai.

Gwamnan ya kalubalanci al’ummar Musulmin jihar Ribas da ta nuna masa wurin da aka rusa Masallacin a fadin jihar.

Ya Allah ka rusashi k**ar yadda ya rusa masallacin Ka.Ya Allah ka rusashi k**ar yadda ya rusa masallacin Ka.
25/08/2019

Ya Allah ka rusashi k**ar yadda ya rusa masallacin Ka.Ya Allah ka rusashi k**ar yadda ya rusa masallacin Ka.

DALILIN DA YA SA NIGERIA TA RUFE KAN IYAKARTA DA KWATONOGwamnatin Tarayya ta sanar da cewa, ta garkame babbar iyakar ta ...
24/08/2019

DALILIN DA YA SA NIGERIA TA RUFE KAN IYAKARTA DA KWATONO

Gwamnatin Tarayya ta sanar da cewa, ta garkame babbar iyakar ta da kasar Benin da ke Seme a jihar Legas. Kodayake ta sanar da hakan ne bagatatan a ranar larabar da ta gabata, inda wannan matakin na gwamnatin, ya janyo ritsawa da dubban mutane da ababen hawa da ke jigila kullum a tsakanin kasashen biyu.

K**ar yadda kafar Premium Times ta ruwaito, an karkame iyakar ce a ranar Talata bayan an k**a wasu manyan motoci shake da kwayar ‘Tramol’ a Legas a cikin wannan watan.

Har ila yau, garkamewar ta cigaba har zuwa safiyar ranar Laraba, inda hakan ya janyo ‘yan kasar nan yin dandazo a bakin iyakar, inda s**a shiga cikin tunanin ko kilan, za a daga masu kafa su samu shigowa cikin Nijeriya.

Bugu da kari, rufe iyakar ya ritsa da wasu yan kasuwar kasar Benin da ke son koma wa gida bayan da s**a shigo cikin kasar nan gudanar da hadar-hadar kasuwancinsu a wasu kasuwannin da ke cikin jihar Legas.

Wasu bayanai sun ce, garkame iyakar ba tare da wata sanarwa ba ya shafa suna kumfar baki a dandalin sada zumunta ranar Laraba.

Kakakin rundunar hukurmar kula da shige da fice ta kasa Mista Sunday James kafar Premium Times ta tura masa sakon karta kwana a kan batuun, sai dai bai bai maido da amsa ba.

Sai dai, hukumar Kwastam sanar a cewa, an garkame iyakar ce sak**akon wasu dalilan tsaro.

A cewar kakakin hulumar ta Kwastam Joseph Attah an garkame iyakar ce saboda ana gudanar da wani aiki na hadin gwuiwa da jami’an tsaron da ke aiki a iyakar Seme.

Joseph Attah ya kara da cewa, za’a kai kwamaki kafin a kammala wannan aiki, kuma mu na iyakar bakin kokarin mu domin ganin aikin bai shafi matafiya ba.

Kakakin ya yi kasa a gwiwa wajen gaza yin karin haske a kan ko an fitar da wata sanarwa kafin fara aikin da ya jawo aka rufe iyakar wanda yin hakan kan iya gurgunta harkokin kasuwanci a tsakanin kasashen Afrika ta yamma.

Address

Kano
700251

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Alkalami posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Alkalami:

Share